Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yin zaune ya fashe da kuka yana fad'in "Mimi ni kika tozarta haka? Ashe duk ladabin da kike mana da girmamamu duk na banza ne wawaye kika d'aukemu? Yau kinsa na ji ni tauyayye ni a cikin hallita, yanda nake d'an tsirit a cikin k'asa haka k'wak'walwata ma da tunani na, ke kad'ai mace amma na kasa kula da tarbiyyarki, uwata me na miki da kika min haka? Talaucinmu ne ya jawo?"

Da sauri Asma'u da jikinta ke rawa ta sunkuya ita ma tana kuka tace "Abba wallahi wallahi wallahi ni dai nasan Mimi bata bin maza, Abba karka yanke hukunci ka tsaya kayi bincik..."

Tsawa ya mata yana fad'in "Binciken uwaki zanyi, ke da ita ai duk kanwar ja ce, tunda kullum tare kuke manne da juna."

Nunawa Asas Asma'u yayi yace "Kaga yarinyar nan da zaku tafi gidanku cewa nayi su tafi tare, amma a k'arshe suka zagaye ita ta dawo ita kuma ta tafi ita kad'ai, to nasan niyyarta da tayi maka tallar kanta ne tunda taga kai aure ne a g..."

Cikin wani matsanancin kuka Mimi tace "Abba...abba ka daina ci min mutumci haka, wallahi ban aikata abinda kake zargina ba, ni ba 'yar iska bace Abba."

Cikin muryar data fara shak'ewa Abba yace "Wacece ba 'yar iskar ba? Ke fita..."

A tausashe cikin son danne abinda ke ranshi kamar an mak'ureshi yace "Dan Allah ko zaki iya barin maganar nan har kuje gida?"

Cike da girmamawa Abba yace "Me zai hana sheikh."

Wani rank'washi ya kai wa Mimi yace "Wuce muje."

Da k'yar ta yunk'ura ta mik'e ga zafin da take d'an jin a k'asanta sakamakon hannun da aka so turbud'a mata, yanzu ma d'an kwalinta a hannu yake dan duk a rikice take a gigice, suna fitar k'ofar gidan kusan shi ne a bayansu sai Mimi dake bayanshi.

Kamar daga sama sukaji muryarshi yace "Daure ki rufe kanki, hakan ba kyau."

Dukansu saida suka kalleshi har da ita data fara k'ok'arin gyara kallabin ta d'ora a kai, yanzu ma dai duk a motar sheikh suka koma gida sai Asas shi kad'ai a motarshi, amma zuciyarshi zallo take sosai yana jin sirikin na sa na neman b'ata mishi rai.


*Idan na ga ruwan comment gobe zaku ga uku ma (peut Γͺtre)*😎


*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:50 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*19*



Duk zaune suke akan tabarma guda sai Asas da sheikh dake kan kujerun roba farare duk da ba sababbi bane, mama kanta na sadde a k'asa dan bata so zama a nan ba saboda kunya da takaici, Mimi daf da k'ofar shiga d'aki take zaune ta had'a kai da gwiwa tana ta shashek'ar kuka, Asma'u na gefenta ta rik'e hannunta gam tana ta murzawa alamar rarrashi, cikin nutsuwa da dattako sheikh ya kalli Abba a nutse yace "Yaran da muka haifa wata rana sukan koya mana darasin rayuwa da bamu tab'a karanta ba, hakazalika wani lokacin sukan sa muji kamar su suka haifemu ba mΓ» muka haifesu ba, idan har Allah ya bawa mutum haihuwa dole wata rana sai ya zama tamkar jami'in binciki na k'asa da k'asa, wata rana kuma saiya koma kamar lauyan dake gaban wanda ake tuhuma, wani zagayen kuma rigar malunta zaka ara ka yafa dan yi musu nasiha a tsanake sannan su fahimci karatu, akwai lokacin da dole uba sai ya zama mai zafi da kausasawa ga yaranshi, kafin wata rana ka zama mai taushi kamar audiga sannan mai sakin jiki dasu dan suma su shiga jikinka. Amma fa duk wannan matakan tsaron zasu biyo bayan addu'ar nema musu shiriya ne, duk yanda zaka kai ga saka ido ko tattare al'amarin yaranka idan Allah bai nufesu da shiriya ba to fa zasu baud'e maka ne, dan haka malam kayi hak'uri ka bΓ’ wa zuciyarka hak'uri, idan har ta b'acin rai zaka bi tabbas zaka iya ganin bayan yarka, idan haka ta faru kuma wace akayi kenan?"

Numfasawa yayi yace "Kayi hak'uri, ga Asas nan yace har yanzu yana son ta da aure, ni nan zan tsaya masa har naga hakan ya tabbata, mu musu fatan alkairi da zaman lafiya mai d'orewa kawai."

Jinjina kai malam yayi ya sauke numfashi yace "Gaskiya ka fad'a sheikh, ni shaidane akan k'wak'waran darasin da uwata ta koyar dani, kuma kamar yanda ka rok'a mata alfarma na yafe mata duniya da lahira, Allah ya tabbatar da alkairi,Allah ya shirya mana zuri'a baki d'aya."

"Ameen ya Allah." Suka amsa malam da Asas, kallon Mimi yayi da niyyar ya mata nasiha mai ratsa zuciya ya ja mata ayoyi da haddisai, sannan ya umarceta ta nemi gafarar iyayenta da ta ubangiji, amma tuna abinda ya faru da abinda likitar nan ta fad'a, alamu ne kenan na eh ta zubar da mutumcinta, sai zuciyarshi ta sake maimaita mishi kalmar nan "Kamaninta bata da suffar cutar da kowa, yanayinta bai nuna hakan ba."

Da sauri ya d'auke kanshi kawai ya mik'e yana fad'in "Saida safenku."

Mik'ewa duk sukayi banda Asma'u da Mimi suka fita sai Mama data shiga d'aki, suna ganin haka Mimi ta d'ora kanta a kafad'ar Asma'u cikin shashek'ar kuka da raunin murya tace "Asma'u kin gani ko? Kinga rashin jin maganarki me ya ja min? Asma'u Abbana ne yake zargina fa."

Dafa kanta tayi tana shafa mata gashinta ita ma tana shashek'ar kukan tace "Kiyi hak'uri kinji Mimi, komai zai wuce insha'Allah."

Ajiyar zuciya duk suka shiga saukewa har Abba ya dawo cikin gidan, a k'ofar shigowarshi ya ci karo da jakarta data jefar a nan, da k'afa yayi cilli da ita hakan yasa yar jakar buguwa a bango ya bayar da k'ara mai d'an nauyi dake nuna bana jakar bane, da sauri ya taka tare d'aukar jakar ya bud'e, ciro wayar yayi yana kallonta yana jujjuyata, sake jifa yayi da wayar ya kalli su Mimi da duk suka sunkuyar da kawunansu, dogon tsaki yaja tare da sake fita y'a bar gidan.

A hankali Asma'u ta zame kan Mimi daga kafad'arta ta mik'e tace "Mimi zan tafi gida nima, saida safe kinji, kiyi hak'uri kuma kar kiyi kuka zai iya haddasa miki ciwon kai."

Jinjina kai tayi ta bita da kallo har ta fita, wata irin k'aunar k'awarta ta take ji a ranta, lallai ita yar halak ce kuma ta cancanci ta so ta, a hankali ta yunk'ura ta mik'e ta shiga d'akin, zaune ta samu mama zugum sai su Yaseen dake rik'e da littafin karatunsu amma da gani kasan suma suna cikin alhini, a hankali ta durk'usa gaban Mama ta d'an rik'o zaninta tana fad'in "Mama, dan Allah kar kiyi kuka a kai na ba kyau mama, kina so Allah yayi hushi dani ne? Mama kin gani wallahi ban tab'a issss..."

Kasheta tayi da mari tare da fizge k'afarta, hak'ik'a duk da basu da tsayi mutanen amma Allah ya basu wata baiwa, wannan baiwar kam ita ce ta k'arfi, k'ashi d'aya garesu da idan suka rik'eka zaka sha mamaki, hakan yasa Mimi k'arasa zaucewa taji wani zuuuuuu! A cikin kanta, da k'yar ta dafe kuncinta tana jin muryar Mama a cikin matsanancin kuka tana fad'in "Mimi a dalilinki fa aka mana wannan terere! Yanzu ke ko kunya baki ji ba domin Allah, yarinya kamar ki Mimi, ina miki kallon k'aramar yarinya ashe ke ma babbar macece ke tunda har kin iya d'aukar namiji, Mimi har ke ce wai za'a baki kud'i da abu dan ayi anfani dake?"

Wani kuka ta kuma fashewa dashi tana zama kan kujerar tana fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Allahuma ajirni fi musibati, waklufli khairan minha."

A hankali Mimi ta muskuta ma su Yaseen da zasu fita daga d'aki saboda ganin har yanzu rigimar bata k'are ba, mik'ewa Mama ma tayi tare da yin k'wafa ta bar mata d'akin, hakan yasa Mimi fashewa da kuka marar sauti kamar zata shak'e kanta ta mutu.

A ranar dai kam bata sake jin motsin Abba bΓ’ dan a masallacin unguwar ya kwana, Mama kuma ko shinfid'a bata fitar waje ba a kan gadonta ta haye saidai ita ma ba bacci tayi ba kamar Mimi dake k'asa kwance.



*Sheikh*


Cikin nutsuwa ya sake gyara zamanshi yana kallon Hajiar da alama kalamanshi sun fara ratsata ya ci gaba da fad'in "Hajiarmu, ai sun gama kyau da daraja tunda Allah ya hallicesu a 'yan adam, domin kuwa fad'ar Allah ne cewa *lallai an hallici mutum cikin mafi kyawun hallita*, ita kuma wannan hallitar Hajia ubangijin daya hallici ta wa hallitar shi yayi ta ki, haka kuma shi ne dai yayi tasu hallitar, hakan ba dan baya son su bane ko kuma sun mishi wani laifi, hakan ganin damarshi, haka ya so kuma babu wanda ya isa ya hana, dan ya fad'a mana a littafi mai tsarki a suratul buruj aya ta goma sha shiga cewa *yana yin abinda ya so ne*, Hajia karmu k'yamacesu dan hallutarsu, mu k'yamace dan munanan d'abi'unsu ko halayensu, kuma mun tabbatar babu su Hajia, hallitarsu hallita ce ta Allah wanda idan ya so yanzun nan zai iya mayar dani irinsu, ko kuma cikin dake jikin Hafsat ta haifo mai kama dasu, duk yin ubangiji ne wannan, Hajiarmu, *shin da wace ni'imace kuke k'aryatawa*? Ni dai ba'a da ja akan cewa Allah ba zai iya salwantar da hallitata ba, ban sani ba ko ke Hajiarmu?"

Da sauri ta girgiza kai tace "A'a sheikh ni a wa? Ni ma bana da ja, dama tun farko raina ya b'aci ne saboda babu wanda ya sanar dani kalar jinsinsu, sai kuma yarinyar da naga zubinta yafi k'arfin yanayin iyayenta a yanda aka fad'a min, bugu da k'ari Salamatu ta fad'a min ta gansu suna fad'a har ana kiranta da karuwa."

Girgiza kai yayi yana fad'in "Subhanallah, astagfurillah! Wannan shaci-fad'i ne na mutane, dama ai babu inda za'a fara maganar aure ba'a samu masu kushewa ba, Hajiarmu Asas yana son yarinyar nan tunda har kika ga ya sameni gida da sassafe haka ya ce na sameki, ki musu fatan alkairi a matsayinki na uwa hakan nada matuk'ar tasiri akan su fiye da yankan wuk'a."

Jinjina kai tayi cike da gamsuwa tace "Shikenan na amince, Allah ya tabbatar da alkairi."

Murmushi yayi yace "Ameen Hajia, nagode da wannan alfarmar da karamci, Allah k'ara girma da lafiya."

"Ameen." Ta fad'a cike da son suruki kuma d'an d'an uwan mijin nata, mik'ewa yayi yana mata sallama ya fita a falon inda ya samu Asas a bakin motarshi da alama shi yake jira.

Yana zuwa cike da zumud'i yace "Ya ake ciki sheikh? Dan Allah ka ce min ta amince?"

D'an zuba masa ido yayi da fari sai kuma ya jinjina kai ya lumshe ido yace "Ta amince, ka je ka ci gaba da shirye shirye."

Rumgumeshi yayi yana fad'in "Alhamdulillah, gaskiya na ji dad'i."

Murmushin yak'e kawai ya masa amma har zuciyarshi wani suka yake ji kamar ana soka mishi allura, ga wani irin mataccen yanayi daya taru ya baibayeshi saboda abinda ya zo mishi wanda bai tab'a tsammani ba, da kuma rashin baccin da bai samu ba a daren jiya ko na minti d'aya, saida ya raba jikinshi da nashi kafin ya d'an bubbuga bayanshi yace "Ni zan wuce, sai munyi waya."

Da kallo Asas ya bishi har ya rab'ashi zai shiga mota Asas yace "Sheikh."

Tsayawa yayi tare da juyowa ya kalleshi, kafeshi yayi da ido saboda yana son fahimtar yanayin da zai shiga idan ya ambaci sunanta sannan yace "Me ye tsakaninka da Mimi?"

Sake zaro idonshi yayi yana k'urawa Asas da mamakin tambayar, a hankali ya had'e fuskarshi yana binshi da kallon tuhumen tambayarshi, lura da haka yasa Asas fad'in "A'a cheikh! Ba wai ina zarginka bane da wani abu, kawai dai na fahimci kamar akwai sanayya a tsakaninku, shiyasa na tambaya."

D'an d'auke idonshi yayi daga kan Asas ya bud'e murfin motar yace "Ba komai tsakaninmu, karka k'ara min tambayar nan."

Wani murmushi Asas yayi ya kallonshi har ya shiga motar, zai ja murfin ya rik'e yayi saurin rik'eshi yace "To ya maganar Ryam d'inka?"

Ba tare daya kalleshi ba yace "Tana lafiya, zamuyi magana a gaba."

Yanda ya amsa mishi yasa Asas bai da wani zab'i daya wuce yar rufe mishi murfin dreba ya ja shi suka bar gidan, saida ya ga b'acewarsu kafin ya nufi b'angarenshi dan shiryawa, yana so idan ya fara zuwa asibiti daga nan saiya wuce ya ga yanda Mimi ta kwana.



*Mim-Ma'u*


Ita maganar duniya bata b'uya ko da k'ark'ashin k'asa aka yi ta, tashin hankalin daya faru a gidansu Mimi tsaf a kunnuwan mutan gidan su Asma'u, dan dama katangarsu d'aya ne, wannan ya jawo cece-kuce har abun ya so juyewa kan maman Asma'u, dan ita kanta Asma'u saida kishiyoyin uwar suka fara yada musu magana suna cewa abokin b'arawo ai b'arawo ne, hakan ya jawo fad'a sosai a gidan suma jiya, dalilin haka kuma mahaifin Asma'u ya fad'a da babbar murya cewa ya soke k'awance tsakanin Asma'u da Mimi har abada.

Ita kanta Mimi yau data tashi sai ta samu kanta kamar bak'uwa a gidan, suna fara had'a ido da Mama kamar yanda ta saba ta duk'a har k'asa tace "Mama ina kwana."

D'auke kai tayi kamar bata ji ba ta wuce aikin gabanta, mik'ewa tayi jiki a sanyaye ta d'ora hannu akan mad'aurin gidan sangensu Yaseen zata kwance, murya a dak'ile Mama tace "Barshi zan d'auke da kaina."

Kallonta tayi zuciyarta na harbawa tace "Amma Mama..."

Kujera ta data ta d'auka ta aza ta kuma tak'ark'are ta taka kujerar ta shiga kiciniyar kwance sangen, kasa katab'us tayi tana kallo har ta kwance duka, mik'awa Yaseen tayi tace "Kai d'aki."

Karb'a yayi ya wuce Mama kuma ta fara tattare shinfad'ar, muk'ut tayi ta had'e kukanta tare da k'arasawa gaban murhun da mama ta fara k'ok'arin hura wuta, shi ma dai cikin fad'a tace "Bana so, ban sakaki ba Mimi, idan baki da abinda zakiyi ki nemi waje ki zauna, dan makaranta ma kin gama zuwanta."

Da tsananin mamaki ta kalli Mama hawayen da take rik'ewa suka gangaro, cikin muryar kuka tace "Mama ku yafe min, nasan nayi laifi amma dan Allah karku hanani samun albarkarku."

Wani tsaki Mama taja tare da k'uk'utawa ta d'auki bargon zata shiga dashi d'aki, har ga Allah bargon yafi k'arfinta amma tsabar hushi haka ta wuce dan kai shi d'aki, a daidai k'ofar shiga tsautsayi yasa mama gurd'ewa ta fad'i ita da bargon, da gudu Mimi ta tunkareta haka ma su Yaseen da suka tsaya bakin k'ofar, kamata tayi ta mik'e cikin jin haushi tace "Sakeni, karki taimaka min."

Cikin matsanancin kuka Mimi tace "Mama me yasa ba zaki bari na taimaka miki ba? Wani ma bana jurar ya cutar daku bare kuma ku naga kuna k'ok'arin haka."

Duk'awa tayi zata d'auki bargon Mama ta fizge da k'arfi ta k'arasa dashi ciki ta aje ta fito, fitowa tayi ta samu Amir na nad'e tabarmar, Mama kuma na hura wuta zata d'ora d'umame, tsaye take saita rasa me zatayi ma sai hawaye kawai.

Bud'e gidan da suka ji yasa Mimi saurin juyawa, tana ganin Abba sukuku dashi idonshi jajir tayi saurin durk'usawa tana fad'in "Abba ina kwana? Abba ina ka tafi mun..."

Nunata yayi da yatsa hakan yasa ta yin shiru, ta gabanta ya bi zai shiga d'akin mama ta kalleshi tace "Ina kwana?"

A dak'ile ya amsa da "Lafiya lau." Su Yaseen ma gaisheshi sukayi ya amsa, nan ya barta tsugune saida ya shige sai kawai ta ja k'ugu ta jinjina a bango ta rakub'e tana hawaye, haka Abba ya fito zai shiga wanka mama ta d'auki bokiti ta zuba mishi ruwa, a yanda suka saba Mimi ke d'aukar bokitin, amma yau basu barta ba Abba ne ya lailayeshi ya kai ban d'akin, tana zaune har mama ta zubawa su Yaseen tuwon suka fara ci Abba kuma ya fito.

Gaba d'aya ta rasa ya zatayi ina zata saka kanta ta ji dad'i, a halin yanzu kam kunyar fita waje take kuma tana kunyar had'a ido da Asas, saidai gashi iyayenta ma na neman zama mata dodo su saka ta fara fatan mutuwa. Mik'ewar su Amir suka wanke hayyane suka d'auki jakunkunan makarantarsu yasa Mimi cikin shashek'ar kuka tace "Amir, lek'a gidansu Asma'u ka kira min ita kafin ta tafi makaranta."

Juyawa yayi zaai fita Mama tace "Kai." Juyowa yayi yace "Na'am."

A d'aure tace "Wuce ku tafi inda zaku je."

"To." Ya fad'a yana bin bayan Yaseen suka fita, tusa kanta tayi tsakanin gwiwoyinta ta sake fashewa da kuka, fitowa Abba yayi yana saka takalminshi ya kalleta yace "Kuka ko? Yanzu kika fara ai Mimi, ai duk wanda yasa iyayenshi kuka shi ma sai yayi marar iyaka."

D'agowa tayi cikin matsancin shid'ewa tace "Abba dan Allah dan girman Allah karku min baki, Abba ban aikata abinda kuke zargina da aikatawa ba, wallahi ban tab'a ko da d'aura niyyar fara bin wannan hanyar ba."

Tab'e baki yayi yace "Maganar banza, shi wanda ya baki wayar kenan d'an mahaukaciya da zai baki ita ba tare da shi ma ya moreki ba."

Rintse ido tayi tace "Abba ka tambayeshi kaji idan kana so, wallahi ko hannuna bai tab'a rik'ewa ba."

Zaune yayi akan kujerar katako ba tare da yace komai ba, ga abinci mama ta aje mishi amma saiya tsura mishi ido yana kallo, ganin kamar baya hayyacinshi yasa mama fad'in "Malam."

D'agowa yayi ya kalleta hakan yasa tace "Lafiya, ka ci abinci mana karka bari hawan jini ya kamaka a banza."

Girgiza kai yayi yace "Wallahi Allah ba dan girman sheikh da nake gani ba, da na mayarwa da yaron nan kayanshi ita kuma na bayar da sadakarta a masallaci."

Yanda Mimi ta k'ura mishi ido tana kallo yasa yace "E! To yaushe zamu d'aukeki gwalagwaje mu kai a wannan babban gida, bayan kasantuwar fak'irai kuma wadanni mun zama iyayen karuwar gida..."

Sake had'a kanta tayi da gwiwa ta fashe da kuka tace "Abba ka daina dan Allah, Abba ka daina babu kyau wallahi, Abba ni ba karuwa bace."

Sallamar Gambo tasa su dakatawa suka amsa, wuri mama ta bata ta zauna suka shiga gaisuwa cike da alhini, kallon Mimi tayi da ko d'agowa ba tayi ba tace "Abban Mimi ba dai har yanzu maganar nan bata wuce ba?"

Kallonta yayi yace "Wucewa? Haba dai yaushe?"

Girgiza kai tayi ta gyara zama tace "Abban Mimi, a gaskiya abinda kayi jiya baka kyauta ba ko kad'an, tabbas laifin Mimi ya isa ya hanaku nutsuwar zuci, amma kuma ai komai yana son sirri, yanda ka tozarta kimar yarinya a idon k'awarta da babban malami da kuma mijin da zata aura abin sam baiyi dad'i ba, ka fa sani duk lalacewar da Mimi zatayi wallahi ba zaka iya cireta a 'ya'yan daka haifa ba. Gashi yanzu kuna ta zargin yarinyarku a banza yarinyar da ko yatsa bai iya wucewa ta gabanta ba, kun d'auki alhakinta sosai gaskiya, dan zaku iya yin komai a tsanake."

Kallon Mimi tayi tace "Kamar yanda na fad'a miki jiya Mimi ki ci gaba da rik'e mutumcin kanki, wannan d'in shi ne darajarki a wannan k'arni, iyayenka ma suna wofantar da kai idan ka zubar dashi a waje."

Kallon Abba tayi tace "Idan baku yarda ba ku kaita wata asbitin, amma ka sani duk tozarcin da zaka jawo mata kanka ka jawo ma, dan kafin a nunata sai an nunaka da yatsa tunda kai ne namiji mai fita."

Mik'ewa tayi tare da fad'in "Sai anjimanku, ina sauri dama zan wuce asibiti nace bari na tsaya dan cika alk'awarina."

Babu wanda yace mata k'ala harta fita a gidan, jiniyar kukan Mimi kawai suke ji amma babu mai sauke ko da numfashi da k'arfi. Da k'yar Abba ya sauke numfashi ya kalli Mama yace "...




*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:50 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*20*




Da k'yar Abba ya sauke numfashi ya kalli mama yace "Kina ganin gaskiya ta fad'a?"

Zuru ta masa da manyan idonta tana kallonshi ba tace komai ba, kallon Mimi yayi tare da fad'in "Tashi shiga ciki."

Mik'ewa tayi tana kuka kamar ranta zai fita ta shiga d'aki, kallon Mama ya sakeyi yace "Ni fa sai naga kamar gaskiya ta fad'a."

Saida mama ta d'aure fusja tace "Ko da gaskiya ne bai kamata mu sake sakar mata fuska ba, ai ta yaudaremu ta munafurcemu, shi kuma wannan laifin fa?"

Jinjina kai yayi yace "Hakane, a gaskiya ban tab'a kawo faruwar haka a raina ba, uwata? Uwata ita ce ta aikata wannan babban kuskure."

Ajiyar zuciya kawai mama ta sauke ba tace komai ba, abincin ya ci gaba da ci yana idawa ya wanke hannu ya fita a gidan. Yana fita kuma malam ya sallamo gidan, jiki na rawa mama ta shiga amsawa tana k'ok'arin d'auko mishi kujera, ta tabbata abinda ya faru ne ya kawoshi gidan, dan ko haihuwa tayi malam ba gidan yake zuwa ba, ai kuwa ciki ya shigo fuskarshi a had'e tsabar b'acin rai, dan har gida Gambo ta biya yanzu ta sanar dashi abinda ya faru jiya, ita tausayin Mimi da ganin yanda ta sameta a gidan yasa ta zuwa ta fad'a mishi.

Kanta k'asa ta durk'usa tana fad'in "Malam ina kwana."

Cikin fad'a yace "Kwanan lafiya? Ina Mimi?"

D'aki ta kalla tace "Tana ciki."

Abinda bai tab'a yi ba a rayuwarshi, sai gashi yayi yau dan kuwa wucewa kawai yayi d'akin yana cire takalmi ya sake yin sallama, da mamaki mama ta bishi da kallo dan ita dai tasan baya haka. Mimi na jin sallamarshi ta sauko daga kan gado ta sake fashewa da kuka, a hankali ta d'ora kanta a k'irjinshi tana sake sako wani kukan, cike da tausayinta ya dafa kanta yace "Amaryata yi shiru kinji, ki rabu da mutanen gidan nan, yau ba zaki kwana a gidansu ba sai nawa, dan na basu amanarki har na gama k'era miki gidanki, shi ne za'a ci min amana haka."

K'wafa yayi a hankali Mimi ta fara jin sanyi a zuciyarta ta ji tana neman yin murmushi, d'aga kanta tayi saidai bata kalli fuskarshi ba saboda kunya tace "Angona ban aikata ba, ban aikata abinda suke zargina ba, kawai dai ina karb'an kud'i ne idan aka bani amma ban tab'a rok'a ba da kaina, ko waya ma dana rik'e bani nace a siya min ba, kawai anga rashin dacewar ace bana da waya ne yasa aka bani, ni kuma na sa hannu na karb'a, amma wallahi kakana ban tab'a zubar da mutumcina ba kafin a bani wani abu."

Kama hannunta yayi suka zauna kan kujerun robar yana kallonta yace "Na sani Mimi, ni ban tab'a ji a raina ba damaa zaki iya aikata wannan mummunan aiki ba, laifinki kawai karb'an abun hannun kowane gara da wawa, ta hakane wata rana wani zai zo miki da buk'atarshi, dan wani in ya baki dan Allah wani kuma wani abu ya hango a tare dake da yake son mora, dan haka saiya fara siye zuciyarki da kyaututtuka marasa anfani."

Numfashi ya sauke yace "Naji dad'i da yaron nan yace bai fasa aurenki ba, hakan ya tabbatar min shi namiji ne kuma d'an halak."

Cikin share hawaye tace "Kakana kunyar Asas nake ji,

Please Login or Register in order to submit comment