Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta samu mama ta shiga cire kayanta, Mama kam kallonta take har ta cire rigar ta saka riga da wando na bacci, tana idawa su Yaseen suka shigo da sallama da murna, duk gaban mama suka zube suna nuna mata ledar hannunsu, da sauri Mimi ta zauna gabanta ita ma ta jawo ledar ta shiga duba kayan, kayan k'walam ne sai turaruka da kuma kud'in daya zuba a ledar, d'aukar kud'in tayi ta ware jaka bibbiyu har guda goma ta ninkesu tace "Wannan na Abba ne."

Ragowar mama ta mik'awa tace "Mama ga na ki."

Kallonta su Yaseen sukayi suka ce "MΓ» fa aka ba, shi ne komai ba zaki bamu ba."

Harara ta dalla musu ta nuna Amir da yatsa tace "Daina kumburo min bakin nan kafin ka ji jini a ciki."

Kud'in data d'ora kan cinyar mama ta koma ta d'auka ta zagi jaka bibbiyu ta mik'a musu tace "Ku yi abinda zakuyi."

Farin ciki ne ya lullub'esu wanda ko dala biyar suka samu a hannu murna suke. Mama dai bata tanka musu ba sai al'ajabin lamarin Mimi, ta d'auka zata d'auki wani kaso a cikin kud'in ita ma, amma ba wannan ne gabanta ba mahaifinta ne yafi damunta, dama kuma ko bata cire mishi ba dole ita zata damk'a mishi, kawai ta bar ta tayi yanda take so ne, dan tsabar kawaici ko d'an abun tab'awa wata rana Allah ya hore Abba ya kawo indai Mimi na gidan ita ke rabawa.



*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:50 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*15*



"Zamu fita daga nan muje gidan Iya Delu, ke zaki zauna a nan ni kuma saina wuce."

Girgiza kai tayi tace "Mimi kina ganin ba matsala? Ya zakiyi idan Abba ya ganeki? Gaskiya ni dai ina jin tsoro ba za'a yi haka dani ba."

Cike da tabbaci da tsaurin ido tace "Babu abinda zai faru Asma'u, kwantar da hankalinki kawai."

Da alamar jimami sosai a fuskarta tace "Zamu ci amanarsu kenan? Yaudarar Abba zamuyi fa Mimi."

Girgiza kai tayi tace "Ba yaudara bace, Asma'u ki fahimceni mana, kinga yanzu idan..."

D'aga mata hannu tayi tace "Matsalata dake taurin kai, indai kikayi niyyar abu babu mai hanaki."

Mik'ewa tayi ta fara k'ok'arin d'aura zanenta bata sake tankata ba, ita ma mik'ewa tayi ta d'auki hijabinta a hannu ta fito dan tasan sunyi fad'a kenan ko zasu shirya sai sun had'e a islamiyyar yamma, takalminta ta saka a k'ofar d'akin ta wuce tana k'ok'arin saka hijab d'in, da kallo yayan Asma'u ya bi k'ugunta yana murmushi, lura da hakan yasa kishiyar maman Asma'u (mahaifiyarshi) cewa "Kai!"

Wannan tsawar data daka mishi tasa har Mimi juyowa ta kalleta, kallonta shi ma yayi yana zazzare ido, cikin jin haushi tace "Dan ubanka me kake kallo baki sake?"

Yatsina baki Mimi tayi ta juya ta saka hijab d'inta ta wuce ta barsu tana jin yana fad'in "To wai mama bani da ikon kallon abinda na ga dama ni da ido na?"

Ita kuma cikin fad'a take fad'in "Dan ubanka duk zalamarka waccen tafi k'arfinka, na d'aya dai kaga taxi ce ita da kowa ma shigarta yake, na biyu ba kowa take kulawa ba sai wanda taga akwai mamora a jikinsa."

Mimi kam ko fa a kwalar rigarta sai ma fita da tayi daga gidan, ita indai ita zaka tab'a kai tsaye to bata da matsala da kai, ka dai saka iyayenta ne ko da ta hanyar zaginta ne bata lamunta ko kad'an, dan taana da tabbacin ko mijin aurenta zata iya tsinke fuskarshi da mari idan ya nemi fad'a ma iyayenta magana.


*Sheikh*


Cikin nutsuwa ya sake tank'washe k'afafunshi yana had'e tafukan hannayenshi ya ci gaba da fad'in "A duk inda zaku shiga a fad'in duniya, a duk halin da zaku tsinci kanku a ciki yarana kada ku yarda kuyi wasa da addininku, addininku shi ne gatanku, addinin islama shi ne alk'iblarku, addinin nan shi ne madogararku, dan haka duk inda zaku samu kan ku kuyi alfahari da addininku, kada bambamcin yare ko k'abila yasa ku ji kunyar nuna kanku a matsayin musulmi, kada wani rud'i na duniya ko kuma muzgunawa tasa ku wofantar da addinin daya baku madafa a sanda baku da tudun dafawa, addinin musulunci rahama ne a garemu kuma alfarma."

A hankali ya kalli Aisha yace "Aysha, ke ce babba a gidan nan, ina sake gargad'inki da ki kula sosai da yan uwanki ki tayasu rik'e sallarsu ta farilla, kada ki barsu suyi wasa da ita a kowane hali, nasan macece ke kuma a halin yanzu kowane lokaci zaki iya shiga d'akin mijinki, amma hakan ba zai hanani sake jadadda miki rik'o da zumuncinku ba, a duk inda aure ko ratuwarki ta gaba zasu kaiki, zaki iya tsayawa tsayin daka wajen ganin kun rik'e zumuncin nan, ko bayan babu ranmu zaku zama gatan junanku."

Cikin tsareta da ido yace "Kin fahimta?" Jinjina kai tayi alamar eh cikin sanyayyar murya tace "Eh Abie, insha'Allah zamu rik'e zumuncinmu, wannan alk'awari na ne a gareku iyayena."

Jinjina kai yayi yace "Masha'Allah, sai kuma kai *Heezam*." Ya fad'a yana kallon k'annan Aisha mai bi mata, a nutse yace "Bana da d'ar a kan ka dan na saka maka ido sosai ina lura da duk wani tako da motsinka, a tak'aice kuma a yanzu dai banga wani abu daya nuna shagala akan sallahrka ba, haka kuma ban ga alamar wasa a cikin karatunka ba, kamar yanda banga wani b'ataccen aboki da zai iya b'ata tarbiyarka ba, saidai hakan ba shi zai sa na zuba maka ido ina kallonka haka kawai ba, Heezam."

Ya kira sunanshi cikin dakakkiyar murya, amsawa yayi a ladabce yace "Na'am Abie."

D'orawa yayi da "Daga yanzu zamu fara fita tare da kai zaman majlisi, sannan ina so kai ma ka fara wani k'ok'ari akan matasa yan uwanka dan bayar da ta ka gudummuwar."

Da ladabi ya jinjina kai yace "Insha'Allah Abie."

Kallon *Aswane* yayi ya saki murmushi yace "Manya masu gari, macijin k'aik'ayi kenan sari ka nok'e, wato yarona Aswane duk gidan nan babu wanda ya kai ka karatu, haka kuma babu wanda ya kai ka iya shegantaka."

Duk dariya aka d'auka a wajen har Hafsat dake shafar cikinta saboda juyawar da yaron cikin ke yi mata, cikin muryar laushi tace "Akwai son gayu fa kamar ya ga ubanshi Asas, amma kuma yafi kowa tsanar irin shigar da matasa keyi ta k'ananan kaya."

Dariya sheikh yayi sosai yana fad'in "Wannan ikon Allah yana bani mamaki, wai kai ka saka riga da wando na zamani ka d'aure k'ugu da ceinture (belt), amma idan ka fita waje ka ga wani matashi zai wyce da shiga irin ta kai saika gyara tsayuwa ka tsayar ka dinga yanko mishi hadisai da ayoyi harda karatun d'ab'ia na d'an adam ma kana nuna mishi rashin dacewar haka."

A sanyaye ya kalli Aswa'ne daya d'aure fuska tamau yace "Sheikh Aswane ya kake nufi ne to? Shin kana so ka koyar da hallacin shigarka ne ga matasa a aikace? Ko kuma dai kana son su k'yamaci abinda kai suka ga kana yi ne?"

Saida ya sauke ajiyar zuciya ya shafa tarin sumar dake kan shi a gaban yace "Abie, ai ni ba irin waccen shigar nake yi ba da ake zazzago wando ana takawa, kuma nima ina so na daina saidai Allah ne ya saka min soyayyar kayan a raina, kuma sun fi yi min kyau idan na saka."

Girgiza kai yayi yace "Kash! A gaskiya tunani da idonka sun fad'a maka k'arya yarona, taya kake tunanin suturar yahudawa zata fi yi maka kyawu fiye data ka suturar? Wa ya fad'a maka kawai kana son su ne saboda Allah ne ya saka maka soyayyarsu? Aswane magana ta gaskiya sutura ta hausa ita ce cikakkiya kuma kamilalliyar sutura, na yarda idan ka ce sun fi maka kyawu a jikinka, to amma kamala fa? Ita ma suna fito maka da ita ne?"

Shiru yayi kan shi a k'asa hakan yasa shi girgiza kai ya gyara zama tamkar zaiyi magana da d'an shekara ashirin ba wanda shekarunsa duka goma sha biyu bane yace "Aswane, wannan suturar da kake sakawa ta hayudu ce, manufa ce dasu data sa suka k'irk'iri wannan suturar, kuma sun cimma burinsu tunda har suka yi nasarar ribatar ire-irenku, amma ka sani cikar kamala na cikin tufafin hausa, fito da asalin haiba da kwarjinin mutum sai tufafin bahaushe, da wannan nake kira gareka d'ana ka siyawa kanka mutumci ta hanyar yafa shigar mutumci a jikinka."

Jinjina kai Aswane yayi yace "Insha'Allah Abie, zan kiyaye."

Jinjina kai yayi ya kalli d'an k'aramin yace "Wannan shi ne autana kuma ba autana ba, *Munzeer* yaron kirki ne, ba ruwanka da rigima ko fad'a, karatu kawai ka saka a gaba ko yaron kirki?"

Cike da jin dad'i yaron mai shekara biyar ya jinjina kai alamar eh, dafa kanshi yayi yana jinjina kai da murmishi yace "Allah muku albarka, Allah ya k'arawa karatun albarka, Allah ya k'ara had'a kanku, Allah ya wadataku da lafiya mai anfani."

Gyara zama yayi yace "Ku tashi ku tafi." Mik'ewa sukayi bayan sun amsa a ladabce, duk da kallo suka bisu har suka b'ace ma ganinsu, saida suka shige ciki kafin ya mik'e shi ma, hannun Hafsat ya kama yana fad'in "Muje ki kwanta ki huta, dare yayi fa."

Murmushi tayi tana ci gaba da shafa yaron cikinta daya dunk'ule wuri d'aya kamar baya motsi, suna shiga d'akin ta fahimci yau kenan zai kawo mata ziyara, dan baya zaune sai mace ta sameshi d'akinshi, da kanshi yake zuwa inda kike sannan ya lallab'aki ya amshi hakk'inshi, dan haka saita daure sosai ta saki jikinta bata yarda ta nuna bata jin dad'i ba, saida ya tayata yin wanka kafin suka k'arasa gadon girma, duk da tana jin d'an cikinta ya dunk'ule mata a mara haka ta jure bata nuna bata ra'ayi ba, har tambayarta yake ya isa haka saita sunkuyar da kai tace "Sai ka gamsu."

Shi kuma a duniyar Allah yana matuk'ar son mace mai raki, rakin ma irin na tsiyar nan, wallahi a duniya yana son y'a ga mace dake mayar da masassara ciwon kai, wacce zata dinga billi tana kuka akan abinda bai kai bai kawo ba, yana so wata rana Hafsat ta gwada yin haka ko sau d'aya ne, da zai yi zaune ya aje hularsa da babban riga da hirami ya dinga mata hidima yana rarrashinta. Da k'yar ya samu gamsuwa ya taimaka mata ta tsarkake kanta ta dawo ta gyara shinfid'ar ta kwanta a matuk'ar wahale.


*Washe gari*


Tana tsaka da tsantsara kwalliyarta a fuska ta ji wayarta dake cikin k'aramar jakar da zata fita da ita tana vibrations, saida ta d'an d'aga labulen d'akin ta tabbatar suna waje suna harkar gabansu kafin ta ciro wayar, zaro ido tayi ganin lambar sheikh ce wacce tsabar mahimmancin data bata har ta iya hardaceta a kan ta, ita kan ta bata san ta bashi wannan mahimmancin ba. Sam bata son d'aukar wayar a lokacin, amma abun mamaki lambarshi kanta kwarjini take mata ta yanda ba zata iya share kiran ba, hannunta da zuciyarta na kakkarwa ta d'aga kiran tana jan sallama, a sanyaye sosai ya amsa da "Wa'alaiki salam."

Shiru ne ya d'an ratsa na dak'ik'u kafin yace "Ki gafarce ni Ryam na sake kiranki, zuciyata azalzalata take a game da lamarinki, dan Allah ki fad'a min idan Abbanki ya dawo na zo na ganshi."

Wani sanyayyan murmushi ta saki a ranta tana fad'in "Allah mai iko, ni Maryam ba kowa ba kuma ba 'yar kowa ba, yau ni ce har babban malami kamar wannan yake min magiya haka?"

Ajiyar zuciya ta sauke tare da tunanin ai Abba ya karb'i lefenta har da ma kud'in aurenta, dan haka tasan duk girmanshi Abba ba zai yarda yayi magana biyu ba, dan haka ta saki murmushin jin dad'i tare da bud'a bakinta tace "Abba ya dawo jiya, dama na rasa yanda zanyi na kira ne."

Wani sanyayyan murmushi yayi shi ma har tana jin sautinsa yace "Na ji dad'i sosai Ryam, zan zo gidanku yau insha'Allah."

Cikin rashin jin dad'i a zuciyarta ganin yanda zata sakashi zama wani wawa haka tace "Shikenan, Allah ya amince."

Da fara'a yace "Ameen, nagode, sai anjima."

A k'asan mak'oshi tace "Uhum." Tana aje wayar ta kalli agogon screen d'in, da sauri ta aje wayar ta shiga gaggawar k'arasa shirinta, ta mik'e kenan tana gyara zaman rantsetsiyar abayar data saka bak'a wulik wacce ta fito da hasken fatarta ta yana kallabin y'a mata kyau sosai, Asma'u ce ta shigo da sallama mama ta amsa, tana shigowa suka kalli juna suna murmushi, ko gyara kayan data barbaza batayi ba ta d'auki jakarta tace "Muje kinji."

Fitowa sukayi Asma'u na fad'in "Wa zai d'auke waccen kayan kuma?"

Kafin tayi magana mama da taji ta tace "Ta bari jakarta ta d'auke mata mana."

Dukansu dariya sukayi kafin Mimi tace "Mama zamu wuce gidan Iya, kinga idan ya gaishesu ita da malam sai mu wuce."

Jinjina kai tayi tace "Allah ya yarda, ku kula dan Allah kunji."

"Insha'Allah." Ta fad'a tana kama hannun Asma'u suka fita daga gidan.

Kamar dai kullum zaka rantse da Allah wata 'yar hamshak'in mai kud'i ce, hatta takonta d'aukar hankali yake yanda duk da duhu ne ana k'are mata kallo, ga k'amshin da take bari a duk inda ta gifta ta wuce, da haka suka isa gidansu Iya D'Γ©lu, da raha suka shiga zolayar juna ita da kakanin nata data samu malam na cin abinci, kamar yanda tun a kan hanya ta fad'awa Asas dan haka suna zuwa ba jimawa ya iso.

Da kan ta ta fito ta mishi iso zuwa cikin gidan, sosai suka gaisa har malam na fad'in "Ai bansan zaka zo ba da ban yarda ka sameni ba."

Cikin shagwab'a Mimi ta kalleshi tace "Angona."

Dariya yayi tare da shafar kumatunta yana fad'in "To ai bana so ya gane kishina ne a kan ki, zan iya cakumarshi yanzun nan mu hau sama."

Dariya sosai Asas yayi yana sunkuyar da kai cike da kunya, Iya Delu ce tace "Ni kuma farin ciki nayi dana ganeshi, dan a take naji na samu miji nima mai jini a jika."

Kallon Mimi tayi tace "Ba kullum cika baki a kan ni na tsufa bane ke kuma sabon jini? To ni ma na k'wace miki miji."

Dariya sosai ake yi har Asas yace "Gaskiya ne, ni ma yanzu dana ganki na ji bana buk'atar sabuwar jinin, dan kuwa da tsohuwar zuma ake magani."

Da irin rahar nan suka musu sallama suka fita tare da Asma'u, saidai a k'ofar gidan ita suka rabu inda Mimi ta sake jadadda mata "Asma'u ki zauna gidansu Jamila, idan na zo zan kiraki a waya saiki fito waje mu k'arasa gida, kin gane?"

Jinjina kai tayi tace "Na gane, sai kun dawo."

Murmushi ta mata tace "To." A raunane tace "Dan Allah Mimi ki kula da kanki kinji."

Jinjina kai tayi alamar to, gidansu Jamila ta nufa ita kuma ta bud'e motar ta shiga, kallonta yayi yace "Ba tare zamu tafi da ita ba?"

Girgiza kai tayi tace "Dama akwai inda zata je, hanya ce kawai ta had'amu."

Jinjina kai yayi tare da tayar da motar suka d'auki hanya.

A k'alla sun d'auki minti talatin kafin suka isa gidan, a sanda ya shiga gaba yana mata jagora zuwa babba kuma k'ayataccen falon, tsoro, fargaba, al'ajabi da kuma kunya ne suka taru suka baibayeta, da haka suka shiga falon Asas na fad'in "Hajiata, fito ga sarakuwarki na kawo miki, zo kiga yar beautyna."

K'asa ta sake yi da kanta tsabar kunya tana sake rik'e jakarta tamau a hannu, da fara'a da kuma al'ajabin ganin kyakyawar yarinyar mai kama da larabawa ta shiga takowa tana fad'in "A'a masha'Allah, yau kam autana ya cika alk'awari."

Tana zuwa ta ja Mimi a jikinta ta rumgume wacce ke neman sulalewa k'asa, sosai tayi mamakin yanda mahaifiyarshi ta tarbeta, bata zame da ita ko ina ba sai kan teburin cin abinci, zaunar da ita tayi tana k'walla kiran "Salamatu! Salamatu."

"Na'am Hajia." Aka amsa daga ciki ana fitowa, tana zuwa Hajia tace "Kinga bak'uwa na yi, ki kawo mana abinci."

Saida ta kalli Mimi da kanta ke k'asa, d'an k'ara lek'a fuskar tayi da son gano a ina ta san fuskar, tunawa da tayi yasa ta jinjina kai ta kalli Asas, murmushi ta k'ak'aro tace "To Hajia."

Juyawa tayi ta koma tana mamakin shi kuma yallab'ai Asas me ya had'ashi da yarinyar? Ita ce zai aura? Wacce ake kira da karuwa, karuwar ma ta samarin unguwa, bugu da k'ari kuma 'yar wada, dan kuwa duk fad'an nan da akayi na jiya a gabanta, ita ce ma suka zaburo suka rabasu sanda suka kacame da fad'a. Haka ta gama duk abinda ya dace ta kawo ta kuma kula da komai amma bata daina kallon Mimi ba, gashi taga daga Hajiar har Asas d'in sai hira suke jan ta da ita da raha alamar dai ta samu karb'uwa a wurinsu sosai.

Saida ta gama ta koma ciki Hajia ta kalli Mimi tace "Takwarata, ci abinci kinji, nan gidan fa ba bak'onki bane."

Murmushi ta sake yi ta sunkuyar da kanta k'asa, da zolaya Asas yace "Kunyar Hajia wai kike ji? Kinga yanzu fa ke ce autarta ko, ni na bar miki yanzu dan na girma, tunda nan gaba kad'an zaki haifa min yara."

Satar kallonshi tayi da mamaki baki bud'e, sai kuma tayi shiru kawai kan ta k'asa tana jin Hajia na fad'in "Matsalata da kai kenan rashin kunya."

Jawo kujerarta tayi ta koma kusa da Mimi ta d'ebo abincin zata kai bakinta, sinne kai ta sake yi cike da kunya tana murmushi, tallabo hab'arta tayi tace "Maryam, ni ma fa mahaifiyarki ce, kinga bana da 'ya'ya dayawa sai guda biyu, ki saki jikinki dani kinga zaki shigo ahalin nan ba da jimawa ba."

Jinjina kai tayi alamar to, sake kai mata cokalin tayi a baki haka yasa ta karb'a cike da kunya, duk yanda ta so zillewa bata samu dama ba haka ta dinga ciyar da ita da hannunta, tana tsaka da cin abincin ne ta kalli Asas tace "Kaga takwarata sai tayi kama da *Fanna*, ko dai 'yar uwarta ce?"

Girgiza kai yayi yace "Bana jin ma sun tab'a had'uwa."

Kallon Mimi tayi tace "Takwarata, waye mahaifinki? Ina ne gidanku?"

Da sauri Asas ya kallesu yana neman k'warewa, to shi dai bai wani zauna ya fad'a mata wacece Mimi ba, yasan danginshi kuma farin sani zasu iya kawo mishi tangard'a, gata ita kuma bata b'oye komai daya shafi asalinta yasan tsaf zata fad'a mata komai.

Mimi ma satar kallonshi tayi kafin tayi k'asa da kanta tace "...




*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:50 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*16*


"Mama ni ba 'yar kowa bace, mu talakawa ne da muke fafuta akan abinda zamu ci, sannan iyaye na..."

"Mutanen kirki ne." Cewar Asas da sauri yana tsare Hajia da ido, duk kallonshi sukayi da mamaki sai Hajia data d'an basar ta kalli Mimi tace "Ke 'yar talakawa ce?"

Jinjina kai tayi ba tare data kalleta ba, a hankali Hajiaa ta aje cokalin hannunta tare da yab'awa fuskarta yanayin rashin jin dad'i, kallon Asas tayi ta mik'e tace "Ka sameni a d'akina."

Lumshe ido yayi irin na ohh shiit d'in nan tare da kallon Hajiar bai ce komai ba, da kallo suka bita har da Mimi dake al'ajabi da mamaki, kallonta yayi ya mik'e yace "Ina zuwa Maah, karki damu kin ji, ki ci abincin."

Da kallo ta bishi kafin ta kalli farantin gabanta, hak'ik'a tana son cin wannan gara da aka wadata gabanta da ita, saidai zalamarta bata kai wannan matakin ba, da taga fuska ne ma zata iya d'iba ta kai wa 'yan k'annanta su goge hak'ora, amma daga yanda ta ga fuskar matar kam tasan sai ta Allah aurenta da Asas yayi wu.

*Suna* shiga a zafafe ta juyo tana fad'in "Asas dama yarinyar nan 'yar talakawa ce?"

Cikin rashin karsashi yace "Hajia miye dan 'yar talakawa ce? Shikenan mu dake da hali ba zamu iya auren 'ya'yan marasa k'arfi ba dan a tallafawa juna."

A kausashe tace "Kaga Asas ba kasancewarta 'yar talakawa ba yasa nake maka maganar nan ba, babbar matsalar shi ne dama ba daga ahalinmu ta fito ba, dangi zasu ga laifina ne na barka ka auri yarinyar da ba nasabarku d'aya ba sannan yar talakawa, kafi kowa sanin yanda ake son had'aka da 'ya'yan dangi amma ka k'i, larurarka tasa na ce a rabu da kai zaka zab'a da kanka, shi ne yanzu zaka zo min da waccen yarinyar."

Sanyaya murya ya sake yi sosai yace "Hajia ta, dan Allah karki hanani auren Mimi, ina sonta da zuciya d'aya ba zan iya rabuwa da ita ba."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "Yanzu ka je kusa da ita ka zauna, idan ta kammala ka kaita gidan auntynka tunda an fad'a mata zaku je can."

Marairaicewa yayi yace "Hajia ba zaki hanani aurenta ba?"

Yatsina fuska tayi tace "Ka je kawai zanyi tunani."

Sake shagwab'ewa yayi yace "Hajia haka zaki tarbi bak'uwarki?"

D'an murmushi ta k'ak'aro tace "Muje to."

Da fara'a ya biyo bayanta suka fito falon, yanda suka barta haka suka sameta, bata yarda ta had'a ido da ko d'aya daga cikinsu ba, zaune sukayi Asas na fad'in "Maah, mun barki ke kad'ai? Kiyi hak'uri."

Murmushin yak'e tayi haka ma Hajia murmushin yak'en ta shiga yi, jim kad'an ya kalli Mimi da kanta ke k'asa bata cin abincin yace "Kina lafiya ko?"

Jinjina kai tayi ta kalleshi tace "Abba yace kar na jima."

Murmushi yayi ya kalli Hajia yace "Hajiata zamu wuce gidan Aunty Hafsat."

D'an kallon Mimi tayi tace "To Allah ya tsare, ku gaishesu da kyau."

Mik'ewa Mimi tayi hakan yasa shi ma ya mik'e haka ma Hajia, k'wala kiran Salamatu tayi tana zuwa ta sunkuya tace "Hajia gani."

A gadarance tace "Ki d'auko min sak'on nan dana ware dan bak'uwata."

D'an d'aga ido Mimi tayi ta kalli Hajia, a kuskure kuma idonsu suka had'u ita ma tana kallonta tana mamakin yanda tace yar talakawa ce ita amma fatarta wata irin fresh da ita, uwa uba ga abayar jikinta wacce ta shekarar bara ta siyowa Hafsat su dayawa da shegiyar tsada, to a ina ta samesu kenan? Bayan tace talaka ce ita. Tana wannan tunanin Salamatu ta kawo manyan ledojin kalar pink guda biyu, ajewa tayi k'asa tana fad'in "Gasu Hajia."

Cike da wulak'anci tace "Ki bata, zasu mata anfani."

D'agowa ta sakeyi ta kalli idon Hajia tsaf kallo na ki fahimceni naa fahimceki, Hajia kan ta saida ta ji wani shakkun yarinyar saboda yanda ta kalleta babu tsoro a ciki da kuma rashin d'aukar raini, mik'o mata ledojin Salamatu tayi tana fad'in "Gashi k'aramar Hajia."

A yangance ta kalli Salamatu ta yatsina fuska dan hakan d'abi'arta ce kafin tace "Nagode, Abbana ya hanani karb'an kyauta irin wannan."

Da mamaki Hajia ta kalleta, sai kuma ta tab'e baki ta kalli Asas tace "Ka d'aukar mata kayan, watak'ila kunya take ji."

Girgiza kai tayi a hankali tace "Bana so Abbana ya min fad'a sakamakon aikata abinda ya haneni."

A ladabce ta juya zata fita tana fad'in "Nagode da karramawa, sai anjimanku." Da

Please Login or Register in order to submit comment