Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi tace "Ba dani zaku tafi ba, dan har yanzu akwai bak'in da basu tafi ba."

Kallon Mimi tayi data dunk'ule tace "Tashi ki gyara hijabinki sai ku tafi."

Girgiza kai tayi alamar a'a, wani kallo kawai ya shiga bin ta da shi, cikin muryar da babu wasa a ciki yace "Jiranki fa nake, ina da abun yi."

Gabanta ne ya shiga fad'uwa da k'yar ta yunk'ura ta d'ago, a kan shi ta sauke idonta wanda shi ma a kan ta na shi idon suke, da sauri ta sinne kan ta saboda wata irin kunya data kamata, ko a tv bata tab'a ganinshi da kaya irin na yau ba, zallar d'inki ne kawai riga da wando tazarce sai hula a kan shi.

Ganin kallon da yake mata yasa Hajia mik'ewa tace "Bari na sama mata ko madara da zata saka a cikinta."

Fita tayi ba tare da ta ji me zai ce ba, rawar da jikinta ke yi ne ta k'aru sai ta rasa yanda zata yi ta sauka a kan gadon, murya a dak'ile yace "Jiranki nake malama."

Hijabi tasa tana murza ido cikin kukan shagwab'a tace "Ni bana son zuwa asibiti, na warke fa babu abinda yake damuna."

Mik'ewa yayi tsaye yace "Ke." Da sauri ta kalleshi dan indai y'a ce ke dole ka kalleshi, da sauri kuma tayi k'asa da kan ta sanda yake fad'in "Sauko a gadon nan kafin na tsula miki tsumagiya, kinsan haushinki ne dani ko?"

Da sauri cikin rashin k'arfin jiki ta shiga saukowa a kan gadon, saida tayi tsaye k'afafunta na mata rawa sosai ta kalleshi tace "Abdu..." Gumtse bakinta tayi sai kuma tace "Yallab'ai, dan Allah idan munje karka bari su min allura."

Wani firgitacen kallo ya mata daya razanata yace "Har a baki sai na ce a miki ko zaki daina yin k'arya."

Da sauri ta shiga nuna mishi da hannayenta tace "Na daina ai tun ranar, wallah..."

Sake zaro mata ido yayi shi yasa tayi shiru saai kuma tace "Tun waccen ranar na daina, ba zan sake ba Allah ko."

Yatsina fuska yayi yace "Wuce muje."

Silipas d'inta dake gaban gadon ta zura k'fafunta tayi gaba jikinta na rawa gab-gab-gab kamar ba zata iya tafiyar ba, saida ta kusa kaiwa k'ofar fita yace "Miye wannan kuma malama?"

Juyowa tayi sai taga ashe yana tsaye inda yake, dudduba jikinta ta shiga yi ganin bata ga komai ba saita kalleshi da alamar tambaya, cikin murtuke fuska yace "Wannan hijabi ne a jikinki?"

Duk'ar da kanta tayi tana kallon hijabin daya saukar mata har wuce gwiwoyinta, d'agowa tayi da mamaki tace "Hijabi ne mana."

A take cike da gatsali yace "Bai min ba, canza shi."

Galala tayi da baki ta kalleshi, ganin bata da niyyar yin abinda yace yasa shi cewa "Na ce ki canza shi ko?"

Turo baki tayi cikin sangarta tace "Ai duk sauran ma haka suke, kuma ba duka kayana bane aka d'auko."

Tab'e baki yayi yace "To nik'ab fa?"

Baki bud'e ta kalleshi tace "Nik'ab kuma? Ni da ba lafiya gareni ba?"

Cikin wurga mata harara yace "Dan baki lafiya sai aka ce jikinki abun talla ne?"

Gumtse bakinta tayi ta sinne kan ta, sama da k'asa ya harareta yace "Shi waccen sharb'eb'en da kike sakawa sai kina son nuna ta Allah ce ke ko?"

Takowa yayi da sauri yana fad'in "Muje, amma ki sani dole ki canza tsarin shigarki, dan wannan bata min ba."

Kaucewa tayi da sauri ya bud'e k'ofar ya fita sannan ta bi bayanshi, tana fitowa haka tayi ta jan hijabinta tana rufe fuskarta saboda bak'in dake nan wasu na ta haramar komawa inda suka fito, gaishesu tayi a ladabce suka amsa tare da fatan sauk'i a gareta. Tana fitowa daga falon ya shiga hangenta daga zaune da yake a motar, kamar wai ba ita ce yake jira ba take wata tafiya kamar wahainiya, yo shi ko Hajia ma ta tab'a sashi jiranta kamar haka kuwa? D'auke kai yayi daga kallonta yanaa d'an jan guntun tsaki.

Baya ta kama zata bud'e ya juyo ya kalleta, saki tayi ta koma gaba ta bud'e ta shiga, kakkauran hannunshi ta kama wanda agogon hannun ta cikashi dam, d'auke idonta tayi a ranta tace "Hummm!"

Saidai yanda ta fad'i humm! D'in yasa shi kallonta dan ta fito, saida ya juyar da kan motar zasu fita ya kalleta yace "Miye?"

Kallonshi tayi tace "Ba komai."

BΓ’ tare daya kalleta ba yace "Ban son k'arya, ki tabbatar kinsan me zaki dinga fad'a min kinji ko."

K'wafar da yayi yasa ta saurin cewa "To." A ranta kuma tana sake k'iyasta yanda ta wani shiga mota d'aya da mijin aurenta, mijin ma kuma tsoho sa'an babanta, yanzu nan a ganta da k'uruciyarta sai kawai ta ce shi ne mijinta, wasu k'walla ne ta ji sun taho mata tare da saka yatsarta ta share kawai tana kallon titi ba mai ma kowa magana.

Yana paka mota kamar jira take tayi saurin fita ta tunkari asibitin, cikin dak'ilalliyar murya yace "Ke!"

Lumshe ido tayi a ranta tace "Ohhh! Wai wani ke! Miye haka dan Allah."

Juyowa tayi a hankali tana kallonshi a ladabce, da ido ya mata alamar "Tsaya a gefena."

Take fuskarta ta nuna alamar rashin jin dad'i, juyawa tayi ta d'an shiga kallon mutanen dake kai kawo, tana cikin yatsina fuska kamar yasan me take tunani yace "Kunya kike ji a ga kin jera da *tsoho a matsayin mijinki*?"

Kumbura fuska tayi da baki tare da jan hijabinta ta rufe daga bakinta har zuwa hanci, k'wafa yayi tare da wucewa gaba yana fad'in "Bansan rashin kunyarki ta kai haka ba Ryam."

Ita dai biyarshi take yi a baya yana shiga lungu da sak'o na asibiti, ganinshi a asibitin yasa duk ma'aikatan da suka ganshi suke gaisheshi da girmamawa, wani matashin ma'aikaci ya tambaya Dr. Rakiya? Dan haka da kan shi ya musu iso zuwa ofishinta dan tana tsaka da duba mata da suka kama layi, sanda zai shiga ofishin ne ya kula bata bayanshi, juyawa yayi saiya hangeta nesa dashi sai wani rufe fuska take, jinjina kai yayi a zuciyarshi yana fad'in "Ba dai ni kike jin kunyar jerawa dani ba? Zaki gane baki da wayo."

Shigewa yayi ofishin ya zauna yana karb'an gaisuwar Dr. Rakiya, saida suka gama gaisawa kafin Mimi ta shigo da sallama k'asan mak'oshi, Rakiya ce kawai ta amsa tana sakar mata murmushi, sosai take kallon yarinyar wacce jiya labari ya karad'e gari sheikh ya aura ko kuma an aura ma sheikh ita, dan har hotonta ta gani wanda aka had'a ita da Asas amma Allah bai nufa ba. Tsaye tayi tana kallon kujerar da zata zauna wacce ke fuskantar sheikh dake zaune, hannu ta kai zata ja kujerar baya taa zauna sheikh yace "To ke da zaki fad'a mata abinda ke damunki, ya kuma zakija baya *Mari*?"

Kallonshi tayi kamar ta gaura masa mari domin ta fahimci so yake ya cizgata a gaban mutane, kaikaitawa tayi ta d'an tsoma mazaunanta tana kallon likitar, murmushi ta sakar mata tare da d'aukar katin marasa lafiya tace "Madame sunanki?"

Saida ta ja hijabinta sosai kafin tace "Mimi...au! Maryam."

K'ura mata ido yayi kamar mai burin rikitata yana sakin murmushin mugunta, Mimi kam data fahimta ko kallonshi ba tayi ba har likitar tace "Sunan mahaifi?"

A sanyaye tace "Uban kowa."

Da sauri ta d'aga kai ta kalleta haka ma sheikh daya sake kafeta da ido, sai kuma yayi murmushi ya d'an d'ago daga jinginar da yayi tare da kai hannunshi ya lalubo hannun Mimi a cikin hijabi ya rik'o, a razane ta kalleshi tare da k'ok'arin k'wacewa, sai kuma ya jimk'e hannun gam yana mata murmushi, ba tare daya daina wannan murmushin ba yace " *Innar Issa*, sunan Babanmu zaki fad'a mata kinji, ki daure ki fad'a mata."

Kyab'e fuska Mimi tayi ta fashe da kuka dan ta lura kawai ci mata mutumci ne ma zaiyi, wai babansu? Sa'an Abba ne fa amma yake cewa babansu, d'auke kanshi yayi daga kallonta ya kalli likitar yace "Dr. Ki saka Maryam Adam Shehu, shekaru 18."

Da sauri ta fizge hannunta tace "Abdul ban kai 18 ba fa, 17 ne wallahi."

Da sauri sheikh ya cije leb'enshi na k'asa sakamakon dariyar data nemi kubce mishi, hannu ya kai akan hab'arshi yana d'an saita kanshi tare da rik'e dariyar. Rakiya kam zaro ido tayi a ranta tace "Tofa! *auren yarinya* kenan."

Duk'ar da kanta tayi tana rubuta abinda ta tambaya, d'agowa tayi ta mik'owa Mimi abun d'aukar zafi, karb'a tayi tare da marairaicewa tace "Dan Allah ba zaki min allura ba ko?"

Murmushi ta mata tace "Ba zan miki ba indai zazzab'inki bai kai matakin ba."

Sheikh dai na kallonta sai k'ok'arin saka abun awon zafin take, saidai dake tun kayan jiya ne jikinta da suka matseta sai hannunta ya k'i shiga bare ta saka abun ya zauna mata a hammata.

Lura da haka yasa Rakiya fad'in "Ko ki zage zip d'in rigar? Dan naga kamar ta kamaki sosai."

A hankali ta aje abun d'aukar zafin ta zura hannayenta baya ta fara kiciniyar cirewa, sheikh kam takaici ne ya kamashi da tunanin haka take saka kayan kenan ita ma kamar dai 'yan zamani. Kamar da wasa sai ko yasa hannu biyu ya jawo gaba d'aya kujerar da take zaune wanda hakan ya haddasa bayar da k'ara akan tiles d'in 'kiiiiiiii! Zaro ido Mimi tayi ganin yanda ya jawota kamar wata beby duk da girmanta, bata gama sarewa da lamarinshi ba saida ya zura hannayenshi a cikin hijabinta ya kaisu a bayanta ya shiga lalubawa inda zai ji zip d'in. Tuni Mimi ta fara kakkaucewa tana babbank'arewa, zafin da yaji a jikinta yasa shi jin kamar ya cire mata rigar gaba d'aya ya rumgumeta a jikinshi ko ya samu damar d'auke mata zafin, saida ya ji ya rik'e zip d'in ya ja shi a hankali tare da sake matsawa daf da ita a kunne ya rad'a mata "Tsofaffi ba ruwansu tunda ba sha'awa garemu ba, miye na d'aga hankali daga cire zip na riga."

D'aukar abun awan zafin yayi tare da d'aga hannunta ya soka mata ya had'e mata hannun sannan ya ciro hannayenshi daga hijabin, Mimi kam addu'a take kar Allah ya d'auki ranta da mamakin tsohon nan, wata tambaya ta jefawa kan ta "To wai me yake nufi ne?"

Gemunshi kawai ta k'urawa ido mai d'auke da farin gashi d'ai-d'ai, saida taji tinnnn! D'in abun awon zafin ta d'an zabura ta kalli likitar data tara mata hannu, cirowa tayi ta mik'a mata ta duba, mik'ewa tayi tana fad'in "Bari mu gwada jininki mu gani."

K'ura mata ido Mimi tayi ganin ta d'auki d'an shud'i abu k'arami ta cire a gidanshi sai kuwa tsinin allura ya bayyana, zabura tayi ta mik'e tsaye tana saka kukan shagwab'a da fad'in "Bana so ni dai na fad'a miki tun farko, Abbana, Abba ma ya san bana son allura wallahi."

Ganin tana shirin zabgawa da gudu yasa shi mik'ewa ya tura kejarar baya, hijabinta ya rik'e yana kallon fuskarta duk ta rud'e yace "Innar Issa ya haka? D'an tsikara miki ne fa za'ayi ba zafi, haba mana *'yan matan tsohonta*, so kike a mana dariya ne."

Dariya Rakiya keyi inda Mimi ta shiga tsatsare k'aramin bakinshi da ido wanda bak'in gashi ma yake hanashi fitowa da kyau,wasu hawaye masu zafi ne suka taho mata akan kumatu, ba tare data d'auke idonta a cikin nashi ba murya a raunane tace " *Bawan Allah*, amma dai ai saida na fad'a maka bana so ko?"

Wani daban yake ji shi wallahi a lokacin a wani sake sakayau, ga isashen lokaci ga kuma wata k'uruciyarshi da yake jin ana neman dawo masa da ita baya, babu masu fad'in gafarta malam, babu ranka shi dad'e, babu sheikh ko malam, babu kurantawa da girmamawa mai cike da kambamawa, babu amsa umarninshi cikin d'aukakawa. Hasalima a nan shi ne ke k'ak'arin rarrashi, kai tsaye ake kallonshi ana fad'a masa abinda akayi niyyar fad'a, yau gashi har yake iya bada umarni sau biyu, bugu da k'ari ma har yayi magana kai tsaye aka ce a'a ba haka bane, wanda ko cikin wa'azi da dubannin mutane ke kallonshi da saurare aka samu akasi da ajizanci na d'an adam ya fad'i ba daidai ba kai tsaye ba'a katseshi, wani saidai bayan an tashi ya fad'a ko kuma a kirashi a waya ko kuma dai a rubuta mishi wasik'a.

Wani k'ayataccen murmushi ya sakar mata tare da jawota gaba d'aya ta kusa fad'awa jikinshi, d'an kashe mata ido d'aya yayi yace "...




_Sadaukarwa ga duk 'yan *duk nisan jifa* da kuma *matar mutum*_



*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:56 PM - Ummi TandamaπŸ˜‡: πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘¨πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ‘?

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


πŸ’«βœ? *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜? *[ T.M.N.A]* β˜? πŸ“–πŸ–ŠοΈ?

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*30*



A tausashe ya rabka sallamar da tasa Salammatu amsawa tana kimtsa zamanta daga kallon tv, kamar zata nutse k'asa dan girmamawa ta shiga, gaisheshi, da girmamawa shi ma ya shiga amsa mata dan ba yarinya bace, cike da kulawa yace "Hajia tana ciki ne?"

Nuna mishi d'akin Mimi tayi tace "Ta shiga ciki zata dubata."

Da ido ya amsa alamar to tare da nufa d'akin, da kallo ta bishi da mamakin yanzu nan fa aka barshi da yarinyar can fitsararriya sai ka ganta da ciki wata rana, tab'e baki tayi tana mayar da kallonta kan tv da fad'in "Maza ho."

K'wank'wasa k'ofar ya fara yi daga ciki Hajia tace "Waye?"

A sanyaye yace "Ana."

Da fara'a tace "Shigo sheikh."

A hankali ya bud'a k'ofar tare da d'ora idonshi akan Hajiar dake tsaye, bai yarda ya kalli inda ya tabbatar tana nan ba saida ya gama gaisawa da Hajia, cikin sakin fuska take fad'in "Da na ga dare yayi ai na d'auka ba zaka zo ba, kuma dana tuna kai ne fa sai na sa a raina zaka zo komai dare."

Wani lallausan murmushi yayi tare da d'an shafa sajenshi yace "Hajiarmu kenan, sabgogi ne dayawa, har zan shiga gida kuma na taho."

Da fara'a tace "Allah sarki, Allah ya bada ladar d'awainiya."

"Ameen." Ya fad'a tare da d'an kaikata idonshi ya kalleta, da sauri ya ji zuciyarshi ta fara bugawa, doguwar riga ce a jikinta ta bacci mai laushi, kan ta kuma babu d'an kwali sai gashinta data d'aure, jibda ce take k'ara shafawa a jikinta gaba d'aya.

Tunda ya shigo bata kalleshi ba, kuma sam bata da niyyar zata kalleshi sai murzawa hannayenta jibda take, d'an cije leb'enshi yayi na k'asa kafin yace "Ya jiki?"

Sai lokacin ta d'aga kai ta kalleshi, a cikin ranta tayi k'wafa tuna abinda ya mata a asibiti da tunanin "Zan rama, sai na mayar da kai kamar *kakana*."

Sakin fuskarta tayi tace "Da sauk'i *malam*."

K'uri ya sake mata da ido da nanatawa a ranshi "Malam?"

Hajia dake ta murmushi tana kallonsu ne ta d'an gyara murya tace "Bari na baku wuri ko."

Da wani matsiyacin sauri Mimi ta kalleta tace "A'a Hajia, ba abinda zai min."

A lokacin shi ma yayi saurin juyawa cike da kunya yana fad'in "A'a Hajia, saida safenku."

Amma jin abinda Mimi ta fad'a sai yasa ya tsaya ya sake juyowa, sai kuma ya jinjina kai ya juya zai fita, bayanshi Hajia ta bi tana fad'in "Dama ina son magana da kai."

Da kallo Mimi ta bisu da addu'ar "Allah yasa ta masa maganar wayata, ina so na samu waya."

Suna fita a falon ta zauna a kan kujera, tunda ta ga ya zauna a k'asa ya tabbatar mata yau uwa ake da ita kenan, dan akwai ranar da zasu zauna kan kujera ita dashi, to ranar ana matsayin malami kenan, cikin dattako ta k'ara gyara zamanta tace "Sheikh, nasan nayi maka hawan k'awara a lamarinka a game da auren nan, saidai ka sani ba nayi bane dan na nuna na isa da kai, na tabbata auren nan zai zame maka alkairi insha'Allah, ina fatan baka k'ullaceni ba ko?"

Da sauri ya girgiza kai yace "Subhanallah Hajia! K'ullata kuma? Ko d'aya wallahi, na d'auki hakan a matsayin abu ne da dama Allah ya rubuta zai sameni, tabbas da ita d'in ba *matata* bace da ban sameta ba ko da kuwa ina son haka."

Jinjina kai tayi tace "Naji dad'in haka, yanzu maganar tariyarta nake so naji, yaushe ka tsara?"

Sunkuyar da kai yayi yana mai jin kunyarta sosai, to shi ya zai ce? Ya fad'i ranar da za'a kawo masa tsarar Aisha? Shiru kawai yayi ya kasa magana har saida Hajia tace "To idan ya maka mu barshi a sati d'aya, lokacin na tabbata ka gama gyara mata na ta b'angaren."

Numfashi ya sauke a sanyaye yace "Allah ya sa haka shi yafi zama alkairi."

"Ameen." Ta fad'a ita ma, d'orawa tayi da "Sannan sheikh dan Allah kayi hak'uri da yarinyar nan, kaga fa shekarunta k'alilan ne, dole sai kana kawar da kai da hak'uri, inba haka ba zatayi abu a cikin k'uruciya kai ka ga kamar wauta ce ko kuma da gangan."

Jinjina kai yayi yace "Insha'Allah za'a kiyaye Hajia."

Murmushi ta masa tace "Naji dad'i, Allah ya maka albarka, sai kuma magana ta gaba."

Jinjina kai yayi alamar saurare, d'orawa tayi da "Waya na ce me zai hana ka siya mata? Kaga zata dinga kiran iyayenta ai."

Da wani irin k'arfi ya d'aga kai ya kalli Hajia yana kiran "Waya kuma?"

Ita ma da mamakin yanda taga firgici a tare dashi ta amsa da "E, waya."

Iska ya feso tare da duk'ar da kanshi yana ambatar "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Shi ya siya mata waya? Yarinyar da baisan irin girma da mahimmancin data bawa waya a rayuwarta ba, idan fa ya bata ta ci gaba da rayuwarta data saba, har shi fa sai Allah ya hukuntashi dan yana da kamasho. Cikin nutsuwa da salon bayar da umarni Hajia tace "Zan jira zuwa gobe da safe sai ka kawo mata."

Lumshe ido yayi tare da d'an sinne kai ya jinjina shi alamar to, shiru babu wanda ya sake magana har saida ya d'an tank'ware k'afafunshi yace "Hajia."

Da kulawa ta amsa da "Na'am." D'orawa yayi da "Ki fara shirin aurar da jikarki Eesha, insha'Allah na mata miji kuma bana tunanin za'a d'auki lokaci mai tsayi."

Da fara'a sosai tace "A'a masha'Allah, wannan ai abun farin ciki ne, Allah ya sa alkairi ya nuna mana ranar."

A sauk'ak'e ya amsa da "Ameen." Jim ya d'anyi kafin yace "Hajia ni zan wuce gida."

Mik'ewa dan ta fahimci so yake ta mik'e kafin yayi tsaye a kan ta shi ma, a hankali ya mik'e sukayi sallama a mutumce tana fad'in "A gaishe min da mazajen kwabon nan."

Murmushi yayi yana amsawa da zasu ji ya fice kamar yace "Wayyo Allah." Hajia ta umarceshi ya siyawa Ryam waya, me zatayi da ita? Su wa zatayi mu'amula dasu? Ko dai ma ita ta ziga Hajia kan a siya mata wayar? Da tunane tunanen nan ya isa gida.



*Saminu*


"Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un!" Abinda ta fad'a kenan sakamakon ganin Saminu zigidir babu kaya a jikinshi da wayarta a hannunshi yana kallon hoton Mimi wanda sukayi ta d'auka ranar kamu, yana kallonta yana ta lailaya dokinshi a dole yake son biyan buk'atarshi daga kallonta, juyawa tayi hankali a watse zata fita, da gudu ya biyota ba tare da jin nauyin jikinshi ba yana d'aura towel d'in shi yana kiran "Maimuna, Maimuna tsaya kiji."

Juyowa tayi a hassale ta kalleshi tace "Me zan ji? Wannan wace irin rayuwa ce? Me kake aikatawa haka dan Allah?"

Fashewa tayi da kuka hankali tashe cikin son rarrashi ya rik'o hannunta, da k'arfi ta fizge tana fad'in "Karka k'ara tab'ani."

Da alamar rarrashi yace "Naji to shikenan, amma dan Allah ki saurareni, Maimuna ba abinda kike tunani bane, wallahi..."

Sai kuma ya rasa me zai fad'a, sake juyawa tayi ya yi saurin shan gabanta yace "Ina zakije Maimuna? Dan Allah ki rufa min asiri, na yarda nayi laifi ki yafe min kinji."

Cikin sako hawaye tana kallon fuskarshi tace "Dama kana sonta ne? Ko kuma dai gaske ne abinda nake ji a gari a game da kai na neman mata?"

Da sauri ya girgiza kai yace "Ko d'aya Maimuna, wannan jita-jita ne na mutane karki yarda, Mimi kuma kamar 'ya ko k'anwa take a garemu ai, ban tab'a jin haka a kan ta ba."

Cikin d'aga murya tace "To me yasa kake kallonta kana son dole sai kaji dad'i ta haka? Fuskarta ce ke birgeka ko kuma albarkatun jikin da Allah ya hore mata?"

Sassauta murya yayi yace "Ba haka bane, Maimuna ina da buk'ata ne kuma ke naga kina saurin gajiya dani, bana so na zama mai takura miki shiyasa ban nemeki ba."

Tsareshi tayi da ido tana kallon fuskarshi, ta jima haka kafin ta sauke numfashi tace "Alhaji zan daina maka k'orafin gajiya idan ka min alk'awarin ba zaka sake kula mata a waje ba."

Da sauri jiki na rawa yace "Na daina, dama kuma bana yi wallahi, yanzu muje to."

A sanyaye ta bi bayanshi suka koma d'akin, d'auke wayar yayi ya aje gefe tare da kwantar da ita akan gadon, saidai tsaf abinda bata sani ba yana saduwa da ita ne amma kuma a idonshi Mimi yake gani, zuciyarshi ta gama haska mishi ita tare da k'awata mishi ita, musamman idan ya tuna kwancin nan nata a asibiti, yanda nonuwanta sukayi carrr daga sama kuma yake iya hangen matashiyarsu jajir dashi, ga s'uwawunta da suka kwanta akan gadon su ma sosai. Da haka har ya samu biyan buk'atarshi saidai babu gamsuwa dan hankalinshi a wani irin yake.



*Ahalin Mimi*


Aje abincin tayi gabanshi tare da zama gefenshi tace "Malam gashi."

D'an zabura yayi ya kalleta da alamar nisa yayi a tunani, Yaseen da Amir da suke gefensu ne suka kalleshi Amir na fad'in "Abba kaga yau ma mama shinkafa ta dafa mana har da nama."

Kallonshi yayi yana dariya yace "Da gaske? To ka k'oshi dai ko?"

Da dariya shi ma yace "E, Abba."

Murmushi yayi tare da jawo kwanon gabanshi zai fara cin abincin, da sauri Mama ta mik'e ta koma gefe kusa da k'ofar shiga ban d'aki, durk'usawa tayi ta shiga kwaranya amai, mik'ewa yayi hankali ya tashe ya k'arasa gareta yana fad'in "Subhanallah, uwar uwata lafiya? Baki da lafiya ne dama?"

Kakarin aman ta take yi bata kulashi ba, saida ta gama ya bata ruwa ta kurkure baki, mik'ewa tayi ta zauna kan tabarbar tana dafe kanta dake ciwo, gabanta ya zauna yana fad'in "Rabi'atu, baki lafiya dama? Me yake damunki?"

A hankali cikin muryar galabaita tace "Ba komai, ba wani abu bane."

Da kulawa yace "To ko gajiyar bikin nan ce?"

Da sauri tace "E ita ce."

Yanda ta bashi amsar ya sa mishi shakku, kallon tuhuma ya mata yace "Uwar uwata, ko dai Amir zaki wa k'ane?"

Da sauri ta kalleshi tana rufe baki tace "Kai." Sai kuma ta kalli su Yaseen, su ma su suke kallo, cike da kunya ta mik'e ta shige d'aki, dariya yayi tare da bin bayanta ya sameta zaune, kusanta ya zauna yana fad'in "Masha'Allah Rabi'a, nagode miki kinji, hak'ik'a wannan abun alkairi ne da farin ciki, Allah ya rabaki da abinda ke cikinki lafiya."

Sunkuyar da kai tayi tace "Malam kunya nake ji wallahi, mun aurar da 'ya kamata yayi ace mun aje wannan gefe yanzu."

Da mamaki ya kalleta yace "Iyeeeh! Kaji min matar nan, me zamu aje gefe d'in? Haramun muka aikata?"

Turo baki tayi ta sake yin k'asa da kanta, mik'ewa yayi yace "Uwar uwata fito ki ci abinci kinji, bayan wannan ma idan da wani rabon ni zan antayo dashi zuwa duniya."

Baki wangale ta kalleshi tace "Inna lillahi! Rashin kunya."

Juyowa yayi ya nunota da yatsa yace "Ke Rabi fita idona in rufe, na lura take-taken iya shegenki ne duk uwata ta d'auka, har take kallona ni da sheikh take fad'a mana tsofaffi."

Dariya Mama tayi ta sunkuyar da kanta, fita yayi ya zauna ya fara ci abincin cike da farin ciki a zuciyarshi, Mama kuma bata sake fita ba a k'arshe ma Yaseen da kansu sukayi shinfid'a suka taka kujera suka d'aura gidan sauro.





Please Login or Register in order to submit comment