Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsira yi maka wannan auren ba ,kawai da ka barmu munyi zaman mu a haka"...

Har cikin ran daddy yasan abunda Haseena ta fad'a ba k'arya a ciki ,amma shima ba yadda ya iya ne ,cewa yayi " Banda abun ki haseena ba dole in k'ara aure Ba ,tunda ba nida wacce ke Sona ,kuma da kike wani maganar Anty Haajar, Anty Haajar ai ba matata bace ko?" ,,, da biyu daddy yayi wannan maganan Dan gaba d'aya yi yake yana duban Haajar...


Wani irin fad'uwar gaba Haajar taji ,,, kauda maganar tayi da cewa "to in banda abun ki haseena,, kin tab'a ganin ka auri mutum badan kana son shi ba? Kuma ma har ka yadda ka zauna dashi ,kaji zaka iya ne ai. Sannan da kike wani zance na ,ni ai ba matar daddyn Ku bace ,kuma tafiya zanyi"... Aikuwar maganar se a kunnen Auta dake gefe tana wasa ,da sauri ta k'araso inda suke zazzaune ta dafa kafad'ar Haajar tare da cewa


" Anty Haajar wai tafiya zakiyi?"


Kowa juyowa yayi yana kallon ta. Murmushin dole Haajar ta kakaro tare da Shafa kan Auta tace "Eh mana Shukra "


Auta tace "To amma dai tare zamu tafi ko?"


Haajar tace "A'ah kina gidan Ku ,nima kinga gidan mu zan tafi!"


Nan fa auta ta shiga rero kuka ba girma ba azziki ,kan kace me kukan har ya soma sakar mata zazzab'i. Da sauri Haajar ta janyo ta jikin ta "Na shiga aljannah na kasa fita ,Shukra Dan nace zan tafi shine kike wannan kukan?"


Gyad'a kai Auta tayi ido jawur. Haajar tace "to na fasa tafiya saboda ke ,idan ma zan tafi to tare zamu tafi kinji yarinyar kirki".


Rumgume Haajar Auta tayi tare da sakin wani ihu " Yeeeeeeeeeh! Anty Haajar tace tare zamu tafi" daga nan bata k'ara bi takan wasan ba ,zuwa tayi ta lafe kan cinyar Haajar ,Haajar d'in na bubbaga bayan ta kan kace me bacci ya kwashe ta ,se wani ajiyan zuciya take sauke wa ,kamar wacce akawa dukan tsiya. Mamaki ne ya kama daddy Dan shi be tab'a tsammanin Shak'uwar dake tsakanin Haajar da Auta yakai haka ba...




Tsabar takaici haseena tace "To wai daddy meze hana ka auri Anty Haajar d'in ta zauna damu, kana ganin dai abubuwan da take mana da kulawar da muke samu a wajen ta ,Wanda ko mahaifiyar da ta haife mu bata yi lokacin mu ba balle har mu samu wannan. Shine me kake tunani idan Anty Haajar ta tafi tabar mu? Ya kake tunanin auren da zakayi ze iya maye mana gurbin ta? ,nidai inaga gaskiya daddy ya kamata ka zauna kayi tunani akai. Nifa se nake ganin Anty Haajar d'in ce ma bata dace damu ba"... Haseena ta fad'a cike dajin haushin Daddy, Dan ita akan haajar gaba d'aya yanzu lefin shi take gani.


Kallon Suxee daddy yayi ,alamar kina jin abunda haseena ke fad'a? Gyad'a masa kai tayi tare da lumshe fararen idanuwan ta alamar gamsuwa da zantuttukan Haseena.




Kafin daddy yace wani Abu Haajar tayi saurin katse zancen da cewa " Dan Allah ka manta da maganganun su ,kasan har yanzu yara ne. Muna tayaka murnar auren da zakayi Daddy, Allah kuma ya tabbatar da alkhairi." Ta k'arashe maganar tare da mik'ewa tsaye ta ciccib'i Auta ta d'ora ta a kafad'ar ta, sannan tace masa "seda safe". Tana kai aya ,tayi ficewar ta.


Suxee da haseena ma tashi suka yi tare dayi masa seda safe suka bi bayan Haajar.


Kusan daddy sumar zaune yayi ,Dan gaba d'aya ya lura yaran shi sun fi damuwa da Haajar sama dashi ,sannan bawai son Haajar bane baya yi , A'ah kawai yana tunanin yadda ze tunkari Haajar ne da zancen so, zuciyar shi na raya mishi Haajar bazata tab'a son shi. Wani d'an siririn tsuki yayi tare da Furta wa a k'asan zuciyar shi "Suna gani ma har sun fi ni son ta ne ,duk son da suke mata be kai kwantankwacin Wanda nake mata ba ,balle har ya kamo k'afar shi"... Haka dai daddy ya koma kamar wani sabon zararre a wannan Daren ,kasa bacci yayi ,kwana yayi yana sak'e-sak'en yadda ze b'ullowa al-amarin, se wuraren asuba bacci yayi awon gaba dashi...


Washe gari da safe, Su Haajar basu zo breakfast a sashen daddy ba kamar yadda suka saba ,a gefen su sukayi ,sedai suxee ta kai masa nasa ,kuma koda taje ta tarar yana bacci ,bata yi k'ok'arin tashin shi ba ,ajiye masa kulolin abincin kawai tayi ta k'ara gaba. Daya fito, dukkan alamu sun nuna masa ba'a nan suka yi breakfast ba ,alama ta d'aya daya gane kuwa shine rashin jin k'amshi na tashi ,Dan 'ka'ida ne kafin su fara cin abinci se an gyara wurin ,k'amshin turaren wuta na tashi kamar baza'a mutu ba. Alama ta biyu kuma ganin kula biyu daya yi akan dinning yasan nashi ne kawai dan ba haka suka saba jera abincin ba... Ya kusa mintuna goma a tsaye yana k'are wa wurin kallo ,kafin daga bisani yaje ya zauna ya fara cin abincin, se dai kwatakwata baya jin gard'in a bakin sa ,haka yake cin abincin kamar yana tauna magani ,tsabar ba haka ta saba zama yaci abincin ba ,har cikin ranshi yake kewar rashin ganin su a yanzu, amma daya yi wani tunani ,se kawai ya dake ,tare da cewa "dani kuke zancen ,bazan tab'a Neman Ku ba ,Dan kanku zaku dawo"... Yana kammala cin abincin shi ,yayi ficewar shi zuwa sabgogin shi...


A ranar yasa aka gyara d'aya daga cikin sassan dake gidan ,tare da zuba duk wani abun buk'ata ,Dan ya musu waya akan kar su zo masa da komai, sedai sashen be kai girman nasu Kubra ba ,sannan shi iya na k'asa ne flat babu bene...


Da daddare aka kawo Amarya. Tun ranar da aka kawo amarya daddy be sake sa su Haajar a ido ba ,abincin ma da yake tunanin ko zasu aiko masa tun a ranar farko shima shiru babu alama ko samatan hakan.


Wani abun takaicin ma, duk hasashen da daddy ke yi shine za'a kawo masa amarya ya amayar da shak'uwar sa ,amma ina sedai hak'ar shi bata cimma ruwa ba...


_Ku biyo ni Dan jin dramar da daddy da lubabatu a ranar da aka kawo ta_πŸ˜‚πŸ‘ŒπŸ»






MUJE ZUWAπŸ’ƒ






TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/2, 2:06 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI_


*____________________________*
























_A ranar da aka kawo lubabatu ,daddy na zaman jiran ta a sashen shi shiru har kusan biyu na dare bata ba labarin ta,,, daya kira ta a waya akan yana Neman ta ,se ce masa tayi shi me yake da baze zo inda take ba, hala be San gajiyar hidima bane, ai seda tace ya biya musu jirgi amma yak'i yace dole sedai ta mota ,to ita yanzu gaskiya ta gaji ,daga kan gado ma bazata iya sauka ba ,idan Abu me muhimmanci yake d'auke dashi yaje ya same ta...shirun da lubabatu taji daddy yayi yasa taja wani d'an siririn tsaki tana fad'in "naga alama ba abunda ke damun ka, saboda haka se da safe". Ta k'arasa maganan tare da yanke kiran_


_Washe gari da 'yan rakiyar amarya zasu koma ,da kanta taje ta sami daddy kwance akan gado yana bacci. Iskan bakin ta ta shiga hura masa a kunne daddy na k'ara bin gado, a tunanin shi ko iskan panka ne ,dadai yaji abun baze k'are ba ,bud'e lumsassun idanuwan shi yayi tare da zuba su akan lubabatu, murmushi ta sakar mishi cike da k'warewa tana fad'in_


" Ango kasha k'amshi! Wannan irin makara haka. To ka tashi kayi wanka ,muje mu samu bak'in mu ,Dan yau zasu tafi yanzu haka ma shirya-shiryen tafiyar suke yi ,gaka se a samu abunda za'a basu ,ina lefin wa'yanda suka yo tafiya fiye da kilomita 200 Dan su kawo maka amarya ,kai fa suka yiwa wannan k'ok'arin ,saboda haka Dan Allah idan zaka sallame su ai musu sallama me tsuko da za'a tabbatar da lallai cewa na zo _GIDAN MISBAHU_ ta k'arasa maganan tare da yin wani irin k'ara. Shidai daddy da ido ya bita ,a ranshi yake cewa wannan kuwa lafiyar ta? Kamar taji me yace tace "Lafiya dai?"


Yak'e daddy ya mata tare da cewa "Bakomai" ,,,,daga haka be k'ara mata ba be rage mata ba ,ya tashi ya fad'a toilet ,wanka yayi tare da d'auro alwala. Towel ya fito dashi iya k'ugun shi... Har lokacin Lubabatu na zaune kan gado. Ko ta kanta be biba ,ya bud'e sif d'in shi tare da d'auko mayukan shafawan shi da turaruka...taso wa lubabatu tayi cike da k'ware wa ta k'araso har inda daddy ke zaune ,karb'an man shafawar tayi daga hannun shi ,ta shig Shafa masa tana wani irin salo me gigita tunanin d'an Adam,,, jin da daddy yayi kamar ze sauka a network yasa yayi saurin dawo wa hayyacin shi tare da mik'e wa zunb'ur ya Fara k'ok'arin saka kayan shi, har lokacin idanuwan lubabatu na kan shi ,se bin shi take da wani mayataccen kallo na k'urulla ,tana had'e yawu...




Daddy kauda kanshi yayi gaba d'aya daga gefen ta ya maida hankali gun saka kayan shi ,seda ya gama yazo ya wuce ta gaban ta ze fita, hannu lubabatu tasa tare da janyo shi baya ,tana fad'in "Haba ranka ya dad'e ,kafa San kai na tsaya jira ,daka gama ai se kace mun in taso muje ko?" Shidai daddy be ce mata ci kanki ba. Taso wa tayi ta sagala hannun ta cikin gurwar hannun shi a haka suka fito se surutai take masa ,wani yayi murmushi wani kuma ya share ta...


Fitowar su yayi daidai da dawowar su Haajar da alama siyayya suka fita yi ,Dan ko waccen su d'auke take da ladodi a hannuwan ta. Ganin su yasa ya k'ara fad'ad'a murmushin dake shimfid'e a fuskar shi...


A zaton shi ko zasu k'araso a gaisa ne ,se dai hasashen shi yasha banban ,Dan kuma gimtsewa suka yi gaba d'ayan su tare da d'auke kai kamar ma basu ganshi ba ,daga k'arshe ma suka canza hanya ,suka bi ta baya...


Wani iri daddy yaji a ranshi. Lubabatu dake ganin duk abunda ke faruwa ,cike da isa tace "Alhajin Allah wa'yancan ba 'ya'yanka bane?"


Gyad'a mata kai yayi alamar eh. Wani siririn tsaki taja tare da cewa "Dan wulaqanci tsabar sun raina mutane shine baza su iya zuwa su gaishe mu ba? Ko ba komai ai naci albarkacin uban su kai ko? Ga bak'in mu a cikin gidan nan ,yaran nan Dan fitsara basu je sun gaishe suba, me kake tunanin bak'in namu zasu d'auka ,ai gani zasuyi kamar yaran basu da tarbiya ,aje ana cewa 'ya'yan mijina basu da ta ido , aini zasu zubar wada daraja, da a gaban mutane sukayi haka me kake tunani ,lefin mu za'a gani ,gaskiya kayi musu magana Dan wannan raini ne"... Ta k'arasa maganan tana goge hawaye ,kona menene ohon mata.


Ai fa nan daddy ya k'ara harzuk'a ,Allah Allah yake yaje gama sallamar bak'in ya koma ta kan su, yaji dalilin su na son zubar masa da mutunci agaban matar data zo jiya-jiya. Sama sama ya gama sallamar bak'in se murna suke yi ,Dan kyauta daddy yayi musu na gasken gaske ba nida kyauta ba, ya kuma basu mota aka maida su har gida cike da abun alkhairi...


Daga nan kai tsaye sashen kubra ya nufa ,d'akin su suxee ya wuce kai tsaye ,yana zuwa ya banka d'akin tare da fara sauke musu ruwan jaraba



" Yanzu Ku har kunyi girman da zaku nemi Ku zubar mana da k'ima da daraja a idon mutane ,me kukayi kenan, kunzo kun wuce ta gaban mutane Baku san Ku gaishe su ba ,wani irin hali ne wannan? To bari kuji Sam Sam bazan d'auki wannan sabon iskancin Baku ba ,waji bane idan kuka tashi kuje da safe Ku gaida mutane"...


Haka dai daddy ke ta zuba ruwan bala'i ba girma ba azziki kamar Wanda aka yiwa abunda yafi haka.




Ga baki d'ayan su ba Wanda yace masa uffan har Auta dake zaune kan centre carpet tana shan ice-cream abun ta. Tab'e baki haseena tayi tare da cewa


"Cabd'i jamm!!! Ita kuma wannan da haka tazo? To Allah ya kawo sauqi"...


Daddy da kamar dama a jiraye yake, tasss!!! Kake ji ya d'auke haseena da wani irin zafaffen mari...


Gaba d'ayan su kamar an musu shock ,Suxee har da dafe kuncin ta ,Dan gaba d'aya ji tayi kamar a fuskar ta aka sauke wannan marin... Zaro ido suka shiga yi fuskar kowa d'auke da mamaki... Hatta auta seda ta razana Dan garin firgita har seda ta b'arar da roban ice-cream d'in ta ,kuka ta fara yi Dan ta tsorata ,da gudu tazo ta fad'a kan Haajar ,Haajar d'in ta rumgume ta tana bubbuga bayan ta alamar rarrashi...


Hannu ya shiga nuna musu tare da cewa " how dare u! Ina magana kina magana ,wacece ke. U better watch ur actions nonsense"... Yana gama fad'in haka yayi ficewar shi kamar Wanda ze tashi sama...




Haseena dafe ta kunci tana k'ara hakaito abunda ya faru kamar a mafarki ,Suxee rik'e da hab'a tana mamakin ikon Allah, Haajar kuwa rumgume da auta dake ta faman sauke ajiyan zuciya...




Suxee tace "Allah gamu gare ka ,jiya jiya daga zuwan ta, a kwana daya hakan ya fara faruwa ,me kuke tunani idan wannan takai wata d'aya a gidan nan? Ya kamata musan abun yi fa. Baku ga wani irin kallo data ke bin mu dashi d'azu ba?".. Cewar suxee


Wani irin murmushin mugunta haseena tayi kamar ba ita aka sauke wa mari yanzu ba tace " Ku banni da ita ,idan tasan wata ai batasan wata ba. Mummy zan kira duk inda suka je su dawo ,Dan sune kad'ai zasu mana maganin wannan me d'anyen kan, mu da muke da Hajiya kubra har za'a zo a nuna mana bariki?"...




Maganar seda taso taba Haajar dariya ,amma ta basar. Tunanin mafita take yi ,kafin daga baya ta sauke ajiyan zuciya alamar ta gano abun yi...
















_kudan yi hak'uri da wannan. Kunsan hidimar sallah ,har yanzu ban gama samun kaina bane, amma Dana warware zaku jini insha Allahu. One luvπŸ’–πŸ₯°πŸ₯°.










MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/2, 9:17 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA TAKWAS_


*____________________________*
























_Satin Lubabatu d'aya gaba d'aya Daddy ya rikirkice ya susu ce ,saboda ya samu kan zaran ,ga daddy mutum ne me tsananin son shan d'umin mace kawai Dan baya samu ne ,kuma gashi shiba ma'aboci Neman mata bane, Allah be tab'a d'ora mishi son bin matan banza ba. Har ya fara manta yadda ake kwanciya da mace tsabar an dad'e ba'a had'u ba ,se ga lubabatu, ita ma se da yayi kamar yanayi tukunna ya samu kanta ,bayan d'an k'aran wahalar data bashi. Dan a ranar farko daze kusance ta ita ta fara tsokano shi ,seda ta bari yawun shi ya tsinke yana gab ,sannan ta fara wani salon iya shege ,wai "Haba Alhajin Allah! Fisabilillahi haka ake wa amarya dama ,ranar da zaka fara kusantar matar ka ce ba wani kyautata wa se kace dai ba auren soyayya ba". Duk yadda daddy yayi k'i lubabatu tayi ,kud'i take so daddy ya bata gashi ranar ba kash a hannun shi ,yace ya mata transfer tace ita bata yadda ba. Sha biyu na dare daddy ya fito zuwa ATM Ciro kud'i ,se bayan ya dawo ya tuna da akwai ma kud'i a motar shi ,kwasa yayi dika ya had'a mata ,kud'i ya bata tsabar su Wanda ko shi be San ko nawa bane... Ai fa Lubabatu wasai, a Daren seda ta kusa mantar da daddy kowa nashi ,Dan seda ta tabbatar masa yayi aure, a wannan Daren daddy seda yayi d'an k'aramin hauka Dan tsabar kad'ewa da zautuwa ,sosai lubabatu ta bashi had'in kai ya murje ta son ranshi... Tun da lubabatu ta gano logon daddy ,shi kenan abun nema ya samu ,ta fara masa yawo da hankali ,idan ya matsa mata se ta nemi wani abun me tsoka Wanda daddy baya iya cewa A'ah._


_Tunda daddy ya gane shima ,se ya sakewa lubabatu bakin aljihun shi ,ya take mata kan maciji tana wasa da wutsiya. Wata sabuwar rayuwa suke bud'e ,aiki in baka yi bani wuri. Koda yaushe lubabatu na mak'ale da daddy tana masa kissa da kisisina ,shagwab'a da karairaya se Wanda ta manta._


Tun su Haajar suna tunanin ko daddy ze neme su ,shiru suke ji babu alamar hakan ,Dan gaba d'aya daddy mantawa yake dasu ,baya ta tasu ,ina ya fito lubabatu ina zashi lubabatu...


Wata safiyar asabar su suxee na zaune suna tattauna matsalolin gidan, Haajar ke cewa "Ni fa se nake ganin kamar bamuyi aiki da tunani ba, gaba d'aya mun yi wawanci wallahi ,ko Abbu Sameer daba fad'a masa fad'a yayi ta mun akan bamu kyauta ba ,to taya ma zamu ci ribar abun matuqar ba muna gano meke tafiya a can d'in ba. Ina ganin ya kamata mu sake taku"... Haajar ta fad'a ,amma a cikin zuciyar ta ita kad'ai tasan me take shirya wa...






Sauke ajiyan zuciya Suxee tayi kafin tace "nima fa abun ya soma damuna wllh Anty Haajar, idan zan iya tuna wa rabon mu da daddy tun randa ya shigo ya bud'e mana wuta ,washe garin kawo Amaryar sa kenan, yau gashi ana Neman wata kwatakwata daddy baya Neman mu ,kamar ma babu mu a gidan se sha'anin gaban shi kawai yake yi. Kuna gani fa kullum da yamma d'aukar matar nan yake suna fita kuma timing d'in su basa dawowa gidan se dare, ni wallahi ina jiyewa daddy tsoron kar yaje ya sakewa matar nan da yawa tazo ta ruzga dashi. Ga dai shi yanzu komai na tafiya daidai da alama tana kula dashi ,Dan ni nasan da akasin haka ne da tuni daddy ya neme mu, amma shirun yayi yawa ya kamata mu saka ido sosai"...


Murmushi Haajar kawai tayi Dan ita tuni tasan duk abunda ke guda na , kawai tana jira lokaci yayi ne.


Haseena tace " maganan ki gaskiya ne Yaya suxee, ni kaina abun ya fara d'aure mun kai ,amma ya kamata muyi wa toka hanci... Anan dai suka gama shirin su akan zasu je sashen daddy da daddare suga wainar da ake toya wa ,bayan Haajar ta jawa haseena kunne akan duk abunda zata gani kar ta yadda ta maganta ,Dan tasan halin ta bata gani bata tanka ba ,bata bi takan Suxee ba Dan ita bata fiye magana ba mace ce me zurfin ciki da qawaci ,duk abunda zesa kaga suxee tayi magana to ba kad'an bane...




Girki sukayi kamar yadda suka saba ,kowaccen su tasha doguwar Riga har Auta kamar masu shirin fita ,sashen daddy suka nufa kowaccen su da abunda take sak'awa a ranta...




Da sallama suka tura k'ofar parlourn suka shiga. Tsakar parloun kan carpet suka hango daddy da lubabatu cikin shigar k'ananan kaya ,daddy na bata abinci a baki ,ita ko lubabatu se zuba masa ruwan shagwab'a take yi ,gaba d'aya daddy yabi ya susuce se biye Mata take ,Dan duk wani abun da lubabatu zata yi burge shi take yi ,baya son jin lefin ta ko abun da ya tab'a ta. Ze kuma iya rufe ido ya ciwa ko waye mutunci akan ta...




Kallon kallon su Haajar suka shiga yiwa junan su. Sun kusa mintuna goma a tsaye ,sallama kuwa sun yi tafi a k'irga amma ba alamar an San da zuwan su balle a musu izinin shigo wa...


"Tofa! Wani sabon salo wai biredi a lefe. Kuga ikon Allah fa. Dole ya manta damu ai" cewar Haseena. Wani d'an guntun tsaki taja tana k'ok'arin fita Haajar ta dakatar da ita. Kallon tsaf Haajar tayi musu kafin ta k'arasa ciki tare da cewa su suxee "kuzo muje" ba musu suka bi bayan ta...




Fuska a sake Haajar ta fara gaida daddy sauran ma suka gaishe shi. Ba tare da ya d'ago ya dubi d'aya daga cikin suba ya amsa musu da "lafiya".


Gaida Amaryar sukayi ,sedai ita ba kamar daddy ba ,ta amsa su ba yabo ba fallasa. Sun d'an dad'e a zaune ba Wanda yace musu uffan kafin lubabatu tace


" Ku se yau kuka ga damar zuwa gaishe da sabuwar uwar taku?"


Suxee da haseena kallon junan su sukayi kafin suka maida duban su gun lubabatu. Haseena har ta bud'e baki zata yi magana Haajar ta kitse mata hanzari da cewa


"Ayi hak'uri. Dama mun d'an bar Ku ne Ku samu Hutu shiyasa bamu lek'o kuba ,amma ayi mana afuwa".




Tab'e baki lubabatu tayi kafin tace " Ba damuwa mun gode da ziyara. Alhajin Allah tashi mu shiga daga ciki na fara jin bacci" lubabatu ta fad'a cikin kissa tana duban daddy.




Ba musu daddy ya tashi ya shige gaba ita kuma tana bite dashi a baya. Kayan kallo ta kashe ,har takai k'ofar shiga bedroom ta jiyo tace



"Idan kun fita ,Ku d'an ja mana k'ofar. Seda safen Ku"... Ta k'arasa maganan tare murd'a k'ofa ta shige. Shigar ta ba dad'e wa ka fara jiyo muryoyin su daddy na mata wasa tana fashewa da dariya...




Su Suxee jiki ba k'wari suka kwashi jiki da kulolin da suka shigo dashi suka koma sashen Ku. A ranar kwana tattaunawa sukayi yadda zasu b'ullowa wannan rikitaccen al-amarin...














MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/6, 7:00 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA TARA_


*___________________________*


















_A Daren ranar Lubabatu tayi wani mugun mafarki akan Haajar. Mafarkin da yayi masifar firgita ta ,lokacin data farko ko ba'a ce maka a tsorace ta farka ba yanayin ta ze tabbatar maka da hakan ,Dan kuwa jik'ewa tayi sharkaf da gumi kamar wacce yaje jihadi da zuciya d'aya. Abun yayi matuqar gigita ta da d'aure mata kai ,Dan wannan kusan shine karo na ukku tana munanan mafarkai akan Haajar, kwatakwata yarinyar bata gaban ta ,amma tun da ta fara mafarkin ta ta tabbatar akwai wani abun a k'asa Wanda bata San dashi ba ,tayi iya dabarar da zatayi wajen tambayar daddy game da Haajar amma ce mata yake 'yar sa ce. A wannan karon data sake tambayar shi game da ita tare da shigar d k'orafin ta akan lallai lallai sedai yasa haajar tabar gidan wanda shine karo na uku...
Cike da masifa daddy yace "So nawa zan gaya miki Haajar 'yata ce ,me yasa kika damu akan ta yarinyar da bata damu da sabgogin kiba? 'Yar Aminina ce Hajj Jamil. Daga yau se yau kuma bana so in sake jin kinyi magana akan ta,,,, maganan Haajar tabar gidan nan Dan wata biyan buqatar kanki kuma be ko

Please Login or Register in order to submit comment