Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Suxee ta fa d'a tarkon so kuma mai tsanani. Tace mata "Ni shawarar da zan baki shine ,ki yi a hankali Dan na fahimci ke baquwa ce ta wannan fannin. Ya na da kyau ki iya bambamce tsakanin SO da kuma QAUNA ,wannan ne zai taimaka miki wajen gane waya kamata ki so da kuma mai son ki na gaskiya." Nan Haajar ta ci gaba da ankarar da ita tare da yi mata 'yan nasihohi kan yadda zata kula da kan ta. Su na cikin hirar ne sai ga Barr ya kira ta a waya ya ce mata ya xo ya na sashen Hajiya. Tace "to ga ninan zuwa" tana gama fad'ar haka ta yanke kiran. Murmushi Haajar tayi tare da tambayar ta "shine? Suxee na murmushi Tace "Eh Shi ne". Ita ma Haajar murmushin ta yi tare da cewa " to motar soyayya! Jira ni in d'auko hijabi na a rage mun hanya". Dariya maganar Haajar din ya ba ma Suxee tace "Kai Anty Haajar. Ni d'in ce kuma motar soyayya?" Haajar tace "ai kin ma wuce mota ,sai da tashar motar". Dikkan su dariya suke yi ,da haka suka k'araso zuwa sashen Hajiya...






Da sallama d'auke a bakunan su suka shiga parlour-n. Mutanen dake ciki suka amsa musu da "Wa'alaikumusallamu". Tun daga nisa Barr ke sakar wa Suxee murmushin qauna. Ita ma bata b'oye farin cikin ta na ganin shi ba. Da haka har suka k'araso suka zauna. Haajar tace " Lah Abbu sameer! Yaushe ka zo?" Hajiya tace "wa? Wai Jamilu? Ai ya dad'e anan muna ta hira abun mu". Haajar tace " shine baka kira mu munzo anyi da mu ba" Haajar ta fad'a cike da tsokana. Yace "Wa ke nan 'yan nan? Wannan hira ai ta girme ki ,Dan ta manya ce. D'a na ganawa da uwar shi, wa ya gayyato bare kuma?" Zaro ido Haajar d'in ta yi tare da cewa "Cabdi jam! Wai ma bare. To Allah yasan yanzu na fika fawa a wajen Hajiya." Hajj Jamil yace "haba wa yarinya ,tukunna dai. Sai dai ki fi daddy amma ba ni ba" cike da raha Haajar ta koma kan kujerar da Hajiyan ke zaune tana ta famar yi musu dariya ta maqalqale Hajiya tare da shagwab'ewa tana fad'in "wai Hajiya ta kin ji ya fi ni fawa?" Hajiya na dariya tace "k'yale shi 'ya ta ,yanzu kuma ai ke ce sarauniyar fadar sauran kuma sai dai su zo a fadawan ki". Cike da jin dad'i Haajar ta sake rumgume Hajiya tana fad'in " dakyau Hajiya ta. Allah ya qara lafiya da Nisan kwana. Ka dai ji ko Abbu sameer?" Hajj Jamil yace "ke Dan uban ki ni ki sake mana tsohuwar mu. Ji yadda ki ka maqalqale mana ita kamar za'a mai da ki ciki" Haajar sake mannewa Hajiya tayi. Hajj Jamil yace "au ba da Hausa nake magana ba". Ta sowa yake shirin yi yayo kanta, Hajiya tace " A'ah haba Jamilu. Ya zaka zo har gidan 'ya ta kana Neman ka takura mata? To ka fita mun a ido kaji na gaya maka. Idan ba haka kuma ka tashi ka tafi mun gode da ziyarar, da ma ai ka canza sheqa. Ina jin ma yau ma makuwa ka yi ba nan kaso zuwa ba". Dariya Haajar ta dinga yi wa hajj Jamil hadda su gwalo. Hajj Jamil yace "gaskiya sai na yi da gaske ,Dan baze yiwu ace wannan yarinyar mai kama da maqota na Neman k'wace mun fada ba". Hajiya tace " to sai ka bada himma". Dikkan su dake parlourn sai dariya suke musu. Sai a lokacin Haajar suka gaisa da Barr. Suxee kuma ta gaida hajj Jamil. Suna cikin haka daddy ya shigo. Ganin duk yadda suke raha yasa yace "Yau kuma wani albishir Ku ka samu ne haka?" Hajj yace "Ina fa albishir. Matar ka na Neman ta k'wace min fada a wurin Hajiya kuma bata isa ba." Daddy yace "yo isa kuma na nawa. Ni kaina nan inajin ka kusa jin ance Hajiya ta zane ni da bulala akan Haajar". Hajj Jamil yace " kace kai ma ba barin ka ta yi ba?" Daddy na dariya yace "Ai kuma sai kayi. Gata nan ka tambaye ta". Hajiya tace " kwayi kwa gaji Ku bari. 'Ya ta kuma li'ilafi quraishun." Hajj Jamil yace "lah! Ka ji Hajiya na Nema ta yi mana baki". Dikkan su suka saka dariya. Har kusan goma na dare su na nan su na ta shan hira cikin raha abun gwanin sha'awa ,Dan idan ka gan su a yadda su ke zaune ba zaka ce ba 'ya'yan Hajiya bane su.




Daddy ne ya fara miqewa yace shi dai zai shige Dan ya fara jin bacci. Da haka ya yi musu sallama ya yi ficewar shi. Matar shi na ganin haka itama ta miqe ta bi bayan shi. Ya rage daga Hajiya, Suxee, hajj Jamil sai kuma Barr, Dan auta ta dad'e da yin bacci tun shigowar hajj Jamil. Barr yau d'in gaba d'aya ji yake an takura masa ,ga shi dare ya yi amma bai samu damar ganawa da masoyiyar sa ba. Ganin lokacin tafiyar shi ya kusa ,kuma matuqar ba shi ne ya kira suxee ba yasan ba zuwa za ta yi ba. Miqewa ya yi tare da cewa " Hajiya ni ma fa jirgi na zai d'aga. Dan na fara jin bacci". Hajiya tace "gaskiya kam ya kamata kaje ka d'an huta. " sai da safe ya yi musu tare da miqewa hajj Jamil hannu suka yi saida safe. Sannan ya dubi suxee da ke zaune kamar babu ita a wajen yace "biyo ni ki amso wa Auta chocolate d'in da na siyo mata, da safe ki ba ta. Saura kuma ki sha mata Abu". Murmushi kawai suxee ta yi Dan ta San mai hakan ke nufi. Shi ya fara yin gaba sannan ta bi bayan shi sad'af-sad'af... Hajj Jamil sai bin su yake da ido ,Dan tun lokacin da Barr ya zo ,har ya kira suxee a waya ,ba jimawa sai ga ta tazo duk idon shi na kai. Ya kauda kai ne kawai ya yi kamar bai Su na yi ba. Gaba d'aya ya kasa samun sukuni Dan haka shi ma ya yi wa Hajiya saida safe ya fito. Waige waige ya shiga yi yaga ta inda zai hango su kamar ance ya waiga hagun shi ,ya hango Suxee a zaune cikin motar Barr mazaunin driver, ta sako qafafun ta a waje ,yayin da shi kuma Barr ke tsaye ya rik'e marfin k'ofar da suxee ke zaune. Kai da ka hango kasan suna cikin farin ciki da jin dad'in hirar su.




Ran hajj Jamil ne ya b'aci over. Wani irin haushi da takaici ya tokare masa maqoshi. Tunanin yadda zai b'ata musu wannan zaman ya fara yi. K'arasawa ya yi har inda suke tsaye. Suxee na ganin shi ta miqe da sauri tare da duqar da kanta k'asa. Barr yace "Ah kai ma ka fito kenan?" Hajj da yake jin kamar zai yi aman zuciya yace "Eh wallahi." Barr yace "To Allah ya ba mu alkhairi" wani baqin cikin ne ya qara taruwa ya tsaya masa a qahon zuci. Kamar kar yace komai sai kuma yace "Dama cewa na yi ko za ka d'an ajiye ni idan ba damuwa. Motar tawa ce tad'an samu matsala dak'yar na samu na qaraso nan yau. Sai gobe zan turo bakanike yazo ya duba". Ba tare da Barr ya kawo komai a ransa ba yace " To ba damuwa". Sannan ya maida duban shi wurin suxee yace "muje in raka ki ciki'". Ba musu ta shige gaba shi kuma yana biye da ita a baya a haka har sai da ya kaita k'ofar sashen Hajiya da ya San shiga kawai zata yi yace " saida safe ko?" Tace "Allah ya kaimu". Kiss ya yi a tafin hannun shi tare da aikata mata. Da sauri suxee ta shige ciki cike da jin kunya.




Duk abun nan da suke Hajj Jamil na kallon su ba tare da sun Sani ba. Ran shi yayi qololuwan b'aci. Dan ko da Barr ya aje shi ko godia bai iya masa ba. Kawai shigewar sa ya yi gida...






Daren ranar Haajar ta yi wani mummanan mafarki akan Kubra. Wai ga su nan a jeji tana gudu kubra na bin ta da gudu da wani mummunan siffa. Addu'o'i ta dinga jerowa sai kalan Wanda ta manta, daga haka Kubran ta b'ace bata sake bin ta ba.


Wannan mafarki ya yi matuqar firgita Kubra. Daddy da ke kwance a kusa da ita da sauri ya tashi yana k'ok'arin kunna wutar d'akin. A firgice Haajar ta farka ,duk ta yi zufa. Tsanan tashin hankalin da ta shiga ya haifar mata da gocewar jini.


A Daren daddy ya kaita asibiti ba tare da ya gayawa kowa ba. Sai dai kafin ma su kai asibitin Allah ya yi na shi ikon ,Dan kuwa cikin da ke jikin Haajar ya zube...




















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/23, 6:58 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ARBA'IN DA BIYAR_


*____________________________*




















Wannan al-amari bai yiwa daddy dad'i ba ko kad'an ,dan kusan har ya fi Haajar d'in damuwa. Yadda daddy ya shiga tashin hankali kai idan ka gani za ka d'auka wannan shine karo na farko da za'a yi masa haihuwa, badan komai ba Sai saboda tsananin Kaunar da yake yi wa Haajar d'in. Haajar ta sha wahala sosai. Ta zubarda jini matuqa ,wannan ne yasa aka buqaci da dole Sai an yi Mata k'arin jini, banda wankin Mara da aka yi mata. Jinin daddy aka iba aka sa ma ta. Hajiya ce ta koma asibitin tana kula da ita ,kwanan su hud'u ta ji sauqi Alhamdulillahi ,aka sallame su suka dawo gida. Mutanen azziki Sai zuwa yi mata sannu suke yi. Hajj jamil ma ya zo gaishe ta ,bayan sun samu sarari ne Haajar ke fad'a masa irin mafarkin da ya yi. Ya jima yana jimanta abun kafin ya yi Mata addu'an Allah ya tsare gaba ,yace kuma ta qara dagewa da addu'o'i. Bayan hajj jamil ya koma gidan shi ya kira yayan shi mahaifin Haajar ya shaida masa abubuwan da suke faruwa ,Sai dai an yi rashin sa'a mahaifin Haajar d'in baya qasar gaba d'aya yaje taron qaddamar da wata gidauniya ta taimakawa nakasassu kan harkan lafiya. Ya kuma shaida masa zai d'an d'auki lokaci a can d'in ,a qalla wata biyar ko shida. Hajj jamil bai ji dad'i ba ,Dan yasan da ace yayan na shi na qasar ,to shakka babu zai bada gudunmawar shi ,musamman da Allah ya yi shi mai tarin baiwa da hikimomi iri daban-daban. Ya na da k'warewa akan duk wata harka na jinnu da sauran su. Wannan ne yasa hajj jamil ya haqura ya bari har Sai ya dawo. Dan babu abunda za su iya babu shi.




Wata d'aya da faruwar hakan ,Haajar ta sake samun juna biyu. Murna agun daddy ba ka ma hannun yaro. Tarairaya kuma Sai kalar Wanda ya manta. Haka hajiy ma ta ke kula da ita sosai. A gefe d'aya kuma soyayyar Suxee da Barr dad'a qarfi ta ke. A kwana a tashi cikin Haajar ya kai watanni ukku. Ta yi kyau sosai ta qara haske. Wata rana da daddare daddy yawo da rana ya taradda Haajar d'in na bacci. Ganin yadda take baccin hankali kwance yasa bai yi yunqurin tashin ta ba. Zuqunnawa ya yi Sai tin fuskar ta ya sumbaci gefen kuncin ta. Ya d'auki abunda zai d'auka sannan ya fice. Suxee ce ta nufo sashen da fara'a d'auke a fuskar ta. Ta zo ta ba Haajar labarin yadda ta yi da Barr akan yana so ya turo. Yanayin yadda taga Haajar d'in ya yi masifar tayar mata da hankali. A sume ta ga Haajar d'in dirsashen a k'asa ga jini na mata zuba ba girma ba azziki. Da gudu ta koma sashen Hajiya ta fad'o mata. Hankalin Hajiya idan ya yi dubu ya tashi, ba shiri ta biyo bayan suxee suka zo sashen Haajar d'in. Anan hankalin ta ya sake ta shi ganin yadda jini ke yiwa Haajar d'in zuba kai kace an yanka rago ne. Rud'ewa Hajiya ta yi nan da nan ta fara kuka ,tace wa suxee "ma za ki kira daddy ki sanar da shi halin da ake ciki. Suxee ita ma hawayen take ,da sauri ta d'aga waya ta kira daddy ta sanar da shi halin da ake ciki. Ba'a fi minti goma ba Sai ga shi ya iso hankalin shi a tashe. Haka ya ciccib'e ta ya sab'a ta a kafad'a ,jinin duk ya b'ata masa jiki yana gudu Hajiya na bin shi a baya. Mota ya bud'e ya saka ta gidan baya. Hajiya ta shiga tare da ita ,Sai addu'o'i ta ke tofawa Haajar d'in. Suxee na gida saboda auta shi yasa ba ta bi su ba ,Sai kuku take yi tana addu'ar Allah ya ta shi kafad'un Haajar. Dan gani take yi rasa Haajar d'in zata yi kamar yadda ta rasa 'yar uwar ta haseena. Ranar kasa cin komai ta yi ,Sai aikin hawaye da ta kasa tsayar da su. Ba jimawa Barr ya je gidan ,a nan suxee ke fad'a masa Haajar ba tada lafiya an kai ta asibiti. Tambayar ta ya yi a ina asibitin ya ke? Ta fad'a masa sunan asbitin da suke zuwa. Ko zama Barr bai yi ba ya ka ma hanyar zuwa asibitin.




A asitin kuwa, farkon abunda aka fara nema shi ne jini. Ba halin ibar jinin daddy Sobada jinin shi ya hau a wannan lokacin. Hajj jamil daddy ya kira Dan dama jinin su iri d'aya ne za kuma su iya ba ma kowa. Leda biyu aka d'iba daga jikin Hajj jamil, kuma ledan jini biyar ake da buqatar a saka wa Haajar a wannan lokacin. Barr na zuwa ya taradda halin da ake ciki. Yace shi ma zai bada jinin. Bayan an gwada shi aka ga cewar shi ma zai iya ba ma kowa jini ,aka kuma yi masa wani gwajin aka gane baya d'auke da wani cutar da ze hana d'aukar jini a jikin shi. Nan ya kwanta aka d'iba leda ukun da ake da buqata ,yayin da aka jona mata wancan na farkon nan da nan Leda biyun ta k'are. Kusan dikkan su anan suka kwana. Sai washe gari hajj jamil yace wa Hajiya ta koma gida ko Dan su suxee su tabar su anan. Ba Dan ta so ba haka Barr ya dawo da ita gida ,sannan shi kuma ya koma asibitin. Ganin da Hajj jamil ya yi na cewar akwai buqatar daddy yabar asibitin ,Dan shakka babu idan yana ganin Haajar a wannan halin babu abunda zai hana hawan jinin shi kaiwa 280. Saboda haka ya yanke shawarar yi kiran yayar shi da ke bin mishi a waya wacce ke jigawa Anty zuwaira ,da mijin ta ya rasu. Kud'in mota ya tura mata. Ba b'ata lokaci Anty zuwaira ta had'o inata-inata ta biyo hanya. Sai yamma liqis sannan ya iso. Hajj jamil da kan shi yaje ya d'auko ta a tasha ,ya wuce da ita gidan daddy wurin Hajiya ,da ma ya sanar wa Hajiya da zuwan ta. Bayan ta yi wanka ta yi sallah ta ci abinci ,ta shirya Hajj jamil ya dawo ya d'auke ta yakai ta asibitin. Ranar Anty zuwaira ce ta kwana da Haajar a asibiti. Yayin da daddy ko kad'an bai so hakan ba. Yasan ko ya tafi ba ze iya gudanar da komai ba. Abinci ma yaqi ci tun jiya. Haka dai Hajj jamil ya lallashe shi suka dawo gida. Yace wa Anty zuwaira idan akwai buqatar wani abun ta kira shi a waya. Tace masa "toh". Gaba d'aya yanayin yadda Anty zuwaira ta ga Haajar d'in ta ji abun duk ba dad'i. Yadda dai aka gaya mata ciwon kwana d'aya ne ,amma idan ka kalle ta sai ka zaci ko ta yi wata ta na jinya. Ta rame ta fed'e ta yi fari tass alamar rashin jini.




Kusan kwanan Haajar hud'u bata farka ba. Kullum kuma su daddy Suna asibitin ba sa koma wa gida dai dare. Ranar da Haajar za ta farka ,ta farka a gigice duk Wanda zai tunkaro ta sai ka je tana fad'in "kar ki zo nan,,,mai nai miki?,,,Ku taimake ni" sambatu dai iri-iri Wanda kai da ka gani ka san ba na lafiya bane. Wannan Abu ya sake d'agawa su daddy hankali. Anty zuwaira ce ta yi wa Hajiya bayani akan lallai ya kamata a maida Haajar gida ,Dan ta fuskanci wannan ciwon ba na asibiti bane ,saboda wasu zantuttuka da Haajar d'in ke sakowa cikin dare. Hajiya tace itama gaskiya a yadda taga Haajar ta farka ta lura da hakan. Ta ma fi tunanin ko shafar aljannu ce. Duk yadda aka so a fahimtar da daddy ina ya kasa fahimtar su sai ma cewa da yake yi "Ni fa matata bata wani aljannu ,saboda me za Ku d'ora mata ciwon iska? Babu abunda ya had'a ta da iska. Kawai rashin lafiya ce. Kuma ko zan k'arar da dukiyata baki d'aya sai na nemo wa matata lafiya." Ganin kamar daddy ya hau da yawa yasa kowa ya zura masa ido. Kusan kwanan Haajar ashirin da d'aya a asibiti babu wani abun ci gaba. Kullum sai ruwa da jini da ake sanya mata, idan aka sanya mata jini yau ko da za'a duba gobe za'a ga kamar ba'a sanya ba. Su kan su malaman asibitin abun yana d'aure musu kai. Ga shi daddy ya k'i sauraren kowa akan a maida Haajar gida ayi na Hausa. Daga k'arshe Hajiya da ta abun na nema ya ci tura da kanta ta sa aka rubuta wa musu takaddar sallama. Da daddy zai yi magana tace masa "Kan naji kan na gani. Wannan umurni ne ba shawara ba". Ba Dan daddy ya so ba haka ya hak'ura aka maida Haajar d'in gida. Kwanan su biyu da komawa gida sai ga Abu na Nema ya fi na da. Dan Haajar matuqar aka bar ta ba kowa a kusa da ita to fa ta fara cin na kare kenan tana nema ta fita. Abun da ya sake K'ullewa ahalin gidan kai. Kowa abun da yake kawowa a ran shi Haajar ta had'u da shafar aljannu ne. Hajj jamil ya sake kiran Dr Imam mahaifin Haajar ya shaida masa halin da ake ciki. Ba Dan ya kammala abunda ya je yi a qasar da yaje ba ,haka yabar komai ya kamo hanyar dawowa gida Nigeria saboda yadda Hajj jamil ya zayyana masa ciwon babu sauqi sai a wurin Allah. Kwanan shi biyu kafin ya iso Nigeria ,sai da ya kwana a jigawa ya d'auko duk wani maganin da zai buqata, sannan ya hawo jirgi safe zuwa sakkwato.




Hajj jamil ne ya je ya d'auko shi ya kawo shi gidan daddy. A mutunce su ka gaggaisa. Babu Wanda bai yaba da dattakon Dr. Imam ba. Mutum ne mai matuqar karamci. Sai a yanzu Hajiya ta gane inda Haajar ta yi gadon mutunci. Sai da ya huta sannan aka kai shi sashen Haajar d'in. Ba qaramin tausaya mata ya yi ba. Ba dan ya na da qarfin hali ba, babu abunda zai hana bai yi mata kuka ba ,musamman yadda soyayyar Haajar take a cikin ran shi. Kaf a 'ya'yan shi babu Wanda yafi so sama da Haajar.


Hajiya ,hajj jamil ,Anty zuwaira ne a zazaune sun zuba wa sarautar Allah ido.


Daddy da ke gefe kamar a jikin shi ciwon yake Dr. Yace a d'aure masa ita da igiya. Kowa ya shiga zaro ido. Hajj jamil yace "Abbu Yusuf mai yasa ba za'a rik'e ta ba sai an d'aure ta?" Murmushi Dr. Iman ya yi tare da cewa "wannan aikin ba na mutum bane Jamilu. Kai dai Ku d'aure ta. Daddy ko motsi bai yi daga inda yake ba ,saboda tsabar tausayin Matar shi da yake ji. Ba Dan ma mahaifin ta bane shakka babu bazai bari a maida masa da mata kamar mahaukaciya ba. Da taimkon Dr. Imam hajj jamil ya samu nasarar d'aure Haajar d'in ,shi ma sai da ya zuba mata wani ruwan magani akai sannan. Sai wani zaro ido take yi tana fad'in " Kai kuma waye? Ka sake ni nace. Ba zaka sake ni ba? Sai na kashe ka mutumin banza". Sai kuma ta fashe da kuka tace "Me nayi miki? Kar ki kashe ni" can sai ka ji ta fashe da wani irin ihu Mara dad'in sauti...




Karatun qurni Dr. Imam ya fara yi na Neman yaddar Allah kan aikin da ze yi. Haajar sai wani dariya ta ke yi tana zage-zage. Wani kundi Dr. Imam ya d'auko ya bud'e. Haajar na ganin shi ta fara ihu tana kururuwa. Duk Wanda ke wurin sai da ya zubar mata da hawaye. Wani magani Dr. Imam ya je ya bud'e bakin ta ya zuba mata. Sannan ya doki tsakiyar kan ta da qarfi tare da take qafar ta na hagu. Shak'e mata wuya ya yi a lokaci d'aya yana ci gaba da karanto alqur'ani. Shak'ar da Ya yiwa Haajar kowa sai da ya d'auka mutuwa za ta yi a yadda take kakari. Zuwa can sai ga shi tayi wani irin amai baqiqirin na sare saren zare. Kundin nan Dr. Imam ya ajiye a gaban ta ,ya danna yatsanta a ciki. Nan da nan hannun ya kama da wuta. Wani haske ne ya mamaye inda Haajar d'in ke tsaye. Can sai ga Haajar ta fad'i a gefe ga kuma wata siffa mai kama da Kubra sak an fitar a gefe. Duk Wanda ke wurin sai da ya girgiza. Nan Dr. Imam ya shiga yi wa wannan sifa tambayoyi ita kuma tana bashi amsa cikin wani yare Mara dad'in saurare da ba Wanda ke iya gane mai take cewa sai shi kad'ai. Hannun ta d'aya ya dad'a dannawa a cikin kundin, tana ihu tana qarawa a haka dai da jikin ta ya k'one gaba d'aya, daga k'arshe sai ga wani haske na bartsi. Daga nan ta watse. Dr. Imam ya yi hamdala tare da komawa ya zauna. Wani magani ya had'a San nan ya dawo kan Haajar da ke kwance kamar gawa. Tsakiyar kanta ya bud'e ya zuba wani magani na gari sannan ya fara yi mata yayyafi da wani ruwan magani da ke cikin kwalba fari. Ya dad'e a zaune kusa da ita yana karanto mata ayoyin waraka daga ubangiji. Kusan mintuna ashirin sai ga Haajar ta mik'e kamar ba ita ba tare da yin salati. Mamaki tayi yadda taga an tattaru akan ta. Ga mahaifin ta zaune kusa da ita. Tace "Me ke faruwa ne? Dan Allah Ku gaya mun"




Ruwan zamzam da aka yi wa addu'o'in shifa mahaifin ta ya d'auka ya bata. Da ido ta ni shi alamar mai zata yi da shi yace "ki karb'a ki sha" ba musu ta karb'a ta shanye tas.. Sannan yace a bata d'ankwali ta d'aura a kanta.




Wani zufa ne ya shiga tsatsafo wa Haajar ta ko ina ,sharkaf ta yi kamar wacce aka tsamo da teku. Nan Dr. Imam ya ce a kunna mata na'urar sanyi Wanda kafin ya fara aiki ya ce a kashe. Hajiya da kanta ta tashi ta kunna panka da kuma na'urar sanyi ,nan da nan iska da sanyi ya karad'e ko ina a parlourn. Sai wani ajiyar zuciya Haajar d'in ke saukewa kamar wacce tayi gudun tsere. Shima Dr. Imam ajiyar zuciyar ya sauke tare da zaro k'yallen goge zufa ya goge zufan fuskar shi ,sannan ya soma

Please Login or Register in order to submit comment