Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

d'aya, duk Wanda ta gani da wannan alamar seda ta tsame shi, sannan ta maida masa sauran ta Jere su tsaf ,komai ta nema masa mazaunin sa na musamman, hatta filon kwanciya da Khaltum ta kawo guda d'aya na mugun abun ta seda Haajar ta sauya wani,,,, seda ta fara turara 'ya'yan Habbatussauda ,sannan ta bishi da turaren wuta me masifar k'amshi, kan kace me wuri ya zagaye da wani daddad'an k'amshi, Wanda kafin ka iya gano ainahin wani irin turare ne ,sedai idan dama ka sama tu'ammali da kayan k'amshi ne kad'ai. Ko ina k'amshi ke tashi ,tun daga dosowa farkon shiva sashen ,parlou ne ,duka d'akuna ukun dake zagaye da parloun da ban d'akin su ,hatta kayan Daddy idan ka bud'e sip din k'amshin turaren kaga na maza ne zaka ji yana bugar k'ofofin hancin ka. Seda ta tabbata an gyara komai ,sannan ta ciro m-card d'in wayar ta ,tayi placing a manyan na'aurar sautin dake parloun, cikin sakan talatin tayi setting d'in komai ,se ga k'ira'ar AHAMD SULEIMAN na tashi a karo na farko a sashen Daddy._


_Gaba d'aya yaran jin su suke kamar a wata sabuwar duniyar daban sab'anin Wanda suke ciki a yanzu. Da daddare tare suka shiga kitchen ,girke-girke sukayi sosai ,sedai babu na Daddy a ciki ,daban Haajar tayi masa nasa saboda rashin lafiyar hawan jinin shi._


_A karo na farko da masu aikin gidan suka ci abincin gidan ,Dan gaba d'aya Haajar seda ta aika musu da abincin data girka had'i da abun sha me sanyi. Ranar kowa ya tabbatar da Haajar tazo GIDAN MISBAHU, Dan alama na sauyin nayi daya kai wa ahalin gidan ziyara._


_Da daddare bayan daddy ya dawo yaga abubuwan ban mamaki ,gaba d'aya gidan se yake gani kamar ba gidan daya Sani ba ,Dan tun daga gate masu gadi suka fara cewa Daddy sun ga abun alkhairi ,a taya su yiwa Hajiya Godia, duk da be San wata Hajiya suke nufi ba da kuma alkhairin da suke magana tayi musu ,tunani ya fara yi ,ko su kubra sun dawo ne? Wata zuciyar tace masa "Alkhairi daga wajen su kubra anya Abu ne me matuqar wahalar gaske"... Da wannan tunani-tunanin daddy ya k'arasa ciki...






Shi dai daddy da ido ya dinga bin su ,be kashe k'wark'watan idon shiba ,se da ya doshi sashen shi ,wani irin masihircin k'amshi me sanya nutsuwa ya daki madaidaitan k'ofar hancin shi ,bin ko ina yake da kallo kamar yau ne rana ta farko daya fara shigowa sashen nashi. Zama yayi kan kujera mazaunin mutum d'aya, tare da jinginar da kanshi had'ida lumshe matsakaitan idanuwan shi ,a lokaci d'aya kuma yana k'ara shak'ar daddad'an k'amshin dake ambiya a parloun, ya jima a haka ,kafin ya shiga d'aki Dan rage kayan jikin shi ,nan ma kusan idanuwan shi zazzago ne basu yi ,Dan ganin abun mamaki. Daya shiga toilet Dan watsa ruwa kusan mintunan shi sama da talatin ya kasa fitowa ,ji yake kamar ya kwana a ciki, Hamdala ya sake yiwa ubangiji daya kawo masa sauyi a rayuwar shi cikin d'an k'ank'anin lokaci, ji yake ina ma ace Haajar matar shice ,gaskiya da se yafi kowa sa'ar mata, amma ta ina ma hakan ze yiwu? Wata zuciyar kuma tace masa ,ka fiye zak'ewa MISBAHU, daga ganin sarkin fawa se miya tayi zak'i?,,,,da sauri ya kauda wannan tunanin ,seda yayi sallah kafin ya fito parlour.


A zazzaune ya tarar dasu Haajar kan kujeran dinning da alama shi suke jira suci abinci,,,, dikkan su sannu da zuwa suka masa fuskokin su d'auke da farin ciki ,shima ya amsa fuske a sake ,bayan ya zauna ya ke tuna rabon da yaga yaran shi cikin irin wannan farin cikin har ya manta. Amma se gashi rana d'aya, kusan har k'ok'arin manta wa da duk wani damuwar su suke yi ,ina ma ace farin ciki da walwala ze d'ore mana kamar haka,,, Daddy ya furta cikin ran shi... Dramar da ake yi wajen cin abincin ne ya dawo masa da hankalin sa.


Cike da shagwab'a da samun wuri Auta tace "Ni fa Anty Haajar ni zaki fara zuba mawa"


Wani siririn tsaki Haseena taja ,tare da cewa "kinga Anty Haajar Dan Allah ni ki fara zuba mun ,wallahi baki ji wani irin azababben yunwa da nake ji ba yau ,wannan irin aikin da muka tik'a da biyana za'ayi ai nasan kud'in da za'a bani yaci ya siya mun gida da mota har da 'yan chicken change"...


Gaba d'aya wajen kowa dariya yake yi har Daddy, Haajar tace " Ayyo! To dama an gaya miki komai a banza ake samun shi? Ai komai na rayuwa da kike ganin shi dole seka wahala tukunna kake samun abunda kake so Haseena ,wannan kad'ai ma ya ishe ki darasi"


"Aikam dai" Haseena ta fad'a tana jinjina kai.


Auta aka fara zuba wa ,tana fad'in "yeeh Yaya haseena ni aka fara zuba mawa" ta k'arasa maganan tana mata gwalo. Kowa se dariya yake mata ,banda Haseena data cika tayi fam Dan kwatakwata ita ba tada hak'uri ne.


Seda ta gama serving d'in kowa sannan ,taji da Daddy da ke cewa "Ai na d'auka 'ya'yan ki kad'ai kika sani ,saura kad'an Gidan Abinci yayi bak'o." Dariya dikkan su suka saka, seda daddy ya saki zancen sannan yama fara wai me nace ma? cewa fa nayi 'ya'yan ta ,kar yarinyar nan ta gano wani Abu a tattare dani fa, gaskiya ba k'aramar kwab'a nayi ba. Seda ya kalli kowa yaga hankalin sa baya kan shi ,kamar ma basu ji meya fad'a sosai ba da farko. Wani ajiyan zuciya ya sauke ,tare da furta Alhmdllh' a k'asan zuciyar shi, Dan shi Daddy Gaba d'aya ganin Haajar yake kamar matar shi ,musamman yadda suka zauna haka ,se yake ayyana inama ita kad'ai ce matar shi kuma uwar yaran shi ,lallai da yafi ko wani namiji alfahari da samun nagartacciyar iyali... Murmushi kawai yayi sannan yayi bismillah tare da kai abinci bakin shi.


Duk wani motsin da yake be San a idon Haajar yake yin sa ba ,kawai dai ta share ne tayi kamar hankalin ta bata wajen shi.


Cikin k'ank'anin lokaci daddy ya kauda abincin dake plate d'in shi ,dama ba wani da yawa ta zuba masa ba, ganin yana k'ok'arin bud'e kula ya k'ara ,Haajar tayi saurin taron hanzarin shi da cewa

"Bari in k'ara maka ,murmushin jin dad'i yayi ,tare da cewa


" Nagode? "


Wani kulan daban Haajar ta bud'e ta zuba masa abincin dake ciki. Nan danan Daddy ya fara auna shi ciki,,,, sedai dak'yar ya k'arasa had'iye abincin bakin shi ,wani irin kallon menene wannan? Yake bin Haajar d'in dashi. Gira ta d'aga mai alamar akwai matsala ne?


Daddy yace "Anya wannan abinci na ne kuwa?"


"Me ka gani?" Haajar ta tambaya kamar bata San komai ba


Yace "Naji abincin ne ba kamar irin Wanda na gama ci ba, kamar ma fa ba'asa gishiri ba ,ko me agwagi ne ake kiran sama na kasa ganewa!"


Dariya dikkan su suka fashe dashi, haseena tace "Daddy me zabo ake cewa ,ba me agwagi ba".


" komai dai menene Ku kuka San shi ,nida ba shiga kitchen nake ba ,taya zan wani San sunayen maggi?"


Haajar ajiye cokalin hannun ta tayi ,tare da nad'e hannaye a k'irji tace "Wannan abincin daga yau irin shi zaka dinga ci ,saboda tsaro"


Daddy wani zaro iro ya shiga yi tare da cewa " ni d'in kuma? Wai saboda me?"


Haajar tace "ka manta masu rashin lafiyar hawan jini abincin su daban ne? To abincin ka kenan har se an gwada ka an tabbatar mana da baka tare wannan ciwon kuma, idan ka bani had'in kai ,wata d'aya yayi yawa kaga komai ya wuce ,ka fara cin abinci kamar namu?"


Shiru Daddy yayi ,har cikin zuciyar shi yayi matuqar jin dad'in yadda Haajar take nuna damuwa da ciwon shi ,Dan shi yanzu har manta wa yake wai yana da hawan jini. Murmushin k'asan zuci yayi , a fili kuma ,had'e girar sama Dana k'asa yayi ,tare da cewa

"Ba wani wata d'aya da zanyi ina cin wannan abincin gaskiya ,kuma bari ki gani"


Basarwa Haajar tayi tare da cewa "OK fine".


Auta ce tace " Anty Haajar nima a k'ara mun, amma ba irin na Daddy ba.


"Oh no my baby girl! Ai bama zaki ci irin na Daddy ba , bari in k'ara miki kinji"


Dariya sosai Auta ke yi , da gudu ta zagaye ta kujeran da daddy ke zaune ta rad'a masa a kunne "Daddy kaga na sake yiwa Anty Haajar wayo ko? Kamar yadda na mata wayo tazo gidan mu. Kaima ka dinga mata mayo irin nawa"


Kusan dariya maganar Autan yaso yaba Daddy, shima rad'a ya mata kamar yadda tayi masa yace "Kice dama wayo kika mata ta biyo ki? To amma me kika ce mata?"


With full confidence Auta tace "daddy ce mata nayi fa idan bata zo gidan muba ,kuka zan dinga yi kuma bazan sake zuwa makaranta ba, to shine ita kuma bata so inyi kuka kuma bata so in dena zuwa makaranta ,shine fa ta biyo mu"..


Dariyar abun Daddy ya dinga yi ,tare da cewa " give me 5" bashi hannu Auta tayi suka kashe ,yace "Good girl ,u make it,,, maza je kici abincin ki kar Antyn ki ta gano kin gaya mun wayon da kika mata"...


Da sauri Auta ta koma kujeran ta ta zauna tana dariya. Haseena tasowa tayi tazo wuce wa tace " Daddy inji abincin ka" wani irin Harara ya watsa mata ,daya sa tayi saurin rufe bakin ta tabar wurin tana dariya. Kallon Haajar yayi data gimtse dariyar ta yace


"Kinga abunda kika janyo mun ko?" Tashi tayi itama tabar wurin tana masa dariya ,ba tare da ta amsa shiba. Parlour suka dawo suka zauna suna kallo cike da raha ,har kusan sha biyu na dare kafin suka koma sashen Kubra...








*____________________________*








Garin kano,,,, a kwana a tashi bikin Daddy da lubabutu ya rage saura sati biyu currrr! Shi Daddy Sam yama manta da zancen wani biki...




















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/30, 1:42 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA BIYAR_


*___________________________*


































_Hajiyar Daddy tayi iya bakin k'ok'arin ta wajen ganin ta binciko halayen Lubabatu Dana iyayen ta ,amma duk Wanda tasa binciken amsar guda d'aya ce ,cewar su d'in Mutanen kirki ne ,sedai lubabatun bazawara ce ta tab'a aure ,shekaran su biyu Allah ya yiwa mijin rasuwa. Wannan shine kad'ai abunda ta iya gano wa ,gashi tayi binciken yafi sau a k'irga amma bayan yabon lubabatu da iyayen ta ba abunda ke zuwa kunnen ta. Ita dai Hajiya hankalin ta be kwanta da hakan ba ,amma ba yadda ta iya dole ta koyarwa zuciyar ta natsuwa da kuma son wannan auren ,Dan sau tari ma idan ta zauna se tayi ta tunanin anya badan bata son auren bane yasa take kawo shakku da kokonto, wata zuciyar kuma tace mata ,duk wani abunda ze fito indai ta b'angaren Hajiya Gwaggo ne to babu alkhairi a cikin sa ,daga k'arshe dai wani sashen zuciyar nata yake ayyana mata cewar 'suwaiba ba yadda zaki yi kuma ba kida abun yi ,daya wuce ki mik'awa Allah wannan al-amarin sannan kuma ki dage da Addu'a tare da nema wa MISBAHU zab'in Allah da alkhairi a cikin wannan auren ,ki kuma ci Gaba da saka mishi albarka ,saboda Addu'ar uwa mace tamkar taki ne tsiro take. Wannan shine kad'ai mafita a wajen ki'... Wani ajiyan zuciya Hajiya ta sauke tare da furta "Allah ya maka jagoranchi acikin al-amurran ka MISBAHU... Wani iska ta furzar tare da tashi taci gaba da ayyukan ta nayau da kullum..._


_Hajiya Gwaggo duk yadda taso ayi cakwaikwaiwa a wannan bikin ya faskara ,saboda lubabatu ta hana ,a cewar ta ita batason bidi'a ,bayan walima babu abunda za'ayi shima se idan an d'aure aure ,yinin biki ma bayi zatayi ba ,saboda bata son duk wani abunda ze tab'arb'are albarkar auren ta ,riya da bidi'a kuma na d'aya daga cikin rukuni na farko dake hana albarkan aure. Badan Hajiya Gwaggo taso ba amma haka ta hak'ura Dan Dole ,Dan gaba d'aya se ma fara jin haushin Lubabatun tayi, a haka dai biki keta k'aratowa ,babu wani alama daga b'angarorin guda biyu da zaka gane cewa hidimar aure ake yi ,aure ne dai gashi nan yadda kasan ma auren na dole ne ,Dan komai a kaffa-kaffa da nuk'u-nuk'u ake yin shi ,ba kowa ne yasan da zancen sha'anin ba ,se na jikin su..._




*______________________*


Ranar asabar ,ya kamata daddy na gida yinin ranar be lek'a koda k'ofar gida ba ,tun bayan daya dawo sallar asuba ,Dan kusan yanzu jam'i baya wucewa shi ,saboda akwai agogo me tunatar dashi koda ya shafa'a wato Haajar.


Bayan ya dawo sallar azahar ,Gaba d'aya dashi dasu Haajar suka d'unguma zuwa gidan gonar shi ,dake ta bayan gidan shi ,Wanda akwai gate da za'a iya shiga kai tsaye ta cikin gidan shi ,tsabar tsafta da kula da wurin ke samu ba dare ba rana yasa idan ba ance maka da akwai gidan gona a wajen ba ,Abu ne me matuqar wuya ga iya ganewa sab'anin sauran gidan gonakin ,sedai d'an abunda ba'a rasa ba na yanayin dabbobi.


Tun daga bakin gate Ma'aikatan wurin keta murna da zuwan daddy, duk Wanda ya gansu da sauri yake k'arasowa yana kwasar gaisuwa da mamakin ganin daddy a wannan lokacin ,bayan lokaci me tsawo daya d'auka baya kawowa wurin ziyara ,yau kuma se gashi.


Sannu a hankali suka shiga zaga wajen suna d'an tab'a hirar yadda abubuwa suka k'ara bunk'asa a wajen , nau'i-nau'i na dabbobi indai naci ne a gida gasu nan barkatai ,kusan cikin wurin ma gaba d'aya ya yiwa wasu dabbobin kad'an dole seda aka killace wasu daga waje.


A cikin hirar da suke yi ne jifa-jifa ,Haajar ke cewa " Ni kuwa Daddy wai kana fitar da zakkah kuwa?"


Dariya maganar taba wa daddy, maimaitawa yayi "wai ma ina fitar da zakkah? To amma me kika gani?"


Itama dariya taba kanta tace "Ah to eh mana, naga gidan gonar nan cike yake da albarkatun dabbobi ,amma banga alamar ana fitar da d'aya daga ciki ba ,Banga kuma alamar ana saida wa ba. Sannan ni a ganina iya wannan ma zaka iya fitar da zakka dashi ba ,ba Dole saka d'iba wani b'angare daga cikin dukiyar kaba".


Daddy rage fara'ar dake fuskar ki yayi ,tare da cewa " A gaskiya Antyn Auta(haka yake kiran ta tun had'uwar su a gidan Hajj Jamil) bazan iya ce miki wani Abu dangane da gidan gonar nan ba, ke ni hasalima bansan komai dake gudana a gidan ba, maganar zakka ko makamancin wannan gaskiya bana yi ,ba kuma bana son yi bane ,duk lokacin dana k'udurci yin wani abun alkhairin wallahil azim se inji na kasa ,ban kuma San dalili ba ,kinga naman miya ma na gida siyan shi nake yi ,ina da me nama dake kawo mun duk wata."


Tsabar mamaki ne ya hana Haajar magana ,tace "to idan ba zaka damu ba ,inaso inyi wani Abu akai ,Amma kafin nan muje mu gana da manajan dake kula da komai na wajen".


Murmushi daddy yayi ,Dan shi harga Allah yana son Haajar a cikin al-amurran shi ,Dan hakan ba k'aramin ci gaba dake kawo masa ba. Ce mata yayi " Karki damu Antyn Auta ,na riga na miki izini da komai nawa tun ba yau ba"


"Nagode sosai" Haajar ta fad'a cike dajin dad'i


"Kar ki damu ,cancantar kice tasa hakan ,ai kinfi k'arfin hakan a waje na ,kana da kamar Wanda yaso naka ne?"


Murmushi Haajar tayi tare da cewa "Babu"


Yace "to kin gani ,Wanda yaso naka ,tamkar kai d'in yaso kacokam ,koba haka bane?" Daddy ya fad'a cike da raha


Ita dai Haajar se faman murmushi take yi tace "Hakane kam"


A haka dai suka suka k'arasa ciki wajen manager ,suna d'an tab'a hirar su na MAKAHON SO DA LINZAMI... Yayin da su suxee kuma suka tafi nasu yin a cikin gidan gonar...






Da fara'a sosai maganer ya tarbe su ,wurin zama ya basu tare da d'auko musu abun sha ,Godia Haajar tayi masa dukda basu sha ba ,kafin ta fara masa tambayoyi akan yadda suke gudanar da aikin gidan gonar. A yadda manager ya sheda mata ,Komai na tafiya yadda ya kamata daga b'angaren su ,ana kuma samun ci gaba sosai ,ribar da ake samu kuma yana tafiya ne kai tsaye ta asusun bankin Kubra uwar gidan daddy. Mamaki ne sosai ya narkar da zuciyar Haajar lokacin da manager ya ambato adadin kimanin kud'ad'en dake shiga asusun bankin kubra a matsayin riba ,Wanda ya tabbatar musu da cewar, ba a cikin wa'yannan kud'in suke biyan ma'aikatan wajen ba ,ba kuma a ciki suke siyan duk wani abun da dabbobin ke buk'ata ba. Shidai Daddy nashi ido ne ,dukda shima ba kad'an ba ya shiga mamaki ,sedai ba yada wani abun da ze iyayi akai, a karo ba farko daya fara jin Kubra ba k'aramin yaudarar shi take ba ,Wanda ya k'ara tabbatar masa da cewar bata qaunar ci gaban shi a rayuwa. Haajar ce ta katse masa tunani data fara cewa


"Duk naji bayanan ka manager na kuma fahimta, sedai za'a kawo wasu 'yan sauye-sauye Wanda ina fatar zamu samu had'in kan ka"


"Insha Allahu ranki ya dad'e" cewar Manager


Murmushi Haajar tayi tare da cewa "ze fi kyau ka kirani da Haajar shine sunana"


Shima manager murmushi yayi tare da cewa "Ayi mun afuwa Hajiya Haajar"


Ita ma dai murmushin ta sake yi masa ,sedai bata k'ara bi takan wannan jayayyar ba ,ta fara masa bayani kai tsaye akan hasashen zuciyar ta.


"Amma kafin kaji sababbin tsare-tsaren da zamu kawo ,zan so sanin nawa ne albashin ma'aikatan gidan gonar nan Gaba d'aya" Haajar ta fad'a tare da maida hankalin ta kacokam wurin manager Dan jin bayanin sa dalla-dalla.


A nutse manager ya fara mata bayani "Eh to, ma'aikatan namu dai sun kasu kashi uku ne: akwai k'ananan ma'aikata masu share share ,akwai masu kula da b'angaren abincin dabbobi akwai kuma masu kula da fannen cinikayya nayau da kullum. kamar dai k'ananan ma'aikatan mu nuna biyan su naira dubu ashirin da uku duk wata ,,, kashi na biyu kuma muna biyan su naira dubu talatin ,se mu kuma kamar ni misali ina d'aukar naira dubu Hamsin da biyu a wata... Kinji yadda lissafin yake"


Wani siririn ajiyan zuciya Haajar ta sauke tare da cewa "Naji naka, nima kuma ina son ka saurari nawa kaji dakyau ,bana so a samu wani tangard'a. Abu na farko ,inaso a datse ribar da ake samu daga shiga asusun madam ,kai tsaye kud'in su dinga shiga asusun ajiyar Alhaji MISBAHU... Na biyu; zaku samu k'arin albashi bisa ga la'akari Dana yi na cewa aikin Ku yafi kud'in da ake biyan Ku ,wannan Abu ne me kyau kuma,,, daga yau ma'aikatan mu kashi na d'aya ,zan fara taKu kenan, albashin Ku ya tashi daga hamsin da biyu ,ya koma saba'in da biyu,,, kashi na biyu kuma daga naira dubu talatin zasu dawo suna d'aukar naira dubu Arba'in da biyar,,,, se kashi na uku masu d'aukar naira dubu ashirin da ukku zasu dinga d'aukan naira dubu talatin da biyar insha Allahu zamu fara daga watannan me kamawa"


Wani irin wage baki manager keyi kamar Wanda akayi wa albishiri da aljannah, zama ya gyara sosai Dan jin sauran bayanan.


Haajar ta d'ora da cewa " bayan wannan kuma ,duk watan Allah ,a dinga ibar kaji na gida Dana turawa ,a raba guda biyar tun daga farkon layin nan har k'arshe bance a cire kowa ba daga gida me gate har Mara gate , a kuma tabbatar da angyara kafin a raba musu ,Dan muradin mu shine sanya nishad'i a zukatan bayin Allah ,,,, sannan kuma ban cire kuba ,duk watan Allan nan idan ya kama ,duk ma'aikatan dake gidan gonar nan ,babba da yaro a basa kaji biyar. Abu na kusa dana k'arshe shine a bud'e gate d'in can na baya ,a kuma buga poster na tallata Nau'ikan dabbobin da muke dasu a gidan gonar nan ,ga duk me buk'ata k'ofa a bud'e take ,ze iya zuwa ya siya ,sannan adadin cinikin da mutum ya muku akwai percentage na bonus da zaku bashi ,Wanda idan na gama tsara komai zan aiko muku ,koma inzo da kaina. Se Abu na k'arshe ,duk bayan sati biyu a dinga aikawa da kaji da kuma naman rago cikin gida. Idan ana da buk'atar wani abun bayan wannan zan yi maka magana... Amma Dan Allah manager ayi k'ok'arin wajen kiyaye wannan yanzu ,idan wani abun ya sake tasowa za'a sanar dakai.."




Godia sosai manager ya dinga yiwa Haajar kamar ze kama k'afar ta Dan tsabar murna ,sama se kusan tunda aka kafa gidan gonar nan dashi aka fara ,amma wannan shine karo na farko daya tab'a samun promotion. Wasu takaddu yaba daddy yasa hannu ,kafin ya musu rakiya ,har waje... Ranar kusan duk ma'aikatan gidan gonar da farin ciki suka kwana na abun alkhairin da Haajar tayi musu... Manager be kawo komai a ransa ba ganin Haajar ta kawo sauyi a gidan gonar lokaci d'aya, musamman daya ganta tare da mamallakin wurin wato daddy, da farko ya d'auka ko lawyer ce saboda yadda take magana da cikakken yak'ini ba tsoro, amma kuma daga bisani yanayin yadda take bada umurni kai tsaye ga Daddy a zaune be hana ba yasa yayi tunanin ko matar Daddy ce, Dan bayan sun fito yake yiwa daddy Allah ya sanya alkhairi, shidai daddy amsa shi kurum yayi ba Dan yasa me yake nufi ba...


Shi karan kanshi Daddy gaba d'aya ya rasa Wani irin farin ciki yake ciki ,Dan babu abunda Haajar tayi guda d'aya Wanda be burge shiba ,kai komai ma tayi burge shi take yi ,musamman yadda cikin d'an k'ank'anin lokaci take ta k'ok'arin kawo wa al-amurran shi canji ,kuma ALHAMDULILLAHI yana ganin nasarori daci gaba...






















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/1, 2:26 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*






*ASSALAMU ALAIKUM. INA TAYA MASOYANA DA D'AUKACIN AL-UMMAR MUSULMAI BAKI D'AYA MURNAR ZAGAYOWAR BABBAR SALLAH, DA FATAR MUN YI SALLAH LAFIYA, ALLAH YA MAIMAITA MANA AMEEN...*


_BABI NA ASHIRIN DA SHIDA_


*___________________________*
























_Babu yadda Hajiya Gwaggo bata yi da daddy ba akan yazo d'aurin aure, amma shi Sam wannan auren baya gaban shi ,hasalima baya wani ji a jikin shi wai shi za'a d'aura wa aure. Ana gobe za'a d'aura auren ,suna zaune a parloun shi ,shida su Haajar ,yake sanar dasu zancen auren. Ba Haajar ba hatta su suxee jin Abu sukayi kamar saukar aradu. Had'a baki sukayi wajen cewa "Aure kuma Daddy?"..._


_Daddy yace " ni kaina ba'a son raina za'a yi wannan auren ba ,sedai muna fatar Allah yasa zuwan ta ya zame mana alkhairi. "_


Tab'e baki Haseena tayi tare da cewa " Wallahi daddy ni na gaji da wannan auren da ke nema maka ,kai me ze hana ka nema da kan ka ,toma da kake maganar Allah yasa zuwan ta ya zame mana alkhairi ,ni fa gani nake duk wacce zata zo koda da alkhairin ne baza ta kai mana kamar Anty Haajar ba ,mu Allah ma da ba'a wani

Please Login or Register in order to submit comment