Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

taso ba ,Dan kuwa kamar yadda ko inada rai ko bana Raye Hajj Jamil nada ikon rik'e 'ya'yana ,to haka nima nake da iko akan nashi 'ya'yan. Idan kuma baka sani ba yau zan gaya miki ,ita d'in wata rashe ce daga cikin rassan gida na ,kuma bango ce daga jikin katangar gida na ,saboda haka ki iya bakin ki akanta ,ki kuma sake takun ki. So nawa kina bijiromun da batu akan ta ina share wa ,har takai ta kawo yau seda kika kaini qul, to kinji Ina fatar kuma zaki kiyaye..." Daddy na gama fad'a mata haka ya tashi ya fice._


_Lubabatu dake nan gumi na tsats-tsafo mata tace "Ni nasani ,nasan za'azo wajen, nasan tunda nake ta yawan mugayen mafarkai akan ta dole d'in ita wata ce amma ba zata zama 'yarka ta cikin kaba. Kuma nayi nayi tabar gidan nan amma kak'i ,k'arshe ma duk lokacin dazan maka magana akan ta se rigima ya had'a mu. To lallai MISBAHU ka d'ebo ruwan dafa kanka ,naso mu zauna lafiya amma tunda kace babban maqiyinka kenan lafiyar yanzu zan fito maka da ainahin wacece ni ,zaka San wacece lubabatu Dan iya dad'i ne kasani baka San d'aci na ba ,gaba na kake gani ba baya na ba, yau zaka tabbatar da sahun giwa ya taka na rak'umi..."_




Tana gama fad'ar hakan ta tashi daga kan gadon ,wayar ta ta nemo tare da Dan nawa D'AN QANI kira... Bugu d'aya biyu ya d'auka " Ka same ni yanzu yanzu a gida " shine kawai abunda naji lubabatu ta fad'a tare da yanke kiran...






Safa da marwa ta shiga yi a tsakar parloun, takai ta kawo tare cije hannu biyu shine kad'ai aikin da take yi. Ba ita taji sanyin rai ba har seda D'AN QANI ya kira ta ya sheda mata gashi nan ya iso ,tace ya shigo ya same ta a parlou. Ajiye wayar tayi ta fad'a wanka.


Ruwa ta sakar wa kanta daga sama har k'asa. Koda ta fito a bakin gado taga daddy yana duba wasu takaddu. A zato na ko zata firgita na shigo wada daddy wani datayi har cikin gida duk da bansan ko waye ba ,sedai bansan lubabatu ba ,a mamaki na k'arasawa tayi ta zauna tare da kauda kan ta gefe. Daddy ne yace "haba yanzu tsakani da Allah kinsan yaron nan BASHAR yazo shine kika barshi a zaune shi kad'ai ,ai da se ki bari ki bashi ko abun sha ne kafin ki shiga wanka."


"Naji"... Shine iya amsar da lubabatu taba daddy tare da zura doguwar rigar ta tabar masa d'akin. Daddy ko a jikin shi Dan inda sabo yaci ace ya saba da halin mata ,be k'ara bi ta kanta ba ,ya d'auki takaddun daze d'auka ya fice abun shi...




Maganganu sosai Lubabatu ta tattauna da Wanda daddy kira da BASHAR ,sun kusa awa uku suna magana kafin daga baya ta rako sa suka fito haraba ze tafi...




A lokacin da lubabatu suka fito ,su Haajar na garden dama fakon ta suke yi Dan akwai abunda zasu yi...




Haseena ce tace " shi kuma wancan waye? Dan ni kwatakwata gayen be mun ba, sannan wannan shine gani na uku Dana masa a gidan nan suna fitowa tare da waccan matar ,ranar ma tare da daddy suka fito su uku har kud'i naga ya bashi"...


Suxee tace "gaskiya bansan shiba ,Dan ni yau na fara ganin sa ,dukda nima be kwanta mun ba ,amma yana da kyau mu dinga kyautatawa mutum zato"...


"Wannan haka yake" cewar Haajar ,ta fad'a dukda itama wani b'angare na zuciyar ta na sak'a mata ba dad'i game da gayen...




"Koma dai menene zan binciki me gadi game dashi idan suka fita. Ku kuje kuyi abunda zaku yi ni zan tsaya anan in kula da komai" inji haseena Dan gaba d'aya ta fisu zafin nama...




Ba musu haajar da suxee suka koma ciki da sauri ,Suxee ce ta shiga ta d'auko wani bokiti me marfi ,ta k'araso inda Haajar ke tsaye tana jiran ta. Gaba d'aya daka gan su kai kaga tafiyar marasa gaskiya ,dan kuwa Tafiya suke suna waigen bayan su ,a haka har suka k'arasa ta baya ,mahad'in tankin dake kai ruwa band'akin daddy yake.




Da sauri Haajar ta bud'e tankin tare da zura tiyo ta ciki ruwan ya dinga kwaranya cikin fulawowin sashen, manufar su shine su rage ruwan kafin su zuba ruwan maganin dake d'auke a bokiti me marfin da suka zo dashi.




Allah Allah suke ruwan ya gama raguwa ,amma ina saboda ruwan Nada d'an yawa ,dukda cewa na band'akin daddy kad'ai ne amma masu aikin kula da ruwan se sun tabbatar dasun cika tankin kafin suke kashe ruwan...






Duk dad'ewar da lubabatu tayi a waje tana magana da wannan gayen su Haajar basu samu damar kammala abunda suke ba, Dan iya kwance marfin tankin ma wani aiki ne me zaman kanshi ,dak'yar Haajar tayi nasaran kwanto shi shima da taimakon suxee...


Gashi har lubabatu ta shigo cikin gida. Tafiya take zuciyar ta na mata sak'e-sak'e iri daban daban, a haka har takai sashen daddy zata shiga...




Marfin tankin dake hannun suxee ne ya fad'o k'asa a bisa kuskure tare da gangaro wa har inda me tahowa ze iya hango shi.




Da sauri Suxee taso ta d'auko amma Haajar ta janyo ta tare da rufe mata baki ,sannan ta mata rad'a a kunne cewar tana jin alamar kamar akwai wani a wajen...




Mamaki ne ya kama lubabatu ta yadda akayi marfin tanki ya fad'o bayan a datse yake, gashi ta duba ba iska ake yi ba balle ko ace iske ne ya yaddo shi, kai iskan ma se me k'arfi ne kad'ai zeyi nasarar yaddo da wannan marfin ,Dan ba wawan d'auri aka asa ba... "Kai sedai idan wani ne a wurin" Lubabatu ta fad'a ,tare da nufar wurin cikin takun ta na k'asaita.






Har ta isa wajen ta zuk'unna zata d'auka... Wanda kuma zata iya nasarar hango su Haajar dake lab'e a bayan tankin ,duk sun sun tsorata ,fatar su shine kada Allah yaba lubabatu damar ganin su ko kuma Allah ya kawo musu wani d'aukin daga gefe ,Dan kuwa idan ta gansu wani sabon shafin dramma za'a bud'e, gashi basu zuba ruwan maganin da suke ta k'ok'arin zuba wa ba....
















_Kuyi hak'uri da wannan jikin ne nawa har yanzu be ida warware ba. Nagode sa Addu'o'inku Allah yabar zumunci_










MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/6, 7:00 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA TALATIN_


*_____________________*












Abunda ke d'auke a bokitin dasu Haajar ke d'auke dashi ruwan magani ne da Haajar ta had'a na K'AIK'AYI KOMA KAN MASHEK'IYA DA FARFATSIN MAK'ARE... Wanda keda matuqar muhimmanci ta tasiri ga duk Wanda ake tunanin akwai sihiri a jikin shi ,hassada ko Abu me kama da wannan.


Ga yadda yake;


HANYA MAFI SAUKI TA WARWARE SIHIRI KO KARYA SAMMU KO JIFA KO RUGUJE TASIRIN MAHASSADA DA MASHARRANTA DA MAQIYA
*_____________________________*




A nemi:
- Kaikayi Koma kan mashekiya
- Farfatsin Mak'era




Kaikayi Koma kan mashekiya Ciyawace ana samunta a gun yan ganye ko masu sai da ganyayyaki na magungunan gargajiya .
Farfatsin makera
Ana samunsa ne shi kuma a makera. In aka ce Farfatsin makera shine lokacin da aka saka karfe a wuta yayi Jah, Yayin da ake dukansa domin mayar dashi wani Abu toh a lokacin da ake dukansa yana fitar da wani B'awo-b'awo fari, toh Wannan sabon b'awon shine Farfatsin makera, shi Farfatsin makera ba baki bane fari ne, kuma Bashi da Karfi Sosai, kuma ba baki bane farine Kamar dalma, amma banda Farfatsin dalmar tukunyar karfe... Farfatsin makera na Asalin bakin karfe.


A hada wadannan abubuwa Guda biyu waje daya a dakesu su dawo gari, adadinsu Ya zama daya, sai a zuba a cikin wani bokiti ko roba ko mazubi me kyau, sai a zuba ruwa a ciki, sai a barshi Ya kwana, washe gari sai a tofa suratul tafiha k'afa bakwai a ciki, a dinga sha da tafin hannun dama sau uku, sai kuma a yi wanka, haka za a dinga yi na kwana uku ko kwanaki bakwai a jere ba a tsallakewa.


Wallahi duk Sharrin mutum duk hassadarsa in Ya matsa maka in kayi Wannan sha da Wankan wallahi sai Ya Koma kansa da yardar ALLAH kuma duk me son ganin bayanka wallahi saidai kai Kaga bayansa, batun Jifa ko sammu ko hassada ko kiyayya cikin lokaci Guda yake ruguzawa, sannan yana boye kurwa (spirit/Arwah) mayu baza su ga kurwarka ba bare su tab'a ka, kuma in mutum yana Cutar da kai daga ranar da kayi Wannan sha da Wankan wallahi Allah zai gwada maka shi ko ita a cikin barcinka a mafarki, in ka gani Kar kace masa/mata komai, ka godewa Allah ka cigaba da neman kariya Kawai... Wannan kenan a tak'aice ,fatar Allah ya k'ara karemu daga sharrin masu sharri...
Domin Neman k'arin bayani zaku iya tuntub'ar Mlm Abdulrashid Adam Ahmad d'an baiwa kan wannan lambar 08060606050.




Lubabatu har ta zuqunna zata d'au marfin tankin ,haseena ta k'araso a guje Wanda har seda ta bangaje lubabatu ,idan kaga yadda tayo gadon kai kace biyo ta akayi, Ba shiri lubabatu ta saki marfin ta kama hannun k'ofar parloun daddy ta shige ,dawo wa haseena tayi da gudu tace wa Haajar "Anty Haajar kiyi sauri ki zuba waccan matar ce ,kuma zata iya fitowa, cikin hanzari Haajar ta tattaka matakalan tahau ta juye ruwan maganin sannan haseena suka mik'a mata marfin tankin ta kulle ta sauko.


Da sauri suka bar wajen ,se haseena suka bari data zuk'unna wajen famfon dake gefen wajen tayi kamar tana wanke fuska... Lubabatu ce ta fito cike da tsiwa ,tana fad'in


" Ke!ke!"


Haseena tayi banza da ita. Seda lubabatu ta k'araso har inda haseenan ke wasa da ruwan famfo ta sakar mata duk a gadon baya "ke kurma ce? Baki ji ina miki magana bane?"


D'agowa haseena tayi tana mata wani kallon raini tare da cewa "dama magana kike? Ai ban d'auka dani kike ba. To da can baki San sunana bane kike ta famar wahalar da fatar bakin ki?"


A hasale lubabatu tace "Bansani ba"


Cike da tsiwa Haseena tace "da kince MISBAHU ma ai da base kin k'araso ba zan juyo ,Dan mune kad'ai 'ya'ya a _GIDAN MISBAHU_, kuma duk inda naji wannan sunan dole zan waiga inji ko lafiya saboda muhimmanci me sunan a waje na" haseena ta fad'a ko a jikin ta...








Ihu lubabatu ta mata "keeee! Karki kuskura ki kawo mun raini k'aramar Mara kunya"... Hannu ta d'aka zata kaiwa Haseena duka




Bata rufe baki ba itama haseena ta daka mata tsawo tare da nuna mata Dan yatsa alamar kashe di " Karki kuskura. Ki tsaya iya matsayin ki amma banda kaiwa kura harawar rago, Dan kuwa ba abincin ta bane. K'ashi se kare shi kuma nama se kura. Is better u mind u own business"... Tana gama fad'ar hakan taja wani siririn tsaki tare da barin waje.




Takaici ne ya taru ya tsaya wa lubabatu a wuya ,ta rasa yadda zatayi ,abubuwa sun cakud'e mata ,ga wancan yanzu kuma ga wannan. Cike da b'acin rai tama fasa komawa sashen daddy ,sashen ta ta wuce kai tsaye, Dan tsabar bak'in ciki ma ko ta kan marfin tankin bata k'ara bi ba...








Bayan haseena ta koma sashen su, ta taradda su Haajar na jiran ta. Tambayar ta sukayi ya tayi da lubabatu Dan basa so ace ta gano ,muddin ta gane an zuba wani Abu a ruwan nan to zata ma iya hana daddy yayi wanka dashi ,wannan shine fargaban Haajar. Haseena tace Ku manta da wannan na gama da matsalar ta.


Haajar tace "A'ah fa"


Suxee tace "Anty Haajar I trust haseena ,she can do more than dis"


Haseena tace "4get kawai. Akan wannan gayen, na tambayi me gadi yace wai Daddy yace ya dinga barin shi yana shigowa saboda k'anin matar shi ne, amma duk da haka ya kamata mu kula sosai ,zan kuma ci gaba da saka musu ido. Yanzu menene next?""...






Da haka dai suka ci gaba da tattaunawa akan yadda tsarin su ze kasance. Wanda a b'angaren Lubabatu ma kusan raba dare tayi tana tufka da warwara.....








MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️






[8/7, 11:58 AM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA TALATIN DA D'AYA_


*____________________________*


























_Da daddare bayan daddy ya dawo kuwa akayi sa'a yayi wanka ,ruwan maganin ya tab'a jikin shi. Tunda daddy ya shiga ruwan nan ya sauka akan shi gaba d'aya yaji kamar an zare masa lakkar jikin shi ,shi dai yasan lafiya qalau ya dawo ,amma yanzu wasu 'yan sauye sauye yake ji a jikin shi Wanda ya kasa gane ko menene ,ba zazzab'i ba balle yace ko rashin lafiya ne ,balle yunwa Dan daya fita seda ya biya ta gidan Hajj Jamil dam ya ciko masa cikin shi, to amma ya rasa me ke masa dad'i._


_Zama yayi har kusan d'aya na dare ya fara tunanin wasu abubuwan da suka wuce ,daya ga dai wannan baze fish she shiba haka ya tashi ya d'auro alwala ya gabatar da sallan lafila ,yayi addu'o'i sosai akan Allah ya shiga lamarin gidan shi ya kuma kawo masa sauyi na alkhairi cikin gaggawa ,,,,wannan shine addu'an shi na k'arshe kafin ya Shafa yaci gaba da zama akan dadduman. Abun mamaki a karo na farko kenan da daddy ya tab'a tashi yayi sallar dare ya rok'i Allah akan sha'anin gidan shi, ba baya sallan daren ba yana yi idan buqatun shi sun taso na kasuwanci ,amma dai akan gidan shi kam kamar wannan ne na farko, be kuma San dalilin daya sa baya iya kai kukan shi ga Allah game da sha'anin gidan shiba, ya dad'e akan sallaye zaune har bacci ya soma d'aukan shi. A baccin Dave wuce mintuna talatin ba yayi wani rikitaccen mafarki daya kasa gane shi..._


Farkawa yayi Kamar daga sama ya fara jiyo hayaniya, hankalin shi be gama natsuwa ba se jin yayi an sa key ana bud'e k'ofar parloun shi tare da banko k'ofar ,shi dai daddy gaba d'aya ya kasa koda motsi zaune yake darsashan kamar an dasa icen karas ya zuba wa sarautar Allah ido yaga waye me shigowa...






Wasu manya manyan gardawa ya gani su uku ko wanne d'auke da bindiga k'irar AK47 fuskokin su rufe da bak'in k'yalle ,ba abunda zaka iya hangowa daga fuskar su se idanuwa. Da ga suka ja daidai inda daddy ke zaune kan sallaya ,be k'arewa idanuwan shi kallo ba seda yaga wani ya shigo yana janye da mutum ,seda suka kawo daidai inda yake sannan suka je fata. Ya duba wa ze gani idan ba Haajar ba ,fuska da idanuwan nan nata sun kad'e sunyi jajir ,gata duk a d'ad'd'aure da igila kamar goro, hatta bakin ta k'yalle suka saka suka k'ulle Dan kar ta musu hayaniya,,,, kaida ka gani base ka tambaya ba kasan 'yan fashi ne kuma guma-guman ,marasa imani...




Da sauri daddy ya mik'e yana fad'in "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!!!"




Wani daga cikin su ne yayi nasarar maida shi zaune ,ta hanyar daka masa kan bindiga a kafad'a. Koma wa zaune Daddy yayi tare da sake maimaita Kalmar "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un!". Har so uku.




K'ofa suka wangale masa ya hango Suxee ,haseena da Auta duk an d'ad'd'aure su a jikin bishiyar dake kallon sashen shi ,ko wacce an rufe mata baki da k'yalle ihun su baza'a ji ba sedai gunguni...




Nan fa hankalin Daddy idan yayi dubu ya sake tashi. Lallai wannan musibar babba ce ,ya furta a cikin ran shi ,ya sake furta Allah gamu gare ka k'asa-k'asa da muryar da shi kad'ai ze iya jiyo abunda yace.




Dak'yar daddy ya iya tattaro wata nutsuwa data k'wace masa had'id'a wata jarumta Wanda shi kanshi be San yana da ita ba, idanuwan shine suka kad'e suka canza launi zuwa ja jamar Wanda aka watsawa barkono Dan tsabar tafasar da zuciyar shi ke yi. Har wani kokuwa lab'b'ansa na k'asa Dana sama keyi wajen furta


" Me kuke so?"


Babban cikin su daya wurgo Haajar ciki ,ya k'araso ya zauna kan kushin tare da d'ora k'afar shi kan gadon bayan Haajar dake kwance malala a k'asa tana shashsheka, yace cike da k'warewa kan aikin shi na ta'addanci "Saurin me kake yi? Dama kana tunanin munzo shan shayi ne ko cin gurasa? Sanin kanka ne Azziki baya kawo mu se tsiya. Daka kwantar da hankalin ma ai zamu gaya maka meke tafe damu Wanda zamu tabbatar maka daba shawarar ka muke nema ba umurni muke baka"...


Bakin daddy be mutu ba sake cewa " Ku gaya mun me kuke so ,idan kud'i ne zan Baku amma kar Ku kuskura Ku tab'a mun iyalina"..


Wani shed'anin dariya wannan d'an ta'addan ya fashe dashi ,seda ya tsagaita sannan yace "kud'i!!! Kud'i kace ko? To daga naira d'aya zuwa naira million hamsin zan iya magance maka idan kana da buqata, kud'in ka chicken change dahar kake mun barazana dasu ,ka adana su dakyau Dan nasan zasu maka amfani wajen cefanan gobe, sakarai kawai"...


Ran daddy iya b'aci ya fara kaiwa maqura Dan kuwa jikin shi har cira yake yi ,Dan ya gane wannan b'arayin ba kud'i ne ya kawo suba illa cin mutunci...




Ogan tashi yayi daga zaune ya fara zagaye su daddy dake tsakiyar su se kace wani gafiya ,yafe yake yana Jan zungureriyar bindigar shi a k'asa dake k'ara tsabar taji ado da albarusai zagaye da ita...






Yace cikin kakkausar murya "Naji ka ambaci iyalin ka ko? Wannan" ya nuna Haajar da bindiga itama iyalinka ce?"


Shiru daddy be amsa suba. Wani irin shed'anin dariya ya sake fashewa dashi kafin yace "Zan kuwa so ka tabbatar mun da haka. Ka kawo yarinya me kyau irin wannan ka aje a gidan ka da sunan holewa kana yaudaran mutane. Gata kyaky-kyawar gaske kuwa" ya k'arasa maganan tare da zuk'unna wa daidai setin fuskar Haajar yana kwashe gashin daya rufe mata ido...




Wani d'aci da takaici ne ya daki k'irjin daddy ,Wanda ya haifar masa da wani irin kishi dashi kanshi be San yana dashi ba, a hasale ya sake maimaita tambayar shi "Nace Ku gayamun me kuke so in Baku Ku fita Ku bar mun gida na"




"Kwantar da hankalin ka ,fita mubar maka gidan ka ai ya zama dole ,kar manta mu bak'i ne amma bana zana ba na tafiya ,ziyara mukan kawo saboda a gana a kuma sada zumunta. Abunda muke so d'aya ne be kai biyu ba. Da kuma zaka bamu had'in kai cikin mintuna da basu Gaza sha biyar ba zamu yi komai mu gama cikin lokaci, kaga ka taimaki kan ka ka kuma yi mana saving time ,Dan lokaci da kake gani Abu ne me matuqar amfani a rayuwar mu." Dake wa tare da sake fuska d'an ta'addan yayi kafin yaci gaba da cewa "kaga wannan kyaky-kyawar budurwan bake so kawai inga ka angon ce da ita nad'an wani lokaci ,idan kayi mun wannan ka gama mun komai ,idan kuma kak'i labari ze sauya"...




Wani irin zaro ido Haajar tayi ,tsantsar firgici da tsoro yasa bugun zuciyar ta tsananta kamar ana harba ganga ,daddy ko jin maganar yayi kamar saukar arado.




" ina baze yu ba ,idan ma turo Ku akayi to kuje Ku sanar da me shi yayi a banza ,Dan wallahil azim sedai Ku d'auki raina dadai in aikata abunda kuke so in aikata" daddy ya fad'a rai a matuqar b'ace...




Ogan 'yan fashin yace "lallai kuwa daka tafka kuskuren dahar kabar duniya ba zaka tab'a manta wa dashi ba. Kaga wa'yancan yaran naka ,ya nuna masa k'ofa ,a gaban ka zan kwanta dasu d'aya bayan d'aya kuma in saka yarana suyi kamar yadda nayi ,bayan mun gama kuma zan kashe su a gaban ba ba'a bayan kaba. Ina tunanin wannan shine Abu mafi d'aci da koda ban kashe kaba ze iya zama sanadiyyar bugawar zuciyar ka cikin sakan talatin. Saboda haka wanne ka zab'a??? Ban kuma cire maka ko wacce a cikin suba hatta 'yar k'aramar cikin su (da cewa auta) Dan k'ananan yaran ma kusan sun fi manya gishiri, kai wannan d'in ma ya nuna Haajar itama bazamu bar maka mutuncin taba warwas zamu maka haihuwar mayya akace ina d'a tace ta cinye"....






Shiru daddy yayi Dan gaba ki d'aya yanzu kam ya sare, babu abunda yake ambata a k'asan zuciyar shi se sunan Allah da Neman taimako a wajen shi. Ganin yayi shiru yasa ogan 'yan fashin cewa




" karka manta na gaya maka lokaci Abu ne mai tsada a wajen mu, saboda haka kai idan tsabar ya gagare ka ni na tsabar maka.... Ku rufe min su"... Ogan ya k'arasa fad'a tare da nufar hanyar waje alamar wajen su suxee ya nufa...




Kuka Haajar take yi tana shurin daddy akan yayi wani Abu ,amma.....


















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/8, 7:20 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA TALATIN DA BIYU_


*___________________________*






















_Har ogan 'yan fashin ya kusa fita ,Haajar ta sance d'aurin dake bakin ta tare da dakatar dashi cikin disash-shen muryar ta da baya fita sosai. Dawo wa baya yayi cikin isa da k'asaita tare da d'aga kai alamar ya akayi?_




_Haajar dake shash-shekan kuka tace "Dan Allah kuyi hak'uri Ku k'yale su kar Ku musu komai ,ze yi duk abunda kuke so yayi indai baza Ku tab'a wa'yancan yaran ba"...




Da mamaki daddy ya kafe ta da ido tare da cewa " Haajar ba kida hankali ne? Ba kiji abunda yake so na aikata miki bane? Fyad'e fa yace ko bakiji bane?"


Wasu hawayen bak'in ciki ne da takaici ya shiga reto a fuskar Haajar wani na bin wani ,k'ok'arin share hawayen ta tayi tace "Daddy naji sosai ,naji abunda suke so ka aikata mun. Amma kai ma baka ji abunda suka fad'a bane akan cewa lallai idan bakayi hakan ba zasu lalata rayuwar su Haseena? Me wa'yannan yaran suka sani? Me suka yi dahar suka cancanci irin wannan d'anyen aika-aikar? Saboda haka bazan iya jure kallon su a irin wani yanayi me kama da wannan ba balle kwatankwacin sa ,na yadda na bada kaina fansa akan su."




Wani irin rufe ido Daddy yayi yana jin wani d'aci a ranshi, a lokaci guda kuma son Haajar ya k'ara ratsa kowani sassa da jijiyoyi na jikin shi. Kafin yayi magana yaji ogan 'yan fashin nan na tafi, tare da cewa


"Good! Kin kyauta sosai. Saboda haka na Baku minti goma. Idan mintuna goman nan suka cika ba kuyi kamar yadda nace ba ,to lallai Ku shirya haihuwar wasu 'ya'yan amma ba wa'yancan na waje ba..." K'ofa yasa aka bud'e, yace "Ku kalla Ku gani"


Waigawar da zasuyi suka ga mutum uku akan su suxee kowanne ya d'ora musu bindiga akai, alamar

Please Login or Register in order to submit comment