Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA D'AYA_


*____________________________*




















_Har ya yanke shawaran yaje ya sanar da Dr.Zaidu, se kuma ya tuna maganar da Dr Zaidun ya gaya masa jiya ,akan an masa allurorin bacci masu k'arfi ,amma ze iya farkawa a koda yaushe,,,,, 'to amma me yasa be farka ba har yanzu?' Hajj Jamil ya tambayi kan shi..._


_Sallar azahar ma kasa fita yayi ,anan cikin d'akin ya sake yin sallah ,Dan gaba d'aya jikin shi ya soma yin sanyi. Wuraren k'arfe uku na rana Haajar ta masa waya akan gata tazo asibitin, ya gaya mata suna Amenity room3. Bata wani sha wahala ba ta gane d'akin ,knocking ta masa ya bata izinin ta shigo, tura k'ofar tayi ta shiga bakin ta d'auke da sallama._


_Gaishe da Hajj Jamil tayi cike da girmamawa ,kafin ta ajiye basket d'in data zo dashi na abinci ,taja kujeran dake gefen gadon ta zauna._


_Ido ta zubawa Daddy nad'an wani lokaci, Gaba d'aya se da ta k'are masa kallo ,se taga kamar ba daddyn data Sani bane a kwanaki bakwai dasuka wuce ,ganin duk yabi ya rame yayi bak'i, tausayin shine ya k'ara kamata ,dukda bata San menene ainahin abunda ke damun shi ba,,, duban ta ta maida ga Hajj Jamil Wanda badan Daddy bane a kwance ,zaka d'auka shine Mara lafiyan, duk yabi yayi wani zuru-zuru. Fasa maganan da zata yi tayi._


_tashi tayi ta nufi basket d'in da tazo dashi. Flask ta Ciro ta aje gefe sannan ta d'auko cup da k'aramin spoon na shan tea. Tea ta had'a me kauri sosai Wanda ruwan zafin yaji kayan k'amshi ,sannan ta zuba doya da sauce d'in k'wai a plate ta kai gaban Hajj Jamil inda yake zaune kan sallaya ,ta aje masa, Dan base ta tambaya ba daga ganin shi akwai yunwa a tattare dashi. Ai Hajj Jamil kamar yana jira ,Kofin tean ya d'auka tare dakai wa bakin shi ,duk da irin zafi da tean yake dashi ,kurb'a ukku yayi sedai ya aje kofi, kan kace me zufa ya fara karyo masa ,Dan idan be manta ba rabon shi da abinci ,tun jiya war haka, A hankali ya fara cin doyan ,seda yaci sosai sannan yayi hamdala tareda ajiye cokalin me yatsu. Ruwan roba me sanyi ta sake kai masa ,ya karb'a yasha. Se a lokacin yaji kuzarin shi ya fara dawowa ba._


"Ya kika baro su Auta?" Ya tambaye ta.


Tace "Lafiyan su qalau ,dak'yar ma na sab'e mata ai ,seda na had'a ta da chocolate sannan ta banni na fito. Su suxee kuma na gaya musu zanje duba abokin ka da aka kwantar a asibiti, Hajiya k'arama taso ta biyo ni ,Dan ita gaba d'aya jikin ta yak'i ya bata, gani take yi kamar Kaine ba kada lafiya! Se da nayi ta bata baki tare da cewa ta d'ora mana girkin dare kafin in dawo ,shine fa ta hak'ura da zuwan."


Murmushi Hajj Jamil yayi Dan yasan Dole za'a zo wajen. Wani murmushin ya sake yi a Karo na biyu ,sedai wannan kaida ka gani kasan na k'unci ne sa takaici. Yace


"Ki duba ki gani ,sun damu dani fiye da yadda bakya tunani ,suna mun kallo d'aya da mahaifin su kuma saboda shi. Yanzu ki qaddara sun samu labarin mahaifin nasu ne a kwance , me kike tunanin ze faru?"


Jinjina kai Haajar tayi ,tare da cewa "hakane kam! Suna da nuna damuwa da mutum sosai ,kuma kamar yadda la lura akwai shak'uwa me tsanani a tsakanin su"...


Kad'a kai kawai Hajj Jamil yayi tare da cewa "Shine farin cikin su ,kuma shima sune kad'ai yake duba yaji sanyi a rayuwar shi. Akwai shak'uwa tsakanin su fiye da yadda tunanin ki ke baki"


Gyara zama Haajar tayi kafin tace "To amma meke damun shi ne haka ,wani irin ciwo ne wannan ,kuma menene dalilin ciwon?" Ta jero masa tambayoyin Jere da juna.


"Heart failure ,da hawan jini ke damun shi".. Ya bata amsa a tak'aice.


Zaro ido Haajar ta shiga yi tare da maimaita maganan " Heart failure da hawan jini??" Idon ta takai inda Daddy ke kwance cike da tausayin shi ta furta _"Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un "_...




" Amma taya akayi wannan gagaruman ciwon ya had'u masa waje d'aya kuma a lokaci guda?"


"Iyalan shi ne sanadi!" Hajj Jamil ya bata amsa.


Da mamaki take bin shi da kallo ,alamar bata gane me yake cewa ba, tare da cewa "Amma taya ya iyalan sa zasu zama sune sanadiyyar nakasa masa rayuwa?"


"Eh iyalan sa!" Ya sake maimaita mata. Ya d'ora da cewa "ko kina mamaki ne?"


"Abun ne ai akwai mamaki. Iyalan sa fa?" Haajar ta maimaita.



Be jira ta sake wurgo masa wani tambayar ba ,ya fara bata labarin Daddy ,tun daga farko har k'arshe ,be rage mata komai ba dan gane da rayuwar Daddy...




















MUJE ZUWA💃




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/26, 9:36 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA BIYU_


*____________________________*
























_Gaba d'aya jikin Haajar ne yayi sanyi matuqa, girgiza kai ta shiga yi a lokaci d'aya wasu hawayen tausayin Daddy na sauko wa daga idanuwan ta. Tun da take a rayuwar ta bata tab'a cin karo da wani labari me kama da wanda taji yanzu ba balle makamancin shi, da wani ne yake bata wannan labarin ba qanin mahaifin taba ,shakka babu ba zata gasgata wannan batu ba ,ta kuma San a tsakanin ta da Hajj Jamil akwai wasa amma ba irin wannan ba._


_Haajar mace ce me tausayi da saurin karaya. share hawayen ta tayi a hankali ta furta "Abbu Sameer!" ,,,, d'ago ido Hajj Jamil yayi yana kallon ta. Tashi tayi daga inda take zaune ,ta koma gefen Hajj Jamil daidai inda yake zaune akan sallaya ta samu guri itama ta zauna._


_Magana ta fara yi masa k'asa-k'asa kamar me rad'a, ta yadda ba Wanda ze iya jiyo me suke fad'a, sun d'au sama da awa d'aya suna magana, daga k'arshe Hajj Jamil yace_


"To shikenan ,ni nasan abunda zanyi. Allah ya taimake mu baki d'aya".


Haajar ta amsa da " Ameen". Sannan ta d'ora da cewa "to yanzu Abbu Sameer me ake ciki game da rashin lafiyar Daddy? Naga tunda na shigo be farka ba?"


Hajj Jamil yace "Yadda kika ganshi haka ,haka yake tun Daren jiya, ni kaina abun ya soma damuna".


Shiru ne ya biyo baya nad'an wani lokaci, kafin Haajar ta mik'e tsaye. Basket d'in da tazo dashi ta nufa, ruwan zam-zam ta d'auko had'e da kofi, dawowa tayi ta zauna ,tare da tsiyaya ruwan zam-zam d'in gaba d'aya a kofin kasancewar ruwan Nada yawa kuma kofin ma Nada d'an girma. _SURATUL FATIHA_ ta tofa k'afa bakwai kowacce da bismillan ta, tsiyaye wa tayi cikin gora, ta rage saura a kofin, sannan ta mik'awa Hajj Jamil tare da cewa


" Abbu Sameer kayi k'ok'ari ka bashi yasha wannan ,ka rage kad'an ka shafe masa sauran a jiki ,tun daga tsakiyar kanshi har tafin k'afar shi. Gobe da safe ma haka ,se kayi amfani da na cikin goran, idan zan zo gobe zan zo da wani ,a k'alla a samu tsawon kwana uku ana masa haka ,da yaddan Allah koma wani irin ciwo ne ze samu waraka."


Cike dajin dad'i Hajj Jamil yasa hannu ya karb'a tare da ajiye wa a gefen sa. Haajar tace "yanzu fa zaka masa base anjima ma"


Yace "to ai kinga yanzu be farka ba ,na d'auka ko se idan ya farfad'o ne?" Girgiza kai Haajar tayi tare da cewa


"A'ah yanzu za'a yi ,ai ma ze taimaka wasa wajen farfad'owan ,shiyasa nace zamuyi kamar na kwana ukku haka ,kafin muga yadda jikin yayi".


Mik'e wa Hajj Jamil yayi ya fara k'ok'arin yin kamar yadda Haajar tace ,sedai ya kasa ma taya ze tsiyaya wa daddy ruwan a baki ,kasancewar bakin nashi a rufe yake. K'arasa wa Haajar tayi wurin gadon tana cewa


" Bari kaga in taimaka maka." Ruwan kofin ta karb'a ta rik'e sannan matse hancin Daddy. Mik'e wa Hajj Jamil ruwan tayi ,tace "kayi bismillah ka bashi."


Nan ya shiga tsiyaya wa daddy ruwan addu'an yana sha, seda taga yasha sosai ,sannan ta sake masa hanci tare sa cewa


"Ya isa haka ,ka shafe masa sauran a jiki."


D'an basu waje tayi ,saboda be halatta taga tsaraicin saba. Waje ta fita ,tace "Ina zuwa". Hajj Jamil yasan manufarta nayin haka ,murmushi kawai yayi sannan ya fara k'ok'arin shafe masa jikin sa. Tunda ya fara shafawa daddy ruwan Addu'an nan yake ta sauke ajiyan zuciya, Mamaki ne ya cika Hajj Jamil, Dan daddy yayi ajiyan zuciya kusan har so uku.


A hankali Daddy ya fara k'ok'arin bud'e idanuwan shi ,ya sauke su akan Hajj Jamil, shi kuma mamaki ne da tsoron Allah ya kama shi ,da sauri ya k'araso yana wa daddy sannu.


Daddy dake kwance ,ji yayi kamar an zare masa lakka ,ga kuma baya jin wani ciwo a tattare dashi ,se dai k'arfin jikin ne da kuzari babu.


Farkawar Daddy yayi daidai da shigowar Haajar ,Hajj Jamil yace " kinga zuwan ki ya zame mana alkhairi, gashi wallahi har ya bud'e ido"


Murmushi kawai Haajar tayi tare da cewa "Dama ze farka ,wuyar ta ayi ne dai kawai". Duban ta ta maida wurin Daddy tace " Sannu Daddy ya jikin naka?"


Murya can k'asa daddy ya amsa mata da "ALHAMDULILLAHI!"


Ta sake tambayar sa "kana jin wani Abu yanzu?"


Girgiza mata kai yayi alamar A'ah. Kallon Hajj Jamil tayi da ikon Allah ya hana shi magana tace "Abbu Sameer ,inaga ze buqaci zagawa bayan gida ,kad'an kama shi ka kaishi."


Kallon mamaki Hajj Jamil yake bin ta dashi ,yace "ta ina kuma ze iya wani zuwa toilet mutumin daya farka yanzu yanzu!"


A hankali ta lumshe matsakaitan idanuwan ta, tare da nad'e hannun ta a k'irji ,tace "ka kaishi ka gani".


Hajj Jamil be San ma'anar ta na cewa hakan ba ,amma ba yada wani zab'i daya wuce yayi yadda tace ,Dan Haajar d'in ce gaba d'aya ta rikid'e masa ,sanin daya mata Ashe ta wuce nan.


A hankali Ya taimakawa Daddy ya tashi, toilet d'in cikin d'akin ya kaishi ,a mamakin shi suna shiga kamar Daddy na jira ,wani irin fitsari jawur kamar jini ,ga yawa ,sun kusa mintuna talatin a band'aki. Ruwa daddy ya shiga antaya wa tun daga saman kanshi ,sakamakon wani zafi daya ji yana taso masa ,had'i da kuskure bakin sa ,kafin nan suka fito.


Ko kafin su fito ,Haajar ta had'a wa Daddy tea me kauri ,sedai bata saka Sikari a ciki ba. Koda suka fito ,ba lefi ya samu kuzari ba kamar yadda suka shiga ba ,Dan har tafiya yake da k'afar shi ,iya gefen shi kawai Hajj Jamil ya rik'o. Seda ya zaunar dashi ,sannan Haajar ta mik'a masa kofin tea-n.


Hankali a kwance daddy ke kurb'an shayin sa, sedai wani d'an karan zufa daya shiga anbaliya yana wanke masa tun daga fuskar shi har zuwa cikin shi ,kamar an kwara masa ruwa. Duk Sanyin dake tashi ,be hana tsufan ci gaba da tsats-tsago masa ba.


Hajj Jamil kallon Haajar yayi ,data ke tsaye ta had'a hannuwa biyu tana ta faman aikin murmushi




A sanyaye ta furta "ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN! Sauqi ya samu...
















MUJE ZUWA💃




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/27, 9:15 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA UKU_


*___________________________*


















_Sosai jikin Daddy ya fara warewa ,har d'an hira suke tab'a wa sama-sama, se wuraren bayan magrib Hajj Jamil ya kira driven shi yazo ya maida Haajar gida. Washe gari tun da wuri ta fara shirin koma wa asibitin dan dubo jikin Daddy, tuwan semo tayi masa da miyar kub'ewa d'anye Wanda yaji bushash-shen kifi ,se Farfesun kayan jiki daya ji kayan k'amshi, har ta kusa kammala wa ta tuno da bata d'ora ruwan zafin tea ba ,da sauri ta kunna d'an k'aramin gas d'in da ba komai akai ta d'ora tare da saka kayan k'amshi,,,, duk d'ora da saukewan nan da Haajar ke yi, ba abunda ta dafa ba tare da ta tsiyaya MA'UL WARDI (ROSE WATER) a ciki ba, musamman a ruwan shayin ,se da ta kusa juye Rabin kwalbar MA'UL WARDIN, seda ta kammala komai sannan ta gasa musu bredi Wanda yaji butter ,k'wai dafaffe da kayan miya, wannan kuma tayi ne Dan Neman sauyi ,amaimakon takai bredin gayan shi ,se tada'an masa mahad'i..._


_Cikin lokaci ta kammala komai da komai ,ta jera a kwando ,fridge d'in kitchen d'in ta bud'e tare da d'auko wani d'an madaidaicin bowl me marfi ,fruit ne a ciki ya kuwa yi sanyi. K'arfe Tara na safe ,drivern Hajj yazo yana jiran ta. Bata yi k'ok'arin tashin su suxee ba ganin suna bacci ,sedai ta ajiye musu nasu breakfast din kan dinning yadda idan suka tashi base sun wahala ba ,ci kawai zasu yi._


_Ruwa ta sake watsawa ,bata wani b'ata lokaci ba ta shirya cikin atamfa d'in kin Riga da sket Wanda yabi jikin ta, mai kawai ta Shafa se madaran turare na jiki me sanyin k'amshi, sanin data yi na Haramun ne mace ta fita tana k'amshi yasa ,bata fesa turare a kayan ta, tana k'amshi amma ba me tashi sosai d'in nan ba ,k'amshi irin se Wanda ke kusa da ita sosai ze iya jiyo shi,,, Abaya ta d'ora akan kayan tare da yin rolling da mayafin. Duk da ba wani kwalliya tayi sosai ba amma kuma tayi matuqar yin kyau. Kwandon kayan abincin ta rik'o da hannu d'aya, d'ayan hannun ta kuma tana rik'e da wayar ta._


_Kamilu na ganin ta fito da sauri ya k'araso Dan ya karb'a kayan hannun ta. Fuskar Haajar d'auke da fara'a tace_


"Lah! A'ah Allah malam kamilu dama ka barshi ,muyi sauri mu tafi dai ,lokaci na k'ure wa."


Gidan baya ta bud'e ta aje kwandon ,sannan ta bud'e gidan gaba ta shiga.


Cikin mintunan da basu gaza goma zuwa sha biyar ba ,suka isa asibitin. Tura k'ofar d'akin tayi ta shiga tare da sallama. Ba kowa a d'akin ,D'aga idon da zatayi ta hango Daddy a zaune akan sallaya ,da alama ramakon salloli yake yi ,motsin ruwan data jiyo a bayi ya tabbatar Mata da Hajj Jamil ne a ciki. Cike da farin ciki ta samu guri ta zauna ,tana d'an danna wayar ta ,a hankali kuma tana d'agowa tana duba Daddy taga ko ya idar da sallan. Hajj Jamil na fitowa ya ganta ,k'ara fad'ad'a murmushin dake fuskar shi yayi ,yana fad'in


"A'ah har kin zo kenan ?"


Tace "Allah ya nufa Abbu Sameer. An tashi lafiya?"


"Lafiya qlau, Alhamdulillah. Ya su Auta?"


Tace "lafiyan su qlau ,ai basu ma San na fito ba ,Dan bacci suke yi koda na fito ,ni kuma bana so in tashe su shiyasa".


Hajj Jamil yace " Ah hakan ma yayi kyau"


"Abbu Sameer yame jiki?" Haajar ta tambaya cike da kulawa


Yace "Alhamdulillahi Haajr ,Jiki da sauqi sosai ,gashi nan ma yana sallah. Ai ke da kin gani kin San jiki yayi kyau".


Murmushi sosai Haajar ke yi Wanda yayi sanadiyyar bayyanar fararen hak'oran ta ,tare da cewa " gaskiya kam jiki yayi kyau. Allah yasa kaffara ne" Bayan Daddy ya idar da sallah ,Haajar ta masa ya jiki ,har cikin zuciyar shi yake jin dad'in yadda take nuna damuwa akan shi da 'ya'yan shi.




Addu'a tayi masa Wanda Manzon Allah s.a.w ya koyar damu idan ka ziyarci Mara lafiya ,ka karanta:


" لاَ بَأْسَ طَهُورٌ إِنْ شَاءَ اللَّهُ
Laa ba'sa tahoorun 'inshaa'Allaah.
: أَسْأَلُ اللَّهَ الْعَظِيمَ، رَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ أَنْ يَشْفِيَكَ
'As'alullaahal-'Adheema Rabbal-'Arshil-'Adheemi 'an yashfiyaka.( k'afa bakwai)...


Daddy jin yayi Haajar ta k'ara kwanta masa arai ,komai nata cikin hankali da nutsuwa take gudanar dashi. Da kanta tayi serving d'in su ,Tas daddy ya cinye har da Neman k'ari ,ga uban santi daya ke ta zuba wa, Hajj Jamil da Haajar se dariya suke masa ,Dan Daddy badai barkwanci ba ,haka yayi ta basu dariya, se dai be jima da gaba cin abincin ba ,Se wani amai ya taso masa ,da sauri ya tashi ya nufi toilet ,har saura kad'an ya fad'i, wani irin amai bak'ik'irin ya shiga kwararawa ba girma ba azziki kamar Wanda yaci guba, ba shiri Hajj Jamil ya aje plate d'in da yake cin abinci ya tashi ze nufi toilet d'in. Haajar tace


"Abbu sameer ka bash-shi yayi aman shine samun sauk'in shi ,dama nasan dole zeyi aman saboda da MA'UL WARDI na dafa masa ruwan shayi ,kuma shi dama MA'UL WARDI haka yake ,indai kana tunanin ko an yiwa mutum sihiri ne ,zaka saka a abinci mutum yaci ,ko kuma ma kaba mutum shi zallah yasha ,tare da tofa wasu Addu'o'i karya sihiri na sirri, saboda haka karka wani tashi hankalin ka ,ka duba kaga ni idan ya gama seka taimaka masa ya wanke jikin sa.


Gaba d'aya jikin Hajj Jamil duk yayi sanyi ,haka ya nufi toilet d'in, yadda ya ga Daddy na kwarara amai ga aman ba kyan wani ba k'aramin tausaya masa yayi ba. Sun kusa minti talatin a toilet d'in kafin suka fito ,Jikin Daddy har wani karkarwan sanyi yake yi ,gado ya koma ya kwanta ,Hajj Jamil yaja masa abun rufa ,tare da rage k'arfin Sanyin A/C, saboda yadda yaga jikin shi na wani cira. Kusan dai daddy ranar a kwance ya wuni da zazzab'i, Dr.Zaidu kuma na iya bakin k'ok'arin shi ,dukda be San wainar da ake toyawa ba.


Ranar Haajar bata wani jima ba sosai a asibitin ta koma gida. Kwana ukku ,duk tayiwa Daddy abinci da MA'UL WARDI se yayi irin wannan aman daya yi kwana biyu da suka wuce ,se dai ba kamar ranar daya fara yi ba. A hankali sauk'i na samuwa. Satin shi d'aya Haajar na iya bakin k'ok'arin ta ,Alhamdulillahi daddy ya samu sauqi tangaram, shi da kanshi ya lura da akwai abunda Haajar ke sako masa a abinci da idan yaci yake saka shi wannan aman ,amma shi kan shi yasan ba aman lafiya bane yake yi ,ga kuma wasu sababbin canji daya ke ji a jikin shi, har wani raman wahala yayi ,yayi bak'i...


Bayan sati d'aya Daddy ya samu kanshi ,aka sallame shi daga asibiti, Tare da Haajar gaba d'aya suka wuce gidan Hajj Jamil. Bayan sun zauna Hajj Jamil ke cewa


"Nifa inaganin idan zaka koma gida tare dasu Auta zaka tafi saboda suna kewar ka sosai ,se dai wannan karon tare da Haajar zaku tafi ,taje tad'an kwana biyu tunda dama anan d'in ba kowa Zaliha bata dawo ba har yanzu ,daga ita ne se 'yan aiki ,itama idan taje can d'in zata fi sake wa ,kuma kaga zata kula dasu Auta"..


Daddy ya dad'e yana jinjina lamarin ,har k'asan zuciyar shi yaji dad'i ,amma be San yadda Haajar zata d'auki lamarin ba. Ganin yayi shiru yasa Hajj Jamil cewa


" ko hakan be maka bane?"


Ajiyan zuciya Daddy ya sauke ,kafin yace "ba wai be mun bane. Ni inaga ita Haajar d'in zata amince kuwa? Karfa mu cika zak'e mata da yawa ,d'an Abun azzikin ma da take yi mana tazo ta dena". Daddy ya fad'a iya gaskiyar sh.


Dariya maganan yaba Hajj Jamil yace " Haajar fa 'ya tace ,kuma kaima 'yar ka ce"


Wani kallo daddy ya masa alamar ta ina?


Hajj Jamil daya gane cewa yana son k'arin bayani yasa yace "Kaddai kace mun baka San Haajar ba? Ko da yake ba lallai kasanta ba ,Dan ba'anan take zaune ba ,tana can tare da Asadussunnah a Sudan ,da wani aiki yakai shi can shine ya tafi da ita ,acan tayi karatun ta, kwatakwata bata shekara biyu da dawowa Nigeria ba"


Zaro ido daddy ya shiga yi tare da cewa "kaddai kace mun 'yar Asadussunnah ce Haajar? Lallai kuma idan hakane nayi b'atan kai, mutum da 'yar shi sukutum"


Hajj Jamil yace "Aikuwa dai"


Mahaifin Haajar Dr. Imam Ali Asadussunnah ,shahararren malamin addini ne daya shahara ba a iya jahar shi ta jigawa kad'ai ba ,Nigeria da kewaye babu inda sunan shi da alkhairan sa na fad'akarwa be zaga ba, a b'angare d'aya kuma k'wararre ne kuma likita ne wajen had'a magungunan Islamic... Wannan kad'an kenan...











*__________________________*




Garin kano... Hajiya Gwaggo ta dage se shirye-shiryen bikin suke yi ita da dangin amarya ,Amarya lubabatu kuwa ta gama shirin ta tsab na amarcewa a gidan daddy, koda yaushe tana sashen Hajiya Gwaggo ,daga su kitsa wannan se su kwance wancan. Ko da bansan me suke kitsewa ba ,amma daga gani kai kasan ba alkhairi bane...






















MUJE ZUWA💃




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/28, 9:41 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSO📚_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ASHIRIN DA HUD'U_


*___________________________*
























_A Ranar da suka dawo gidan ,a ranar Suxee da Haseena suka zazzaga da Haajar ko ina na gidan ,tare da nunnuna mata wasu abubuwan ,a sashen kubra sukayi branch har ita ,saboda su suxee ,bata son duk wani Abu daze sa tayi nisa dasu._


_Duk da basu da masaniyar ko tasan komai game da gidan su ,amma shak'uwar su da ita yasa suka kasa b'oye mata komai, duk wani Abu na rayuwar gidan a wuni d'aya ta San shi ,hakan kuma ba k'aramin taimaka mata ze yi ba ta fannin zamantakewar ta a gida. Auta kuma kamar an tsoma ya a aljannah ,Dan kuwa murna take sosai da suka taho tare da Haajar gidan su._


_A ranar base gobe ba ,Haajar tasa aka fitar da duk wani na'urar jin sauti a gidan ba tare da wani shakku ko tsoron me ze je ya dawo ba. Haka ma duk wani hoton bango ,se dai na iya sashen Daddy kawai tasa aka kwashe aka k'ona su. Ita dasu Suxee suka shiga sashen ,suka gyara masa shi ,gyara Wanda tun da yake be tab'a samun irin sa ba ,Dan seda ta sauya wa komai mazauni ,idan ba ka lura dakyau ba ,kana shiga sashen zaka zata ko wasu kayayyakin aka sauya, Hatta kayan daddy na cikin Sip seda ta fito dasu duka ,wani abun mamaki data bi kayan d'aya bayan seta ga akwai killatattun kayan da akawa alama da farin zari ta wuya ,mamakin duniya ne ya hana ta magana ,kwatakwata jikin ta be bata daidai ba ,Dan haka tabi kayan d'aya bayan

Please Login or Register in order to submit comment