Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai daddy yayi cikin zuciyar shi ya sake godewa Allah. A fili ya furta " Lallai Allah ne abun godiya"...




Suna zaune likita ya zo ya kawo takaddar sallama nasu Haajar tare da magungunan su. Had'ida sheda musu cewa Haajar ta dawo sati na sama a sake duba ta. Hajj Jamil ya tambaya ko da wani matsalar ne? Likita ya mik'a mi shi sakamakon gwajin da aka yi wa Haajar. Karb'a Hajj Jamil yayi bayan ya karanta ya saka a aljihu...




Gaba d'aya suka d'unguma a mota zuwa gidan Hajj Jamil. Haajar na ganin an d'au hanyar da ba na gidan daddy ba ,tace wa Hajj Jamil dake toqa motar "Abbu sameer ina kuma za mu je?" Ba tare da ya juyo ba yace "Gida na zamu je mana". Girgiza kai tayi tare da cewa " A'ah Dan Allah! Ina so muje gidan daddy akwai abunda nake so in d'auka". Gaban daddy ne ya yanke ya fad'i lokacin daya ji Haajar ta ce aje gidan shi. Ba kad'an ba ya tsani yaji wani labari akan gidan balle har ace wani Abu ya sake kai shi gidan...




Hajj Jamil be k'i ta tata ba ya karya motar zuwa gidan daddy...




















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/17, 3:30 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ARBA'IN_


*____________________*




















Har sun kai k'ofar gida barrister Kabir ya yi wa Hajj jamil waya akan yana babban asibiti ,Wanda shi ne mai bincike akan case d'in gobarar gidan daddy ,komai na tafiya ne a k'ark'ashin kulawar Hajj Jamil. Hajj jamil yace masa ya same shi a gidan daddy yanzu... Parking ya yi a k'ofar gida tare da kashe motar. Dikkan su suka fito suka shiga gidan a tare. Tunanin wani sashen za su suka fara yi. Hajj yace su nufi sashen bak'i Dan shi ne kad'ai a gyare, kuma anan zauna lokacin da al-amarin nan ya faru saboda zuwan jama'a ,wasu ya sauke su anan wasu kuma ya kai su masauqin bak'i. Gaba d'ayan su can suka nufa kai tsaye banda Haajar ,da ta zagaya ta bayan gidan da alama ma gidan gona ta nufa. Lubabatu na jin zuwan su ,nan da nan ta isa sashen Har ta na fad'uwa. Kuka ta rushe musu da shi tare da jajanta musu kan abunda ya faru. Wani irin kallo kowa ke bin ta da shi Wanda ya sa ta sha jinin jikin ta, da mamaki kowa ke jinjina rashin kunya da ta ido irin na lubabatu...


A ce duk abubuwan nan da suka faru ,duk sintirin nan da aka yi ta tayi na asibiti babu ita ba labarin ta ,ba zuwa ba aike. Ai ko itace hajiya suwaiba uwar Daddy zata rarrashi zuciyar ta tazo idan ma tace duk rad'ad'in abun ne bai gama sakin ta ba...


Haka kowa dai ya share ta idan ta kamo wancan batu ta saki ta kamo wannan duk na borin kunya. Babu Wanda yace mata ci kan ki. Gara ma hajiya har ta iya amsa gaisuwar ta. Mik'ewa tayi tare da cewa "bari in kawo muku ruwa". Tana gama fad'ar haka ta mik'e tabar parlourn. Auta ce tace " Ni hajiya bacci nake ji" hajiya tace "to muje ciki, daga nan ma na yi alwala Dan na ji kamar an fara kiran sallah". Hajj jamil yace " mu ma bari muje mu yi sallan hajiya ,mu na dawo wa yanzu" hajiya tace "to Ku dawo lafiya jameelu" daga nan daddy suka fita zuwa masallacin da ke cikin gidan shi ,a cewar Hajj jamil idan suka fita masallacin waje mutane za su yi ta zuwa mu su jaje ,kuma yanzu ya fi buqatar daddy ya samu Hutu kamar yadda likita ya jaddada masa...








Fitowar su ya yi daidai da isowar Barrister Kabir. A tare suka shiba masallaci bayan sun fito sun jima suna tattaunawa kafin suka k'araso Dan Barr Kabir ya yiwa hajiya jajen abunda ya faru...


Hajiya na d'aki kan sallaye ,suxee ta shigo tace mata "Hajiya kizo anyi bak'o" shafa addu'a hajiya ta yi tare da cewa "To ga ni nan zuwa". Ta fad'a tare da miqe wa ta nufi parlourn.


Barr dake zaune kan kujera mazaunin mutum d'aya ,yana ganin hajiya ta fito ,har k'asa ya zuqunna yana gaishe ta, tare da jajanta mata kan abun da ya faru. Barr Kabir ba tun yau ya san hajiya ba ,da kuma tarin alkhairan da hajiya ta yi masa a rayuwa, Dan karatun da ya je yayo game da shari'a a qasar waje Allah ne sanadi hajiya ce sanadi ,Dan ita ta biya masa komai da komai ba tare ma da daddy ya sa ni ba. Wannan na d'aya daga cikin abunda yasa ba zai taba iya mantawa da hajiya ba. Auren sa na farko ma hajiya ce ta nema masa ta kuma yi masa komai duk a sanadiyyar zaman shi abokin daddy na k'uruciya kuma an yi zaman mutunci da iyayen shi lokacin da suke raye. Wanda Allah ya yiwa matar tashi rasuwa wajen haihuwa ,bayan ta Haifa masa 'ya mace wacce taci sunan hajiyar daddy suna kiran ta da HAJIYEYE. Zaman lafiya da soyayyar da Barr Kabir yayi da marigayiyar matar shi yasa ya kasa k'ara aure sama da shekaru bakwai ,kullum jiya iya yau ,hajiya ta yi masa fad'a amma koda yaushe maganar Barr Kabir shine shi fa a ganin shi ba ze tab'a samun wacce zata maye masa gurbin matar sa ba. Daga k'arshe ma da hajiya ta matsa masa ,sai ya ce ta sake nemo masa ,in dai ita ce zata nemo masa ya yi mata alqawarin ze yi aure Dan ba yada shakku ko haufi akan zab'in hajiya. Tun daga wannan lokacin hajiya ta sarara masa ,Dan a cewar ta ita ma sai ta yi bincike mai tsawo akan wacce zata samo masa ,Dan qaunar da ke yiwa Barr Kabir yasa bata son duk wani abun da ze zo ya kawo wa rayuwar shi cikas. Ta na kuma son shi da qaruwa kamar yadda take son Daddy da abun da ta Haifa da abun alkhairi. Wannan kuma na cikin karamci irin na hajiya ,duk Wanda ze zauna tare da ita to fa lallai ne yasan kirkin ta.




Bayan sun gama gaisawa ,nan suka shiga tattauna abun da ya faru ,da kuma yadda ya shirya case d'in ganin sun samo bakin zaren. Suna zaune Lubabatu tayo sallama kamar wata mutuniyar azziki hannun ta d'auke da tiren lemu. Har gaban hajiya taje ta aje mata ,ta juya zata fita Barr dake bin ta da ido ya dakatar da ita. Gaban lubabatu ne ya yanke ya fad'i ainun. Hannu Barr Kabir ya sa a aljihun gaban rigar shi ya d'auko wayar sa. D'an danne danne yayi a wayar ,wani folder ya shiga da ke d'auke da hotunan lubabatun. Sake duban ta yayi ya kuma mai da kan shi kan wayar ya duba dakyau ya ga lallai itace ba wa ta bace.




Ita dai lubabatu sai kallon shi take yi ta na so ta gane inda tasan wannan fuskar amma ta kasa tunowa.






Tashi Barr Kabir ya yi yazo har inda lubabatu ke tsaye ,ya dinga zagaye ta yana qare mata kallo Sama da qasa ,Wanda ya sa lubabatu tsarguwa. Kowa ya zuba wa sarautar Allah ido yaga me ke shirin faruwa.


Barr Kabir yace "kin yi kama da wata matar marigayi Alh sambo".




Dummm! Gaban lubabatu ya yanke ya fad'i ,tabbas tasan ko waye ya mata farin sani musamman da ya ambato mata sunan Alh sambo. Zufa ne ya shiga tsiyayo mata ,kan kace me jikin lubabatu ya fara karkarwa.


Murmushi Barr Kabir yayi kafin yaci gaba da cewa "ko da yake duniya ta fa d'i ba lallai ya zama ke ba ,ina ga dai kamar Ku ce ta yi yawa.




Girgiza kai lubabatu ta shiga yi cike da sarqewar murya tace " umm...ummm ba ni bace". Ta na gama fadin haka ta yi hanyar waje da gudu. Sai dai a rashin sa'a sai jin tayi taci karo da mutum.


'Yan sanda ne sai dai ba'a kayan aiki su ke ba. Saboda kar su ja hankalin mutane, wanda Barr Kabir ne ya tura mu su adireshin unguwan da layin. Cafke ta suka yi ta na ta kokarin ta k'wace ,tare da cewa "Ku sake ni in tafi ,ba ni na kashe shiba wallahi Ku sake ni"


Barr Kabir yace "da ma wa ya ce kin kashe shi ai yana nan da rai ba mutuwa yayi ba.




Hannu lubabatu ta Dora akai tare kurma ihu tana fadin " na shiga uku na lalace"


Barr yace "ba ki shiga ba za dai ki shiga" yana gama fadin haka yace su tafi da ita.














MUJE ZUWAπŸ’ƒπŸ»




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️




[8/17, 3:30 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ARBA'IN DA D'AYA_


*_______________________________*
























Ba su kai ga fita da ita ba Sai ga Haajar ta shigo ,wacce sun shigowar su ta fice bata San wainar da ake toya wa ba. Hannun ta rik'e da wani buhu duk ya yi datti ,ba kuma Wanda yasan me ke ciki sai ita data shigo da shi. Tace wa 'yan sandan "Ku dakata tukunna". K'arasawa ciki ta yi , sai da ta k'arasa tsakar parlourn in da kowa ze iya hango ta ,sannan ta zuqunna tare da zaro abun da ke cikin wannan buhun. Da sauri daddy ya mik'e tsaye yana bin abun da haajar ta Ciro a buhun.


" wannan ba akwatin takaddu na bane?" Daddy fad'a tare da nuna akwatin.


Haajar tace "ka sake dubawa dakyau dai ka gani. Ta fad'a tare da mik'a masa akwatin. Karb'a ya yi tare da zama a lokaci d'aya ya bud'e akwatin ya shiga duba takaddun da ke ciki...


Da ido daddy ya bi ta, cike da matsuwar son jin k'arin bayanin In da ta samo akwatin bayan a idon shi komai ya k'one na sashen shi.


Haajar ta fara da cewa " daddy nasan za ka yi mamakin yadda aka yi na samu wannan akwatin? To ba abun mamaki bane ,ba kuma tantama wannan akwatin dukiyar ka ne Allah ya dawo maka da shi Wanda babu abunda ya samu matsala. Sai zan so Ku saurare ni Dan jin a inda na samo da kuma yadda aka yi na samu akwatin". Kowa natsuwa ya yi yana sauraron haajar. Wani ajiyan zuciya ta sauke kafin ta shiga ba su labari Tun daga lokacin da lubabatu ta turo musu 'yan fashi da makami akan azo aci zarafin su... Shirin ta akan sace akwatin dukiyar daddy da ta yi sannan ta k'ona d'akin saboda ta kauda hankalin kowa,,, da yadda ita haajar d'in ta wargaza wa lubabatu shiri ta hanyar canza akwatin da wasu takaddun na bugi,,, ta d'ora da cewa "Tun lokacin da marigayiya Haseena ta gaya mun cewa ba ta yadda da wannnan mutumin dake zuwa gidan nan a matsayin k'anin lubabatu ba ,na sanya ido akan su ,na ke kuma kula da shige da fitan su. Na dinga bibiyar ta ,har lokacin da suka shirya sace maka dukiya. A wannan Daren ta d'auki akwatin ta kai gidan gona ,ta yi rami mai zurfi ta saka a ciki ,ba tare da tunanin me ze ya dawo ba. Bayan tabar wurin na b'atar mata da hankali ta hanyar musaya akwatin da irin sa. A washe gari ta kunna wuta a d'akin sannan ta fito tana kururuwar a taimake ta. Wannan ta Ku da ta yi yasa tayi wasa da hankulan mu. Gobarar da ta sake tashi a b'angaren kubra ma duk ita ce ta haddsa shi. Saboda ta ji duk irin sab'anin da Khaltum da Kshri suka sa mu a lokacin da kubra ta je sashen khaltum suna maida wa juna magana..." Nan Haajar ta zayyana musu duk irin abun da ta ji na sab'anin da su kubra su ka sa mu ,Tun daga zuwan su Germany har dawowar su. Daga nan ta ci gaba da cewa "Bayan Khaltum ta ji komai ,daga wannan lokacin sai ta fara tunanin duk wata hanya da zata bi Dan d'aukar fansa akan kubra. A nan lubabatu ta yi amfani da damar ta ,ta zuba wa khaltum magani a abun sha ta kai mata ,sannan ta zayyana mata duk yadda zata yi Dan d'aukar fansa. Idon khaltum ya rufe a wannan lokacin saboda haka sai ta yi tunanin ko lubabatu na so ta taimaka mata ne ,ba tare da ta yi shawara da kowa ba ta je ta aiwatar da duk yadda lubabatu ta tsara. Dalilin faruwar gobar na biyu kenan, Wanda yaci rayuka ,amma khaltum ba ta mutu ba a yanzu haka tana babban asibiti ana kula da ita. A ranar da gobar zata shi, ba nida lafiya daddy yace in shirya ya kai ni asibiti. Allah ya jiqan haseena ita ta fara shiga band'aki ta ga ruwan famfun baya zuwa ,da ta gayamun sai na fito na zagaya ta baya da niyyar in duba. Bayan na duba ruwan zan koma ciki. A ta wajen ajiye motoci naga wannan mutumin da lubabatu ke kira da qanin ta ,ya karb'a k'yallen da baba lawan ke goge mota sannan ya aike shi ,bayan baba lawan ya tafi aiken da a yi masa. Se da ya waiga ya ga ba Wanda ke ganin sa ,ya zuqunna ya sacce d'an bakin wannan motar da baba lawan ke gogewa da alama yasan da ita za'a fita, ya na gama wa ya yi wa lubabatu waya ta fito ,duk ina tsaye da baya ba tare da sun ganni ba, bansan dai me suka tattauna ba amma na ga ta bashi wani envelop da alama kud'i ne a ciki ,daga nan kowannen su ya kama gaban shi. Ita ta koma ciki shi kuma yayi tafiyar shi. Yana fita na yiwa 'yan sanda waya tare da yi musu kwatancen shi suka kama shi da kuma abunda take k'ok'arin aikatawa suka ka ma shi. Da mu ka fito za mu fita ,na cewa daddy kar mu shiga wannan motar mu shiga d'ayan. Ya yi mamaki ,ya tambaye ni ko lafiya ,nace masa lafiya qalau kawai dai sanyin A/c nne ba na so. Duk da ba wata hujja na ba da ba daddy ya biye min a tunanin shi ko duk zafin zazzab'in ne. A wannan ranar shirin lubabatu na k'arshe shi ne ta salwantar da rayukan mu gaba d'aya. A d'ayan b'angaren kuma ga gobarar da za ta tashi za'a yi marus ,a wayi gari ba kowa a gidan sai ita. Daga nan ta shirya 'yar k'aramar wasa na akan idan komai ya wakana kamar yadda ta tsara ,za ta yi haukar k'arya Wanda mutane za su yi tunanin ko duk iftila'in da ya faru ne ya tab'a mata k'wak'wal. Da ga nan bayan ta warke komai na daddy zai zama na mallakin ta."... Kowa da ke wajen kusan daskarewa ya yi Dan jin wannan al-ajabi. "Abu sai kace shirin film cewar Hajiya...




Ta ku Haajar ta yi har inda lubabatu ke tsaye rik'e a hannun matakan tsaro tace "Wannan wasar ya k'are daga yau. Cin mutuncin da kike ganin kin mun kuma dama a wurin ki yake haka. A zahiri kuma ni matar daddy kamar yadda kike matar shi ,a yanzu haka kuma ina d'auke da cikin shi sanadiyyar abun da ya faru. Ke kuwa kina ji kina gani za'a fitar da ke daga cikin gidan nan, ba ma cikin gidan daddy kadai ba hatta rayuwar shi kin fita kenan fitar da babu dawowa har abada da yaddar Allah..." Mai da duban ta tayi gun Barr tace "za Ku iya tafi da ita. Idan wancan case din ba bamu da masaniya akai tuhuma ce to ga Wanda kuke da tabbaci akai".

Ihu lubabatu ta shiga kurmawa ba qaqqautawa ,tana fadin " Wallahi sharri take mun ban aikata ba ,wannan kawai an hada ne Dan a rabani da mijina saboda anga yana so na.

Barr dake tsaye yace "wancan ma ba tuhuma bane ,saboda yanzu mun kai shekara goma muna cigiyar ta Allah be sa mun gan ta ba sai yau. Muna kuma da izinin kamata mu danqa ta hannun hukuma duk lokacin da muka yi ido hudu da ita. Zamu tafi ita, idan komai ya daidaita zan dawo Ku ji komai". Barr yace wa matakan tsaro Ku tafi da ita.




Ihu lubabatu ke yi tana fadin " Ku taimake in. Na shiga uku tun ban mutu ba ga matambaya sun iso min. Alhaji kana gani za'a tafi dani ka yi musu magana kar ka bari su tafi dani". Jin zata Tara musu jama'a yasa su ka rufe mata baki da wani k'yalle tare da ficewa da ita...


Suxee da hajiya sai kuka su ke yi. Suxee na kukan rashin 'yar uwar ta haseena da baqin cikin irin mutuwar da tayi. A b'angare daya kuma tana takaicin irin turbar da mahaifiyar su ta mutu a kai. Gaba daya tausayin kan su ya kama ta a lokaci daya taji son Haajar ya qara shigar ta. Hajiya ita ma kukan rashin jikar ta take ,da tausayin d'an ta irin jarabtar da Allah ya yi masa na mata ,ace mata uku babu ta Allah a cikin su. Da badan Allah ya kawo musu Haajar a rayuwar su ba da yanzu labari ya sauya. Duk da wannan shi ne karo na farko da hajiya ta ga Haajar ba k'aramin kwanta mata ta yi ba ,musamman yanzu da ta ji irin tarin alkhairan da ta yi a d'an zaman ta a gidan yasa ta ji ta a ran ta fiye da yadda ya ji son ta a farko.


Hajj Jamil dake gefe mamakin duniya ya hana shi magana. Duk wani abunda Haajar ke yi tana sanar mishi amma Sam ba yada masaniya akan abubuwan da ta zayyana a yanzu. "wato Haajar ta wuce duk yadda nake tunani?"" Ya fad'a a k'asan ran shi ,a fili kuma ajiyan zuciya ya sauke tare da cewa "Godia ya kama ta mu yi wa Allah ,ga me faruwar wa'yannan abubuwa. Abunda ya faru ya riga ya faru ba ma fatar makamancin wannan ya sake faruwa ,sai dai mu ce Allah ya tsare gaba ya kuma k'ara tsare mana imanin mu... Zuwa yanzu komai ya faru ya wuce ,mun ji komai. Abu daya da ya rage shine misbahu in gabatar maka da Haajar a matsayin matar ka. Tun lokacin da ka kwanta a asibiti ,na fad'a mata komai a kan ka saboda yadda naga ta damu dakai, ta kuma amince akan tana son ka zata aure ka. Daga wannan lokacin naje na nema maka auren ta a wajen mahaifin ta yaya na Dr. Sheikh Imam Ali asadussunnah, ya kuma amince da duk baya nan dana Je masa da shi. Ban baro jigawa ba sai da aka d'aura auren ka da ita. Tun lokacin Haajar ta dawo gidan nan da zama ,ta zo ne a matsayin matar ka. Kuma ita ta buqaci da a b'oye maka har zuwa wani lokaci saboda a samu daidaito, saboda kuma ka nemi soyayyar ta da kan ka ,ba Dan wani ko wata ya had'a Ku ba. Kamar yadda ka ji ta fad'a a yanzu cewa tana da juna biyu ,haka zancen yake.





Duk abunda ya faru bana qasa a guiwa wajen sanar da hajiya. Tasan komai akan auren ka da Haajar, Dan har ma na tab'a had'a su a waya suka gaisa. Ko ba haka ba hajiya?"


Hajiya ta amsa da "wannan haka yake"


Daddy da tsoron Allah ya taru ya tsaya masa a zuci ,mamaki ,tsoro da alajabi ne ya hana shi furta ko da kalma daya. Jinjina kai ya shiga yi a hankali ya furta "Ikon Allah"...




Ba tare da ya sake cewa komai ba ,Dan shi gaba d'aya ganin abubuwan da suka faru yake kamar a mafarki. Ba tare da ya sake furta kalma d'aya ba hajj jamil ya rufe taron da addu'a. Hajiya ma addu'a tayi musu sosai na samun zaman lafiya mai d'aure wa a rayuwar auren su. A gefe d'aya kuma ta yi Haajar godia bi sa namijin k'ok'arin da tayi ,a cewar hajiya ba mace ko namiji yayi irin wannan k'ok'arin yaci a jinjina mishi. Suxee in banda kuka ba abunda take yi. Hajiya da Haajar sai aikin lallashin ta suke yi. Sai da Hajj jamil ya saka baki kafin ta sassauta kukan da take yi...




Da daddare Hajj jamil ya yo musu take away gaba d'ayan su.A ranar Hajiya tare suka kwana ,ita Haajar, auta da kuma suxee.






Bayan sati d'aya...












MUJE ZUWAπŸ’ƒπŸ»




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/18, 9:58 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA ARBA'IN DA BIYU_


*____________________________*


















Bayan sati d'aya... Komai ya fara daidai ta. _GIDAN MISBAHU_ ya fara farfad'o wa daga dogon hutun da ya je na farin ciki da kwanciyar hankali. Sosai Haajar ta samu karb'uwa a wajen daddy, ta kuma ba shi had'in kai wajen gudanar da rayuwa mai inganci. Hajiyar daddy ta so ta koma ,amma Haajar ta yi ta lallashin ta akan ta hak'ura ta zauna tare da su a garin sakkwato. Ba Dan Hajiya ta so ba amma Dan dole ta hak'ura ta zauna ,saboda kwarjini da kuma k'imar Haajar da take gani ,a cewar ta kuma babu abunda Haajar zata ne ma a wajen ta ta gaza yi mata shi matuqar abun nan bai fi k'arfin ta ba. Sashen bak'i aka gyara wa Hajiya. Ita kuma Haajar aka gyara mata sashen da ke gefen sashen da hajiya ke ciki. Sosai Haajar ke kula da duk wani buqatun hajiya da ma na gidan gaba d'aya. Ko da yaushe indai daddy ya fita to dikkan su suna tare da hajiya ana hirarrakin barkwanci ,wannan yasa Haajar ta k'ara samun karb'uwa a wajen hajiya ,take kuma yi mata gata irin na uwa da 'ya ,musamman da ta samu labarin cewa mahaifiyar Haajar d'in ta rasu. Hasalima ba ta wani San dad'in uwa ba ,tun tana k'arama Allah ya yiwa mahaifiyar ta ta rasuwa. Sashen kubra da Khaltum kuwa rushe su daddy yasa akayi Dan baya son yana gani ko tuno duk wani abunda ya dangance su.




A gefe d'aya kuma yana matuqar kewar kubra. Dan duk wani abunda take yi masa ,sanyin halin shi da hak'urin shi bai sa ya manta da zamantakewar su ba ,duk da ko bai tab'a jin dad'in zama da ita ba koda na sakan d'aya. Amma duk lokacin daya kalli Suxee da Auta ,fuskar kubra yake gani k'arara a tare da su. Wannan yasa ya ka sa mantawa da ita gaba d'aya, amma Dan ta khaltum da lubabatu da ma ba zab'in ran shi bane ,Dan haka baya wani tuna cewa zamantakewa ta aure ta tab'a had'a

Please Login or Register in order to submit comment