Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

d'inkin ta koma cikin gida. a parloun Hajiya ta baje d'inkunan. Sai da ta fara zare nata Dana amarya da na hajiya zaliha da ta bada da kuma sauran 'yan uwanta da suma gaya mata za su zo bikin, dama ita Hajiya da auta tuni aka kawo musu nasu, sannan tace ga wa sauran 'yan uwa ga ankon data sanya a d'inka musu riga da sket na kwaddebuwa atamfa mai kyau da tsada. Kowa ya gwada Wanda ze yi daidai da jikin shi. Ai fa nan parlour ya kwacema da murna. Nan fa aka shiga gwaje-gwajen kaya ,sai godia suke mata da San barka. Tace duk Wanda basu samu ba su jira zuwa da safe za'a kawo wasu kayan, Dan tela biyu ta baiwa d'inkunan Dan a samu a gama cikin lokaci. Wannan abu yaiwa kowa dad'i musamman wa'yanda basu saka da kan su a lissafi ba ,sai suka ga Haajar bata ware su ba. Washe gari musamman Haajar ta d'auko mai kwalliya ta biyata dan a fito da amarya. Da safe misalin k'arfe takwas amarya tayi wankan ta na farko ,dama gashi tasha lalle da kitso. Ta fito cikin wata atamfa ruwan ganye mai ratsin fari, a inda takalmin k'afar ta da pos d'in hannun ta had'ida mayafin ta duk ya zama fari. Sarka da d'ankunnen dake wayar ta had'ida awarwaro da zobban dake hannun ta duk na gwal ne da Barr Kabir ya sanyo mata a lefe. Ba k'aramin kyau tayi ba duk inda ta wurga sai d'aukar ido take yi tana zuba wani mayataccen k'amshi. Guda kake ji ya kace ma ko ina da ko ina. Ga mak'awan gargajiya da suka doko sammako daga can wajen shigowa gida ,ganga suka shiga kid'awa suna wake daddy da kuma Haajar sai kace su ake yi wa biki. Sai da Haajar ta aiko tace amarya za su wak'e mata sannan suka canza salon gagangar su.




Da daddaren tela ya yiwa Haajar waya akan ga d'ikin su ya kammala. Dama kamar yasan shi take jira, ta yi ta kiran wayar shi tsawon kwana biyu wayar shi a kashe ,ga shi hatta kayan da amarya zata saka yana wajen shi. Hak'uri ya ba Haajar tare da bata uzuri. Haajar tace ba komai. Ta cika masa ragowar kud'in shi sannan ta amso d'inkin ta koma cikin gida. a parloun Hajiya ta baje d'inkunan. Sai da ta fara zare nata Dana amarya da na hajiya zaliha da ta bada da kuma sauran 'yan uwanta da suma gaya mata za su zo bikin, dama ita Hajiya da auta tuni aka kawo musu nasu, sannan tace ga wa sauran 'yan uwa ga ankon data sanya a d'inka musu riga da sket na kwaddebuwa atamfa mai kyau da tsada. Kowa ya gwada Wanda ze yi daidai da jikin shi. Ai fa nan parlour ya kwacema da murna. Nan fa aka shiga gwaje-gwajen kaya ,sai godia suke mata da San barka. Tace duk Wanda basu samu ba su jira zuwa da safe za'a kawo wasu kayan, Dan tela biyu ta baiwa d'inkunan Dan a samu a gama cikin lokaci. Wannan abu yaiwa kowa dad'i musamman wa'yanda basu saka da kan su a lissafi ba ,sai suka ga Haajar bata ware su ba. Washe gari musamman Haajar ta d'auko mai kwalliya ta biyata dan a fito da amarya. Da safe misalin k'arfe takwas amarya tayi wankan ta na farko ,dama gashi tasha lalle da kitso. Ta fito cikin wata atamfa ruwan ganye mai ratsin fari, a inda takalmin k'afar ta da pos d'in hannun ta had'ida mayafin ta duk ya zama fari. Sarka da d'ankunnen dake wayar ta had'ida awarwaro da zobban dake hannun ta duk na gwal ne da Barr Kabir ya sanyo mata a lefe. Ba k'aramin kyau tayi ba duk inda ta wurga sai d'aukar ido take yi tana zuba wani mayataccen k'amshi. Guda kake ji ya kace ma ko ina da ko ina. Ga mak'awan gargajiya da suka doko sammako daga can wajen shigowa gida ,ganga suka shiga kid'awa suna wake daddy da kuma Haajar sai kace su ake yi wa biki. Sai da Haajar ta aiko tace amarya za su wak'e mata sannan suka canza salon gagangar su.






Zuwa sha biyu amarya ta sake canza kala inda ta fito cikin wata dakakkiyar shada mai tsada d'inkin doguwar riga daya amshi jikin ta. Haajar ba ta yi wanka ba sai da ta tabbatar ta gama shirya komai ,masu abinci sun gama sun kawo tare da ma'aikatan su da za su yi aikin zuba abincin. D'aki daya aka ware sai da aka cika shi da ruwa da kuma lemummuka. Sai da Haajar ta yi sallar azahar lokacin ana shirye-shiryen zuwa d'aurin aure sannan ta yi wanka. Ganin lokaci na k'urewa yasa tabar na ta shirin taje Dan ta shirya mijinta. Cikin wata arniyar farar shadda daddy ya shirya d'inkin babban riga wanda anko ne suka yi shida aminin shi hajj jamil. Misalta muku irin kyawun da daddy yayi b'ata lokaci ne Dan wallahi idan ka gan shi a wannan rana kai ka zata shi za'a je d'aurowa auren. Haajar ma saida tace "kai masha Allah! Ashe dai mijina kyakykyawan gaske ne? Wannan haka haka sai kace Kaine angon" daddy na dariya yace "to aini kullum ma ango na Dan yanzu ma da za'a bani dama Dana tabbatar miki da hakan" Haajar tace "to ank'i a baka daman" dariya yasa tare da cewa "matsoraciya" itama dariyar take yi tace "na dai ji". Nan fa soyayya ta dawo sabuwa Dan gaba d'aya Haajar ji take yi kamar kar daddy ya fita ya zauna tayi ta kallon shi ,ta kasa d'auke idon shi akanta. Yace " malama wannan kallon fa? Duk salon ki shanye dad'in gani na Amaryar da zan kawo ta rasa gane komai ko? Kinfa San ni mijin mace hud'u ne?" Haajar na dariya tace "Ah haba ai kuma Matan ka na aljannah d'an birni". Yace " allah ko?" Tace "yo wace zata wani so ka duk ka tsofe ka yi laushi ,me zata tadda ni din dai". Dariya dikkan su saka daddy yace " zaki yi baya ni ne ai idan na dawo ja'ira".






Da haka daddy ya fito sakamakon hajj jamil daya yi masa akan yana jiran shi. Sai da ya fara shiga ya gaisa da su Hajiya. Taubasan shi sai tsokanar shi suke yi. Sannan yayi ficewar shi. Kwalliya aka tsantsarawa Haajar ta shirya cikin atamfa super Holland launin d'orawa da fari, d'inkin riga da sket pisis, Kai idan ka ganta kace ma ita ce Amaryar Dan tsabar kwawun da tayi. Fitowar ta yayi daidai da zuwan masu kid'an k'waryan data gayyato. Har ma sun fara k'ida mutane na rawa. Sai cigiyar ta suke ta lasifika suna fad'in "ina uwar amarya uwar gida a gidan alhaji Misbahu?" Kowa yayi wanka ya shirya ,tare da Hajiya zaliha da muqaraban ta suka sauko. Nan aka fara fito da abinci da abun sha ana kakkaiwa jama'a ,abinci sai kalan Wanda kake so. Ta sa aka warewa Hajiya da muqarabanta na su daban aka kai musu. Seda ta tabbata komai na tafiya da daidai sannan taje ta tutse suxee taci abinci dak'yar sannan ta sake canzo kaya suka fita fage. Suna tattaka rawa ga ruwan liqi da dake tashi. Aifa nan biki ya dawo kan su ,tsakanin Haajar da su idan ba wai ka San su ba ba lallai bane ka iya tantance wacece Amaryar daga ciki. Awa d'aya da fara kid'an k'warya suka sake komawa suka canzo shiga suka dawo. Mutane sai ido suke bin su da shi. A aka har aka dawo d'aurin aure ,su daddy suka wuce walimar da suka shirya na bayan d'aurin aure, wanda ya tara dandazon al-ummah. Wasu ma sai a ranar suka san daddy nada budurwar 'ya mace. Anci an sha a wurin walimar,wanda Hajj jamil ne ya shirya komai ,shine kuma mai kula da bak'in su. Sai wuraren la'asar suka yo gidan daddy da gayyar su. Gidan cindim yake da jama'a Dan se ka yi da gaske ma kafin ka samu wurin da zaka wuce. Mamaki ne ya kama daddy lokacin daya hango Haajar a tsakar fili tana takawa. Ba k'aramin kyau tayi masa ba. Sab'ewa su hajj jamil yayi ya kutsa har tsakar filin ya shiga yi mata lik'i, nan fa kallo ya koma sama. Yana mata liqi tana masa. Abokan su daddy suka dinga tambayar hajj jamil ko ita ce 'yar daddy?. Hajj jamil yace musu a'ah Matar shi ce. Nan fa aka shiga aka dinga musu liqi. Kafin daga baya suka fito zuwa sashen Hajiya. Har yamma ana ta shan sha'ani. Sai shida na yamma Haajar ta sallami masu k'idan k'warya saboda za su fara shirye-shiyen zuwa wurin dinna bayan magriba.




Misalin k'arfe takwas suka gama shirin su na zuwa dinna. Amarya tasha kyau ita da angonta. Haajar ma sai da taja daddy ,Hajiya zaliha kuma tare da hajj jamil. Komai ya tafi gwanin sha'awa. Duk Wanda yaje sai ya fito da tsaraban kayan biki kama daga jaka ,memo ,ankicip, kofin tangaras nashan shayi, kayan mak'ulashe da sauran su, Wanda duk Haajar ce ta dau nauyin komai.










Abun yayi matuqar k'ayatarwa. An shash-sha hotuna. Haajar Sai da ta keb'e mai hoto d'aya dake ta faman d'aukar su hoto ida da daddy ba tare daya Sani ba. Misalin k'arfe goma sha d'aya na dare aka tashi daga dinner. Kai tsaye gida suka nufa. Suna isa 'yan biko na zuwa. Ruwan lallen da aka jik'awa suxee aka bata taje ya ti wanka. Sannan ta fito. Haajar da kanta ta shirya ta cikin wata exclusive atamfa sannan ta d'ora mata alkyabba akai. Sashen Hajiya aka kaita su ka yi Mata nasihohi sannan aka kaita wurin su daddy, hajj jamil ne ya mata fad'a sosai shi dai daddy tun da yace "Allah ya sanyawa auren albarka" bai sake cewa komai ba. Suxee ta yi kuka kamar ba gobe, Haajar ma hadda hawayen ta. Daga nan aka wuce da amarya gidan ta. Haajar ta wuce mata da duk wani abun da zata buqata kafin gobe. Ko da suka dawo kai amarya kusan d'aya saura na dare. Lokacin duk ana zaune ana dudduba hotunan dinnan wa'yanda suka d'ad'd'auko da waya.




Anan sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya suxee da Barr Kabir...
















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[8/31, 3:27 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA HAMSIN DA D'AYA_


*_____________________________*




















Washe gari misalin qarfe goma na safe su Haajar su ka fara shirye-shiryen zuwa gidan amarya ,saboda walimar da za'a yi yau a can gidan amaryar sha biyu na rana, wanda karantarwa ta sunnah manzo S.A.W yazo mana da shi ,wato walima bayan aure. Daga gida suka yi komai da za'a rabawa 'yan walimar, sannan suka d'auki duk wani abunda yayi saura na amarya Dan awuce mata da shi. Misalin sha d'aya su Haajar suka fara wucewa kafin wasu 'yan uwa suka ce zasu biyo bayan su idan lokaci yayi. Koda suka je Barr Kabir baya nan ,suxee ce kawai. Ta gyara ko ina da ko ina a gidan ta sanya turaren wuta sai k'amshi ke tashi. Tana ganin su Haajar ta fara murna hadda guntun hawayen ta ,Dan daga jiya zuwa yau ji take kamar ta shekara ne bata gidan su, sosai take kewar kowa nata. Gaggaisawa suka shiga yi ,bayan sun zauna suxee taje ta kakkawo musu abun sha. Haajar ta wuce uwar d'aki ,suxee ba ganin haka tabi bayan ta. Yanayin tafiyar suxee kawai Haajar ta gani ta gano cewa wani abun ya faru. Ba tare da suxee ta kula ba Haajar ta kafe ta da ido ,suxee na ganowa ta fashe da kuka tare da rumgume Haajar. Tausayin suxee ne ya kama Haajar, ta shiga bubbuga bayan ta alamar lallashi. Cikin muryar kuka suxee tace "Anya Anty Haajar zan yi zaman aure kuwa? Ba kiji yadda nake ji ba ,duk abubuwan da nake yi k'arfin hali ne wallahi saboda abunda kika gayamin cewa kar in bari kowa ya gane abunda ya faru tsakani na da mijina. Amma Anty Haajar yadda nake jin labari ba haka na gani ba. Wasu daga cikin qawaye na sunce min sai bayan sati d'aya ko sati biyu da auren su mazajen su ke kusantar su ,amma ni duba ki gani fa jiya-jiya. Kika kuma cemin ba zafi bayan ba haka bane". Suxee ta qarashe maganan tare da fashewa da wani sabon kuku. Abun yaso ya bama Haajar dariya amma sai ta dake tare da ci gaba da bata hak'uri " Hajiya k'arama ki dena kukan nan, ko so kike wani ya shigo ya gane wani abun ya faru ,bakisan wannan sirrin ki bane? Ko ni bai kamata ki gayamun ba".




Girgiza kai suxee tayi tare da share hawayen ta sannan tace "A'ah Anty Haajar. Ni a matsayin mahaifiya na d'auke ki ,bana tunanin zan iya b'oye miki komai. To idan ban gaya miki ba wa kike so ingayawa damuwa ta?" Haajar tace "hakane! To amma ki dena kuka. Sannan da kike zancen wai qawayen ki na gaya mi sai anyi sati ko sati biyu kafin mazan su su kusance su, angaya miki hadisi ne ko ayar allah? Babu wani nafsi daya ce haka, hasalima a karantarwa ta sunnah anfi son randa aka kawo mace mijin ta ya kusance ta shine maqasudin wannan walimar ta bayan aure. Idan kika ga miji ya d'aga wa matar shi qafa wannan ra'ayin shine da ganin damar shi, saboda haka ya kamata ki lura dakyau"






Nasihohi sosai Haajar ta sake yiwa Haajar kan yadda zata tafiyar da rayuwar auren ta ,musamman ta fannin shimfid'ar mijin ta ,dan abunda Haajar ta lura da shi a maganganun suxee alama ce ta Barr mai yawan buqatar mace ne ,musamman yadda ya jima be yi auren nan ba ,ga shi ta lura suxee nada raki Wanda ze iya kawo mata naqasu a zamantakewar ta da mijin ta. Fad'a tayi mata sosai ,sannan ta bata wasu abubuwan da zata yi amfani dasu , ta had'a mata ruwan magarya da sassak'en b'aure mai zafi ta zauna. So biyu tana canza mata ruwan sannan tace tayi wanka ta fito ta shirya ,lokacin wacce zata mata kwalliya ta Kira tana hanya. Masu sanya rumfar walimar kuma suna harabar gidan suna aikin su. Gyara mata ko ina Haajar tayi ,ta jera mata jayan ta a sip ,sannan duk wasu muhimman abubuwan da suxee zata buqata ta ajiye mata su a kusa-kusa kamar kayan hakin maye ,drowa d'aya ta mata. Seda akayi sallar azahar sannan me kwalliya tazo ,lokacin mutane sun fara taruwa. D'an light make-up aka yi wa suxee. Ta shirya cikin wani material purple mai kyau da tsada, tare da d'ora alkyabba akai. Bayan angama Haajar ta dube ta tare da cewa "kai masha Allah Mrs Kabir kinyi kyau sosai." Suxee tace "nagode Mrs Misbahu". Dariya suka sa. Suxee tace " to Anty Haajar kizo a miki kwalliyar mana" Haajar tace "wa ni? Ai Kema kinsan ban damu da irin kwalliyar nan ba ,nafi gane in Shafa hoda in mits-tsika mai a baki kawai ya ishe ni". Fanna mai kwalliya tace " ai kinsan su kyawawa daban suke ,kwalliya bata wani dame su ba." Dariya suka yi Haajar tace "kin dai ga kyawawan gaske nan a gaban ki" ta nuna suxee. Suxee tace "kai Anty Haajar abun hadda zolaya?" Dariya Haajar tayi tare da cewa "ai kowace mace ma kyakykyawa ce saidai idan bata samu gyara ba". Fanna tace " hakane kam". Se da suka yi sallan azahar sannan aka fara shirye-shiryen walima. Misalin k'arfe biyu na rana ancika. Malama khadija itace wacce zata gabatar da nasiha a walimar. Tana zuwa walima yakan kama. Nasihohi sosai malama khadija tayi tare da tsakuro musu wasu daga cikin magungunan da zasu iya had'a wa da kan su ba tare da sun cutata ba. Sannan tayi tsawatarwa game da wuta da aljannah. Haqiqa ta fad'akar ,kowa yaji dad'in zuwa walimar. Sai la'asar taron ya fara watsewa ,duk Wanda zai tafi kuma da tsaraba yake tafiya ,na turaren wuta, kayan snacks da abun sha Wanda Haajar ce duk tayi wannan hidimar. Bayan la'asar duk mutane sun gama watsewa sai su Haajar kad'ai suka rage. Sai da suka gyara mata duk inda aka b'ata suka baza turaren wuta. Haajar ta sake dafawa suxee ruwan sassaken b'aure ta zauna sannan tasa tayi wanka ta canza kaya ,wani had'ad'd'en gumba na aya Wanda yaji kwakwa ,da dabino Haajar ta had'a wa suxee da madara tace "maza ki kafa kai ki shanye".bayan ta shanye ta tsiyaya mata tsumi Kofi d'aya shima ta shanye ,sannan tace " ya isa haka. Karki dinga shan abubuwa ya miki yawa, Dan suna da k'arfi zaki iya buguwa idan kika cika". Suxee tace "ai naji Anty Haajar, Dan har yanzu ban dena jin shi a mak'oshi na ba." K'arfe biyar su Haajar suka yiwa suxee sallama suka koma gida...






Sai da akayi sati sannan Haajar ta dena aikawa su suxee abinci. Bayan sati d'aya aka kai hajiya gidan suxee ta wuni mata ,sai yamma daddy ya tura driver ya d'auko ta. Bayan sati biyu da zuwan hajiya suxee da Barr Kabir suka kawo ziyara gidan daddy. Kowa yayi murnan ganin su ,suxee tayi kyau abunda ya k'ara haske tayi 'yar k'iba ,haka shima Barr. Tun rana sai dare suka musu sallama suka tafi. Tun bayan biki Hajiya zaliha Matar hajj jamil bata sake komawa gidan Haajar ba ,Haajar ce ma suna hira da daddy wata rana da daddare take cewa ya kamata taje ta dubo maman sameer gobe. Washe gari da daddy zai fita ya aijye ta a gidan ,yace idan ya dawo da yamma zai biyo ya d'auke ta. Hajiya zaliha tayi murna sosai da ganin Haajar. Haajar tace "ya naga duk kin rame lafiya kuwa?" Hajiya zaliha tace "ina fa lafiya ,tun bayan biki nake nan banda lafiya" Haajar tace "ya salama! Ko ince ,amma wllh banda labari kuma Abbu sameer na zuwa gidan mu amma ban ji a bakin shi ba" Hajiya zaliha tace "aikin San halin shi ko yasan Abu indai ba tambayar shi kayi ba ,ba lallai ya fad'i ba." Haajar tace "to amma meyake damun ki haka? Kin rame sosai, Kodai ta samu ne?" Haajar ta fad'a cike da tsokana. Hajiya zaliha tace "kedai bari. Shi d'in ne fa, sai wahalar dani yake yi". Murna sosai Haajar tayi tare da yiwa Allah hamdala. Tace " Ashe dai biki bai qare mana ba? Kai amma naji dad'i sosai. Allah ya raba lafiya, ya bada rayayye ko rayayye mai albarka". Hajiya zaliha ta amsa da "ameen". Kusan Haajar ce tayi mata aikin gidan ranar. Sun sha hira sosai ,sai yamma liqis an ma kusa kiran sallan magrib daddy yazo d'aukan ta. A mota take bashi labarin Hajiya zaliha nada juna biyu ,shima daddy yayi murna sosai kai kace Matar shi ce aka ce tana d'auke da cikin. Tsokanar Haajar ya shiga yi akan cewa suma ya kamata ace sun d'au harman na biyu. Haajar tace " haba dai! Dan Allah kayi hak'uri ranka ya dad'e. Su Hassan fa ko yaye su ban yi ba" daddy yace "to idan kuma Allah ya kawo kuma fa?" Haajar tace "wannan kuma ba yadda zan yi" yace "to Dan haka wannan ma ba yadda zaki yi da shi na jikin ki" zaro ido Haajar ta shiga yi tare da cewa "menene kuma a jikin nawa daddy?" Dariyar mugunta daddy ya mata tare da cewa "ciki mana" Haajar tace "na shiga uku. Dama ina da wani cikin bayan na cin tuwo ne?" Ganin duk yadda ta rud'e yasa daddy cewa "ke wasa nake miki fa ,duk kin bi kin wani firgice. Da akwai keda yake jikin ki ai zaki sani" ajiyar zuciya Haajar ta sauke tare da dafe k'irji tace "haba! Yanzu naji zance". Dariya daddy ya shiga yi mata. Nan suka saki zancen suka d'auko wani, a haka har suka k'arasa gida.








Bayan sati biyu da zuwan Haajar gidan Hajj jamil. Take cewa daddy tana so taje asibiti a duba ta. Daddy yace mata saboda me? Dan shi dai lafiya qalau ya ganta. Tace masa baccin da take yi ne yayi yawa ,ko da yaushe bacci kamar 'yar k'waya, se yawan kasala da take fama da shi. Daddy k'in yadda yayi aje asibitin ,haka ya dinga mata kwana-kwana ,har sai da cikin ya kai wata uku lokacin ya fara fitowa. A lokacin ba yadda Haajar ta iya amma kuma bata murna da cikin saboda a cewaf ta su Hassan ba suyi k'waren dahar zata yi musu qanne ba. Tunda Hajiya ta sani sai tace Haajar ta dinga basu nono so d'aya a rana ,dama ba wani damuwa sukayi da nonon ba sosai ,da haka har suka dena sha suka koma shan madara zallah. A b'angaren suxee ma tana can d'auke da ciki wata biyu. Murna a wurin su Haajar ba kama hannun yaro. Allah ya taimaki Haajar ko kafin watan haihuwar ta ya tsaya su Hassan sun iya tafiya suna gudun su ko ina ,ga yaran da jikin girma Dan idan ba an gaya maka cewar basu shekara biyu ba ba ganewa zaka yi ba, baki ne dai babu. Matar hajj jamil ce ta fara haihuwa ,ta samu mace ,murna a wurin daddy da hajj jamil abun sai Wanda ya gani. Daddy ne yayi komai na sha'anin suna, ranar suna yarinyar taci sunan Hajiyar daddy wato suwaiba ,ana mata laqani da Aslamiyya ,duk da shi hajj jamil suxee yayi wa kara ba Hajiya ba ,saboda qaunar da yake mata har yanzu babu abunda ya ragu. Kowa yaji dad'in karar da yiwa Hajiya ,Hajiya ma ta taka rawar gani sosai Dan ita aka yiwa takwara.








Da farko ma ta d'auka ko sunan mahaifiyar shi zai saka, da ta yi masa magana sai yake ce mata ,ba yada ra'ayin hakan ne kawai ,iyayen ma da ba sanin su yayi ba ,Dan an haife shi da kwana tara mahaifiyar shi ta rasu a wurin dangin ta ya taso ,shekarar shi biyu da wata shida kuma Allah ya yiwa mahaifin shi rasuwa ,a wurin kakannin shi ya taso ,bayan sun rasu ne ya dawo hannun kawun shi da zama. Kunga kuwa ina wata shaquwa? Hajiya ce take zuwa gidan hajj jamil tana yiwa Hajiya zaliha duk wani abunda ya kamata har bayan suna ,Dan Haajar kam tayi nauyi ,ranar suna ma dak'yar ta samu taje ,shima tana zaune wuri d'aya bata iya tab'uka komai ba. Wata d'aya da haihuwan Hajiya zaliha Haajar ita ma ta haihu inda aka sake samun 'yan biyu ,sai dai wannan karon duk mata ne. Ranar suna Hassana taci sunan mahaifiyar Haajar Halimatus sa'adiya ana mata laqani da Ummi ,hussaina kuma taci sunan Kubra ana mata laqani da Amna. Haajar tayi hakan ne saboda suxee. Dukda daddy bai so ba ,amma ta nuna masa bata yadda za'ayi ya k'yamaci Kubra Dan ko duk yadda yaki yaso jinin ta na yawo a jinin shi ,ga kuma 'ya'yan ta nan na ci gaba da rayuwa a doron duniya. Ba Dan yaso ba haka ya hak'ura, Dan Haajar ba dai iya magana cikin hikima ba ,Hajiya ma taji dad'in abunda Haajar tayi sosai ,suxee ko hadda kukan ta da taji an saka sunan mahaifiyar ta.


Cikin suxee ya girma ,wannan ne yasa aka tura mata auta Dan ta taya ta wasu aikace-aikacen ,tunda daddy yace kar ta dawo gida har sai Allah ya sauke ta lafiya...




Kwana arba'in da biyar tsakinin haihuwar Haajar. Suxee itama Allah ya sauke ta lafiya ya bata santalelen d'an ta namiji mai kama da Barr Kabir Sak kamar an tsaga kara.

Please Login or Register in order to submit comment