Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hajja Fati tace" ni fa aganina kawai boka a b'adda ta, ta yadda hatta mahaifiyar ta data haife ta bazata k'ara tunanin ta haifi me sunan taba. Kawai a jefa ta wata uwa duniya."


Kundin tsafi boka RUBATSI ya buga ,kafin Yace


"Wannan Abu ai me sauk'i ne da k'arfin tsafi." Hannu ya maida cikin kundin tsafin dake gaban shi ,tare da rufe ido ,se wasu sambatu yake yi irin nasu na guma-guman arna. Cikin mintin dabe Gaza sha biyar ba ,se ga aljani ya bayyana. A firgice kubra ta k'ank'ame hajja Fati, Dan kubra badai tsoro ba. Ita kanta hajja Fati dukda taurin rai irin nata ,ba k'aramin girgiza tayi ba.




Cikin wani harshe wanda ba wanda yake gane me suke cewa ,irin nasu na tsakanin Aljani da wakilin aljanin RUBATSI ke magana da wannan aljanin. Suna gama wa kuma b'at aka neme aljanin aka rasa, a wannan karon fitsari ne ya kusa tsiyayowa daga marar Kubra...


Boka RUBATSI Yace


"Wannan da kuka gani aljani SUFURSUNARI kenan. Cika aiki nake kiran shi. Kada Ku damu shine ya karb'i aikin Ku. Sedai ya buk'aci da akawo gashin kan wannan matar da aka d'aura auren ta da mijin ki ,da kuma d'ankwalin dake d'aure akan ta lokacin dazata shiga gidan. Ga wannan " ya mik'a musu wasu k'ullin magani da SUFURSUNARI yazo dashi. Yace "wannan Jan maganin ki tabbata Mijin ki yaci a abinci ko abun sha, sannan wannan bak'in kuma inaso kiyi girki ki had'a shi a ciki ,ki aikawa Amaryar. Wannan kenan ,na sallame Ku..."




Mak'udan kud'i Kubra ta Ciro ta zube su a gaban boka RUBATSI, sannan suka kama hanyar komawa gida.










B'angaren hajiyar Daddy kuma. Bayan sun kammala cin abinci da daddare ,tace "idan ka gama kazo d'aki inason ganin ka" ta fad'a tare da mik'ewa ta wuce gaba ,shi kuma daddy yana bin ta a baya, har suka shiga d'akin ta. Gefen gado ta zauna ,shi kuma ya samu guri a k'asa ya zauna. Hajiya ta kira sunan shi "Daddy!" Dan haka kowa ke kiran shi saboda sunan kakan shine yaci.


D'agowa yayi cikin ladaba Ya amsa da "na'am Hajiya!"


Ajiyan zuciya Hajiya ta sauke kafin ta soma masa magana cikin sigar lallashi


"Daddy sanin kan ka ne ,duk uwa baza yi abunda ze cutar da 'ya'yan ta ba koda kuwa 'ya'yan shegu ne balle na sunnah. Hak'ik'a rayuwar gidan ka kullum dashi nake kwana arai ,kwatakwata Allah be baka matar azziki ba, kubra mata ce da sedai ace Allah ya kyauta kawai, to na gaji da d'abi'un ta ,Sam baza'a ci gaba da tafiya haka ba. Saboda haka na binciko maka wata 'yar azzikin daga 'ya'yan qawaye na. Na shirya komai ,har ma an d'aura auren Ku d'azu da ranannan. Fatar zaka karb'a wannan auren hannu bibbiyu?"...


Darammm!!!Dasss!!! Gaban daddy yayi wani mummunan fad'uwa kamar an buga durom. Kasa cewa komai yayi se ma k'asa da yayi dakai.


Lura da yana yin daya shiga Hajiya tayi. Tace


"Daddy ko hakan me yi maka bane? Idan baka so base anje ko inaba se a warware auren ,tunda burin ka ka watsa min k'asa a ido, ka kuma nunawa duniya ban isa ba ,to ai shi kenan". Hajiya ta fad'a a fusace.


Cikin nuna damuwa daddy yace " Hajia kiyi hak'uri ,dama kubra nake tunani ,kar taga kamar ba'ayi mata adalci ba, sannan kinsan yadda zaman namu yake"


Jinjina kai Hajiya tayi kafin tace
"Naji kuma nasan komai ,sannan ka kwantar da hankalin ka ,wannan auren na maka shine dan ka samu kwanciyar hankali da nutsuwa a gidan ka. Kubra kuma bata isa tayi maka abunda Allah be nufa akan ka ba ,saboda haka ,muna nan mun sa rok'on Allah, komai kuma ze zo da sauk'i ,albarka ta na tare dakai. Allah yasan ya wa abun albarka"


"Ameen" daddy ya amsa. Kafin suka fara tsare-tsaren yadda komai ze kasance.




A washe gari ,a ranar ne daddy ze koma ,kuma lallai lallai Hajiya tace sedai ya wuce da Amaryar shi, ba yadda ya iya haka ya amince






Amarya kaltum ce a zaune taci ado ,ba lefi kuma tana da kyawun ta daidai misali daka ganta base an gaya maka kasan shuwa ce. Hajiya khairi itace mahaifiyar kaltum. Zaune suke tana gayawa kaltum yadda shirin su ze kasance


"Kaltum kin dai ga yadda nasha bak'ar wahala na kuma b'ata naira kafin na samu auren nan naki ya tabbata ko? To ba bacci zaki je yi ba ,tun wuri ya kamata ki San me kike yi ki kuma San gidan da zaki shiga. Kin dai ji abunda malam ya gaya mana ,matar shi kanta hatsabibiyar mata ce ,idan ba munyi da gaske ba zata ma iya kad'o ki... Ungo wannan" ta mik'a mata wasu qullolin magani tare da wata laya. Tace


"Wannan maganin ki tabbata dashi zaki rik'a masa girki ,wannan layar kuma a cikin filon da yake kwana akai anan zaki tsaga ki sake se ki d'inke da farin zare, daga nan magana ta k'are ,se na ji labari daga wajen ki."


"Karki damu hajiyar kaltum ,kisa aranki anyi an gama komai ,be matar shi kad'ai ba hatta hajiyar shi se ta dawo k'ark'ashin iko na"...cewar kaltum da kwatakwata ma idan ka ganta bazaka ce tana magana ba ,zubin ta irin zubin salihan matan nan ne ,sedai masifar dake cikin kaltum ya fita girma ,ita da kanta tsoron shu'umancin ta take yi...


Dariya suka fashe dashi tare da kashe hannu... Hajiyar kaltum ta dafa kaltum tare da cewa


" nasan ki sarai kaltum. Barewa bazayi gudu d'an ta yayi rarrafe ba. Fatar Nasara 'ya ta"...


Wani irin shu'umin murmushi kaltum tayi me k'ara wa fuskar ta kwarjini da haiba tare da lumshe manyan idanuwan ta ,tace


"Nagode Hajiya ta"...






















MUJE ZUWAπŸ’ƒ




TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/14, 6:32 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA BIYAR_


*_____________________*











_GARIN SAKWKWATO_


_Tun kafin su k'araso, daddy yasa aka gyara d'aya daga cikin sassan dake gidan shi ,sashen dake tsakanin na kubra Dana shi ,nan yasa aka gyara wa Khaltum._ _Duk wani abunda ake buk'ata kama daga ,kayan d'aki Dana kitchen da duk wani abunda yasan ana zuba wa a d'akin amarya seda yasa aka zuba wa khaltum su, kaya masu kyau da tsada na zamani ,duk daddy yasa an zuba su a sashen Khaltum._




_Tun da aka wangale musu gate suka shigo ,khaltum ke santin gidan ,komai na gidan me tsari ne ,bata gasgata maganar hajiyar taba ,seda suka shiga harabar gidan anan ta gane wa idanuwan ta aljannar duniya._ _shiru ita dai ta kasa cewa komai. Bayan driver yayi parking ne ,daddy yace wa suxee_


"Yauwa Hajiya k'arama (sunan dayake kiran ta dashi kenan ,kasancewar sunan hajiyar shi ya saka mata). Kije ki nuna wa Antyn Ku sashen ta ,na gaya miki ai shine na tsakayi ko?"


Suxee k'ara fad'ad'a murmushin dake fuskar ta tayi ,Dan ita tun lokacin da daddy ya sanar musu auren ,dad'i taji mishi sosai ta kuma taya shi murna ,Haseena ce dai ke aikin kumbure-kumburen ta ,da k'ananan maganganun ta ,a cewar ta ,suna fama da kubra ,shine za'a tashi a k'ara musu wani jangwam d'in. Seda suxee tayi da gaske ,sannan haseena ta sassauto. Amsa masa tayi da


"To daddy"! Sannan ta kalli haseena tace " Haseena ke kuma kid'an taya mu d'aukan kayan zuwa ciki"


Yatsine fuska haseena tayi ,kafin tace


"Nifa Yaya suxee gaba d'aya na gama gajiya ne ,ga baba lawali nan kisa ya shiga muku dasu" tana gama fad'in haka ,anan tabar su ,tayi wuce war ta.


Murmushi daddy yayi ,shida kanshi shakkar haseena yake yi ,Dan haseena badai masifa ba kam ,ita bata iya Abu da zuciya biyu ba ,ko ya maka dad'i ko karya maka ,idan gaskiya yazo zata fad'eta. Magana yawa baba lawali akan ya taya su suxee shiga da kayan ciki. Suxee ce ta fara yin gaba d'auke da jakar kayan Khaltum ,ita kuma tana biye da ita a baya sad'af sad'af kamar wacce tayi k'arya.


Da talatu suka fara cin karo a sashen khaltum, gaishe su tayi sannan tace wa suxee


"Hajiya k'arama Dama Alh ne yayi waya akan mu gyara wannan sashen za'ayi bak'i ,sannan yace daga yanzu ni zan ci gaba da kula da sashen".


" good" suxee ta fad'a, kafin taci gaba da cewa "to bak'i dai gasu sun zo ,kuma ba masu tafiya bane ,masu zama ne insha Allah" a zuciyar khaltum kuwa cewa tayi zama daram-dam ma kuwa. Suxee nuna khaltum tayi tare da cewa


"Talatu wannan da kike gani ba bak'uwa bace ,Amaryar daddy ce ,da fatar zaki yi mata biyayya kamar yadda kike wa sauran manyan gidan?"...


Washe baki talatu tayi tana fad'in " Ah Ah! Kice Alh aure ya k'ara? To ubangiji Allah ya basu zaman lafiya."


"Ameen " suxee da khaltum suka amsa dashi ,kafin ta mik'a wa talatu jakar kayan khaltum, tare da cewa


"Anty Amarya muje ciki in nunna miki yadda gurin yake kafin in k'arasa cikin gida ko?"

Ba musu khaltum tabi bayan ta ,talatu kuma na biye dasu a baya. Wani had'iyar yawu khaltum tayi lokacin da taga irin dukiyar da aka narka a sashen ta. Komai na garin me tsari ne. Babban parlour ne a k'asa Wanda ke zagaye da d'akuna uku kowanne da toilet d'in shi a ciki. kitchen had'e da store a ciki ,se dining area daga cikin parloun. Yadda k'asan yake haka saman yake sedai shi d'aki biyu ne ,da babban parlour. Komai a tsare yake gwanin ban sha'awa.


Da murmushi shimfid'e akan fuskar suxee tace


"To Anty Amaryar ,wannan shine b'angaren ki ,da fatar komai ya miki? Idan da akwai abunda kike buqata zaki iya sanar da talatu se ta fad'a mun "


Wani guntun numfashi khaltum ta sauke ,kafin tace


"Kar ki damu kanki suxee komai yayi ,nagode sosai da kulawar ki. "


"Bakomai Anty Amarya kema ai yanzu kin shigo cikin mu. Ni zan wuce sashen mu" suxee ta fad'a tare da mik'ewa.


"A huta gajiya. ki gaida mumyn taku Dan Allah kafin in shigo" khaltum ta fad'a kamar mutuniyar kirki


"Zata ji insha Allah" suxee ta bata amsa sannan tayi ficewar ta...


Sashen su ta nufa. Seda ta fara laqewa d'akin kubra taga bata nan ,sannan ta sauko k'asa zuwa d'akin su. Wanka haseena tayi sannan tawa Auta. Suxee ce ta shigo d'auke da sallama ,kan gado ta fad'a tare da fad'in


"Wash Allah! Na gaji sosai. Haseena akwai ruwan zafi a hitan toilet kuwa naga kamar kunyi wanka?"


"Eh akwai" haseena ta bata amsa a tak'aice ,Dan gaba d'aya haushin suxee take ji ,musamman data ga ta fiye zak'ewa akan auren da daddy ya k'ara.


Kaya suxee ta cire ,ta fad'a wanka. Bayan ta fito ne ,tana cikin shirya take cewa haseena "kin shiga d'akin mummy kuwa?"


D'an d'agowa haseena tayi tana duban ta lokacin tana had'awa Auta cornflakes ,maida duban ta tayi kan abunda take kafin tace


"Banje ba! Da alama ma bata gidan nan."


"Taya akayi kika gane, keda baki duba ba?"


"Ji fa Yaya suxee, to ni a abubuwan mummy wanne ne ban Riga na gama karanta ba? Muddin kika shigo baki ji tashin sauti ba ,to karki ma wahalar da kanki da zuwa duba ta ,bata nan ne kawai. Mummy na nanne zata bari kunnuwan jama'a ya sarara?"


Murmushi suxee tayi ,ko ba'a fad'a ba tasan gaskiya Haseena ta fad'i. Tace " Hakane kam. Bata ma nan Dan na duba".


"Uhm" inji haseena alamar kan ki ake ji.


Waya Haseena ta janyo tare da dialing wata number Dana ga ta saka 'MY HEADACHE'. Seda ya kusa tsinkewa sannan aka d'auka...

"Kina ina?" Haseena ta tambaya. A mamaki ne muryan kubra naji ya daki speakern wayan.

Kubra dake hotel tare da wani hamshak'in d'an siyasa suna aikata masha'an su ta amsa da


"Ina gidan hajja Fati. Ya akayi kun dawo ne?"


"Eh mun dawo ,Dan Allah ki dawo gida haka ,nace dai hajja Fatin nan koda yaushe kuna tare kamar cingom? To idan baki dawo Dan mu ba ,se ki dawo Dan kishiyar ki"!!




A zaton Haseena ko fad'in hakan ze tashi hankalin kubra ne ,amma amamakin ta ,dariya taji kubran nayi tare da cewa


"Cool down baby! Wacece kuma kishiya ,ban dawo Dan 'ya'ya naba, shine zan wani dawo Dan wata Abu wai kishiya? To ban gama abunda nake yi ba ,idan na gama ai zan dawo ko?


Haseena tantama take anya ma kubra taji abunda ta fad'a kuwa? Sake maimaita mata tayi


" mummy aure fa nace miki daddy ya k'ara shine kuma kike dariya?"


"Nasani ai Haseena, ba abunda bansani ba akan auren shi ,da naso in hana bama za'a kai yanzu ba ,banda lokacin su ne kawai." Cewar kubra


Haseena harta bud'e baki zata yi magana


"Mummy! " kubra ta katse ta


"Ke ni karki dame ni ,kisha fa mun kan Auta. Take care"...


Bata jira jin me Haseenan zata k'ara ce mata ba ,ta yanke kiran. Misalin k'arfe takwas na dare ,kubra tabar hotel d'in cikin shirin ta na zuwa club ,a cewar ta akwai babban casu da za'ayi a _shisha palace_ ,Wanda bata ka wani dalili daze sa tayi missing ba...




A b'angaren kubra kuwa ,abinci ta girka mai rai da lafiya iya k'warewar ta. Ta shirya komai akan dining sannan tayi dialing numbern daddy data rubuta wa _Alhaji na_, bugu d'aya biyu daddy ya d'auka. Cike da kissa kubra ke magana


" Dadddy na gama girki ,ka gaya wa su Hajiya k'arama ko"


Cike dajin dad'in yadda ta nuna damuwa da 'ya'yan shi yace


"To zan fad'a musu ,zaki gan su"


A shagwab'e tace "daddy to kai fa?"


Yace "karki damu ,ni bana jin yunwa ,idan ma ina da buk'ata Hajiya k'arama ce me girki na ,da abincin ta k'adai na saba. "


K'ara kashe murya tayi zatayi magana ,amma se jin tayi ya kashe wayan. Tsaki taja ,tare da fad'in


"Can da yawar ka. Tukunna ma ,ba'a fara wasar ba ai".




Daddy dase a lokacin yayi saving numbern khaltum, yana yanke kiran ya kira suxee dake kitchen ita da haseena suna shirya masa abinci, sheda mata yayi yadda yayi da khaltum ,tace


" to daddy zamu je insha Allah " shine amsar data bashi sannan ta yanke kiran. Haseena ce ta dube ta ,tare da cewa


"Keda waye kuma ?"


Suxee tace


"Daddy ne ,wai muje inji Anty Amarya ta gama mana abinci"


Baki haseena ta tab'e tana fad'in


"Ikon Allah. Wani iyayi ne wannan kuma? Da can kafin tazo wake dafa mana? Inace muke dafa wa kan mu?"


Suxee da dama tasan za'ayi haka tace


"Haba haseena daga abun azziki? Ina lefin ta?"


Haseena tace "kinga ni ban hanaki zuwa ba ,nidai bazani ba ,se kije keda Auta.


Auta dake tsakar kitchen d'in tana wasan ta ta karb'e da


" nima baza niba Yaya suxee "...


Suxee kad'ai taje taci abincin ta ta dawo.






Satin kubra d'aya a gidan ,hankalin ta a kwance ,tana cin gashin kanta ,babban abunda ke damun ta shine ,daddy ko so d'aya be tab'a neman ta da mu'amalar aure ba. A Daren ranar ta shirya tsaf Dan tunkarar shi , A wannen Daren ne kuma kubra ta dawo, wacce kusan tun tafiyar su daddy ,bata gidan se yau Allah yayi dawowar ta...




























MUJE ZUWAπŸ’ƒ






TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/14, 9:39 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA SHIDA_


*_____________________*











_Kubra Kai tsaye sashen ta ta nufa. Da shigar sauti ta kunna sannan ,sannan ta shiga wanka. Kwalliya ta zauna ta tsantsara Wanda ya amshi kyaky-kyawar fuskar ta, doguwar Riga ta zuba ,Wanda ya amsa sunan shi ,gashi daka gani kai kace Dan ita akayi rigar... Wani abun se mata masu diri_


_Haseena najin kid'an na tashi ,dariyar takaici tayi ,Auta ce ta tambaye ta_


"Yaya haseena waye ya kun nawa mummy hoppers d'in ta?"


Cike da takaici haseena tace

"Waye kuwa ze kunna mata? Kakar d'an k'wairo ce ta dawo da kanta ,kyaji ma fiye da haka"


Suxee dake fito wa daga toilet ,dariya maganar haseenan ya bata ,tace


"Wllh ba kida kirki haseena! Mummyn ce ma kakar d'an k'wairo? A'ah kakar Baban gida kaka dawo ne ,shine ke tashe"


"Ai tama wuce nan alqur'qn". Haseena ta bata amsa ita fuskar ta d'auke da dariya.


A tare suke je duba ta ,Kafin sukai har auta ta riga su kaiwa. Cab'e ta kubra tayi fad'in


" Auta ta takaina! Nayi kewar ki sosai." Tsuke baki auta tayi tare da cewa


"Ni bakiyi kewa na ba ,inda haka ne shine zaki yi tafiya baki je dani ba? Ni sauke nima ,mun b'ata" ...Auta ta fad'a ciki da yarinta


Murmushi kubra tayi tare da shafo gefen fuskar ta ,tace cikin sigar lallashi


"Haba Auta ,yau kuma da mummy ake fad'a? To kiyi hak'uri ,ba gashi yanzu na dawo ba? "


Sallamar su suxee ne ya katse ta. Gaishe ta sukayi a ladabce ,kafin suka samu guri suka zaune kan lallausan kushin d'in da yayi daidai da tsarin parloun.


Suxee tace "mummy da kin gaya mana zaki dawo ai da se mu gyara miki waje ,ko musa a gyara"


Wani uwar harara haseena ta banka mata tare da cewa

"Meyasa kike bin son ran mummy ne Yaya suxee? Kafin kice haka me yasa bazaki fara tambayar ta inda taje ba harna tsawon sati d'aya. Kuma da izinin wa taje , nasan tabbas daddy be Sani ba."


Alama suxee tayiwa haseena alamar ta rufe mata baki ,amma Haseena bata ji waji ba ,ta d'ora da


"Ya ga gaskiya ga rantsuwa! Idan ma bazata dawo Dan kowa ba aise ta dawo Dan mu. Tsakanin mu da mahaifiyar mu ba wani shak'uwa ko jin k'ai ,se anyi magana tace tana son mu. Yanzu ki duba fa irin abunda sakacin ta ya janyo mata ,gashi nan daddy yaje ya k'aro aure ,kuma duk akan halayen ta ne. Sati d'aya da zuwan Anty khaltum kenan. Amma bata San mummy ba mummy bata San taba ,idan ta gane irin halin da muke ciki dake wallahi ba abunda zaki siya mana se wulaqanci, Wanda b zamu lamunce ba."


Wata uwar tsawa suxee ta daka wa haseena


"Enough haseena!!!"


"Ank'i ayi enough d'in." Haseena ta maida mata a hasale ,sannan ta maida duban ta ga kubra tace


"Idan baki gyara ma inaga an kawo wacce zata gyara ki ,idan kuma ita ma d'in ba'ayi dace ba ,ina add'uan allah ya kawo me canza ki da gaggawa.
Ya kamata ki iya takun ki Dan girman Allah karki ja mana gori da gore-gore. Yanzu bamu kad'ai bane a gidan, na rok'e ki"... Haseena ta k'arasa maganan tare had'a hannayen ta biyu alamar rok'o. Tana kaiwa nan tayi ficewar ta.


Suxee da kamar taci kanta ,kallon mummy take idon ta cike da hawaye tace " mummy kindai gani ko? Kin ga abunda son zuciyar ki yake nema yaja miki ko? Duba fa ,haseena 'yar cikin ki take tsaya wa a gaban ki ta gaggaya miki maganganu marasa dad'i, duk da akan gaskiyar ta take kuma duk abunda take fad'a nasani kum kema kinsan gaskiya ne. Dan Allah mummy...




"Ke!ke!!! Malama dakata mun Dan Allah. " kubra ta katse suxee ,sannan taci gaba da cewa...


"Naku a mene ku kuma? Rayuwa ta ko rayuwar Ku? Na hanaku kuma kuyi yadda kuke so ne? Se kune 'ya'yan ciki na zaku hanani sakata in wala? To baki isa ba, Wanda ya ajiye Ku ma yayi kad'an. Dan Allah matsa mun in wuce ,inje inyi abunda ze fish-she ni." Kubra ta fad'a kamar zata bangaje suxee. Anan tabar auta ta nufi sashen Daddy.


Mamakin wani irin hali kubra keda shi ,ya hana suxee koda taku d'aya. A ranta take cewa "wato duk cin kashin mummy akaina ya k'are ,amma Haseena idan tana yi mata fad'a ko tari. To indai hakan ze sa ta gyara zan bar ta da Haseenan taji idan da dad'i.


" Allah ya kyauta" shine abunda suxee ta furta a fili ,sannan ta kama hannun Auta suka sauko k'asa zuwa d'akin su.




Kubra tafe take Cikin takun ta na k'asaita kamar wacce bata son taka k'asa a haka ta nufi sashen daddy...


Khaltum ce zaune kan kushin d'in da ke cikin uwar d'akan daddy. Taci ado se zuba wani fitinannen k'amshi take, kai kace baza'a mutu ba.


Tana jin an shigo parloun a cewar ta ko su suxee ne ,se kawai tayi maza maza ta haye kan gado ta kwanta ,a cewar ta ko da su Suxee idan daddy ya fito ya ganta akan gado ze hak'ura ya bata lokacin ta. Bata San daddy ya wuce nan ba indai akan 'ya'yan shine. Ganin ba kowa a parlour yasa kubra ta nufi bedroom d'in shi. Knocking ta fara yi Dan ta tabbatar ko yana ciki, shiru bata ji alamar akwai mutum ba ,sake knocking tayi ,cikin tsawa khaltum tace


"Dallah wai waye ke damun mutane ne haka?"


Duk da kubra bata San muryar wacece ba ,amma tasan baze wuce gurguntaccen auren da akace mata yayi ba. Bata yi magana ba ,se sake knocking d'in d'akin data yi. A fusace khaltum ta taso tana fad'in


"Uban waye?" Tana bud'e k'ofar se jin k'arin mari kake yi




"Tassss!!!












TO MASU KARATU, DAN JIN WAYA MARI WANI A CIKIN SU ,SE KU BIYO NI A SHAFI NA GABA IDAN ALLAH YA KAIMU...






MUJE ZUWAπŸ’ƒ






TAKU HAR KULLUM


SIDIYA...✍️
[7/15, 2:49 PM] SIDIYA...✍️: 🏠🏠 *GIDAN MISBAHU*🏠🏠
🏠🏠🏠🏠🏠🏠
🏠🏠🏠🏠
🏠🏠
🏠
*_🏠(base on true life story)_*🏠


*_🏠INTELLIGENT WRITERS ASSOπŸ“š_*
(On ward together)




*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)✍️*









_BABI NA BAKWAI_


*_____________________*












_A take khaltum ta fara ganin wasu taurari na mata yawo tsabar gigitar data yi. Seda ta natsu hankalin ta ya dawo jikin ta ,sannan

Please Login or Register in order to submit comment