Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da gudu Baba sule ya juya yay cikin masallacin shikuma ya dunkule hannu ya daki iska. "f*ck wlh zakici ubanki ne ahannuna" azuciye ya shiga masallacin ya hango Baba sule nama Abba magana akunne tashi Abba yay tsaye yazo inda yake tsaye yace "son are u serious?" murmushi yama Abban ya gyada kai, kamashi Abba yayi yamai peck a goshi tsabagen farin ciki, kafin yajuya da sauri yakoma gaban masallacin yadau mike ya tsaya yace "asaurara jama'a, asaurara" shiru akayi duk aka maida hankali kan Abba, yay murmushi ya kalli Baba yace "dama muntaba zuwa neman ma dana auren Bilkisu amma munyi latti lokacin, to gashi dannawa har yanzu yace yana ciki fa, alfarma muke nema ataimaka mana abamu malam" "Allahu Akbar" kawai aketayi a masallacin malamai nata kabbara suna cema malam "Allah ya fitar dakai kunya" wan Baba ya kalli Malam dayay shiru yace "kabasu Bilkisu tunda danshi na sonta kaga munfita kunya" murmushi Baba yay ka kalli Abba yace "na amince kuma nabaku ubangiji Allah ya sanya albarka" zokaga murna wajen Abba da Baba Suleman kamoshi Abba yayi ya zaunar dashi kusa dashi nan fa aka gyara zama liman ya daura aure tsakanin AYAAN ABDULRASHEED DA BILKISU ABDULBASY akan sadaki dubu dari da hamsin.
[7/15, 12:21 PM] Ummi Tandama: ♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦


Maman Abd Shakur

29 - 30

Bayan Mama ta kaisu dakin Umma dan nanne ba jama'a sosai sai gaishe gaishe suke sanan Umma ta kwalama Layla kira yarinyar ta shigo da gudunta ta sanya yar atampa ta mai kyau ja ta anko, Umma tace "yi maza jeki kira Bilkisu tazo ta gaishe da baki ai kinsan inda take paty ko?" yarinyar ta gyada kai tana washe baki tana kallon su Mami dasukai shigan alfarma sunyi kyau da sauri ta juya tafita daga dakin, wani gida dake nan kusa da gidansu ta shiga gidan Mrs Alkaleey matar amarya ce badai kirki ba tanason Bilkisu saisa ma tace "tazo itada kawayen ta suyi party anan" da gudu ta shiga babban falon inda kawayen Bilkisu yan dogon Bauchi suka cika ko ina su Fa'iza, Fateema, Walawa, Aisha Shehu, Maryam Umar, Fadila, Bass, Maymuna, Hajjaju, Zainab, Reemar, Hajaea gasunan rututu dai ancika falon Mrs Alkaleey sai hira ake anacin shinkafa da salad ana hiran samari da first night, ganin bata falo yasa tai hanyar bedroom din Mrs Alkaleey kwankwasa kofar tayi akace ta shiga, turawa tayi ta shiga ciki, baki tabude tana kallon Yayar tata da Dr Binta ke kokarin zage mata zip din jan lace dakeda ratsin baki din jikinta, ga Maryam Gafai agefe tana kokarin nada dankwalin da za'a daura mata, takowa tayi tazagayo ta gaban ta ta tsaya tsabagen mamaki hannu tasa ta kama bakinta, Mrs Alkaleey tace "rufe mana bakin ke" washe gibi tayi tace "wlh Anty Baby kinyi mugun kyau" murmushi Bilkisu tayi daya lobar da dimple dinta takara kallon fuskarta ajikin madubi dudda kayan data saka na daidai karfi ne, dan wanan lace din ma Baba ya saimata bai hana kyawunta yafito ba, Maryam Gafai ta rangada mata ubansun dauri, an mata riga na sket da ja da bakin lace din da akama aiki awuyan rigan, tasaka bakin takalmi hill da kuma bakin jakarta mai kyau, an saka mata wani hadadden sarka barawon zinare da dan kunen shi da warwaro harda ma zobe, gashi Dr Binta ta chanchara mata makeup da tunda take bata tabayi ba, anyi parking gashinta anmata donut a tsakiya sanan akai daurin dan kwali mai step aka fito da gashin ta tsakiyan daurin. Tsarki ya tabbata ga ubangijin dayay wanan hallitar! abinda su Reemar keta fadi kenan lokacin data fito falo, Walawa tace "gaskiya Isyaka yau zai sha dadi, anya xai sarara miki kuwa yau idan ankaiki? Kinyi romo romo da yawa yar malam" tai maganan tana wani irin shu'umin murmushi, Fadila tace "koma kakide kakide ne tayi mudai gobe da sassafe zamu faso gidan muzo mu ga yanda take tafiya" dukansu suka fashe da dariya, zama tai akan kujera hawaye ya taru a idanunta sosai zatai kuka dan haka nan taji wani irin kuka takeji duk hankalin ta atashe yake, dafata Mrs Alkaleey tayi tace "karki biye musu kinji ki bata kwalliyar ki, inhar kikai musu kuka haka zasuyi ta zolayar ki" Laylah data kasa dena kallon yar tata tace "Anty Baby Mama ce tace nazo nakira ki wai kinyi baki" ihu dakin ya dauka Bass tace "an daura, an daura su Isyaka ne, tashi kije yar malam amuku wa'azi tare" kaman bazata tashi ba saikuma ta mike tsaye, Raiyana ta dauko bakin gyale mai kyau ta daura mata akai share dan kwallan dataji ya zubo mata tayi ta kalli Reema tace "muje ki rakani" tashi Reema tayi tadau gyalen ta saba akafada suka fita bayan ta kara jan gyalen ta tarufe fuskar ta.

Tunda suka fito daga gidan kanta ke kasa sabida yanda taga maza sun cika layin alamun andaura auren kenen, ahaka har suka shiga cikin gidansu aiko ana ganin ta matan dasuka cika tsakar gidan suka hau guda ayyiririri ga amarya ga amarya, kara lullube fuskar ta tayi har suka shiga dakin Umma da Layla ta nuna musu, Umma ce dake daga bakin kofa ta yaye mata gyalen data rufe fuska dashi tace "ai sai abude fuskar ko tunda kin shigo amarya, ga baki kinyi daga kano iyayen Ayaan ne" dukda bata gane waye Ayaan din da Umma ke fadi ba hakan bai hanata dago kai ta kalli manyan mata biyu dake zaune akan doguwar kujeran ran Umma da aka wadata su da abincin biki agaban suba suma ita suke kallo a kunyace ta dukar dakai ta tsugunna tana wasa da hannayenta dasuka sha lallin amare ahankali tace "ina yinin ku Mumy kunzo lpy" atare Big Mummy da Mami suka amsa mata da lpy lau tareda yima ta godiya akan abinda tama Ayaan, sai a lokacin ma tagane ashe iyayen mara mutuncin mahaukacin nanne, suka mata fatan alheri tareda addu'a zama lpy duk kanta nakasa dan bata yarda sun sake hada ido ba dan kunyan su takeji sosai, Mami ma takasa daina kallonta har kasan ranta takeji kam inama ace Ayaan ya sameta din ya aura da tai farin ciki sosai yarinya mai natsuwa haka da kunya. Ganin takasa tashi yasa Umma tace "to tashi kuje ku koma wajen kawayen ku" ahankali ta mike tsaye tadan kallesu kafin tasake dukar dakai tace "mungode Mummy Allah kiyaye hanya" tajuya da sauri tafita Reema tabiyota abaya tana murmushi suka fito zaure zasu fita waje, tsayawa tayi tana kara lullube fuskar ta da gyale sanan suka fita suka koma gidan party.

Sai bayan sallan la'asar dan lokacin hartai sallan la'asar har an chanza mata kaya wanan karan amtapa ne ajikin ta milk colour anmai kwalliyan black ajiki, wayyo Allah bakaramin kyau Bilkisu tayi ba tasa takalmin dazu baki da gyalen da jakan tana zaune cikin su Walawa daketa mata tsiya Baaba da wata kawarta sukazo gidan, gyalenta suka saka mata sukai mata lullube sanan suka kalli kawayen Baaba tace "kudan bamu aronta" suka fice tana biye dasu abaya har gidan Baaba da babu mutane saidai su Mama, Umma, da bakin dazu na kano datake iya hangosu ta huji hujin gyalen dake jikinta, sallama ababban falon Baaba taji Baaba tayi ta shiga da ita ta zaunar da ita kusa da mutum dabata san kowaye ba, saikuma taji Baaba ta cire gyalen daga kanta ta maida mata dashi kafada kafin tajuya tafita daga dakin, tasami su Mama dasu Mami da ita suke jira duk suka fita daga gidan dan komawa gidan su, kana ganin fuskar Mami kaga farin ciki lullube akan fuskarta, Baba dashi kadaine zaune adakin da Ayaan da aka ijiye Bilkisu kusa dashi dan su Abba basu dade da fita daga gidanba sunje dauko wasu abokan shi daya kira ya fadi musu zancen auren Ayaan, ajiyar zuciya Baba yayi yana tausayin yanda ma zai fadama yar tashi abinda Isyaka yayi hakanan dai ya tatataro jarumtar shi ya fuskanceta yakira sunanta "Bilkisu" dago kai tayi ta kalli Baban nata tace "na'am Baba" yace "inaso ki zama jaruma mai karban kaddara aduk yanda tazo mata, karki sa komi aranka ki dauka komi yafaru ne ayanda Allah yakeso, ahaka Allah ya tsara tun kafin ma a hallice mu" yadanyi shiru kafin ya nisa yace "yau awurin daurin aure Isyaka ya tashi agaban kowa" saikuma yay shiru kafin yay murmushi me ciwo yace "yace yafasa auren ki baya sonki yajuya yama fita daga masallacin abinshi" tunda yafara maganan ta dago kai take kallon mahaifin nata badadan shi bane ke gayamata maganan nanba da wlh zata iya cewa karyane Isyakan ta bazai taba yimata hakaba, yace "bazai aure kiba, shine dama mahaifin Ayaan yataba zuba nemama danshi auren ki lokacin ankusa bikin ki da Isyaka, shine yau bayan abin yafaru Ayaan yace shi abashi yana sonki shine nasa aka daura auren ki da Ayaan ga sadakin ki nan" ya daura mata kudin ajiki, kaman ma bata duniyar nan haka takejin ta Isyaka yace bazai aureta ba, andaura mata aure da Ayaan din dabama tasan wayeshi ba, dan bilhakki takara manta wani Ayaan, Isyaka na ne yace "bazai aureni ba?" da sauri ta kalli Baba da rinannun idanunta dasuka cicciko da hawaye dan shima ita yake kallo tace "Baba Isyaku nane yace bazai aureni ba? Menamai Baba, wlh banmai komiba dan Allah kace yayakuri Baba" tafashe da kuka sosai kaman zata mutu, Baba ya girgiza mata kai yace "i shiru ki manta da zancen isyaka danke matar wani ce yanzu, nasan ban kyauta miki ba dan banji ta bakinki ba, amma a matsayina na uba zan iya zaba miki miji nagari daga ganin Ayaan yaron ne dan gidan arziki, ga mahaifin shi da kirki da daraja musulmai, nariga na musu bayanin jarabawan da zaki zana sun amince daki zauna agida bayan gama jarabawan saiki tare, yanzu dai bari na barku tare kudan tattauna ni natafi wajen su mahaifin ka" yay maganan yana kallon Ayaan da kanshi ke kasa tun dazu, dago kai yayi ya kakalo murmushi yace "to Abba" Baba yafita yana kallon Bilkisu dake wani irin kuka dake tabamai zuciya gidan yarage daga shi sai ita.

Baba nafita tamike tsaye zata fita dan bama tason ganin koma waye mijin da Abba yace yamata, hanyar fita daga dakin tayi cikin kuka fuuu taji an wani irin fincikota danhar saida gyalenta yafadi kasa saura kiris tafada kanshi amma ganin wanda take shirin fadawa jikinshi yasa ta dage ta tare kanta tafadi agabanshi tana kuka, wanan mugun Baba ya aura mata dama, wutsiyar hanunta daya kama tabi da kallo, hawaye masu dumi suka zubomata tafara kokarin fizge hanun nata amma yaki sakinta saima wani irin matsiyacin kallo dayay yace "Ke! bazaki natsu ba" ko kallon shi bataiba saima daddagewa data keyi zata fizge hannun, hannun yabi da kallo ba karamin kyau lallen yayiba barinma yatsunan ta da dogayen kumbunan ta da aka zagaye su da ja, yasake mata wani irin kallon yadanyi murmushin gefen baki yace "bakiji dadi bama na taimaka miki? Wanan kazamin yaron yace baya sonki shine nace ni bari indan rufamiki asiri sabida tausayin mahaifin ki danaga hawan jini yana neman kamashi za'ai abun kunya, shine na taimaki rayuwan ki inda bahaka ba mezanyi dake jibeki fa dan Allah" wani irin bakin ciki da maganganun shi yasa taji yasa ta daddage taja wata shegiyar tsaki. "mtswwww" fizgota yay wanan karan saida tafado a kirjinshi, gabaki daya hanunta daya rike yamaida shi ta baya ya lankwasa hakan yasa tai wani irin ihu. "wayyo Allah Mama zai kasheni" tafashe da kuka mara sauti jikinta ko ina rawa yake, dan lumshe ido yayi jin yanda numfashin ta na kuka ke sauka akan fuskarshi kafin ya budesu ya sauke akan hawayen dakebin kuncinta ba kakkautawa ya daure fuska tamau tareda sake matse hannun tabaya ihu tayi sosai har saida ta bankare ta daura dayan hanunta akan kafadarshi duk cikin azaba, hanun yabi dawani irin kallo da sauri ta janye tana kuka sosai tana yarfe hannun harda shesheka, sakinta yayi tareda tureta harsaida ta fadi akasan wajen ta tashi ta zauna da sauri ta kamo hanun daya kama tana kallon yanda yay ja takara fashewa da kuka tana hurama hanun iskan bakinta dan zafi yake mata, tsaki yay yafita daga dakin, akofar gidan yaga su Abba da abokanen shi dasuka zo tareda Malam ya gaidasu sanan yaja Abban shi gefe kaman zaiyi kuka yace "Pops am going to the hotel nidai nagaji wlh i need to sleep" da sauri Pops yataba kanshi yace "shikenan Mah Boy jeka huta muma dasu maman ka Anjima bayan Isha zamu dawo hotel din, gobe da safe zamu dawo akara gaishe gaishe da sanin juna kafin mu wuce kano ko" gyada kai kawai yayi yawuce ya shiga mota yaja yabar wajen.
[7/15, 12:21 PM] Ummi Tandama: ♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦


Maman Abd Shakur

31 - 32

Anan falon Baaba taci kukan ta ta koshi, ji take kaman tahadi yi zuciya ta mutu maisa Baba yamata haka tunda Isyaka yace bayayi basai abarta ba anwani hadata da wanan basamuden mugun, ahaka bacci yay awon gaba da ita a wurin.
Hayaniyan dataji yatada ita daga baccin daya dauketa Baaba tagani zaune da wasu bakin gidansu dasuka zo daga kauye anata hiran rabon kudin da Abba yay tayi, fashewa tai da kuka hakan yasa suka lura ma tatashi Baaba tace "hakuri zakiyi ai Isyaku duniya ce tanada girma yama kanshi, ki yakuri ba gashi Allah ya musanya miki ba mai sonki wanda kika taimaka, ni wlh inxakiji ta tawama kinfi dacewa dashi, tashi kije kiyo salla kici abincin ki karfe sha biyu fa" tashi tayi ta karbi toculan da Baaba ke mikamata ta karba tafita daga dakin ta wuce yo alwala.

Misalin karfe takwas na safe tafito daga wanka daure da zani a kirji Baaba dake zaune gaban murhu ta bita da kallo yanda take uban sheki, murmushi tayi tajuya tacigaba da dama kokon datake yi, daki ta shiga ta shafa mai ta shirya cikin doguwar rigan kampala shaddan purple da fari da Baaba ta iniye mata aiko yay mata shegen kyau tana cikin fama da daurin dankwalin dan takasa sabida dan kwalin yay kaba kaba Baaba ta shigo tace "ke imaza yapa gyalen tunda kin kasa daurin kije Baban ki ya aiko Muji ya kiraki iyayen mijin ki suna hanya zakuyi sallama su tafi, mike" Baaba ta dagata ganin bamata da niyyar tashi tadau gyalen ta yafa mata tace "imaza tafi nima ganinan zuwa" fita tayi daga gidan jikinta duk asake har gidan su da babu wasu mutane sosai dan yan uwan su kadanne suka rage dakinsu tayi tana shiga uwar daka tafada kan Maman su tafashe da kuka sosai dagota Mama tayi ta share mata hawayen dasuke zubowa tace "kiyakuri Baby, nasan yanda kikeji, haka Allah ya kaddara zai faru dama chan Isyaka ba mijin ki bane, bahakanan Allah ke hadaka da wani arayuwa ba rana daya ba, kin hadu da Ayaan ta dalili ne, asheko shine wanan mijinki, ki yakuri kinji anriga andaura babu yanda zakiyi" cikin kuka tabude baki zatai magana Mama ta girgiza mata kai tace "banison ji" sallaman da akayi yasa Mama ta amsa ta fita ganin Mami ce itakadai dan sauran duk sun shiga falon Baba yasa Mama tai murmushi tace "barka da zuwa kun iso, shigo" shigowa Mami tai tasami waje ta zauna tace "ina kwana ya gajiyan bik" Mama tace "lpy lau ya taku gajiyar" murmushi Mami tayi tace "Alhamdulillah ina yar tawa?" murmushi sosai Mama tayi tace "tana ciki bari nakira miki ita" da sauri Mami tace "a'a kibarshi dan Allah ni nashiga?" a kunyace Mama tace "kai dan Allah keda yarki kike wani tambayana, ni kinga ma tafiyata bari naje agaggaisa" Mama tadau hijabi ta fice zuwa dakin Baba, Mami ta daga labulen da sallama ta shiga dakin, a kunyace ta mike tsaye dan taji Mama na magana bama ta tsaya ta saurara ba sabida kukan ta take, tsugunnawa tayi tanadan murmushi ahankali tace "ina kwana Mumy" hannu Mami tasa ta dagota sama kafin ta sumbaci gaban goshin ta, lumshe ido tai a kunyace dan bata sababa, Mami ta zauna da ita akan gado kafin ta zauna agefenta tana murmushi tace "Allah miki albarka Bilkisu kiyakuri kinji, Ayaan zai kula dake karkija komi zamu rikeki amana" jakar hannunta ta bude ta ciro wata sabuwar Samsung ta mika mata kin karba tayi saima kara sunnar da kanta kasa datayi tana wasa da bakin gyalenta, ajiye mata wayar Mami tai agefe tace "ga wayar kinan nasamiki number na aciki, zan dinga kiranki, kiyi karatun jarabawa da kyau kinji Allah yabada sa'a" ahankali tace "nagode Mumy" shafa kuncinta Mami tayi kafin ta tashi tafita daga dakin itama ta shiga falon Baba anata magana.
Fadawa tayi kan gado tafashe da kuka sosai tarasa inda zatasaka ranta taji dadi, zumbur tamike kaman an tsikareta tafito daga dakin Maman ahankali tai hanyar zaure tana tafiya sadaf sadaf tana bude kofa tafita zaure saida tadan labe abayan kofa kafin tadan leka kofar gidan kosu Baba nanan awaje ganin babu kowa sai kusan motoci uku dake fake akofar gidan nasu akukkule yasa tai wuf tafito, tana waige waige ganin lallai ba kowa dan ko almajiri daya babu yasa ta gyara gyalen kanta tareda tattare doguwar rigar dan tadan mata tsawo ta arce a guje.
Ayaan da tunda take leke leken ta daga bayan kofa yake kallon ta dan yana cikin mota ya kunna AC yana sha, gajiya yay da surutan su yay fitowar shi waje, dayake glass din motar tinted ne saisa bata lura dashi ba, gyara zama yay ya kalli madubin window motar yanda take tafiya gudu gudu, sauri sauri ya kafeta da ido tareda hade hannayen shi biyu ya dunkule yakai karamar yatsan shi daya yadaura akan lips dinshi kaman mai tunani, ganin tasha layin tai kwana yasa ya kunna motar yaja yabita.

Babban wuri ne haka da akamai runfa sabida asamu inuwa, mutane ne zazzaune daketa aikin hannu, wasu na sakan hula wasu kuma na aikin wuyar shadda, da sauri da sauri take karasawa wajen fatanta Allah yasa ta ganshi anan dan tasan baida wajen zuwa sai nan, anan duka abokan shi suke, tsayawa awurin tayi tana kalle kalle ganin bashi awurin kaman ance ta daga kai ta hangoshi kan bencin dake gaban wani shagon dake gefen wajen, ga yar jaka agabanshi yanata diban kayanshi dake gefenshi akan bencin yana jerasu acikin jakar, da gudu tai wurin tana share hawayen dataji yafara kwararowa, kaman daga sama yaji ance "mena maka kafasa aure na?" dago kai yayi asanyaye ya kalleta gani tayi idanunshi sunyi jajir suma harma sun kumbura, kasa daurewa tayi tafashe da kuka sosai tasa gyalenta tana sharewa bata ma damu da mutanen dake shiga shagon siyan abu bama cikin kuka tace "maiya sameka idanunka sukai haka? Mena maka? Maiya sa kace kafasa aure ne kasan illar da hakan yamun kuwa? Inda kasan baka sona maiya sa tuntuni baka fadaba sai a wurin daurin aure? Maisa kamin haka eh?" baki yabude zaiyi magana saikuma yafasa yay shiru taga ya kurama bayanta ido, da sauri ta juya dan taga maiyake kallo Ayaan ne acikin mota yay wining glass down idanunshi sanye cikin bakin glasses, daure fuska yay tamau ya kalleta babu alamun wasa atattare dashi yace "get in" kaman bada ita yake ba ta juya ta kalli Isyaka daya cigaba da hada kaya abinshi kaman bashi a wurin tace "kasan yanda nake sonka kuwa shine ka cutar dani haka ko, maiya sa kamin abinda kami..." tsawan dataji yasa takasa karashe maganan datake yi. "are u deaf nace kishiga mota mutafi" yay maganan har lokacin yana zaune cikin mota afirgice ta juyo tafashe da kuka sosai batare data shiga motar ba mutane sai kallon su suke, bude kofar yayi yafito yana wani irin taku da duk taku daya saitaji har a kokon ranta, da sauri ta runtse ido sabida wani irin mugun tsoron dataji yana shigan ta, hanunta dataji ya fizga kaman zai katsa yasa ta bude ido janta yayi ya bude mota ya wurgarta ciki kafin ya koma ta dayan side din yanama Isyaka dasuka hada ido wani irin kallo, da sauri Isyaka yadau jakar ya juyama motar baya kirjinshi na bugawa, wani irin dan iskan murmushi yayi kafin ya bude motar ya shiga ya bata wuta, kuka take kaman ranta zai fita kanta nakan cinya.

Bai tsaya ko inaba sai gidan dam, wurin babu kowa gashi very peaceful sai iskan bishiyoyin daketa kadawa da kukan tsintsaye dake wucewa, zagayawa yay ya bude side din datake har lokacin kanta nakan cinyanta kuka take sosai cikin kakkausar murya yace "fito" ko dago kai batayi ba balle yasa ran zata fito, hakan yasa ya jawota da karfi luuu ta taho zata fada kanshi dan ko karfi daya bataji dan rabonta da abinci tun jiya ya matsa gefe da sauri hakan yasa ta zube akasa, wani wahalanlen kuka tasaki ahankali tana share guwiwar hannunta daya bugu da kasa, ya dawo ta gabanta yay wani irin tsugunnawa daya karamai kyau yana karkada key motar dake hanunshi yana mata wani irin kallo yace "baki da natsuwa ko, bakisan kinada aure ba zakije kina ma wanchan dan kauyen magana" turo baki tai cikin kunci tace "Isyaka na niba dan kauye bane karka sake cemai dan kauye" takarashe maganan tana wani lankawasa wuya gawasu sababbin hawaye dasuka zubo mata tsabagen takaici, dagota yay da karfi ya jingineta jikin mota ya kafeta da ido da sauri ta kawad dakai tareda sa bayan hannu tana goge kwallan yace "ke ki natsu fa banason raini ko kadan wlh, auren taimako nayi, na taimake ki da mahaifin ki danaga hawan jini na neman kamashi da almajirin chan yace yafasa auren ki" murguda mai baki tayi dan wlh yakaita bango tace "eh almajirin ne aidai Allah ya halicce shi, kuma ahaka nakeson abuna har yanz..." bakinta daya kaima duka da karfi yasa tai shiru ta fashe da kuka, hanunta ya kama yakai baya ya murde hakan yasa ta bankare tana ihu. "wayyo Allah na Mama zai ciremin hannu" hadata yay da mota ya matseta danhar jikinsu na gogan juna ya kalli kwayar idonta yace "wlh idan kika sakemin rashin kunya sai namiki abinda zaki dinga kuka tunda ga yau har ranan daza'a kawoki gidana".....
[7/17, 11:57 AM] +234 814 359 8303: ♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦


Maman Abd Shakur

33 - 34

Ya ja hanunta ya bude side dinta ya wurgata ciki kafin ya koma mazaunin driver ya shiga ya yatada motar yabar wajen, duk tacika mai mota da kuka abakin layin su yay niyar sauketa hango su Abba da Malam awaje yasa yawani dakamata tsawa. "ke!" atsorace ta dago kai ta kallai hannu ya daura akan lips dinshi alamun tai shiru hakan yasa ko tai shiru har yakarasa kofar gidansu, aiko su Abba sukabi motar da kallo parking yay yafito da sauri ya zagayo ta inda take ya bude mata daidai nan su Walawa dasuka zo wurinta suka fito daga gidansu, murmushi both Abba da Baba harda Baba Sulaiman duk sukayi hankalin su yakara kwanciya ganin Ayaan da Bilkisu tare. Fitowa tayi daidai lokacin su Walawa sun iso sai kallonshi suke atare suka gaidashi "ango ina yini, ina kukaje kaida Amaryan tun dazu mukaxo fa" murmushin dole ya kakalo ganin su Abba a wajen itakuma wucewa tai cikin gida abinta, su Walawa sai uban surutu suke mai yana yake daga baya sukamai sallama rapper kudi yaciro yabasu suka karba sukamai godiya kafin su koma cikin gidan.
Sai bayan azahar suka tafi bayan sun cika gidan da kayan abinci da kudi duk yanda malam yaso yaki karba kin yarda Abba yayi yace ai yanzu anzama daya kafin su wuce kano kowanensu rai fess.

**************
Tun tanama su Umma, Mama da Baaba kuku asaurareta ana lallabata har yazo kowa yafita harkan ta to uban ma me zasu iya aure dai anriga an daura saidai kuma abisu da fatan alheri, ganin babu mai sauraron ta danhar su Walawa sunfison Ayaan sunce mezatayi da Isyaka daya wulakan tata ranan daurin aure yace bayaso, tama godema Allah yaro dan gayu yace yanayi, hakadai ta tattara ta manta da alamarin tacigaba da zuwa school abinta ta dage da karatun exam, Mami na yawan kiranta ganin haka yasa duk Friday

Please Login or Register in order to submit comment