Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Mami tace "menene ba yanzu nan yabar nan ba bayan yay treating kafar hajiya baima tsaya ya auna BP taba fa haka Munari takece min" girgiza kai Abba yayi yace "sako hijabi ki sameni akasa, Boy doesn't sound gud something is wrong" yana maganan yana fita Mami tadau babbar hijabin ta saka ta bishi abaya, Big Mum suka gani tana dingisawa tana zuwa sanye da hijabi hanunta rike da plate tana ganin Mami da Alhaji tace "ina zaku haka nida nazo na debi fruits a fridge nawa ya kare" Mami tace "ga Alhaji nan shinake bi wai Ayaan ba lpy" arude big mumy ta kalli Abba tace "meya sami Boy Alhaji? Mutafi mutafi mugano danmu" gaba Abba yayi suna biye dashi Big Mum ta kalli Mami tace "kedai wlh Allah wadaran halinki Ayaan baida lpy ne shine wai Ayaan" direba Abba yakira ya shiga duk suka shiga aka jasu sai gidan Ayaan.
Yanayin parking motar Ayaan dasuka gani awajen yasa Abba yacema driver yay parking duk suka sassauko Abba ne yafara shiga tsakar gidan ko lura damai gadi ma baiyi ba sai Ayaan daya hango a tsugunne jikinshi nawani irin rawa uncontrollably, da sauri Abba yay kanshi yana "Boy, Boy" dago shi Abba yay yay cupping fuskarshi, hanun Abba yakama gam gam yarike da kyar ya bude baki yace "Pops where is mah wife?" hanunshi Abba yakama ganin kaman ma baya hayyacin shi yay cikin gida dashi yana binshi luuu su Mami suka bisu abaya hankali tashi, shikuma direba ya taimaka ma mai gadi ya shigar dashi dakinshi ya kwantar dashi yanamai sannu.
Zaunar dashi Abba yayi yana kallon jinin daya ga a stairs bakinshi na furta "innalillahi wa innalillahi raji'un" Big Mum tafashe da kuka sosai ya kalli Mami datai shiru tana kallon Ayaan da jikinshi ke wani irin rawa hancinshi jini na zuba yace "ban ruwa Firdausi, mara sanyi" da sauri Mami tai kitchen ta dauko goran ever mara sanyi ta bude ta mikamai Abba ya karba da hannu daya dayan hanun nakan kafadar Ayaan yakai goran bakinshi yana tofamai addu'o'i, Kukan da big Mum keyi yasa Abba ya dakama ta tsawa akule yace "ke kokimana addu'a kokiyi shiru" yasama Ayaan goran abaki ya tsiyaya mai ruwan da kyar yasha sanan yadawo kusa dashi ya zauna ya kwanto dashi yadaura kanshi akan cinyarshi yana kara tofamai addu'an ko jikinshi zai dena rawan, kafin yaciro wayarshi daga aljihu number governor kano yakira gabaki daya, ringing biyu gwamna da kanshi da dauka, Abba yamai explaning abinda ke faruwa.

Within 15 good minutes karan motocin police kakeji suna shigowa anguwa, ansace matar da tilo ga Abdulrasheed Gwanaye ai dole gwamna dakanshi ya turo polisawan, tundaga waje CP yafara saka team dinshi bincike wasu na interrogating mai gadi daya farfado kafin yazo da kanshi har bakin kofa yay sallama Mami tabashi izinin shigowa shida wasu manya police guda uku suka shigo ya tura biyu dake tareda shi sama bincike sanan ya zauna kusa da Abba dake ma Ayaan dahar lokacin bai dawo daidaiba addu'a, saida Abba ya idar sanan ya nisa yace "Alhaji naga akwai CCTV camera a compound din" sai a lokacin ma Abba yatuna yace "harda ma falon nan akwai" IG yace "ina computer to zanzo mu kalla dan musan meya faru" da kyar ya mike tsaye Abba ya rike shi yace "Boy" gyada ma Abba kai yayi da kyar alamun zai iya, Abba yarike shi sukai sama IG nabiye dasu abaya, Mami da big Mummy ma suka bisu, wani daki sukaje nan suka tariyo computer har zuwa daidai inda goons din sukazo sukai horn mai gadi yafita waje dubawa sai gashi daya daga cikin su sanye da mask ya shigo da mai gadi yana dukanshi kafin ya sumar dashi ya bude musu gate bakin van din ya shigo, pursing video IG yayi ya rubuta plate number motar down sanan ya danna play suka cigaba da kallo gashi sun shigo sun fiffito daga motar sunyi cikin gidan sun bude kofa sun shiga falo sukai upstairs, dayake babu CCTV a sama basu ga maiya faru ba saidai ihunta dasuke ji da lokacin datake kiran Ya Ayaan, runtse idonshi yay da karfi wasu hawaye masu bala'in zafi suka zubomai da sauri ya share, saikuma inda daya daga cikin su yasa kafa yatokare mata ciki tafado ta fasa kai wani irin dunkule hannu yayi zai daki computer da sauri IG ya rike shi calmly yace "be strong Man, i know how u feeling, zamu kamasu idan ma kidnappers ne dan basuyi kama da yan fashi ba, inda yan fashi ne da sata xasuyi, indai har kidnappers ne zasuyi contacting dinku, so u people should stay alert zasu iya kiranku kowani lokaci, yanzu dai one good thing is zamu nemo motar nan tasu ta hanyar plate number nan koma ina motar take a fadin kanon nan, sanan Alhaji" ya kalli Abba yace "yakama ta yanzu akwai body guard dazasu dinga yawo da family ka most especially ur son, yanzu dai zan koma office zan zuba team dina akowani hanya da express way na barin garin kano zamu kamasu da izinin Allah, one last thing is i need hoton ta, dan nan CCTV footage fuskar ta is not clear sosai dan musa a media incase idan wani yagan ta" Da sauri Abba ya kalleshi yace "kanada hoton ta Boy kabamu?" saida yarike hanun Abba sanan ya iya magana da kyar yace "yafashe" Abba ya kalli Cp yace "wayarshi tafashe dazu amma zasu samo hoto bari yadawo daidai tukun" ajiyar zuciya cp ya sauke yace "shikenan we will use dis for now, please take care of him he doesn't look good" yanuna ma Abba Ayaan sanan yawuce yafita daga dakin, da taimakon Abba suka fito sabida jirin dayake ji sosai suka zauna afalon sama ya daura kanshi akan kafadar Abba shi kadai yasan yanda yakeji, Abba sai addu'a yakemai jin yanda zuciyar shi kewani irin rawa, tashi Big Mum tayi ta kalli Mami datai wani irin tagumi daurewa kawai take danji take kaman tai ihu tace "bare na shiga bayan gida" gyda mata kai kawai Mami ta iyayi tai shiru tana tunani abu kaman mafarki Bilkisu da dazu dazun nan tana tare da ita, da dingishi Big Mummy ta shiga dakin dake kusa dana Bilkisu ta maida kofar ta rufe, bayi ta shiga ta rufe sanan tafito da wayarta daga zani wacce tuntuni ta maidata silent, message din Bala tagani da sauri tabude;
“hajiya mun dauketan muna warehouse din saidai fa, Ahmad ya bugeta sabida gardaman dataso tamana kanta yafashe har yanzu bata farfado ba”
Da sauri big Mummy tamai reply
“Bala bakace min gobe zakaje Bauchi ba, inaso da daddaren nan kudau hanyar Bauchi kunemi wani daji achan ku karasata kuyar, sabida yanzunan za'a baza police ako ina agarin nan, banason ko gawanta su tsinta agarin nan, ka tabbatar bata numfashin daga yanda nake ganin yaron ma dazaran ta mutun shima rayuwar tashi karewa zatayi, ka tabbatar kunbar garin nan yanzu, yanzunan zakaji alert din kudi, kudin aikin ka kuma saina tabbatar kai komi da kyau sanan zan biyaka miliyan goma, kubar garin nan yanzu, i repeat yanzu! ". Tura mishi dubu dari tayi sanan ta kashe wayar gaba daya ta wanke fuskarta tafito daga bayin tadawo ta dayan gefen Ayaan ta zauna tana tofamai addu'a tana matse kwalla, ahankali Mami ta tashi ta dauro alwala ta shiga daya daga cikin dakunan tafara salla.

Bala na ganin text dinta ya kinkimeta yasata amota sauran ma suka shiga suka bar gidan.


Shigowa dakinshi Abba yayi dauke da cup din coffee da Mami tahada mai, yana zaune ya jinginar da kanshi a bangon gado ya lumshe ido, lokaci daya wani irin hadadden zazzabi ya sauko mai, zama kusa dashi Abba yayi yana dafe kafadar shi tareda ijiye tea akan bedside drawer ahankali yace "Boy" fadawa yay jikin Abba murya chan Kass dake rawa sosai yace "Pops please bring her back, Pops dan Allah kace sudawo min da ita konawa suke so zanbasu or they should take me instead" ba karamin tashi hankalin Abba yayiba bayason abinda zai tabamai Ayaan, Ayaan nada mugun rauni akan abinda yakeso wanan tun yana karami yasan da haka, wlh koma su waye suka dauke Bilkisu sai yasa hukuma tamusu hukuncin daya dace dasu, daga kanta bazasu sake marmarin dauke wani arayuwar su ba. Ahankali yace "i promise u, Boy i promise you, ko ina ma suka kaita saimun nemota, even if it takes nai hiring private investigator, even if it means putting all i habe at stake saina nemo ma matarka, i promise u Son, don't worry wanan alkawarin baban kane" sake kankame Abba yayi sosai saiga hawaye shar sun zubo da kyar yace "Pops they hit her, she's hurt, kanta yafashe, Pops he dare hit mah wife wlh saina ka.." hawaye yahana shi karasawa, yafashe da kuka ahankali yana shesheka ajikin Abba, bakaramin damuwa Abba yay ba rabon daya ga kukan Ayaan tun yana grade1, haka yadinga lallashin shi, ranan yanda sukaga rana haka sukaga dare dan wani irin ciwo ne da mugun zazzabi yarufe Ayaan sosai, koda gari yawaye baya gani da kyau tsabagen zafin zazzabin Mami takira Dr.


Wuraren biyar na yamma suka shigo garin bauchi sundanyi tafiya mai nisa kafin suyi parking agaban wani daji, wani babban buhu daya daga cikin su ya dauko yazo inda take kwance kaman matatta dan sunma dauka ta mutu ne, ya bude bakin buhun da kyau biyu daga cikin su suka ciccibeta suka sakata aciki suka kulle bakin buhun sanan wanda ke tukin yafito yazo tabaya ya bude musu suka daukota da sauri sukai cikin dajin da ita da saurin bala'i. Jogging din daya sabayi kullum da yamma tunda yazo farm house din Abban shi hutu yauma yafito yanayi, sanye yake da singlet din sport mai ruwan toka da dogon wando shima mai ruwan toka kafanshi sanye da bakin sport shoe sai kanshi acikin head phone yana jogging abinshi tunda idanunshi suka sauka akan bakin van yaji baida natsuwa, barin ma lokacin dayaga sun fito dawani babban brown sack sunyi cikin dajin dashi hakan yasa yaji bai yarda dasuba, labewa yay abayan wani bishiya har suka fito duk yana kallon fuskar su kafin yaga sun shiga cikin van din sun tada sun tafi, da sauri yay cikin dajin daidai ta inda yaga sun fito yasa hannu ya janye headphone din daga kanshi ya maida wuyanshi sanan ya cigaba da tafiya da sauri sauri yana shiga dajin yana kalle kalle amma baiga buhun ba har yay giving up yana shirin ya juyo yaga buhun akan wani babban dutse da sauri yay wurin yana addu'a, ahankali yay bismillah ya daura hannunshi akan buhun yana tattabawa jin kaman mutum yasa yay maza ya kwance daurin bakin buhun da kafafun ta yafara cin karo, ahankali hanunshi na rawa yay bismillah ya daura akan feet dinta kafin yadan dago takan ya zare buhun gabaki daya daga jikinta, yabi jinun daya bata goshin ta da kallo, da sauri ya kamo hanunta yana checking pulse dinta ganin akwai yasa yagane da ranta, da sauri ya ciccibeta yana kallon fuskar ta kaman yay kuka yafita daga dajin da mugun gudu baxai ma iya komawa farm house ya dauko car ba hakan yasa ya tare wani me machine din dake zuwa yahau kai yace kai ni town hospital. Yana zuwa hospital wani babban abokin shi mai suna Dr Ameenu ya karbeta aka taru akanta.


*Kano*
Ayaan fa gashinan gashinan ne, kaman zararre kaman lafiyayye baida aiki se sumbatun kiran sunan Bilkisu kokuma yadau filo yarike yanama filo magana, Abba yay yay dashi sukoma gida yaki ya makale adakin Bilkisu anan yake kwana yarike kayanta gam ya rungume yana fadin am sorry, am sorry, please come back. Big Mum dadi kaman zai kasheta har addu'a take Allah sa bakin cikin rashinta yasa yama mutu gabaki daya yanda dazaran Alhaji shima yamutu ta rike dukiyar gam gam.
Babu wanda yataba kawo tanada hand abacewar Bilkisu, anjira anjira yan kidnappers din sukira amma shiru.

Yau satin ta biyu a hospital din, kullum Guy din daya kawota yake zuwa dubata duk wani kudi da akai bukata na treatment dinta zai biya.
Yauma kaman kullum misalin karfe biyar yay parking motar shi a parking lot din asibitin ya fito yana sanye da farin lallausar yadi daya haska chocolate fatar shi, sai uban kamshi yake yay cikin asibitin yana taku daidai yana kada key mota daya rike yay office din Dr Ameenu kai tsaye, Dr Ameenu na ganinshi ya nunashi da yatsa yace "kaiko Aaman sai shegen gayu babu matan aure tuzurun banza kawai" tabe baki yayi tareda fizge cold bottle water dake hannu Dr ya zauna akan kujera saida yadan sha ruwa kadan sanan yaja tsaki yace "sabida kadanyi aure last month ne zaka faramin iskanci, lallai muma Allah bamu masu sonmu" yay magana yana shafa dan gajeren gemunshi sanan yaja wata yar siriruwar tsaki agajiye yace "ya patient dina har yanzu bata tashi daga coma bawai" gyara zama Dr Aminu yayi yace "i think rashin tashin ta has something to do with buguwan kanta, but once ta tashi we will conduct some special test akanta, but let's just wait till then" ahankali yace "okay" kafin ya mike tsaye dauke da ruwan goran a hanunshi yace "bari naduba ta" yafita daga office din dakin dayasa asata na mutum daya yaje ahankali ya bude kofan ya shiga yana kallonta har yanzu tana kwance as usual cikin kayan asibiti da nurses suka saka mata bambamcin kawai yau babu oxygen din da aka saba samata, kanta nannade da bandeji, kujera yaja ya zauna yadan kalleta nayan mintina kafin ya jingina goran ruwan daya dauko a jiki ya tura hanunshi acikin aljihu ya ciro wayarshi yana daddannawa. Motsin dayaga bargon da aka lullube dashi nayi yasa ya tsaya da danna wayar dayake yi ya dago kai ya kalli fuskarta, motsin dayaga saman idonta nayi yasa yadan matso da kujeran shi kusa da gadon yana kallonta batare dayace komiba, motsin data fara sosai yasa yay magana cikin calm voice dinshi yace "Hey open ur eyes, u are safe now" motsi tacigaba dayi kafin ahankali tabude idonta suna rawa harta bude duka ta saukesu akan fuskar wani mutum data gani yana kallonta ga cool murmushi akan fuskar shi, dakin tabi da kallo tana jujjuya kai tana wani irin fir fir da ido kafin idanunta su sauka akan goran ruwan data gani akan jikinshi da sauri ta yunkuru zata tashi da sauri ta dafe kanta tasaki wani irin kuka, da sauri yadan matso yace "careful" da karfin tsiya ta tashi zaune ta fizgo ruwan data gani ajikinshi tana dambe da ruwan tana kokarin budewa amma takasa hakan yasa ya tsaya yana kallonta, fashewa tasake yi sosai da kuka tana dafe kanta dake mata zafi, ahankali ya mika hannu ya karbi ruwan zata fizge ya girgiza mata kai ya bude marfin ya mika mata, karba tayi da sauri ta kafa abaki wani irin mugun kishi takeji, daidai lokacin aka bude kofar dakin afirgice ta saki ruwan hanunta tai wani irin ihu da yasa ya kalleta da sauri dan dama kofar ya kalla sanin either Dr ko nurse ne zasu shigo, tsalle tayi ta diro daga gadon ta labe abayan shi tafashe da kuka tana bobboye wa, da sauri Dr Aminu ya karaso da murmushi kan fuskarshi yace "wow alhamdulillah at long last yaushe ta farka Aaman?" matsawa yayi sabida Dr ya ganta da kyau tasake biyoshi ta labe abayan shi, ahankali ya juyo hanunshi daya cikin aljihun shi ya nuna Dr Aminu yace "he's ur doctor zoki zauna" ya koma ta wurin gadon da sauri ta sake bishi ta tsaya a inda ya tsaya tana tana kallon fuskarshi hakan yasa yama Dr Aminu kallon irin wats wrong with her dinan, singnal da hannu Dr Aminu yamai hakan yasa yakara kwantar da murya ya nuna mata gado yace "sit" makemai kafada tayi, hakan yasa ya zauna abakin gadon da sauri itama ta zauna tana kallon fuskarshi, dan murmushi yay mata yace "sunana Barrister Aaman Muhammad, nina ganki lokacin wayansu sun shigar dake daji acikin buhu sun yar, now i need you to tell me who you are sabida mu kira iyayen ki suzo su dauke ki, Ya sunanki?" tunda yake maganan ta kafeshi da ido ko motsi batayi, anatse yace "ya sunanki?" nuna kanta tayi akaro na farko tai magana cikin siririyar muryarta tace "ni?" gyada mata kai yayi ahankali tace "nima bansani ba, ya sunana?" ta wurgamai tambayar itama tareda tsareshi da ido tana kallon fuskarshi, da sauri ya kalli Dr Aminu, dan matsowa Dr Aminu yayi hakan yasa ta matsa kusa da Aaman da sauri hartana neman bigeshi da sauri ya matsa, ganin haka yasa Dr ya tsaya batare daya karaso ba ya kalleta yace "fadama na waye baban ki to" da sauri ta nuna Aaman, kallan kallo daga Aaman har Dr Aminu sukayi hakan yasa Dr yace "wanan bashine baban kiba, waye Maman ki to?" sake nuna Aaman tayi, ahankali Dr ya kalli Aaman yace "muje office" yay gaba Aaman ya mike tsaye da sauri itama ta mike ya kalleta yace "jirani ina zuwa" makemai kafada tayi kaman yarinyar tafashe da kuka da sauri ya kalli Dr Aminu daya tsaya ya kallesu yace "wai meke damunta ne?" ajiyar zuciya Dr Aminu ya sauke yace "inhar abinda nake tunani hakane inaga nin sanadiyar injury data samu akai yasa tasami shafewan kwakwalwa, ma'ana she lost her memory saisa kaga kaida tafara gani tasani take yarda dashi, yanzu u are her everything kai zaka koya mata sabawa da yarda da mutane for now kafin mu dubata musan wani treatment zamu daurata akai".
♦♦ *SANGARTATTCE* ♦♦




Maman Abd Shakur

63 - 64

Dan juyo dakai yayi ya kalleta nayan sakanni yana nazarin abinda Dr yafada, gashi tawani labe abayan shi tana wani zazzaro ido, yujawa yayi ya kalli Dr Aminu yace "Man come and examine her please" ya matsa gefe da sauri tasake binshi kaman zata shige jikinshi hakan yasa ya juyo da niyar mata masifa ganin yanda take kallonshi yasa yakasa ya nuna mata bed yace "sit" make mai kafada tayi kaman zatai kuka tana shafa cikinta tana kallonshi da sauri ya dauke kai yace "menene?" da kyar tace "yunwa" juyo dakai yayi ya kalleta yace "sit lemme get food for you" zama tayi ya juya zaiyi wajen Dr Aminu daketa kallonsu da gudu ta mike ta bishi hakan yasa ya tsaya chak tareda juyowa, shagwabe mai fuska tayi Dr Aminu yace "u know something, sata ta zauna na dubata tukun" baice mata komiba yay wurin gado ya zauna abakin gadon da sauri itama tabiyo shi ta zauna abakin gadon tana haki, Dr Aminu yadau stethoscope daya ijiye akan fridge din dakin ya maida wuyan shi yana zuwa wurin su, ihu tayi ta koma kusa dashi sosai ta rikemai riga da hannu daya tana nuna Dr da hannu daya, ahankali yasa hannu ya fizge rigarshi data rike da kyar yace "hey calm down" ya mika hannu ya riko Dr Aminu yace "he's my friend, babu abinda zai miki, Dr kine so don't be afraid okay" gyadamai kai tayi tana kwalalo ido tana kara mamatso wa kusa dashi, saida ta rike hanun rigarshi gam gam sanan tabari Dr Aminu ya dudduba tareda cire mata bandejin kanta ya chanza zuwa plasta yasa adaidai wurin ciwon sanan yay mata murmushi ganin yanda take yatsine fuska alamun zafi yace "wai Barrister zaka sha aiki anan wlh" yadau byro yana rubuce rubuce sanan ya mikama Aaman, fizge hanunshi yayi ya mike tsaye da sauri itama ta mike ya karbi takardan, Dr Aminu yace "zaku iya tafiya da ita na sallame ku, memory loss dinne dai banda haka brain dinta yabugu dan haka zakaga tana abubuwa sai ahankali, yanzu dai ran Wednesday zaku dawo ranan ne likitan brain din asibitin nan ke zuwa zai dubata nasan zai mata memory loss test sabida ya gane if long term memory loss ko short term ne, tasamu daganan saiya daurata akan medications in sha Allah she will be fine, but u need take extra care of her gaskiya" shiru Aaman yayi yana kallonshi ko motsin kirki yakasa, ahankali Dr Aminu ya dafashi turo baki tayi tasa hannu ta ture hanun Dr Ameenu daya daura akan kafadar shi dukansu atare suka kalleta, turo baki tayi tana kallon Dr saikuma ta kalli Aaman ta washe mai hakora da sauri ya dauke kai ya kalli Dr, Dr Aminu yace "i know wat u are thinking amma karka damu duk mai taimako baya tabewa, dazaran ta warke saika kaita wajen iyayen ta kaga yanzu idan ka barta wat if mutanen dasuka so kasheta sukazo suka karasa ta? Gwara ka tafi da ita chan farm house din for now inyaso ai zaka iya kiran gida chan Abuja Ummy tazo hutu, nasan kuma Abba zai barta tazo, in yaso saita tayaka kula da ita idan zakaje site, u can go now buy this drugs for her kabata abinci taci kuma she need it" dan ajiyan zuciya ya sauke saikuma ya kalleta yanda dogayen kitso guda biyun da wata nurse tamata sabida ciwon dake kanta ke lilo tana kusa dashi takara washemai baki da sauri ya dauke kai ya kalli Dr yace "ina zamu samu hijabi" shiru Dr yayi kaman mai tunani sai chan yace "i think inada hijabin Maryam a office dina bari na dubo na kawo muku" da sauri yafita hakan yasa tawani irin juyar dakai ta harari kofar tana turo baki ta gefen ido ya kalleta abinma mamaki ya bashi, zama yayi akan gadon yaciro wayarshi yana daddana wa, da sauri ta zauna tana kallon wayar, hannu tasa ta fizge wayar da sauri ya dago kai ya kalleta nunamai wayar tayi saita boye abaya tana makemai kafada, abinma dariya yadan so bashi hakan yasa yay mata murmushi 4 d first time, ware ido tayi saikuma ta ijiye wayan akan gado ta mike tsaye tana tafa hannu sosai tace "yeeeeee" dan girgiza kai yayi kawai yace "funny" yadau wayar ya maida aljihu, ana bude kofa ta dawo kusa dashi ta zauna da gudu, Dr ne ya shigo dakin rike da maroon hijab ya mikama Aaman ganin yanda taketa murguda mai baki, karban hijabin yayi yace "thank u" ya mika mata hijabin da sauri ta karba tana jijjiga hijabin tana dariya kaman taga kayan wasa, ganin batama san meba yasa ya fizge ya warware ya saka mata kallon kanta ta dingayi tana jajjjan hijabin tana kokarin cirewa hakan yasa ya girgiza mata kai yace "No karki cire" da sauri takara tambayar shi "karna cire?" gyada mata kai yayi itama da sauri ta gyadamai kai, slippers yabata tasaka sanan yay hanyar fita Dr nagaba, da sauri tabishi suka fita a pharmacy ya tsaya ya saimata maganin duk tana kusa dashi tana kallon fuskarshi sanan suka wuce har wurin mota ya bude mata ya nuna mata ta shiga, ta shiga ya rufe ya zagaya duk tana binshi da ido sanan ya ahigo ya tada motar sukabar asibitin.

Cikinta ta rike ta hijabi tana shafawa tana tabe baki kaman mai shirin kuka tana kallonshi, ganin hankalinshi nakan tuki yasa ta kece dawani irin shegen kuka da sauri ya juyo ya kalleta yace "menene?" wani sabon kukan takara kecewa dashi tace "yunwaaa" da sauri yace "okay okay dena kukan, zakici apple?" gyadamai kai tayi hakan yasa yay parking abakin hanya daidai wajen masu saida fruits yasai mata apples dayasa aka wanke mata ya biya ya mika mata karban ledan duka tayi da sauri ta ciro daya tafara ci tana murmushi, kallonta yayi da sauri ta dago dara daran idanunta ta kallai washe mai baki tayi tasa hannu taciro katoton data balla yake cikin bakinta taciro ta mikamai da sauri ya girgiza kai yace "no bazan ciba" wani irin ihu tayi, ta kece dawani irin kuka da sauri ya mika mata hannu yace "okay okay, sorry karki yi kuka bani to" sakamai tayi ahannu tana washe baki kaman ba ita take ihu da kuka yanzun nan ba, ya karba yana dan murmushi kafeshi tai da ido tana jiran yaci tareda shagwabe fuska ahankali tace "ci" kallon Apple din yayi yanda yay dama dama da miyau sanan ya

Please Login or Register in order to submit comment