Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da ango 'yan kad'an suka rakasu wurin cake d'in babu 6ata lokaci suka yanka Khaleel ya bawa Jiddah a baki itama ta yanko tare da d'an tsugunna wa kad'an ta bashi nan aka hau tafi.

Suhaima ba k'aramin birgeta suka yi ba sai sakin murmishi take ita kad'ai, zuwa yanzu ta d'an saki jikin ta da zaman wajen, amman sam duk da haka har yanzu bata ji sha'awar ta auri irin d'aya daga cikin wad'annan masu kud'in ba, tana kallon yanda su Zahra da sauran sisters d'in Jiddah suke wurgo mata harara tsanarta k'arara akan fuskar su, d'aga kafad'ar ta tayi alamar ko a jikin ta, tana fatan jibi iyanzu tana k'auyen su cikin gidan su, sai su harari wata ba ita ba.

Ana gaf da tashi a wurin Sabeer ya shigo cikin hall yana sanye cikin wata light blue sky na shadda tsadaddiya har da hula akanshi, d'inkin shi irin wanda matasan yanzu suke yin shi ba k'aramin kyau yayi ba, a daidai lokacin kuma Suhaima ta taso zata fita daga hall d'in don amsa kiran wayar da Yaya Aliyu yake yiwa Jiddah.


Karo suka yi da junan su inda Suhaima ta bige kanta da kafad'ar shi, dafe goshin tayi tare da yamutsa fuska tace
"Washh Allah na "

D'ago kan da zata yi ta bashi hak'uri suka had'a ido da junan su, kallon second 3 Suhaima tayi mishi ta gane ko wane tuni jikin ta ya fara rawa tsoro ya kamata kada ya d'auki fansar abin da tayi mishi a wajen da batasa kowa ba sai Jiddah, shima Sabeer kallon ta yake cikin mamakin me ya kawo ta nan kuma don ko acikin mafarki ya ganta sai ya gane ta wane ya kawo ta wajen bikin k'anwar shi? Ta dalilin wata zo nan? wad'annan tambayoyin ya yiwa kanshi a lokacin d'aya.

Ganin ya zuba ido yana kallon ta yasa ta saurin fita daga hall d'in, cikin zafin nama ya bita yana cewa
"Hey tsaya mana kece wan...."
Kafin ya k'arasa maganar tashi yaga wayam babu kowa a wajen, ta gudu kenan abin da zuciyar shi ta fad'a ba guduwa tayi ba 6oya tayi, ina ta 6uya kuma?.

Daga d'an nesa kad'an na hango Suhaima tana lek'en shi jikin ta na 6ari zuciyar ta na bugawa da k'arfi, ganin yana dube dube a wurin ya sake fad'ar mata da gaba, bata k'ara rud'ewa ba sai da taga ya nufo inda take.

Yana daf da k'arasa wa inda take ne yaji an rik'o hannun shi da sauri ya juya ga ashe Mumy ce da tarin kannen shi, wayyo Allah ya furta cikin zuciyar shi don yasan yanzu yaran nan zasu sa mishi ciwon kai da hayaniyar su
"Yah Sabeer kazo mu d'auki pic's please "
Cewar wata sistern shi zai yi magana kenan Mumy tayi musu magana da ido, dariya suka yi don su fahimci me take nufi, aikuwa hannun shi suka kama zuwa cikin hall d'in bashi da yanda zaiyi ya bisu yana tafiya yana dube dube har sai da suka wuce ciki sam ranshi babu dad'i ba haka yaso ba yaso ta tsaya su yi magana ta fahimta amman dole ya binciko wanda yayi inviting d'in ta zuwa wajen nan.

Fitowa Suhaima tayi daga inda ta 6uya tana sauke ajiyar zuciya har da gumi ta had'a duk tayi wani iri kallo d'aya mutum zai mata yasan a firgice take, zama tayi a gefen wasu flower's tana sauke numfashi....





Aishat A Muh'd 🤸🏻‍♀
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: A SANADIN SON KI

Written by
Aishat A Muh'd

♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz



PAGE 36-37





Suhaima ta d'auki wajen 5 minutes kafin ta d'an nutsu ajiyar zuciya ta sake saukewa a karo na ba adadi tace
"Alhmdllh Allah nagode ma da wannan mutumin bai kamani ba da yau nasan zai ya rama abin da nayi mishi"
Suhaima ta furta hakan a sarari, wayar hannun ta ne ya cigaba da ringing dole ta dai daita nutsuwar ta tayi picking ganin sunan Yaya Aliyu ne akai.

Bayan sun gaisa ta tambaye shi jikin Aunty Aliyah daga nan shima ya tambaye ta yanayin zaman nata don tun da ya tafi hankalin shi yak'i kwanciya sam ga jikin Aliyah sai a hankali, boye mishi gaskiya Suhaima tayi tace tana nan lafiya yanzu ma suna wajen party dinner d'in Jiddah, daga k'arshe yayi mata nasiha sosai tukunna suka yi sallama ta ajiye phone d'in saman k'afarta tare da rafka tagumi tana tunanin yanda za'a yi ta koma cikin hall d'in bayan taga Sabeer ya shiga ciki, nan take zuciyarta ta bata shawarar zaman ta anan waje har a tashi nan take ta aminta da shawarar zuciyar ta sake gyara zama tayi tana jiyo sautin kid'an da yake tashi a wajen partyn.


Sai wurin 11 na dare aka tashi lokacin Suhaima har ta fara gajiya da zaman jiran Jiddah ta fara gyangyad'i a wurin, sam Suhaima batasan har an tashi ba gyangyad'in ta kawai take sabida ta gaji gashi bata saba kaiwa wannan lokacin ba batayi bacci ba gashi ba'a saitin k'ofar shiga hall d'in take ba balle a taji fitowar mutane.


Sai da aka watse a wurin bai fi mutane d'ai d'aiku ba Suhaima ta farka daga gyangyad'in da take tamkar wadda aka tasa haka ta bud'e ido firgigit, ganin yanda duhu yayi sosai yasa Suhaima rarumo wayar Jiddah dake saman k'afarta ta duba time, wani zabura tayi ta mik'e tsaye cikin tashin hankali ganin har k'arfe 11:30 tayi na dare, ai d'ora hannun ta tayi dukka biyun a saman kanta tace
"Wayyo Allahna na shiga uku ni Suhaima yau nice a waje har k'arfe goma sha d'aya da rabi innalillahi "

Lokaci d'aya hawaye suka fara zubo mata ga wani mugun tsoro da sanyi da take ji, tafiya ta fara yi ta nufi k'ofar hall d'in taga duk yawan mutanen nan wayam sai wasu d'ai d'aiku wanda batasan fuskar su ba, tuni Suhaima ta samu waje d'aya ta raku6e ta fara rasgar kuka kamar wadda akai mata dukan tsiya.

Kuka sosai take har da majina ta rasa mafita don duk a rud'e take ta kasa dai daita nutsuwar ta balle ta sami mafita gashi phone d'in Jiddah a hannun ta wa zata kirawo acikin familyn ta mutanen da basu yi maraba da zuwan ta cikin su ba matsayin bak'unta na kwanaki biyu, balle ta samu damar kiran wani daga ciki ya taimaka mata, gashi idan ma ta kirawo Yaya Aliyu d'aga musu hankali kafin ma yazo ma koma mai ne ya cinye ta kuma bata yi wa Jiddah adalci ba idan ta fad'a mishi yanzu ya zata yi wayyo Allah na, sake rushe wa da kuka Suhaima tayi sosai tana nan a raku6e taji an dafa mata kafad'a tare da cewa
"Hey what are you doing here? "
Wata irin firgita Suhaima tayi tare da jiyowa a tsorace had'a ido tayi da wannan guy d'in na d'azu yana tsaye daf da ita ya hard'e hannun shi a kirji, wani k'ugi cikin ta yayi wanda tana tunanin ma Sabeer yaji k'arar da cikin nata yayi matse k'afafun ta ta fara yi saboda daf take da sakin fitsari a tsaye jikin ta kuwa sai rawa yake wanda ya sanya wayar Jiddah ta fad'i a k'asa da bag d'in ta.

Kallon ta Sabeer yake up and down yana sakin wani murmishi wani sanyin dad'i ne yake ratsa cikin zuciyar shi da gangar jikin shi, sauran kad'an dariya ta kubce mishi ganin yanda take matse k'afa tamkar wanda yake jin fitsari ya matse shi irin sosai d'in nan har k'arar da jikin ta yayi sai da yaji sautin.

Ganin murmishin da yake ba k'aramin sake rud'ar da Suhaima yayi ba aikuwa fakar idon shi tayi ta tattara gown d'in ta da hannun ta kafin Sabeer ya ankara yaga Suhaima ta zura da gudu tayi hanyar fita daga gate, ba shiri shima ya d'auki phone d'in da bag nata da suka fad'i ya bita da gudu shima.

Suhaima da ta bud'e kofar gate d'in zata fita da sauri ta dawo baya jin wani irin sanyi da ya busa ta gashi wajen duhu babu wadaccen haske sosai a wurin nan ta tsaya waje d'aya tana rawar jiki, da haka Sabeer ya cimmata tana tsaye sai ruwan hawaye da yake tsere saman kyakkyawar face d'in ta, ganin Sabeer a kusa da ita da sauri Suhaima ta bud'e baki tace
"Don girman Allah kayi hak'uri da abin da nayi maka tsautsayi ni bazan sake ba har abada kayi hak'uri kada kayi min komai bansan kowa anan ba "

Sosai ta bashi tausayi ganin irin rud'ewar da tayi cikin sanyin murya yace
"Hey calm down babe babu abin da zan miki just I'll help you"
Kamo hannun ta yayi ganin har yanzu bata daina rawar jiki ba kuma a rud'e take, jan hannun ta yake har cikin mota ya zaunar da ita tukunna ya zagayo seat d'in driver ya zauna kallon ta ya tsayayi na tsayin wasu minutes, kallon yake cikin wani irin yanayi ita kuwa kanta a sunkuye batasan abin da yake ba tsoro ne fal a tattare da ita addu'a take cikin zuciyar ta Allah yasa kada ya cutar da ni, kafin yayi wa motar key suka bar wajen sun d'an yi nisa suna tafiya tukunna ya jiyo ya kalle ta still har yanzu kanta a sunkuye.

D'an girgiza kai yayi tare da sakin dan murmishi yace
"Ina zamu je, i mean ina ne gidan da zan kai ki? "

D'an satar kallon shi tayi ta fad'a duniyar tunani ita da take bak'uwa a garin yau ne zuwan ta na farko ina zata gane gidan, don haka sai tayi shiru kawai.

Ganin haka yasa Sabeer yace
"Ina jiran ki fah kinsan dare yayi fah idan baki da wajen zuwa kuma sai mu wuce guest house d'ina mu d'an huta zuwa gobe "

Wani zaro ido Suhaima tayi tamkar idanun ta zasu firfirto wani tsoro da nadamar shiga motar shi ya dirar mata lokaci d'aya ashe d'an iska ma ta shiga motar shi yau na shiga tara ba uku ba, dariya sauran kad'an ta kubce wa Sabeer ganin yanda Suhaima ta koma.

"Don Allah kasan gidan su amaryar Jiddah? "
Suhaima ta fad'a cikin rawar murya, da mamaki ya kalle ta kafin yace
"Oh nan zaki je kenan? "
Da sauri Suhaima ta d'aga kanta alamar eh, mamaki ne sosai ya kama shi ta yanda akayi Suhaima tazo gidan tun da yasan halin 'yan gidan su da basa huld'a da talaka sai mai kud'i d'an uwan su.


Kuyi hak'uri da wannan fan's mu had'u a next page muji ya zata kasance.
Ga Sabeer da Suhaima sun had'u shin komai zai faru kuma?...


Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: A SANADIN SON KI

Written by
Aishat A Muh'd

♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz



PAGE 38-39




Babu wanda ya sake magana a cikin su kowannen su da tunanin da yake cikin zuciyar shi, amman Suhaima har yanzu hankalin tashe yake ganin har yanzu basu zo gidan ba ta sadaukar sace ta ma yayi tuni wasu sababbin waye sun cigaba da zuba saman fuskar ta, d'an kallon ta Sabeer yayi kad'an yana girgiza kai cike da mamakin ta ko wahalar kuka bata yi. Da haka suka k'arasa gidan Suhaima tana ganin an shiga cikin gidan ta tabbatar shine sai da ta saki ajiyar zuciya na kwanciyar hankali kafin ta sanya hannun ta saman face nata da niyyar goge hawaye sai taga an mik'a mata tissue kar6a tayi ta goge tukunna ta fara kok'arin bud'e kofar motar, kamar ance ta jiyo ta kalli side d'in su Jiddah aikuwa ta hango Jiddah tana tafiya cikin sauri tana goge fuska, da sauri Suhaima ta k'arasa fita kamar abin arzik'i ta rufe kofar motar sai ta zuro kanta ta jikin window da yake ya sauke glass d'in.

Sabeer har zai yi wuce zuwa parking lot sai yaga ta zuro kanta sai ya tsaya ya d'auka godiya zata yi mishi sai hasashen shi yasha banban da na Suhaima don cikin tsiwa ta fara cewa
"Uhm Malam ka d'auka godiya zan maka da ka zuba ido kana kallona har da bud'e kunnuwa don jin abin da zance, to ban gode ba kuma hak'urin da na baka d'azu in mistake ne, me yasa ma ka tausaya min ka d'auko ni da ka barni acan ma da nafi jin dad'i... "

Da sauri Suhaima ta fitar da kanta tare da zurawa da gudu zuwa inda ta hango Jiddah a tsaye sai safa da marwa take, sakamakon wata cafka da Sabeer ya kawo mata ganin ta gudu ne yasa shi dunk'ule hannun shi ya naushi d'aya hannun kafin ya jingina kanshi jikin kujera yace
"Hmmm lallai babe d'in nan da na kama ki yau a hannuna da sai gane kuren ki sai tsiwa da shegen tsoro fal ciki"

Shi mamakin ta ma yake tun da suka taho take kuka jiki yana rawar tsoro, amman wai har ta samu bakin tsiwa da taga ya kawo ta inda take buk'ata, kwafa yayi tare da k'arasa wa parking lot yayi parking tukunna ya nufi part d'in su yana cilla key yana cafewa zuciyar shi yau cike take da farinciki da nishad'i ya ganta a inda bai ta6a zaton zai ganta ba kuma yana kyautata zaton dalilin Jiddah tazo tun da yasan itace mai shige shigen talakawa sosai a cikin families d'in su yayi mamakin yanda Jiddah har tasan k'auyen su Suhaima ta ganta suka fara k'awance. Da wannan tunanin ya k'arasa cikin part d'in su kai tsaye bedroom nashi ya wuce yayi wanka sannan ya sanya wasu fararen sleeping dress ya kwanta amman ya kasa bacci sai tunanin abin da ya faru tsakanin shi da Suhaima yake yana zuba murmishi shi kad'ai.


Da gudu Jiddah ta k'araso wajen Suhaima a lokacin da ta hango ta rungume ta tayi tana kuka tace
"Suhaima don Allah kiyi hak'uri wallahi na d'auka kin biyo wasu ne sai da na neme ki na rasa na d'auka kina gida sai da na dawo na neme ki na rasa, hankali na ya tashi sosai yanzu haka da kika ga na fito komawa zanyi na duba ki sai na hango ki... Waya kawo ki? Naga kamar motar Yah Sabeer kika fito ko shine ya dawo da ke? "

Duk wannan maganar da Jiddah take da tambaya babu saurarawa tana yi tana kallon Suhaima, abin ma sai ya bawa Suhaima dariya kafin ta bud'e baki tace
"Kaiii Jiddah irin wannan tambayar gashi na dawo sai hankali ya kwanta amman ni bansan sunan wanda ya taimaka min ba naga dai kuna yanayi dashi "
Ajiyar zuciya Jiddah ta sauke ta kwanciyar hankali kafin ta tace
"Mybe shine tun da naga motar shi ce amman naji dad'in abin da Yah Sabeer yayi dole nayi mishi godiya, gaskiya Suhaima kinci sa'a sosai don Yah Sabeer sai a slow wallahi"
"Koh? "
"Eh mana don baki san halin shi ba ne, gashi da miskilanci da shagwa6a don ko k'aramin yaro bazai nuna mishi shagwa6a ba "

"Hmmm ni bacci nake ji na gaji wallahi "
"Ai dole zo muje kiyi wanka ki kwanta "
Hannun ta Jiddah ta kama suka nufi side d'in shi shiru kake ji ko'ina kowa yayi bacci, don haka d'akin Jiddah suka nufa kai tsaye, bathroom Suhaima ta shiga wanka tayi tare da yin alwala ta fito wata catton sleeping dress dogowa Jiddah ta bata ta sanya da hula sannan ta sanya hijab sallahr isha'i tayi tare da yin shafa'i da wuturi tayi 'yan addu'o'in ta kafin ta tashi ta koma inda ta ajiye bag d'in da ta zo dashi.

D'auko wa tayi ta bud'e gift's d'in da Aunty Aliyah ta bata ta d'auko taso wa tayi ta zo inda Jiddah ta kwanta saman bed tace
"Jiddah ga gift's d'in da Aunty Aliyah ta bani na baki "
Cikin mamaki Jiddah ta tashi zaune tare da kar6ar sarkar tana dubawa, nan take ta fad'ad'a fara'ar ta sannan ta rungume Suhaima tana cewa
"Wayyo dad'i nagode sosai tana da kyau, me yasa baki fad'a min da wuri nayi mata godiya ba "
Suhaima fuskar ta d'auke da murmishi tace
"Itace ta hana na fad'a miki don babu waya tace sai mun tafi na baki "
"Naji dad'i sosai kiyi mata godiya Allah ya bata lafiya ya raba ta da abin da take d'auke dashi lafiya"
"Amin "
Cewar Suhaima kafin ta d'ora da cewa "sai wani godiya kike tamkar wadda aka bata wani babban abu "
D'an hararar ta Jiddah tayi tare da cewa "Hmm ke kika ga haka Suhaima amman tabbas wannan kyautat a wuri na babba ce "

'Yar dariya Suhaima kawai tayi ta kwanta ita ma bayan Jiddah tayi light off ne Suhaima tace
"Jiddah ina son gobe ki had'a ni da driver ya kaini wani mall zan yi siyayya "
"Me zaki siyo? "
"Ina ruwan ki idan na siyo kya gani "
"Alright Allah ya kaimu goben"
"Amin "
Da haka kowannen su yaja blanket ya lullu6a tare da addu'ar bacci babu dad'e wa bacci ya d'auke su mai nauyi da yake an gaji saboda hidima ta biki.


Washe gari da safe wajen k'arfe 11 aka d'aura auren Jiddah da Khaleel wanda d'umbin mutane masu kud'i goggagun 'yan boko tare da 'yan siyasa manyan likitoci da 'yan kasuwa suka halatta bayan d'aurin aure ne suka wuce reception ta maza, cikin gida kuwa matane a ciki taf ana hidimomi irin na biki.

Jiddah ce gaban dressing mirror tana sanya sark'ar da Aunty Aliyah ta bata sai da ta gama sanyawa tsaf ta jiyo ta kalli Suhaima wanda taci gayun ta cikin wani lace ash mai touch d'in flowers pink tayi kyau tamkar itace amaryar sai kashe selfie take abin ta.
"Yah babe kin gani koh na had'u? "
Cewar Jiddah kenan tana kallon Suhaima, kallon ta Suhaima tayi a haka sark'ar tayi mata kyau amman bai kamata ta sanya ta yanzu a lokacin bikin ta don tayi arha da yawa tana kallo ta ajiye gold d'in ta a gefe ta d'auki wannan ta sanya. D'an murmishi Suhaima tayi tare da cewa
"Wow amarya a gidan Khaleel kinyi kyau sosai sai dai ki cire sark'ar nan please "
"Because of what? "
"Bata cancanta ki sanya ta ba yanzu "
Har Jiddah ta bud'e baki zata yi magana aka turo k'ofar bedroom d'in aka shigo, Umman Jiddah ce ta shigo tasha kwalliya cikin wata tsadaddiyar shadda an zuba gold's a jiki sai fitar da k'amshin turare take, da sauri Suhaima ta gaida ita ba yabo ba fallasa ta amsa tana nufar Jiddah wadda take tsaye, cikin mamaki tace
"Me zan gani Jiddah, mene haka a wuyan ki? "
"Uhm Umma sark'a ce tayi kyau? "
Wata harara Ummna ta zabga mata tare da cewa
"You're very stupid Jiddah na rasa mene akan ki wallahi ranar bikin ki zaki sanya wannan banzan sark'ar mai araha haka ko 'yan aikin gidan nan zasu sanya sark'ar da suka fi wannan tsada balle ki, wanne stupid ne ya baki ita?"

A hankali cikin sanyi jiki Suhaima ta tashi ta nufi bathroom ta shige idanun ta suna fitar da hawaye yau a gabanta ake kiran Aunty Aliyah stupid wadda ta d'auke ta tamkar mahaifiya a wajenta yau da ace wata ce ba Umman Jiddah ba da sai inda k'arfin ta ya k'are wallahi.

Gaba d'aya ran Jiddah ya 6aci sosai cikin jin haushin abin da Umman ta fad'a, Jiddah ta bud'e baki tace
"Haba Umma me yasa kike haka ne "
"Dalla can rufe min baki kafin ranki ya 6aci kiyi maza ki cire ta sannan ki fito parlour za'a d'auki pic's sauran ki taho mana da yarinyar nan "
Tana gama fad'in haka ta fice daga d'akin, wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mata me yasa me yasa iyayen ta suke wannan halin na kyamar talaka me yasa suke abu tamkar basu da ilimi sun san Allah ne mai azurta bawan shi a lokacin da yaso, ba wayon su ko dabarar su ne yasa suke da kud'i ba a yanzu idan Allah yayi sai ya kwace kud'in.

Da sauri ta sanya hannu ta goge hawayen fuskar ta tare da jiyowa jin an dafa kafad'ar ta, Suhaima ta gani tana murmishi itama murmishin yak'e tayi kafin tace
"I'm so sorry Suhaima akan abin da Umma tayi miki"
"Haba Jiddah ni fah babu abin da akayi min "
Ta k'arasa fad'i tana cire sark'ar jikin Jiddah bayan ta gama cirewa ne ta d'auko mata wanda su zata sanya ta d'auko wannan ta sanya.

"Wow kin had'u tawan ni yanzu ki had'a ni da driver na tafi "
"Okay dear "
D'auko phones nata tayi ta kirawo driver magana tayi na tsayin 2 minute's sannan ta mik'a wa Suhaima wayar tace
"Yana waje yana jiran ki driven "
"Okay thank U "
Daga haka ta d'auki bag nata suka fito tare ta kofar baya Jiddah ta nuna wa Suhaima ta fita don batason wani ya sake 6atawa Suhaima rai, bayan Suhaima ta fita driven shi ya hango ta yayi mata magana aikuwa nan ta shiga mota yaja suka bar gidan.

Tun da Suhaima ta fito daga part d'in su Jiddah tazo ta wuce ta shiga mota yana kallon ta, wani mirmishin mugunta ya saki duk gajiyar da yayi dakyar yake d'aga k'afa gudowar shi daga wajen reception ko gamawa ba'a yi ba ya taho don duk ya gaji da hayaniya ganin Suhaima ne yasa duk yaji gajiyar ta wartsake cikin sauri ya shiga mota ya bisu a baya...



Aishat A Muh'd ✍🏻

[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: A SANADIN SON KI

Written by
Aishat A Muh'd

♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz



PAGE 40-41




Tafiya suke Suhaima sai wara ido tana kalle kalle sosai taji garin na Kano ya birgeta daman Yaya Aliyu yana bata labarin yanda yanayin garin yake kodayaushe cikin sha'awar zuwa take sai gashi a dalilin Jiddah tazo ta, karatun Qur'an ne yake tashi a motar k'ira'ar Shureim cikin suratul Ma'idah sosai karatun yake ratsa cikin zuciyar Suhaima har wani lumshe ido take tana bin karatun a hankali cikin k'asa k'asa da muryar ta.


Agaban wani k'ayataccen mall driver yayi parking tare da cewa "mun iso ranki ya dad'e"
D'an murmishi Suhaima tayi tare da cewa
"Okay bari na shiga na fito "
"A fito lafiya "
Bud'e k'ofar motar tayi ta fito cikin takun nutsuwa take tafiyar duk da kuwa yanda gaban ta yake fad'uwa don bata ta6a zuwa irin wannan wajen ba, kawai d'auriya tayi kada ta ba da kanta amman zuciyar ta fal tsoro kamar ace kyat ta zura da gudu, har ta k'arasa wajen k'ofar shiga ta shiga ciki.

A hankali Sabeer yayi parking kusa da motar da ta kawo Suhaima, fitowa Sabeer yayi sannan ya k'arasa wajen motar tun kafin ya k'araso drive ya ganshi don haka da sauri ya fito daga motar yana cewa
"Yalla6ai barka da rana"
Sabeer bai tsaya bawa driven amsa ba yace
"Salisu me kake anan? "
"Yalla6ai na kawo k'awar Jiddah nan zata yi shopping "
"Okay zaka iya tafiya gida "
D'an shiru Salisu yayi kafin yace "Yalla6ai Jiddah tace na jirata ta gama na mayar da ita gida don bak'uwace anan "

D'an shan mur Sabeer yayi kafin yace "Oh baza kayi abin da na saka ba? "
Cikin d'an tsoro da biyayya Salisu yace
"Ayi min afuwa Yalla6ai yanzu zan tafi "
Yana gama fad'in haka ya shiga mota yaja ya bar wajen zuciyar shi cike da d'an tsoro yanzu idan ya koma gida me zai cewa Jiddah idan ta tambaye shi ina k'awar ta, gashi bazai iya musu da Sabeer ba don kada ya rasa aikin shi don dashi ya dogara.


Salisu driver na tafiya Sabeer ya saki wani murmishi dani kaina bansan ma'anar shi ba kafin ya shiga cikin mall d'in cikin takun

Please Login or Register in order to submit comment