Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kada 'yan uwan Sabeer su rabasu, tabbas ta kamu da son Sabeer wanda tasan idan suka rabu su ba k'aramin tashin hankali zata shiga ba.

"Kiyi min magana Baby please, ki daina kuka kin ga yanda idanun ki suka koma kuwa? "

Ganin yanda ya d'aga hankalin shi ya sanya bud'e idanun ta dakyar ta kalle shi kafin tace
"Zazza6i da ciwon kai ne kawai suke damu na"
"Sai me kuma? "
"Shikenan "
D'an kallon ta yayi sannan yace
"Baby fad'a min gaskiya abin da su Mumy suka yi muku shi ya sanya ki kuka ko? "
Da sauri ta d'ago kanta ta kalle shi cikin mamakin a inda yasan me akayi musu, d'an girgiza kai na takaici yayi then yace
"Nasan komai Baby, idan don wannan kike damuwa don Allah ki daina sanya shi cikin zuciyar ki kada ya janyo miki wani ciwon please, sannan zan d'auki mataki "

"Amman dai bai ka......."
Hannun shi ya sanya saman bakin ta ya rufe tare da cewa
"Baby kiyi shiru kawai, bari na kirawo doctor ya duba min ke "

Langa6e kanta tayi cikin yanayin shagwa6a tace
"Ni Allah bana son allura ne da shan magani, zan warke a hakan kawai "

"Ke kinma isa amarya fah kike taya ciwo yazo bazan d'auki matakin gaggawa akanshi ba sai yayi k'arfi ya hanani cin amarci nah tabbb yarinya naki wasa ne "

Sanya face nata tayi cikin kirjin shi tana d'an murmishi don ya bata kunya, tana ji ya kirawo Doctor Aishat wadda take babbar likitace ta gynecologist ce tana aiki a hospital d'in Dr Faridah wato Mumy.

Tsayin 5 minutes suka d'auka suna waya kafin ya kashe ya kalli Suhaima wadda ta lafe ajikin shi dauriya kawai take amman kanta ciwo yake sosai, shafa kanta yayi da hannun shi yana cewa
"Sannu Baby nah yanzu Doctor Aishat zata zo ta duba ki "

"Amman bazata yi min allura ba koh? "
"Eh zance kada tayi miki tunda bakya so"
D'aga kanta tayi kawai.
"Baby jikin ki yayi zafi sosai sannu dama zan iya dawo da ciwon jikina dana dawo dashi"

Hannunta ta d'ora saman face d'in shi tana shafa kwantaccen gashin sajen shi zuwa gefen bakin shi, lumshe eyes nashi yayi yana jin wani abu na ratsa shi kai hannun ta yayi bakin shi yayi kissing d'in tsakiyar tafin hannun ta, wanda daga shi har ita da bata jin dad'i sai suka ji wani yanayi atattare dasu.

"Kada ka damu zan samu sauk'i insha Allah"
"Amin Baby nah "

Sunan zaune suka ji door bell kafin ya tashi kuma ya bud'e yaji phone nashi na ringing, bayan ya d'auka ne Doctor Aishat take mishi bayanin gata a k'ofar parlour a tsaye.

"Baby bari naje na bud'e mata door ta k'araso "
Yana gama fad'in hakan ya fita daga bedroom d'in, yana shigo da ita ya koma bedroom ya d'auko Suhaima cak kamar wata Baby ya kawo ta parlour duk kunya ta kama Suhaima sosai sai wani sunkuyar da kai take shi kuwa gogan ko ajikin shi sai ma kok'arin had'a ta da jikin shi yake, yayi da Suhaima sai nok'ewa take.


"Yalla6ai me yake damun amaryar taka? "
Cewar Dr Aishat kenan ganin idan ta cigaba da shiru Sabeer zai bata kunya yanzu.

"Uhm Dr Aishat zazza6i ne ke damunta da ciwon kai sai kuma..... Uhmmm kin dai gane bansani ba ko taji ciwo? "
Ya k'arasa fad'a yana shafa bayan kanshi, kamar k'asa ta tsage ta shige ciki haka Suhaima taji a lokacin, yayin da Dr Aishat ta maze don tasan tatsuniyar gizo bazata wuce k'ok'i ba.

"Yalla6ai na fahimta inason zan duba don nagane ko taji ciwo "

"Okay ba damuwa "
Kafin Suhaima ta ankara ya d'auke ta sai bedroom ya kwantar da ita saman bed yayi da Dr Aishat take binsu a baya, ganin ya tsaya bashi da alamar fita ya sanya tace
"Yalla6ai ka taimaka ka d'an bamu waje kad'an"

Ba dan yaso ba ya fita daga bedroom d'in, bayan ya fita ne Doctor Aishat ta duba Suhaima nan ta gane bata ji wani ciwo sosai ba idan tana amfani da ruwan d'umi ma zuwa nan da kwanaki biyu zata warke, nan ta fara kok'arin yi mata allura aikuwa Suhaima ta sanya kuka tare da rirrik'e hannun Doctor d'in, sai Sabeer ta kirawo dakyar ta yarda akayi mata da rarrashi da lalla6a tare da sanya ta ajikin shi aka samu akayi guda biyu sannan ta bata magungunan da zata sha, kuma ta basu shawarwari na yanda Suhaima zata kula da kanta har ta samu sauk'i.

Tukunna tayi musu sallama ta tafi bayan Sabeer ya taka mata zuwa bakin k'ofar fita parlour, kitchen ya wuce ya bud'e frige fresh milk ya d'auko tare da cup ya dawo d'akin lalla6a ta yayi har tasha maganin da fresh milk d'in babu dad'e wa bacci ya d'auke ta da yake har da maganin sanya bacci aciki.


Yana zaune kusa da kanta ya rik'e hannun ta yana aikin kallon ta kawai jinshi yake kamar a mafarki yau wai shine da Suhaima a matsayin ma'aurata, sannan abin da su Mumy suka yi yaji haushi sosai Jiddah ce take fad'a mishi a waya bayan tabar gidan Suhaima, da yaso yin magana dasu Mumy but Daddy ya rarrashe shi kan yayi hak'uri komai mai wuce wa ne wataran sai labari ya zuba musu ido kawai, shi ya cigaba da kula da matar shi don bata da kowa a kusa sai shi.


Kiran sallahr mangarib ne ya tashe shi daga zaunen, addu'a yayiwa Suhaima sannan ya tashi ya fita side nashi ya shiga yayi alwala ya wuce masallaci sai after ishsha ya dawo gidan, yana shigowa farfajiyar gidan ya had'u da driven Jiddah bayan ya gaida Sabeer ne ya bashi sak'on Jiddah na basket mai d'auke da foodflaks 3 sai Jug kar6a Sabeer yayi sannan ya d'auko kud'i ya bawa driven, sosai driven yayi godiya kafin ya tafi, shiga cikin gidan yayi hannun shi rik'e da basket d'in cikin zuciyar shi yana jinjinawa Jiddah da matuk'ar kok'arin da take akan su, yaji dad'in kawo abincin nan daman yanzu yake shirin fita yi musu take away sai gashi na kuma ta hutar dashi, addu'a yayi mata cikin zuciyar shi na Allah ya sauke ta lafiya.


Ajiye basket d'in yayi saman dinning table sannan ya wuce bedroom ya tarar har Suhaima ta tashi tana bathroom don yaji k'arar zubar ruwa, don haka sai yawuce nashi side d'in yayi wanka ya shirya cikin wani catton na kayam bacca and sky blue ya fesa different perfumes masu dad'in kamshi, tukunna ya koma bedroom d'in Suhaima ya tarar har ta fito daga bathroom sallah ma take.


Shiga yayi cikin d'akin ya zauna kan sofa ya d'an lumshe idanun shi, bacci ne sosai cikin eyes nashi ga gajiya, tana idar da sallahr mangarib and ishsha ne bayan tayi shafa'i da wutiri tare da addu'o'in ta ne sai ta tashi ta cire hijab d'in jikinta.


Tana sanye da wata sleeping dress white tsayin ta iyakar shi tsakiyar cinyar ta sai zanin da ta d'aura tayi sallah, batasan Sabeer ya shigo ba sai kawai ta warware zanin ta ajiye shi sannan ta k'arasa wajen dressing mirror ta taje gashinta tare da sanya perfumes ajikinta.

Duk wannan abin da take Sabeer yana kallon ta yayi luf ne kawai ajikin sofa, tuni ya fara jin wani canjin yanayi a jikinshi don kuwa Babyn shi tayi mishi kyau amman sai dai ya had'iye abin da yake ji dole yabar ta taji sauk'i.

Tashi yayi tsaye yana wani binta da kallon k'asan ido ya k'arasa inda take tana d'aure kanta da ribbon hannun shi ya sanya ya cikin gashin kan nata yana wani yamutsa shi, a d'an tsorace ta jiyo ganin Sabeer ne ya sanya ta sauke ajiyar zuciya........



Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ✍🏻
[4/9, 5:00 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ






*PAGE 83-84*





Ganin Sabeer ne ya sanya ta sauke ajiyar zuciya tare da juya kanta, rungume ta yayi ta baya ya sanya kanshi cikin gashin kanta da wuyan ta yana shak'ar kamshin daddad'an perfumes d'in ta saukar d'umin numfashinshi a wuyanta shi ya saukar mata da wani irin kasala, hannun shi ya sanya yana shafa dogon hannun ta daga kafad'a zuwa 'yan yatsun hannun, kasa jure abin da yake mata tayi sai kawai ta juyo tare da fad'awa kan kirjin shi tsam ya rungume ta ajikin shi yana saukar da ajiyar zuciya, suna nan tsaye wajen 5 minutes ahaka kafin kuma ya bud'e baki yace
"Baby muje kici abinci sai kisha magani "

Hannun ta ya rik'o zuwa parlour har kan dinning table ya zaunar da ita kan kujera, sannan shima ya zauna yana zuba musu abinci, kasa barinshi tayi da ya zuba musu ta kar6i serving spoon tana zuba musu.

Abaki suka dunga bawa junan su har suka k'oshe sannan ta tattara kayan ta kai kitchen, ta dawo ta gyara dinning table d'in, zama suka yi a parlour suna kallo tare da ta6a 'yar soyayya.


Sai da Sabeer ya bawa Suhaima hutun kwanaki biyu sannan aka d'ora daga inda aka tsaya, soyayya, kulawa da duk wata kauna suke nuna wa junan su, cikin farinciki da kwanciyar hankali suke abin su, babu mai zuwa gidan sai Jiddah ce ke lek'o su, sai dai waya da take yi dasu Yaya Aliyu kullum Sabeer kuwa yana kok'arin zuwa gida gaida iyayen shi, amarcin su suke sha yanda suke so babu mai tak'ura musu ko house girl basu da ita Suhaima ta hana Jiddah ta kawo mata tace ba yanzu ba.


Akullum cikin nuna wa junan su so suke biyayya sosai da kyautatawa Suhaima ke yiwa Sabeer yayin da shima yana kok'arin wajen sanya ta farinciki koyaushe, idan ka shiga gidan su kuwa sai ya birge ka saboda tsananin yanda suke kula da junan su.


Motarta tuni Jiddah ta aiko mata da ita gashi Sabeer ma ya bata kyauta ta mota mai matuk'ar kyau da tsada da sabuwar tsadaddiyar phone, sosai Suhaima tayi mishi godiya ta nuna mishi dad'in da taji addu'a sosai yasha ta daga bakin ta, gashi yana koya mata driving duk weekend da yamma zasu fita yana koya mata, yanzu matsalar ta d'aya shine ta cigaba da karatu amman tun da tayi mishi maganar sau d'aya ya nuna ba yanzu ta hak'ura duk da tsananin son da take yiwa karatun ta cigaba da farantawa mijinta rai ta barwa Allah za6in alkhairi akan makaranta.



_*After 3 Month's*_


Zuwa wannan lokacin idan kaga Sabeer da Suhaima sai kayi mamaki sun k'ara wani kyau musamman Suhaima ta k'ara cika sosai tayi 'yar kiba kad'an, bata fita ko'ina sai zaman gida kullum sau d'aya ta sake jarraba zuwa gidan su Sabeer amman har ta karaci zaman ta babu wanda yace mata ci kanki har gwara lokacin da Daddy ya dawo ya zauna sun d'an ta6a hira dashi amman ko a fuska bata nunawa Sabeer jin haushin abin da suka yi mata, Sabeer a lokacin tuni ya fara aiki da company d'in shi da Daddy ya bashi kyauta.

Zaune suke a garden da wani yammaci lokacin damina ne garin yayi luf luf dashi sai iska mai dad'i da take kad'awa mai ratsa jiki da sanya mutum nishad'i.

Suhaima tana sanye da wani wandon jeans iyakar shi rabin cinyar ta blue sai half vest white, yayin da Sabeer kuma yake sanye cikin 3quater kawai suna zaune kan wani babban carpet ga kayan fruits da juice da ruwa a gefen su.

Sabeer ne yake danna laptop d'in shi da hannu d'aya, d'ayan hannun kuma yana rungume da Suhaima ta gefen shi, cikin shagwa6a ta bud'e baki tace
"Ni Allah ka bar aikin nan kazo ka goya ni idan ba haka ba zanyi maka kuka "

D'ago kanshi yayi ya kalle ta sai wani turo baki take murmishi yayi tare da jan hancin ta yace
"Oh Baby rigima naji zan goya ki amman kiyi min afuwa na k'arasa aikin nan please "
D'aga kanta tayi, da sauri ya rik'o d'ayan hannunta yace
"Amman ban da kuka please"
D'an murmishi tayi sannan tace
"Toh bazan yi ba "
"Yawwa 'yammata na "

Cikin 10 minute's ya k'arasa aikin tare da rufe laptop d'in ya kallo ta cikin murmishi sannan ya sunkuya yace
"Baby taho na gama "
Cikin sauri ta taso tare da d'anewa bayan shi, yatsina fuska yayi sannan yace
"Wash! Bayana Baby kin k'ara nauyi zaki karya min baya "

Turo baki tayi cikin shagwa6a tace
"Ni.... Ni Allah ban wani k'ara nauyi ba kai ne ka dad'a zama babba "
"A'a Baby fad'i gaskiya "
"Toh bakai ne kake d'ura min abinci ba da yawa "

Dariya yayi yana cewa "a haba Baby fad'i gaskiya dai "
Hannun ta ta sanya tare da d'an mintsinin shi a damtsen hannun shi, wata 'yar k'ara ya saki
"Laaa Baby kika mintsine ne, aikuwa sai na rama "
Kafin ta ankara ya kwantar da ita akan carpet ya bi jikinta ya kwanta gaba d'aya sai ya saukar mata da nauyin shi , dakyar take jan numfashi tace
"Wayyo don Allah ka d'aga ni dear "
Yana dariya yace
"Nak'i wayon yarinya sai na rama ko kuma yau da dare na hanaki bacci kin yarda "
Da sauri ta d'aga kanta dariya ya sake yi sannan ya d'aga ta, hannun ta ta zube su kan carpet tana sauke numfashi, janyo ta yayi kan k'afafun shi tare da had'e bakin su waje d'aya wani salo na daban yake nuna mata itama babu 6ata lokaci take mayar mishi da martani.

Sunyi nisa cikin wannan yanayin ne yaji wayar shi na k'ara, ba don yaso ba ya d'auki wayar yana jan tsaki don an katse mishi jin dad'in shi.

"Hello Yaya na haihu "
"What! Da gaske kike? "
Cewar Sabeer yana tambayar Jiddah, cikin dariya tace
"Allah Yaya da gaske nake an samu Baby girl"
"Masha Allah na tayaki murna 'yar kanwata Allah ya raya "
"Yaya ka fad'awa Suhaima ita na fara kira wayan ba'a d'auka ba"
"Okay babu damuwa "
"Toh yaushe zaka kawo min Besty tun da kuka yi aure bata zo ba fah?"

"Jiddah surutu huh, yanzu kina buk'atar hutu ne kije ki huta zan kawo ta ne"
Cikin shagwa6a tace
"Yaya ka kawo min ita gobe don Allah idan zaka fita office "
"Okay naji "
Nan ya kashe wayar tashi, kallon Suhaima yayi wadda take kallon shi tun fara wayar shi ya ce
"Albishirin ki Baby "
Matsowa kusa dashi tayi sosai tace
"Goro fari k'al dear "
"Mene tukuici na idan na fad'a "
D'an dariya tayi kad'an sannan tace
"Ka fad'i duk abin da kake so zanyi maka "

"Jiddah ta haihu ansamu Baby girl "
Wani ihun murna ta saki tare da rungume shi tana dariyar farinciki kallonta yake duk tabi ta birkitashi ta kashe mishi jiki.

"Dear ka tashi mu tafi ganin Baby please "
"No Baby yanzu mangarib ta kusa ki bari sai gobe don gaskiya yanzu kin gama birkita ni tashi mu tafi ciki before mangarib tayi "


Sanin halin shi ya sanya ta biye mishi suka tafi, sai da suka sha soyayyar su tukunna sukayi wanka tare da yin alwala ya tafi masjid ita kuma ta shige bedroom nata don yin sallah, bayan ta idar da sallahr ne ta samu damar kiran Jiddah don yi mata barka kafin tazo sunsha hirarar su sosai kafin suyi sallama da juna.



_*Washe gari*_


Tun asuba da tayi sallah take faman gyaran aikin gidan bayan ta gama ta had'a breakfast sannan ta jera saman dining table, bedroom ta wuce ta cire kayanta ta d'aura towel ta shige bathroom don yin wanka, acan Sabeer ya same ta suka sha soyayya then sukayi wanka suka fito shirya junan su suka yi, yana sanye cikin wata blue na suits sai necktie black da black shoes yayi matuk'ar yin kyau.

Yayin da Suhaima kuma ta shirya cikin wani swiss lace brown da touch na red d'in flower's tayi kyau sosai, fita suka yi zuwa dinning table agurguje suka yi breakfast, sannan ta wuce d'aki ta d'auko mayafi babba red colour ta yafa sai flat shoes da handbag redred in colour perfumes masu sanyin k'amshi ta sanya sannan ta fito.

"Wow! Baby na kinyi kyau sosai "
Cewar Sabeer yana rungume ta ajikin shi.
"Nagode Dear kai ma kayi min kyau "
Kissing ya bata goshi sannan ya rik'o hannun ta suka fito zuwa compound.


Suna zaune bayan mota driver nayin tuk'i suka fita daga gidan hanyar gidan Jiddah suka nufa.

"Baby nima yaushe zaki haifa mana Baby? "
Ya fad'a yana shafa flat tummy d'in ta, kunya ce ta kama Suhaima dakyar ta iyacewa
"Duk lokacin da Allah ya bani sai na haifa mana "
"Haba Baby ina kula fah dake tun daga kika zo gidan nan baki yi period ba yau 3 Month's har da 'yan kwanaki da auren mu, ai nasan da ajiyata anan shiru kawai nayi miki "

D'an tunani ta fad'a yi tabbas rabon ta da yin period tun lokacin sauran 2 week's bikin su amman koda tana gida sai tayi 2 months bata ga period yazo mata shiyasa idan ta tashi yi take fama da menstruation pain mai tsananin zafi.

"Kinyi shiru Baby ko ba haka bane? "
Tana shirin yin magana suka shiga gidan Jiddah don haka sai ta mayar da bakin ta tayi shiru.

Tare suka fito daga motar hannun su sark'e cikin na junan su, suna kok'arin shiga parlour ne aka bud'e kofa tare da fitowa, sai da gaban Suhaima yayi mugun fad'uwa ganin Mumyn Sabeer ce wadda ta jima da zuwa duba Jiddah da Babyn ta, idanun ta akan hannayen Sabeer da Suhaima fuskar ta sam babu alamar fara'a.

Jikin Suhaima na rawa take kok'arin kwace hannun ta amman Sabeer ya rik'e k'am yak'i ya cikata don haka kawai ta tsugunna tana gaida Mumy, bata amsa ba sai kau da kai da tayi.

Sakin hannun Suhaima yayi bugging d'in Mumy tare da bata peck a cheek nata, cikin sanyin jiki Suhaima ta mik'e daga tsugunnan da tayi.

Kallon ta Mumy take yi sosai wanda ya sanya Suhaima k'ara rikicewa gabanta banda fad'uwa babu abin da yake, wani irin fad'uwa gaban Mumy yayi masifar yi a lokaci d'aya da ta hango wasu canji atattare da Suhaima wanda tasan tabbas sai mace mai ciki ne take canjawa irin haka abin ka da likita, wani mugun gumi taji ya karyo mata tun daga saman gashin kanta zuwa fuskarta da jikinta.

Zame hannun ta tayi daga na Sabeer ta fara tafiya zuwa wajen motar ta hankalin ta a masifar tashe duk yanda zata yi sai tayi don ganin ba'a haifi wannan cikin ba, don bazata ta6a had'a zuri'a da 'yar kauye ba abin da bazai ta6a yiwuwa ba dole tasan yanda zatayi cikin ya fita idan yaso duk lokacin da ta samu ciki sai tana zubar dashi.

Tasan halin Sabeer yanda yake masifar son yara dole ya rabu da ita daga lokacin da ya gane ita take zubar mishi da ciki duk da son da yake mata kuwa a wannan lokacin ne zata aura mishi yarinyar da take son ya aura wannan dabarar ta shine kawai zai kawo k'arshen zaman Sabeer da Suhaima, wani shegen murmishi Dr Faridah ta saki tare da shiga mota tabar gidan zuciyar ta fes take jin ta gani take kamar ma Sabeer ya rabu da matsiyaciyar yarinyar nan..........



_To fah reader's kunji tunanin Dr Faridah ko zata yi nasara akan Suhaima ta rabata da Sabeer, ina jiran comments naku yanzu labari zai fara, ƙų ¢ıɠąცą ɖą ცıŋą ɖơŋ ʝıŋ ყąŋɖą ʑąɬą ƙąʂąŋ¢ɛ_.



Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[4/9, 6:30 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ






*PAGE 85-86*





Da kallon mamaki Sabeer da Suhaima suka bita dashi kawai kafin kuma Sabeer ya rik'o hannunta yace
"Sorry Baby nah akan abin da Mumy take miki bana jin dad'in haka ko kad'an "
Cikin rarrashi ya k'arasa maganar gashi fuskar shi d'auke da damuwa, d'an murmishin yak'e Suhaima ta saki sannan tace
"Kada ka damu don Allah komai mai wuce wa ne, mu tafi ka ga Baby kada ka makara a office ".
"Thank U Baby nah da yanda kike da fahimta i luv U "
Suhaima na shirin bashi amsa kenan Jiddah ta lek'o da kanta tana cewa
"Don Allah Yah Sabeer mene haka tun d'azu kuna tsaye anan ka hanata shigowa "

Hannun shi ya sanya tare da janyo kunnen ta d'aya yace
"Jiddah kin raina ni da yawa zan miki duka na tsayar da ita d'in mata ta ce ai "
D'an ihu ta saki na jin zafi kafin ta marairaice fuska tace
"Sorry Yah Sabeer na tuba na daina "
Yanda tayi d'in dole yasan ya shi murmishi ya cika mata kunnen, kamo hannun Suhaima tayi suka wuce cikin gidan.

Masha Allah abin da Sabeer ya fad'a lokacin da ya kar6i Babyn fara ce tas har wani ja ja take yi kyakkyawa da ita ta d'ebo kamannin D'an fillo family, wani son yarinyar ne ya shiga zuciyar Sabeer har yana imagine gashi Suhaima ta haifa mishi Baby yana d'auke da shi.

Kallon Suhaima yayi wadda take zaune kusa dashi tana lek'en Babyn don itama kanta tayi mata kyau ba kad'an ba.

"Baby kema kina so koh, ki haifa mana mu ma please "
D'an murmishi tayi kafin tace
"Toh my dear kayi addu'a Allah ya bamu masu albarka "
"Amin Baby "
Jiddah ya mik'awa Babyn don ya makara ma sosai, tashi Suhaima tayi ta rakashi har bakin mota suka yi sallama ta dawo cikin gidan, bayan ta gama ganin Babyn ne sai ta gyarawa Jiddah bedroom nata sannan ta wuce kitchen don shirya abincin rana.

Tana tsaka da girkin 'yan uwan Jiddah suka fara zuwa gidan kasa fita tayi su gaisa tayi don gabanta sai fad'uwa yake, dakyar ta k'arasa girkin ta zuba a foodflaks sai kawai taja kujera a kitchen ta zauna tare da had'a kai da gwiwa tana tunani.

Awannan yanayin Jiddah tazo ta same ta tausayin Suhaima ne ya kamata, dafa kafad'ar ta tayi a tsorace Suhaima ta d'ago kanta ganin Jiddah ce ya sanyata sakin ajiyar zuciya.

"Suhaima ki rage tsoron su fah wallahi, taya zaki zauna a kitchen bazaki fito ba saboda su? "
"Uhmmm Jiddah wallahi bana son kallon wulak'anci da k'ask'ancin da suke min, ina jin tsoron fita mu gaisa dasu kada su gwasale ni kamar yanda suke yi min "

"Kada ki damu Suhaima komai zai wuce amman baza ki tak'ura kanki ba saboda su don haka ki fito daga kitchen "

Babu yanda zatayi haka ta fito hannunta rik'e dana Jiddah, wani kallo na wulak'anci suka bita dashi kamar yanda Suhaima ta tsani ayi mata, babu wanda ya amsa gaisuwar ta sai ta6e baki da suke Jiddah ma sai da ta samu alakoran harara a wajen su.

Bedroom d'in ta Jiddah ta kaita ta zauna amman duk da haka a tak'ure take har so take lokacin tashin Sabeer daga office yayi yazo su wuce gida, duk da ya kirawo ta awaya amman ba'a kwanciyar hankali ta amsa ba mishi ba, har tunanin ranar suna take batasan irin wulak'ancin da zasu yi mata cikin mutane ba.

Atak'ure take har zuwa bayan mangarib sannan Sabeer yazo suka tafi gida, kallo d'aya yayi mata ya fuskanci tana cikin damuwa girgiza kanshi yayi yana yana sauke numfashi dole ya takawa 'yan uwan shi birki akan abin da suke yiwa Babyn shi bazai jure ba ko kad'an ganin ta cikin damuwa.

Duk damuwar da take tattare da ita sai da Sabeer ya cire mata ita ya mayar da gurbin farinciki a wannan daren sosai Suhaima ta k'ara jin wani son mijinta cikin zuciyar ta yanda yake faranta mata rai itama tana addu'ar Allah ya sanya ta haihu don cika mishi burin shi.


Ranar suna tun safe Sabeer ya kaita don yak'i barin ta ta kwana ko komawa bata sake yi ba sabida yana gudun kada a sake 6ata mata rai duk da kuwa nacin da tayi mishi, sosai Sabeer da Suhaima suka kashe kud'i wajen had'a wa Babyn kaya da kuma ita kanta Jiddah

Please Login or Register in order to submit comment