Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

idanun ta jinta ya d'auke na wucan gadi, don tun da Maman ta ta haifeta ba'a ta6a yi mata irin wannan marin ba, kafin ta dawo hayyacin ta daga marin Sabeer ya zage iyakar k'arfin shi ya hau dukan ta da belt, tuni Fadilah ta fara ihun kuka da neman agaji da k'arfi sosai take ihun wanda ya sanya k'arar ihun ta ya tashi Mumy da Daddy daga baccin su, a kid'ime suka fito daga bedroom d'in Daddy suka yo d'akin Sabeer don tanan haka suke jin k'arar ihun.


Da k'arfi suka tura kofar suka shiga hankalin su a tashe sosai, ganin duhu ne ya sanya Daddy kunna bulbs d'in room d'in tuni haske ya gauraye d'akin, hango tilon d'an su suka yi yana dukan Fadilah cike da fusatar da basu ta6a tsammanin yana da ita ba.


Da sauri Daddy ya nufi wajen shi yana cewa
"Son What wrong with U? "
Amman Sabeer bai kula shi cigaba yake da dukan ta kawai wanda yanzu babu bakin kuka sai hawayen da suke zuba cikin idanun ta, ganin bazai tsaya da dukan ya sanya Daddy rik'e shi gam a cikin jikin shi tare da kallon Mumy yace
"Janye Fadilah ki fitar da ita "
Jiki ba kwari Mumy take kok'arin d'aga tana kallon fuskar d'an nata wanda take hango kwantaccen 6acin rai akan fuskar tare da wasu hawaye da suke zuba a kan fuskar tashi gaba d'aya sai taga ya rikid'e mata ya zama wani mutum na daban kamar ba Sabeer ba, gashi idanun shi sunyi ja da fuskar shi, jikin Mumy gaba d'aya yayi sanyi haka ta ja Fadilah suka fita daga bedroom d'in ta tana tunanin me ya had'a Fadilah da Sabeer har yayi mata wannan mugun dukan.


Bayan sun fita daga bedroom d'in Daddy ya zaunar da Sabeer kan bed amman sai Sabeer ya zame ya zauna akan lallausan carpert d'in d'akin ya dafe kanshi da dukka hannu biyun yana hawaye wai yau shine yake kok'arin aikata zina wannan wacce irin bak'ar rana ce a wajen shi.


Bottle d'in faro Daddy ya d'auko a frige tare da glass cup ya tsiyaya a ciki tukunna ya rufe bottle d'in ya d'ora saman frige sannan ya k'arasa wajen Sabeer ya dafa mishi kafad'a tare da d'ora mishi bakin cup d'in a tsakanin lips nashi bai yi musu ba ya bud'e bakin ya sha ruwan sosai tukunna ya zame bakin shi ya kwanta a k'asan yana d'ora kanshi saman k'afafun Daddy.


Hannun shi Daddy ya sanya yana shafa lallausar suman kan Sabeer sun d'auki wajen 5 minute a haka, tukunna Daddy yace
"Sabeer sanar da ni abin da ya faru tsakanin ka da Fadilah har kayi mata wannan mugun dukan? "
dakyar Sabeer ya iya bud'e bakin shi yace
"Ba komai "
Hangame baki Daddy yayi yana kallon shi cikin mamaki har zai sake magana sai ga Mumy ta shigo room d'in cikin tashin hankali zata fara magana Sabeer ya dakatar da ita yana cewa

"Mumy leave me alone please"
Zata matso kusa dashi da sauri ya tashi ya koma saman bed ya kudundune cikin blanket zuciyar sai wani tafasa take sosai yake jin haushin Mumy don yasan duk ita ce ta nuna mata room d'in shi, kallon Daddy Mumy tayi ta marairaice fuska hannun ta ya rik'o tare da cewa
"Yana buk'atar hutu ne na fuskanci ranshi a 6ace yake sosai "
Cikin damuwa Mumy tace
"Yanzu bai fad'a maka abin da ya faru nima Fadilah tak'i fad'a min sai kuka kawai take"
Ta k'arasa maganar tamkar zata fashe da kuka, cikin kwantar da hankali Daddy yace
"Ki bari zuwa gobe nasan ya huce zai yi bayani amman nasan Fadilah tayi mishi laifi babba "

Haka suka fito duk jikin su a sanyaye sosai baccin ranar basu iya bacci ba tsakanin Sabeer, Mumy, Daddy da kuma Fadilah kowa sai juyi yake akan bed da tunani kala kala cikin zuciyoyin su.

Bayan sallahr asubah ne Sabeer ya fito daga side d'in su cikin shigar white T-shirt da 3quater yellow ya shiga motar shi k'irar Benz driver yaja shi, sai da suka yi tafiya mai d'an nisa tukunna driver yace
"Yalla6ai ina zamu je? "
D'an shiru Sabeer yayi yana tunani kad'an kafin yace
"Ina son ka kaini d'aya daga cikin wani k'auye mai kyau da ke makwabtaka da mu "
D'an murmishi driver d'in yayi tare da cewa
"Angama yalla6ai "
Yana gama fad'in haka ya nufi wata hanya, yayin da Sabeer ya kishingid'a a bayan motar a hankali yake jin zuciyar shi na yin sanyi...





Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz


Wannan shafin naki ne kyauta Zahra Maman Kausar da Ahmad thanks for luv and support, ina jin dad'in yanda kike k'aunar nvls d'ina, Allah ya bar zumunci ya raya mana Kausar da Ahmad, Amin ❣




PAGE 21-22




Cikin nutsuwa Suhaima ta fito daga d'akin ta cikin shirin uniform na tahfiz da yake ranar asabar ce, cikin kitchen ta k'arasa inda Aunty Aliyah take had'a abin karin kumallo ganin sinasir take yi ne ya sanya Suhaima sakin murmishi da yake tana son sinasir sosai, cikin jin dad'i tace

"Wow Aunty sinasir kike mana yau amman naji dad'i sosai bari nayi sauri na tafi kada nayi latti "
Murmishi itama Aunty Aliyah tayi tare da cewa
"Ai shikenan sai kin dawo, zaki sha 'yar tafiya kuwa yau don Yayan ki ya fita tun asuba zuwa kai kaji da kwayaye kasuwar birni "

D'an murmishin ta mai kyau Suhaima tayi tare da cewa
"Yeeeeee ai ni yau naji dad'in haka zan tafi a k'afa saboda kullum shi Yaya shi yake kaini kuma yaje ya d'auko ni ko'ina mutum zai je sai dai a kai shi ni fah yanzu na girma " ta k'arasa fad'i tana rawa har da juyi duk dad'i ya ishe ta.

Rik'e baki Aunty Aliyah tayi tana cewa
"Tabbb kenan dad'i kike ji ai kyasha tafiya kuwa yau "

"Eh naji Allah ya dawo da Yaya lafiya ni na tafi kada ki ja min latti "

Suhaima ta k'arasa fad'a tana dariya ta fice daga gidan da sauri, tabar Aunty Aliyah itama tana dariya kafin ta mayar da hankalin ta kan abin da take yi.



Cikin d'an sauri Suhaima take tafiya saboda ganin ta kusa latti aikuwa tana shiga cikin makarantar aka rufe kofa lokacin kaman 'yan latti yayi, wata ajiyar zuciya Suhaima ta saki ganin Allah ya taimake ta bata sha dukan latti ba da sauri ta wuce cikin ajin su, da yake k'auyen nasu babu laifi akwai masana ilimin addini dana zamani dai dai gwargwado, musamman ma ilimin addini sun fi bashi muhimmanci fiye dana boko, shi yasa suke da makarantar islamiyya da tahfiz.



K'arfe 11 na safe aka tashi su Suhaima nan tayi sallama da k'awayen ta ta wuce zuwa gida, don ba 'yan kusa da su a makarantar, saboda sune kusan gidan su na k'arshe k'arshen k'auyen, a nutse take tafiyar ta kanta a sunkuye yake tana tilawar karatun alqur'an a hankali koda kana kusa da ita ba lallai kaji abin da take fad'a ba sai dai kaga le6en ta na motsawa a hankali alamar dai akwai abin da take karantawa.


Tayi nisa da tafiyar ta don tayi wajen rabin tafiyar da zata kaita gida, horn taji ana yi mata amman sam batasan da ita ake ba tafiyar ta take kawai abin ta hankalin ta kwance.


Bata ankara ba taji mota ta goge ta kad'an a jikin ta har sai da madubin motar na waje ya bige ta a gefen hannun ta, wani irin zafi Suhaima taji a hannun ta da sauri ta d'ago kanta tana kallon motar da ta bige ta zata wuce saboda hanyar bata da kyau sosai akwai 'yan kwazazzabai shi yasa bata sauri, ganin mai motar bashi da alamin tsayawa ya bata hak'uri ko yayi mata sannu ne yasa Suhaima cikin fusata tace

"Kan ubancan! lallai mutumin nan baka da mutunci a bige ka ko sannu babu ka wani wuci kamar ka bige dabba ba mutum ba "

Ta fad'a da k'arfin ta ranta a 6ace, ganin ba alamar tsayawa yasa ta d'auki wani dutsen wuta a k'asa ta saita glass d'in motar ta jefa da iya k'arfin ta sai dai bai samu glass d'in ba sai fitilar motar ta baya ta samu, aikuwa babu 6ata lokaci ya ba da sautin k'arar fashewa, babu shiri mai driving d'in motar yaja motar ya tsaya.


Suhaima kuwa dad'i ne ya kamata da taga hakan taso ma glass d'in ta samu ta fasa tun da bashi da mutunci har da sakin wani murmishin mugunta.

Cigaba tayi da tafiyar ta abin ta har ta k'araso inda motar tayi parking amman babu wanda ya fito daga motar gashi glass d'in motar mai duhu ne ba'a ganin na ciki, sai dai na cikin ya gan ka, ita Suhaima ko alamar tsoro babu a tattare da ita ta wuce motar, baifi taku hud'u tayi ba tsakanin ta da motar taji alamar an bud'e kofar motar amman bata jiyo ba saboda bata da ra'ayin ganin wanda ke cikin motar.


Cikin fusata na cikin motar ya nufi inda Suhaima take tafiyar ta cikin zafin nama ya sanya hannun shi ya janyo hijab d'in ta na baya, tare da jiyo da Suhaima saitin inda yake ya d'aga hannu zai mare ta cak ya tsayar da hannun shi ya kasa karasar dashi kan fuskar Suhaima kamar yanda yayi niyya, sakamakon had'a ido da yayi da ita duk wani 6acin rai da ya kwaso shi yaji ya tafi a lokaci d'aya.

Kallon kyakkyawar face nata yake da eye's nata masu matuk'ar d'aukan hankali, runtse idon ta Suhaima tayi cikin tsoro jikin ta har ya fara 6ari na tsoro don ta zaci mari zata sha, eyelashes d'in ta yabi da kallo yanda suka bi idon suka kwanta kan beautiful face nata.


Jin bataji saukar mari ba ya sanya ta bud'e idanun ta a hankali ta sauke su kan fuskar kyakkyawan saurayin da yake gaban ta, ganin yanda ya zuba mata ido yana kallon ta ya sanya ta fincike hijab d'in ta da ya rik'e mata tare da gyara taayuwar ta aka wani rik'e kugu cike da tsiwa tace

"Malam lafiya da zaka wani rik'e min hijab? "

Sai da ya guy din ya lumshe idanun shi don jin saukar dadad'ar voice d'in Suhaima kafin ya sake bud'e idon nashi yana cigaba da kallon ta tamkar wadda ya samu wata tv yana kallo ko motsin kirki baya yi, sosai abin ya bawa Suhaima mamaki cikin zuciyar ta take cewa shi wannan baya jin tana magana ne ko kurma ne shi? da alamar ma daga birni yake.


Cikin tsiwa ta sake cewa "wai malam baka ji ina maka magana ko kai kurma ne? "

Ganin again ya kuma share ta sai kallon ta kawai da yake yi ne har da wani hard'e hannaye saman kirjin shi yasa Suhaima juya bayan ta cikin sa'a ta hango wani yaro na kusa da su hannun shi rik'e da robar ruwa a kanshi ya d'auko zai tafi gida.

Dad'i ne ya ishi Suhaima har da d'an murmusawa na mugunta don tasan abin da zata yiwa wannan mayen d'an birnin, yaron yana k'arasowa inda suke zai wuce da sauri Suhaima ta sanya hannunta saman kanshi ta d'auke robar ruwan.

Kafin yaron ya juyo tuni ta watsawa wannan guy d'in ruwan a jikin shi dukka tare da jefar da robar gefe d'aya, lokaci d'aya drivern da yake tsaye jikin motar da wannan yaron da Suhaima ta d'auki ruwan shi suka d'ora hannu a kansu cikin tashin hankalin da abin da Suhaima ta aikata, wata k'atuwar ajiyar zuciya ya sauke lokaci d'aya jin wannan ruwan mai shegen sanyi a jikin shi tsikar jikin shine ya tashi kafin ya sanya hannun shi a fuskar shi yana goge ruwan da yake di'gowa daga saman gashin kanshi yana kok'arin bud'e idon shi.


Ganin haka ya sanya Suhaima kwasa da gudu ita da yaron har ma yafi Suhaima gudu tamkar shi yayi laifin daman tuni ya mance da wata robar shi don anashi tunanin aka tashi kama da Suhaima har dashi za'a had'a, sai abin ma ya bawa guy d'in dariya sosai ganin yanda suke gudu kallon su yake fuskar shi d'auke da murmishi har sai da ya daina ganin su....




Ku hak'uri da wannan ban da charge wollah, ku biyo ni next chapter don jin abin da zai faru.



Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz


Ina kike Basmah Er lele wannan shafin naki ne kyauta ina tayaki murnar kammala littafin ki TAURA BIYU Allah ya Kara basirah da k'arfin ido, Allah ya bar zumunci. 👄



PAGE 22-23




Sai da ya daina ganin su tukunna ya dawo da idanun shi jikin shi inda yaga yanda ya jik'e sharkaf da ruwa, wani irin sanyi ne yake ji yana ratsa cikin jikin shi sosai.

"Yalla6ai kayi hak'uri don Allah kada ka fad'awa su Alhj da Hajia nasan korata zasu yi, ka rufa min asiri amman sam wannan yarinyar bata kyauta ba "

D'an murmishi Sabeer yayi ya bud'e baki zai yi magana atishawa ta taho nan ya fara yin ta sai da ya jira ta sau 4 tukunna ta tsaya, driver sai sannu yake yi mishi gaba d'aya hankali shi a tashe.

"Don't worry driver kwantar da hankalin ka mu tafi gida sanyi nake ji "

Sai lokacin driver ya d'an ji hankalin shi ya kwanta, da sauri driver ya bud'e mishi kofar mota ya shiga sannan ya rufe tare da komawa driver sit ya zauna tukunna yayi wa motar key suka bar wajen.

Sanyi sosai Sabeer yake ji ga atishawar da yake faman yi but still idanun shi nakan hanyar da Suhaima tayi, sosai yake jin wani abu game da yarinyar da ya gani tsiwar ta ta birgeshi yana fatan ya sake sanya ta a cikin idanun shi anan gaba.


Har suka kusan k'arasa wa gida Sabeer na tuna abin da ya faru tsakanin shi da Suhaima yana wani murmishi shi kad'ai, abin ba k'aramin mamaki yake bashi ba ganin ta tsaye mishi a rai, gate man yana bud'e gate Sabeer ya hango ilahirin Iyalan Alhj Ahmad d'an fillo sun firfito suna tsaye kallo d'aya mutum zai yiwa Alhj Ahmad d'an fillo, Hajjah Hauwaa da Alhj Hussien Daddy da Hajia Faridah Mumy a karanto tsantsar tashin hankali saboda sun nemi d'an lele an rasa inda yake kuma ba'a san inda ya tafi ba ga wayar shi a gida ya barta, tuni jikin driver ya fara 6ari na tsoro.


A hankali Sabeer ya bud'e motar ya fito ko driven bai tsaya jira ba, suna ganin fitowar shi suka saki ajiyar zuciyar kwanciyar hankali tare da tahowa inda yake hankalin su a tashe ganin jikin shi jagwab da ruwa, cikin rud'ewa Alhj Ahmad d'an fillo ya rik'o kafad'un Sabeer yace

"Sabeer wane shege ne ya jik'a ka haka? "
D'an murmishi Sabeer yayi kafin yace
"Ba damuwar ku bace kada wanda ya sake min wani tambaya ku rabu da ni and then kada wanda yace zai tak'urawa driver ya fad'a mishi "

Yana gama fad'in haka ya jiyo zai tafi da sauri Mumy ta rik'o hannun shi tare da cewa
"Amman son........ "
Bata k'arasa fad'in abin da zata ce ba ya dakatar da ita da hannun shi tare da cewa
"Please Mumy "
Ya zame hannun shi yayi gaba zuwa part d'in su, gaba d'aya jikin su yayi sanyi sosai kuma hankali ya tashi sosai musamman ganin shi a jik'e kuma yana ta atishawa, suna ganin driver ya wuce ta gaban su bayan ya gama parking motar basu da ikon yi mishi magana saboda kada su 6atawa Sabeer rai.


Sabeer yana shiga bedroom d'in shi toilet ya shige wanka yayi da ruwan d'umi tukunna ya fito ya gyara jikin shi tsaf cikin wani 3quater ash colour da T-shirt white mara hannu, fesa different perfumes yayi bayan ya gama ya kwanta tare da lullu6e jikin shi da lallausan blanket, lumshe idanun shi yayi tamkar mai jin bacci amman ba baccin yake tunanin kawai Suhaima yake ya dad'a tuno d'an k'aramin bakin ta tana mishi tsiwa, shi kad'ai yake juyi kan bed yana murmishi, yana tuna yanda ta watsa mishi ruwa ta gudu dakyar bacci ya d'auke shi mai nauyi zuciyar shi fal tunanin yarinyar da suka had'u da ita.


Duk wannan abin da yake Mumy na tsaye ta jikin window duk abin da yake tana kallon shi cike da mamakin murmishin da yake, tana tunanin me yake tunani haka yake irin wannan murmishin, ganin ya samu bacci ne yasa ta bar jikin windown zuciyar cike da tunani.





***** ******** *****




Suhaima sai da ta k'arasa kofar gida tukunna ta tsaya da gudun da take, sai da ta daidaita kanta sannan ta shiga gidan da sallama a nutsen ta, kamar ba itace mai gudu yanzu ba, Aunty Aliyah da ke zaune kan kujera tana wankin kaya ta amsawa Suhaima sallamar tana d'ago kanta ta kalle ta tare da cewa
"Suhaima sai yanzu kin dad'e yau hala surutun kuka yi aka tsayar da ku "

Wata dariya ce ta kubce wa Suhaima ta fara yi har da rik'e ciki da hawaye, cikin mamaki Aunty Aliyah take kallon ta kafin ta kuma cewa
"Lafiya Suhaima dariyar me kike haka? "

Amman Suhaima ba bakin magana sai da dariyar ta take, sosai Aunty Aliyah ta saki baki da hanci tana kallon Suhaima da ke dariya tamkar wata mahaukaciya har abin ya fara bata tsoro har ta fara tunani ko gamo tayi a hanyar makaranta, dakyar Suhaima ta tsayar dariyar saboda ganin yanda Aunty Aliyah ta fara rawar jiki na tsoro, zama tayi kan saman kayan wankin da Aunty Aliyah ke wankewa tace

"Aunty wani abu ne ya faru lokacin da nake tahowa gida shi yasa kika ga ina dariya "

Ajiyar zuciya Aunty Aliyah ta sauke ta kwanciyar hankali don sai yanzu taji hankalin ta ya kwanta, kafin ta bud'e baki tace
"Me yafaru? "

Nan Suhaima ta bata labarin abin da ya faru tsakanin ta guy d'in nan, don Suhaima bata iya 6oyewa Aunty Aliyah abu saboda shak'uwar da suka yi da juna sosai sun zama tamkar wasu k'awaye ko irin Yaya da k'anwar ta, sosai abin ya bawa Aunty Aliyah dariya don har yanda Sabeer yayi Suhaima take kwatanta mata, cikin dariya tace
"Allah ya shirya ki Suhaima, yanzu da ace ya kama ki fah ko ya mare ki "

"Tabbb da sai na rama Aunty duk da yafi ni tsayi sai nayi tsalle na rama, amman fah Aunty kyakkyawa ne kingan shi tamkar wani balarabe mybe ma baya jin hausa shi yasa yake kallo na "

"Uhm Allah dai ya kyauta, amman Suhaima ki daina irin wannan gangancin don kada ki tsokani wani wataran mara hak'uri ya cutar mana da ke "

"Toh Aunty na daina insha Allah, har yanzu Yaya bai dawo ba? "
"Eh bai dawo ba mybe akwai abin da ya tsayar dashi "
"Allah ya dawo dashi lafiya "
"Amin "

D'an shiru suka yi na 'yan minutes Aunty Aliyah na cigaba da wanki, can tace
"Ni kuwa Suhaima ina Jiddah ne kwana biyu shiru? "
D'an murmishi tayi tare da cewa
"Aunty Jiddah tana nan lafiya, hidimar biki ce ta sanya ta a gaba amman mun yi waya da ita jiya da yamma a wayar Yaya "
"Oh haka ne fah sauran kwanaki nawa auren "

"Sauran 2 week's fah Aunty gashi na rasa me zan siya mata matsayin gift's "
Suhaima ta karasa fad'a cikin yanayin damuwa.

"Kada ki damu anjima zamu yi magana yanzu kije ki cire uniform kizo ki karya tukunna"

"Toh Aunty "
Tashi tayi ta nufi bedroom nata don canja kayan jikin ta, bayan ta canja kaya ne sai kawai ta k'urawa mirror ido tana kallon shi, ta fad'a tunani beautiful guy d'in da ta yi mishi tsiwa d'azu ta d'an jima tana tunanin shi a haka har sai da Aunty Aliyah taji ta shiru ta fara kwalla mata kira tukunna ta sauke ajiyar zuciya ta fito waje tana amsa kiran da take mata...




Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz


Where are U guys dis page is dedicated to oll My sisters of (Exclusive Writers Forum), i luv U all my sisters i really luv U guys like totally 👄



PAGE 24-25




Bayan kwanaki 2 kamar yau ranar laraba da yammaci wajen 4:30,Suhaima tana zaune a bedroom nata gyaran wardrobe d'in ta take gefe d'aya kuma Aunty Aliyah zaune gefen gadon tana mik'o wa Suhaima kayan da ta linke ita kuma tana jera su a wardrobe sai hirar su suke cikin kwanciyar hankali.


"Assalamu Alaikum "
Kamar a mafarki Suhaima ta jiyo sallamar Jiddah, aikuwa da sauri ta wullar da kayan hannun ta da Aunty Aliyah ta mik'o mata, da gudu ta fita waje zuwa tsakar gidan cikin farinciki.

Jiddah tana tsaye a tsakar gidan sai murmishi take tana rarraba ido don hango ta inda Suhaima zata fito, tana hango fitowar ta a d'aki aikuwa da gudu ta k'arasa inda take suka rungume junan su suna dariya cikin tsantsar farinciki na jin dad'in ganin juna don anjima ba'a had'u ba.

Cika junan su suka yi cikin murmishi Suhaima tace
"My besty sannun ki da zuwa"

Kunshe da marmishi kan face d'in Jiddah tace
"Yawwa tawan kwana da yawa "
Ta fad'i hakan suna kok'arin k'arasa shiga d'akin Suhaima, cikin fara'a Aunty Aliyah tace
"Lale maraba da mutanen birni Jiddah kece tafe yanzu da yamma? "

Zama Jiddah tayi akan sallayar da Suhaima ta shimfid'a mata a k'asa ganin kan gadon kaya ne akai, sannan Suhaima ta fita zuwa kitchen don samo wa Jiddah abin motsa baki.
"Aunty kam nice tafe yanzu, ina yini? "
"Lafiya qlau Jiddah, ya gida da iyayen ki? "
"Duk suna nan lafiya Aunty suna gaida ku "
(Hmmm Jiddah ta fad'i hakan ne kawai, amman gaskiyar zance iyayen ta basu san wasu su Aunty Aliyah ba, kawai suna jin tana basu labarin Suhaima duk a zaton su friend nata ne na schl, ko zuwa nan gidan nasu da take basu san da zuwan ba).

"Muna amsa wa, ya fama da hidimar biki don nasan satin da zamu shiga shine na bikin koh? "
Aunty Aliyah ta tambaye ta tana mik'ewa tsaye, cikin d'an jin kunya Jiddah tace
"Ehh Aunty haka ne, ina Yaya Aliyu? "
"Ya zagaya cikin gona ne amman yanzu zaki ga ya shigo "

Har Aunty Aliyah zata fita daga d'akin da sauri Jiddah ta tsayar da ita tare da sanya hannu cikin hang bag nata ta d'auko wani kyakkyawan invitation card guda biyar ta mik'awa Aunty Aliyah tare da cewa

"Aunty wannan card d'in d'aurin aure ne na Yaya Aliyu da na Baba Adamu ne "
"To shikenan zan bashi idan ya shigo "
D'an marairaice fuska Jiddah tayi tare da cewa
"Amman Aunty zaku je ai? "
D'an murmishi tayi tare da cewa
"Me zai hana Jiddah insha Allah zamu je, Allah ya kaimu dai lokacin da rai da lafiya "
"Amin Aunty, sannan don Allah ki dad'a tunawa Yaya Aliyu sauran kwanaki 2 d'aurin aure zan zo na tafi da Suhaima "
"Zan fad'a mishi Jiddah kuma zai barta insha Allah "
'Yar dariyar farinciki Jiddah tayi tare da cewa
"Yawwa Auntyn mu ngde "

Daidai lokacin Suhaima ta shigo d'akin hannun ta d'auke da k'aramin tire wanda ta sanya abinci aciki da kuma lemon so6o acikin k'aramin jug na roba sai cup d'in shi k'arami, ajiye wa tayi gaba Jiddah Aunty Aliyah kuma ta fita don ta barsu su yi hirar su.

Bud'e plate d'in Jiddah tayi aikuwa ta had'a ido da wani lafiyayyen dambu wanda yasha zogale

Please Login or Register in order to submit comment