Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yayi ba kada d'an mutane ya mutu ta sanadin su haka kuma ta 6angaren Suhaima kuka sosai take tana zaune kusa da Sabeer idanun nan tamkar wad'anda zasu zazzago saboda kuka duk ta d'auki laifin ta d'ora wa kanta me yasa Sabeer bai bari ya harbe ta ba ya tureta, da dare wajen 11pm dakyar Yaya Aliyu da Aunty Aliyah suka lalla6a Suhaima ta tafi d'akin ta sai dai sam babu bacci a idanunta balle kuma maganar abinci.


Wanda rabon da taci tun da rana shima ba wani ci tayi sosai ba, ko yunwar ma bata ji baccin ma k'in yi tayi don gani take idan bacci ya d'auke ta kafin ta tashi Sabeer ya mutu tayi kukan har hawaye sun daina fita daga idanunta gashi sun kumbura sunyi ja sai zugi suke mata da rad'ad'i, daga k'arshe alwala ta d'aura ta shimfid'a abin sallah ta fara sauke sallahr mangarib da ishsha sannan ta fara nafila tana mai mik'a kukanta wajen Ubangiji ya tashi kafad'ar Sabeer tsayin daren nan a haka ta d'auka tana nafila sai da tayi sallahr asubah bacci yayi awon gaba da ita mai nauyi.



*_ Washe gari 11am_*

Firgigit Suhaima ta farka da baccin da yayi awon gaba da ita idanunta ta sauke kan agogo taga har 11 na safe mamakin nauyin baccin da ya d'auke ta take kafin kuma brain nata ya tunano mata abin da ya faru jiya da yammaci.

Zumbur tayi ta Mike cikin kid'ima ta fita daga d'akin, babu kowa a tsakar gidan kai tsaye d'akin Sabeer ta nufa ta shiga ko sallama bata samu damar yi ba.

Ta kutsa kai ciki a kwance yake sai Yaya Aliyu da yake sanya mishi magani a k'afar wajen harbin micijin daga gefe kuma Aliyah ce zaune ta zabga tagumi fuskarta d'auke da damuwa.

Zubewa Suhaima tayi a k'asa kusa da Sabeer cikin rawar murya tace
"Yaya bai farka ba har yanzu? "
Cikin damuwa Yaya Aliyu yace
"Eh Suhaima bai farka ba amman ki cigaba da yi mishi addu'a Allah ya tashi kafad'un shi "

Wani marayan kuka Suhaima ta saki nan Aunty Aliya ta janyo ta jikinta tana rarrashin ta, ana cikin haka sai ga Babaa Lantana, Baba Adamu da kuma Ashiru sun shigo kowanne hankali shi a tashe Ashiru har da kukan tausayin Sabeer.


Nan suka zauna kowa yayi jugum sai sautin kukan Suhaima ne yake tashi a cikin d'akin, sai da azahar tayi tukunna suka fita don yi sallah, Suhaima kuwa a d'akin tayi sallah ko wanka yau babu saboda tashin hankali (oh su Suhaima ashe dai ana son Sabeer ana tsoron kada ya margaya......lol ).

Bayan ta idar da sallahr ne ta zauna kusa dashi tana mishi addu'a duk ta wani rame saboda tashin hankali, har yammaci dai Sabeer bai farka ba kuma still har zuwa yanzu Suhaima na zaune a d'akin babu abin da yake fitar da ita sai alwala.

Sai bayan sallahr mangarib ne Suhaima na zaune kusa dashi taga ya farka a razane tare da yin magana da k'arfi yana cewa
"Suhaima ki gudu maciji ne a bayanki Suhaima....! "
Ya k'arasa maganar da fad'in sunan Suhaima da k'arfin gaske, da sauri Suhaima ta k'ank'ame hannun shi ana cikin haka Yaya Aliyu ya shigo da gudu bayan shi Aunty Aliya ce yana ganin Sabeer ya farka sai dai a razane yake cikin farinciki Aliyu ya rungume shi yana zubar da hawaye cikin zuciyar shi yana godiya ga Allah da ya sanya Sabeer farka wa.

Nan dai aka kirawo mai magani ya duba shi ya bayar da wanda zai sha tukunna ya tafi, Suhaima tana zaune a gefe ta zubawa Sabeer ido hawaye farinciki na zuba a idanunta.

Tun da Sabeer ya fara nutsuwa daga firgitar da yayi suna had'a ido da Suhaima da yayi mata kallon seconds ya d'auke kanshi bai k'ara kallonta ba, a hankali ta matso kusa dashi cikin sanyin murya tace
"Sannu Sabeer "
Ko kallon inda take baiyi ba ya d'auke kanshi, sau uku tana mishi sannu amman k'arshe sai ya kwanta kawai ya juya mata baya kawai.

Tuni Suhaima ta tsure sai faman rarraba ido take gaba d'aya jikinta yayi sanyi, kallon ta Aliyu yayi tare da cewa
"Suhaima tashi kije kiyi wanka kici abinci, yau fa ko wanka da abinci baki yi ba tunda ya farka kije ki huta "

Cikin sanyin jiki da rawar murya tace
"Toh Yaya "
Tana gama fad'in haka ta mik'e jiki babu kwari ta fita yayin da Aliyu da Aliyah suka bita da kallon tausayi lallai Suhaima ta fara son Sabeer bana wasa ba.

Tana fita Sabeer ya tashi zaune tare da cewa
"Aunty ko zan samu ruwan d'umi nayi wanka "
"Sabeer ka hak'ura da wanka sai gobe yanxu kayi brush kasha ko tea ne sai kasha maganin "
Cewar Aliyu kenan.
"Toh amman bazan ji dad'in jikina ba wallahi"
Sabeer ya k'arasa maganar cikin shagwa6a abin ka da shagwa6a66e komai zai yi saiya sanyo shagwa6a murmishi kawai suka yi suna mai sake bashi hak'uri, daga nan yayi brush yasha tea sannan aka bashi magani dakyar yasha yana yatsina fuska saboda ya tsani shan magani balle wanda bai ta6a shan irin shi ba tunda Dr Faridah ta kawo shi duniya, a wannan daren dakyar bacci ya d'auki Sabeer saboda sharewar da ya yiwa Suhaima ta tsaya mishi a rai sam bai ji dad'in abin da yayi mata.


Haka ma Suhaima dakyar ta iya yin wanka ta d'an ci abinci sannan ta kwanta bacci sai lalla6awa yayi ya d'auke ta.



Abu kamar wasa Sabeer baya kula Suhaima duk da tana kok'arin shigowa sau biyu safe da dare tana duba shi wani lokacin har da rana tana kawo mishi abinci amman baya kallon inda take balle ya amsa sannun da take mishi, gaba d'ayan su ba k'aramin hora junan su suke ba har Sabeer ya warke ras yana fita amman bai daina share Suhaima ba duk da ya karanto tsantsar sonshi akan fuskarta da cikin idanunta, kullum itace cikin gyaran d'akin shi.


Da sallama ta shigo d'akin hannunta da k'aramin flaks da cup wanda tayi mishi kunun gyad'a ta shigo d'akin, wani sanyin dad'i ne ya ratsa Sabeer jin sautin daddad'ar muryar Suhaima don rabon da yaji muryar tun jiya da safe saboda ciwon kan da ya hanata zuwa inda yake, amman sai ya maze ya amsa sallamar dakyar tare da d'auke kallon shi daga saitin k'ofar.

Shiga tayi ta same shi zaune kan katifa yana danna laptop yana sanye da wani 3quater da T-shirt mai k'aramin hannu yayi kyau sosai ga gashin jikinshi sun kwanta luf dasu gwanin sha'awa, zama tayi a gefen katifar tare da ajiye abin hannun ta a k'asa tace
"Wash! Na gaji yau, ya jikin ka? "
D'an kallonta yayi na D'an second's tayi mishi kyau cikin wata gown light blue tayi rolling da black veil sai tayi kyau sosai duk ire iren kayan da Jiddah take bata ne, d'auke kanshi yayi cikin zuciyar shi yana cewa zai sanya a kawo wa Suhaima gowns masu kyau daga dubai don ganin yanda suke mata kyau sosai.

"Uhm... Uhm ga kunun gyad'a nayi maka na zuba maka? "
"Bana sha tafi da abin ki "

Da d'an sauri ta kallo shi sai taga hankalin shi yana kan laptop, wani abu ne ya tokare mata makogaro muryar ta na rawa tace
"Don Allah kasha tun d'azu nake aikin yi maka shi fah please "

"Nace bana sha ana dole ne ko kuma na sanya ki "
Hawaye ne suka zubo akan face nata kafin kuma ta fashe da kuka ta fara diddira k'afa a k'asa kamar wata small babe, hankalin shi a tashe ya ajiye laptop d'in tare da cewa
"Toh ni me nayi miki da kike min kuka? "
Cikin shagwa6a tace
"Ba... Ba kai ne ba kace min baka sha kuma sai fushi kake dani bakason kula ni"

Nan ta cigaba da kukan sosai ta bashi dariya hannun shi ya sanya ya rik'o hannunta don bazai jure ganin Suhaima a haka ba tana mishi kuka agaban shi, had'uwar hannun su waje d'aya shi ya saukar musu da wani yanayi a tsakanin su, sake runtse hannunta yayi da d'an k'arfi har sai da Suhaima tayi d'an k'ara kad'an.

D'an sassauta rik'on yayi tare da cewa
"Sorry! "
Can k'asan mak'oshi yayi maganar.

"Don Allah Sabeer kayi hak'uri bana jin dad'in baka min magana idan na duba ka "

Girgiza kanshi yayi idanunshi cikin nata yace
"Komai ya wuce Suhaima but zan tafi na bar muku gidan ku "
D'an zaro ido tayi tare da cewa
"Saboda me? "
"Saboda wanda nazo domin ita bata sona gwara na hak'ura na koma inda na fito "

D'an shiru tayi kafin ta d'ago kanta tace
"Waya ce maka ba'a son ka "
"Ke kika fad'a min "
Ya k'arasa fad'i yana nunata da hannu.
"Ni.... ni ba haka ba fah nake nufi ba kawai dai...... "
Kasa k'arasa fad'a tayi don ganin yanda ya zuba mata ido tamkar wanda zai cinye ta da idanun shi......



Aishat A Muh'd ✍🏻
[3/3, 9:27 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




*PAGE 63-64*




Kasa k'arasa fad'in maganar tayi ganin yanda ya zuba mata ido tamkar wanda zai cinye ta da idanun shi, jin tayi shiru ne kuma ta sunkuyar da kai yasa shi sanya hannun shi ya d'ago face nata kafin yace

"Uhm ina jin ki Baby kawai dai me ".
Kasa jure kallon cikin idanun shi tayi sai ta lumshe idonta, kallon eye's lashes nata kawai yake cike da sha'awar kissing nasu sai dai ba yanzu yake son aikata hakan ba, d'an bud'e idonta tayi suka had'a eye's nasu kafin cikin d'an jin kunya Suhaima ta janye idanunta saboda ganin har idonshi ya fara canja launi tace
"Ya wuce fah, yanzu ka hak'ura zaka sha kunun ? Kada kace min a'a please "

Mak'e kafad'a yayi cikin shagwa6a da langa6e kai yace
"Nak'i wayon sai kin fad'a min idan ba haka ba bazan sha ba yarinya "

Sam Sabeer ya mance da duk wani shiri da yayi na share Suhaima, lallai ba k'aramin so yake mata ba, maganar tace ta katse mishi tunanin shi da yaji tana cewa
"Haba Yaya nah na zuba maka "
Dariya ta bashi sosai jin sunan da ta kirawo shi.
"Yaya na koma yau kuma?, wannan ai sunan Babban Yaya ne ni miji ne ba Yaya ba "

D'an rufe hannunta tayi da tafin hannunta sai ta d'an wara yatsun tana kallon shi ta haka kafin tace
"Ai kaima kazama Yaya tunda Yayan Jiddah ne kuma ka girme ni"
Tana gama fad'in haka ta janyo cup ta had'a mishi kunun ta ajiye mishi a gefen shi.
"Koh! "
Ya fad'in hakan yana kashe mata ido d'aya wani kunya ne ya sake kama Suhaima sai kawai ta mik'e zata gudu har zata fice daga d'akin taji yace
"Suhaima har zuwa yaushe zaki furta min kina sona ne?, ki tausaya wa rayuwata Suhaima ki amshi soyayyata nayi alkawarin kasancewa dake cikin tsayin rayuwata bazan ta6a wulak'anta ki ba ko na guje miki ina yi miki wani so wanda baki bazai iya kwatanta miki ba "
Cikin sanyin murya ya k'arasa fad'in haka fuskar shi d'auke da damuwa.

Jikinta ne yayi sanyi sosai har ta gaza d'aga k'afanta sai kawai ta tsaya itama zuciyar ta yayi rauni sosai ga wani sabon son Sabeer da ya k'ara shiga cikin zuciyar ta, gashi yanda ya sadaukar da rayuwar shi don ya ceci nata lafiyar da rayuwar koda iya hakan tasan Sabeer ba k'aramin sonta yake ba don haka bazata bar wannan damar ta kubce mata, don haka batasan lokacin da bakin ta ya furta

"Ina sonka Sabeer nima bazan iya rayuwa babu kai ba "
Tana k'arasa fad'in haka ta juya da gudu tabar d'akin cikin jin kunya.

Sabeer kuwa zaune yake kamar mutum mutumi saboda tsabar mamakin abin da ta furta mishi, anya ba mafarki yake ba kamar yanda ya saba tunanin shi da ne ya katse a lokacin da hannun shi ya dangwarar da cup d'in kunun gyadar har yayi nasarar zubo mishi a hannun shi wata 'yar k'ara ya saki kad'an, kafin kuma ya wuntsala kan katifar ya fara juyi na jin dad'i tabbas ba mafarkin da ya saba ba ne, da gaske ne Suhaima tace mishi tana son shi, sai da ya gama juyin murna sannan ya d'auki phone nashi num d'in Daddy ya lalubo ya kira.

Daddy yana picking ko sallama Sabeer bai yi ba saboda tsabar zumud'i cikin murna yace

"Daddy ka tayani murna Suhaima tace tana sona zata aure ni Daddy! "
Wani sanyin dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar Daddy fuskar shi cike da fara'a yace
"Alhamdullilah congrats son, yaushe zaka dawo don muna kewar ka? "
Yana dariya Sabeer yace
"Very soon Daddy! "
"Okay ya kamata ka dawo sai a fara maganar aure, uhm son za'a zama babba "
"Kaiiii Dad! har da tsokana koh? "
Ya fad'a cikin shagwa6a, dariya Daddy yayi kafin su cigaba da hira har zuwa lokacin da suka yi sallama, kwanciya Sabeer yayi ya lumshe idanun shi yana tuno lokacin da Suhaima take fad'a mishi tana son shi zata aure shi da wannan tunanin bacci yayi awon gaba dashi.

Lokacin da Suhaima ta fito da gudu daga d'akin Sabeer sauran kad'an ta bige Aunty Aliya tayi saurin kaucewa tana cewa
"Sorry Aunty nah"

"Lafiyan ki kuwa Suhaima? "
Fad'in Aliyah kenan.
"Aunty lafiya qlau wallahi "
tana gama fad'in haka ta wuce d'akin ta da sauri yayi da tabar Aliyah baki sake tana kallonta.

Kan bed ta fad'a tana murginawa akai tana wani murmishi dagani murmishin farinciki ne take, jinta take sakayau kamar ta sauke wani babban abu akanta.

"Ina son ka Sabeer, i luv U so much "
Fad'in Suhaima a fili tana rufe fuskarta da hannunta kamar mai jin kunya wani na ganin ta.


Tun daga wannan lokacin wata tsaftacacciyar soyayya ake gudanarwa tsakanin Sabeer da Suhaima, bawa junan su kulawa suke tare da tattalin juna, Yaya Aliyu, Aunty Aliya da su Babaa Lantana da Baba Adamu sun yi matuk'ar farinciki da kar6ar soyayyar Sabeer da Suhaima tayi.


Yammaci ne irin na bayan sallahr la'asar Sabeer da Suhaima suna zaune a tsakar gidan saman wata babbar tabarma hira suke yi irin ta masoya.

"Assalamu Alaikum "
Suhaima ta tsinkayi sallama da muryar da bazata ta6a mance ta ba, don haka zumbur ta mik'e da sauri ta nufi k'ofa nan suka had'u da juna, wani ihun murna Suhaima ta saki tare da yin tsalle ta rungume Jiddah cikin tsananin farincikin ganin ta.

Sai dai kuma jin abu ya tokare ta yasa ta sakinta tare da yin baya kad'an tana kallan d'an tudun da cikinta yayi, cikin dariya tace
"Besty kaddai mun samu Baby "

Dariya Jiddah tayi tare da kawo hannu ta d'an bugi kafad'ar Suhaima cikin k'asa k'asa da murya tace
"To sarkin tonon silili kina son ki kunyata ni gaban su Yaya "
Hannunta ta rik'o tare da juyawa da nufin su k'arasa wajen tabarmar su zauna, sai suka had'a ido da Aunty Aliyah wadda ihun Suhaima ya fito da ita daga d'aki ba shiri.

Cikin farinciki Aunty Aliya tace
"Jiddah yau kece a gari"
Cikin dariya Jiddah tace
"Ni ce wallahi Aunty ina Yaya Aliyu da Ameer ne ban gan....... "
Sauran maganar Jiddah ta mak'ale a bakinta saboda had'a ido da Sabeer da tayi.

Cikin mamaki tace
"Yaya Sabeer! "
Da murmishi kan face nashi yace
"Sai yanzu kika kula dani kenan "
Tana dariya tare da rufe bakinta tace
"Yah Sabeer ba haka ba ne wallahi d'okin ganin Besty ne ya sanya ban kula da kai ba "

D'an murmishi kawai yayi kafin ya wuce ya tafi, da mamaki sosai Jiddah take bin shi da kallo ko a mafarki bata zaci Sabeer zai zauna a irin wannan yanayin ba, kuma tayi farinciki da hakan don tun ba yanzu ba take sha'awar wani nata ya auri Suhaima saboda son da take mata, kama hannun ta Suhaima tayi suka zauna nan ta kawo mata ruwa kafin su fara gaisawa da Aunty Aliyah tana yi mata barka da samun Baby sun d'an ta6a hira kafin su wuce cikin d'akin Suhaima.


Nan suna shiga hira ta 6arke tsakanin su Suhaima sai tsokanar Jiddah take yanda tayi k'iba, Jiddah na dariya tace
"Yarinya sai kin yi uku nama don nasan Yah Sabeer zai baki kulawa ba kad'an ba"
"A haba taya zan yi ukun ki da ban ganu ba"
"Babyn kune ya sanya min wannan k'ibar don kiji yana zuwa nan duniya zan koma kamar yanda nake "

Da haka suka cigaba da hirar su inda Jiddah take fad'awa Suhaima abin da ya sanya bata zo ba lokacin da suka dawo daga honeymoon laulayin ciki ne ya sanyata a gaba sai yanzu ta samu dama dama.

Sai wajen mangarib Jiddah ta tafi cike da kewar Suhaima bayan ta ajiye musu tsarabar su har ta tafi dai basu k'ara had'uwa da Sabeer ba.....



Aishat A Muh'd ✍🏻
[3/6, 11:04 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




*PAGE 65-66*




Suhaima ta shigo gidan kenan daga rakiyar Jiddah k'ofar gida sai taji rik'o hannunta a d'an tsorace ta juya don duhu ya fara yi gaf ake da kiran sallahr mangarib.

Had'a ido tayi da Sabeer yana mata wannan kyakkyawan murmishin nashi
"Matsoraciya kawai "
D'an sauke ajiyar zuciya tayi kafin tace
"Ni Allah kaban tsoro na kusa sanya ihun neman taimako "
'Yar dariya yayi kafin yace
"Sorry Baby nah kin cika tsoro, haka jiya kika cika mana kunne da ihu don kinga lizard ya shiga toilet kina wanka "
Murmishin dariya Suhaima tayi don ta tuna lokacin Allah yaso ta ko cire zanin jikinta bata yi ba ta hango shi manne jikin bango.

"Baby ki rage tsoro please bana son ganin abin da zai na tsorata ki "

D'aga kanta tayi alamar toh kawai nan ya cika mata hannu tare da cewa
"Baby anjima zamu yi magana fah da kai lokaci yayi da ya kamata mu yi aure na bar rungumar pillow koh yah? "
Ya k'arasa fad'in haka yana d'aga mata gira ya cigaba da cewa
"Nasan kema kina buk'atar hakan koh? "
Kunya ce ta rufe Suhaima don haka sai kawai ta ruga da gudu zuwa cikin gida tana 'yar dariya a hankali, bayanta Sabeer yabi da kallo yana murmishi kafin kuma ya juya ya fita zuwa masallaci.

Suhaima tana shigowa tsakar gida ta nufi wajen alwala, nan tayi alwala ta wuce d'aki tana shiga ta shimfid'a abin sallah ta fara sallahr mangarib after ta idar ne ta janyo Qur'an ta hau karatu har zuwa sallahr ishsha bayan ta idar ne sai tayi addu'o'in ta daga k'arshe ta rufe addu'ar da neman za6in Allah tare da yiwa mahaifiyar ta addu'a kamar yanda ta saba, bayan ta kammala ne sai ta kwanta saman sallayar tana mai fad'awa duniyar tunani ta yanda zata iya d'auke kai daga duk wani wulak'anci da family d'in Sabeer zasu yi mata, ta jima tana wannan tunanin kafin kunnen ta ya jiyo mata kiran sunan ta da Aunty Aliyah take mata.

Tashi tayi tare da kallon k'aramin agogonta taga har 8:32 na dare, da sauri ta rarumo hijab nata ta d'an fesa turare ta fito tunawa da tayi Sabeer ya fad'a mata zasu magana anjima, tana fitowa ta tarar da Aunty Aliyah a zaune tana bawa Ameer mama.

Zama tayi kusa da ita tare da cewa
"Aunty ga ni "
Yawwa Suhaima daman Sabeer ne yake kiran ki yana k'ofar gida"

Tashi tayi ta wuce ta fita a k'ofar gida ta hango shi zaune shi da Ashiru wajen ta nufa tayi musu sallama cikin sanyin murya, Sabeer sai da ya lumshe idanun shi kafin ya bud'e su akanta ya amsa sallamar ta.

Ashiru ya gaida Suhaima ta amsa cikin fara'a kafin ya tashi yace
"Toh Yaya ni sai da safe zan shiga gida "
"Okay Ashiru sai goben"
Yana gama fad'in haka ya wuce gidan su, sannan Sabeer ya dawo da hankalin shi kan Suhaima wadda take tsaye yace
"Amarya ta zauna mana kada ki gaji da tsayuwa "
D'an nesa kad'an dashi ta zauna saman wani dutse, nan ya fara tsokanar ta yana dariya ita kuma kunya yake bata don har yanzu ta kasa sakin jiki dashi musamman idan ta tuna abin da tayi mishi a baya.

Bayan ya gama tsokanar ta ne sai kuma ya gyara zama cikin nutsuwa yace
"Suhaima! "
D'an d'ago wa tayi ta kalleshi kad'an saboda jin yanda ya ambaci sunan nata kafin tace
"Na'am! "

D'an ajiyar numfashi yayi kafin yace
"Suhaima ina son gobe zan koma gidan mu fah"
A d'an razane ta d'ago tana kallon shi don lokacin da ya fara maganar kanta a k'asa yake tana wasa da 'yantsunta.

"Yes! Baby gida zan tafi zanje na samu Daddy yazo neman min auren ki, mun gama magana da Yah Aliyu dasu Baba don sam ban so awuce 2 month's ban mallake ki matsayin mata ta ba"

"Wata 2 fah Sabeer haba me ma laifin nan da 2 year ".
Cewar Suhaima kanta a sunkuye don bazata iya jurar ganin irin kallon da Sabeer yake mata, ji take kamar ta kwashe da dariya saboda tasan tsokanar shi take so take taga yanda zai yi don haka danne dariyar ta.

Aikuwa wata harara ya dank'ara mata kafin yace
"Sun yi kad'an ma 2yrs a barshi nan da shekaru goma ma yafi"

Ba shiri dariyar da take danne wa ta kubce mata aikuwa ta fara kyalkyala dariya amman ta nutsuwa, sakin baki Sabeer yayi yana kallonta sai a time d'in ya lura tsokanar shi take, lallai kuwa idan ya kama Suhaima a hannun shi zata yi bayani.

"Ya hak'uri mai da wuk'ar tsokanar ka nake a daina harara ta"

D'an murmishi yayi tare da cewa
"Lallai yarinyar nan kin rainani da yawa but zaki bayani idan kika shigo hannuna duk sai na rama abin da kike min "

Marairaice fuska Suhaima tayi tare da cewa

"Wayyo Allah kayi hak'uri ni fah tsokanar ka nake yi amman bazan k'ara ba"

Mak'e kafad'a yayi tare da cewa
"Nak'i wayon yarinya sai nima na rama "

Ya k'arasa fad'i yana dariyar mugunta, baki ta murgud'a kafin ta turo shi gaba
"Lallai ma yarinya ni kike murgud'a wa baki?"
Girgiza kanta tayi sannan tace
"Ni fah ba da kai nake ba ".
"Toh naji dawa kike? "
A shagwa6e tace
"Ni kawai nayi ne".

Murmishi kawai yayi kafin yace
"Baby mu dawo maganar mu, mene ra'ayin ki? "
Kanta a sunkuye tace "ni mezance toh Allah ya za6a abin da yafi alkhairi ".
"Amin Baby nah, ko zaki rakani mu tafi tare? ".

D'an zaro ido tayi tare da dafe kirji tace "waiii ni! rufa min asiri don Allah "
D'aga kafad'un shi yayi kafin yace "to mene aciki "
"Tabbb ni dai bazan iya ba wallahi "
"Sarkin kunya kawai kin cika kunya Baby amman ina daf da cire miki ita kad'an zan rage miki ita"
Waro idanunta tayi gaba d'aya tare da cewa
"Tabbb daman ana cire kunya "
"Eh mana sosai, idan kina so ma yanzu sai na fara cire miki " ya k'arasa fad'a yana dariyar mugunta
Da sauri ta girgiza kanta tare da cewa
"A'a bana so ina son kayata "

Hannun shi ya sanya a gefen shi ya d'auko d'aya daga cikin phone's nashi, ya mik'o mata cikin mamaki take kallon shi ta kasa kar6a
"Baby kar6i mana "
Hannu tasa ta kar6a sannan yace
"Ki rik'e wannan a hannun ki kafin kizo gidana mu je ki za6i wadda kike so "

"A'a Sabeer baza mu yi haka gaskiya ka rik'e wayan ka, sai muna magana da wayar Yah Aliyu ".

D'an 6ata rai yayi kafin yace
"Baby bana son irin haka king kin 6ata min rai, idan kina son raina yayi sanyi ki kar6a "

"Ayyah sorry na kar6a nagode sosai Allah ya saka da alkhairi naji dad'i "

Wani sassanyar murmishi ya saki sannan yace
"Baki k'arasa

Please Login or Register in order to submit comment