Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tabbatar da hakan? "
"Sosai ma Yalla6ai "
Ta fad'a hakan tana k'ak'alo murmishin yak'e, don Dr Faridah ce ta tsara mata abin da zata ce idan ba haka ba zata koreta daga hospital nata.

Murmishin mugunta Dr Faridah ta saki bayan ta gama kallon maganar da Daddy yayi wa Dr Nabilah ta laptop d'in ta, kwantar da kanta tayi jikin kujera tana juyi tace
"Daddy duk binciken ka bazaka ta6a gane gaskiya ba dole Sabeer ya rabu da matsiyaciyar yarinyar nan "
Ta k'arasa maganar tana dad'a sakin wani murmishin.
Mumy ta mance da _rana dubu ta 6arawo rana d'aya ta mai kaya, za'ayi walkiya duk daren dad'ewa zaku ma a gane abin cikin dubu_



Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[4/10, 1:26 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ


♻ *Eҳ¢ʂųιı۷ɛ щγıɬɛγ'ʂ ʄơγųɱ*



*PAGE 91-92*





Sabeer k'in yarda yayi a zubawa Suhaima jinin kowa sai nashi hakan ba k'aramin k'ara fusata Mumy yayi ba amman ta danne don batason nunwa.

Jiddah itama tayi kuka ta tausayawa Sabeer sosai mutane sosai suka zo dubiyar Suhaima har dasu Yah Aliyu, Aunty Aliyah, Babaa Lantana da Baba Adamu duk sun zo, haka ma friend d'in Sabeer wato Musaddiq da matar shi Mufidah sun zo, kowannen su da abubuwan kayan duban shi.

Sati d'aya Suhaima ta d'auka a hospital ta samu sauk'i sosai don kulawa sosai Jiddah da Sabeer suke bata gashi ma yak'i yarda Babaa Lantana ta zauna saboda shi yake kwana da ita dole ta hakura da zaman jinyar Suhaima, duk da har yanzu tana cikin takaicin zubewar cikinta bata sanya shi cikin ranta sosai ba ita take ma da k'arfin gwiwar rarrashin Sabeer da yayi hak'uri ya kar6i kaddarar da Allah ya d'ora mishi.

Kwanakin ta goma a hospital aka sallame ta don ta warke garau da ita, bayan an sallame su gida suka dawo abin su sosai Jiddah ta gyara mata gidan tsaf sai da tayi mata girki na dare sannan ta tafi gida.

Awannan daren Sabeer yayi addu'a Allah ya sanya kwallon shi ya fad'a raga, sun nunawa junan su so da kulawa sosai a wannan lokacin sai gabanin asubah suka samu damar yin bacci.




_*After 4 Month's*_



Da dare misalin wajen 10 na hango Suhaima tana fitowa daga bedroom nata, tana sanye cikin wata white sleeping dress irin transparent d'in nan gashin ta yasha gyara sai kyalli yake ta zubo shi ga wani k'amshi mai dad'i da take fitarwa tayi kiba abin ta.

K'arasa tayi inda Sabeer yake ta shige jikin shi, wanda tun tahowar ta yake kallonta kasa k'arasa aikin yayi a laptop d'in ya rufe ta tare da janyo ta jikin shi yana shinshina ta yace
"Baby kinyi kyau sosai "
"Thank U "
"Ni fah ice cream nake son sha yanzu "
D'an zaro ido kad'an yayi kan yace
"Baby yanzu fa 10 ta wuce fah kiyi hakuri sai gobe please "

"Allah idan bansha ba bazan iya bacci ba ka taimaka min Yah Sabeer please "
Ta k'arasa maganar kamar zatayi kuka, bubbuga bayanta yake yace
"Okay Okay naji Baby za'a kawo miki yanzu, amman ya akayi na koma Yah Sabeer kuma"

Kashe mishi ido tayi tare da kad'asu tace
"Abin sirri ne "
Yana dariya yaja hancin ta sannan yace
"Bari na dawo a fad'a min sirrin "

Tashi yayi yana kok'arin fita tace
"My dear a sanya min flavours na vanilla and strawberry "
"Okay Baby na"

Fita yayi ya samu driver da bai riga ya tafi gida ba ya tsaya hira da maigadi Sabeer ya aike shi siyo mata ice cream d'in sannan ya dawo ciki.

"Baby fad'a min sirrin da ya sanya aka kirawo ni da Yah Sabeer "
'Yar dariya tayi tukunna tace
"Kaiii my Dear baka mantuwa ni fah ba komai "

"Aikuwa yarinya sai kin fad'a min "

Nan ya fara yi mata cakulkuli tana tuntsira dariya shima dariyar yake sauran kad'an ta fad'o daga saman kujera ya rik'o ta tare da d'orata kan k'afar shi yace
"Baby naga fah alamun Allah ya amshi addu'a ta don kin sake canjawa musamman hips d'in ki da boobs nake sun k'ara cika anya ban ajiye miki ajiyata ba, ga kwanaki biyun nan wani irin kwad'ayi kike ji dashi dama Doctor na karanta kamar yanda Mumy taso nayi da yanzu na gane "

Sai da gaban Suhaima ya fad'i da taji ya ambaci sunan Mumy amman sai ta share tace
"Nima bansani ba my dear amman nasan tunda na dawo daga hospital sau d'aya nayi period d'ina kuma yanzu muna 4 Month's fah "

"Allah nagode maka insha Allah shine ma gobe zan kirawo Dr Aishat ta duba min ke "

Suna cikin haka aka danna door bell Larai mai aiki ce ta bud'e k'ofar ta kar6i sak'on ta kawo wa Sabeer, kallonta Sabeer yake shi sam yarinyar bata kwanta mishi a rai ba shi yasa yake sanya mata ido aduk wani motsinta.


"Hajiya na tabbatar da abin da na fad'a miki don naji suna hirar yanzu "
Daga can 6angaren akayi mata magana nan ta dunga gid'a kai kamar k'adangaruwa alamar tana fahimtar abin da ake fad'a mata, sun d'an jima suna waya kafin ta ajiye wayar nata.

Apalo kuwa bayan Suhaima ta gama shan ice cream d'in ne Sabeer ya d'auke ta suka nufi side nashi, a wannan lokacin kowannen su sai da ya zage wajen nunawa d'an uwanshi irin son da yake mishi, sunyiwa kansu alk'awarruka acikin wannan daren wanda har daga cikin alk'awarin su na zasu rayu da juna har abada bazasu rabu ba da junan su, soyayya sosai suka gwada wa junan su, sai bayan Suhaima ta samu bacci ne Sabeer yaje yayi wanka tare da d'aura alwala ya fito, shimfid'a abin sallah yayi ya fara nafila sai da yayi raka'a biyu sannan yayi addu'a sosai Allah ya sanya Suhaima ciki ne da ita ya dad'e yana addu'ar samun yara nagari tare da addu'ar Allah ya kad'e duk wata fitina da tashin hankali azaman su na aure, sai bayan yayi sallahr asuba bacci mai nauyi ya d'auke shi, ko da Suhaima ta idar da nata sallahr ta tarar ya koma bacci itama jikin shi ta kwanta suka koma baccin nasu da yake weekend ne.



_*10:35 am*_


A lokacin suka tashi daga bacci suka yi wanka simple gown Suhaima ta sanya ajikinta shima Sabeer ya shirya cikin 3quater white da T-shirt white itama a palo ya zauna yayin da Suhaima a gurguje ta shirya musu breakfast.


Kallon Larai tayi tace
"Don Allah d'an had'a min kunun gyad'a cikin cup d'aya "
Jiki na rawa tace
"Toh Aunty "
Sannan Suhaima ta fita daga kitchen d'in, ta kaiwa Sabeer breakfast d'in kan dining table ta had'a mishi komai, zama tayi alokacin ya k'araso inda take yace
"Baby taho nayi feeding d'in ki "
"A'a ni bana son cin komai kunu zan sha kawai "
"Ayyah Baby gashi ni ban iya ba kizo mu je kitchen kina fad'a min nayi miki "

"Kabar shi na sanya Larai ta dama min "
D'an 6ata fuska yayi yana shirin magana Larai ta k'araso wajen gaida Sabeer tayi bai amsa ba sai ma kau da kan da yayi.

Ajiyewa Suhaima cup d'in tayi cikin murmishi tace
"Na gode Larai "
"Ah ba komai duk abin da kike so ki fad'a min Aunty "

Tana gama fad'in haka tabar wurin d'an hararar Suhaima yayi kan yace
"Baby ni fah i hate dis gurl zata bar gidan nan soon a sama miki wata"

"A haba dear me ta tsare maka? "
"Ni bata kwanta min ba a rai "
Murmishi tayi kawi ta fara shan kunun sam Sabeer kasa cin abincin yayi yana kallon ta don sai yaji zuciyar shi na ayyana mishi kunun nan bai yarda dashi ba, amman ganin bashi da wata hujja ne ya sanya shi kawai barinta tana sha.

Bayan ta gama shane ta fara bashi abinci abakin shi ganin yak'i cin nashi, bayan ta gama bashi suka dawo parlour zama Sabeer yayi ita kuma Suhaima ta mik'e tsaye kallon ta yayi kafin yace
"Baby ina zaki? "
"Fitsari nake ji Dear bari naji na dawo "

Shiga bedroom d'in ta tayi ya bita da kallo kawai, Suhaima na shiga bathroom ta tsugunna zata yi fitsari sai kawai ganin jini tayi yana zuba maimakon fitsari, a razane ta mik'e tsaye jikinta na 6ari lokaci d'aya taji marar ta tana k'ullewa kasa d'aga k'afar ta tayi sai kawai ta zube akasan tiles d'in bathroom ta kwallawa Sabeer wani irin kira da k'arfi.


Sabeer da yake zaune yana kallon film d'in furious 7 a mbc 2 yaji kiran da Suhaima take mishi da sauri ya tashi ya nufi d'akin nata kai tsaye bathroom ya bud'e ganin bata cikin d'akin, idanun shi ne suka sauka akan tiles d'in toilet d'in wanda ya kasance fari jini gaba d'aya ya rina wajen, ga Babyn shi durkushe tana murk'usus tare da kiran sunan shi.

Saboda tsabar tashin hankali sau ran kad'an Sabeer ya zube a k'asa jikin shi na rawa ya d'auke ta kawai ya fito daga d'akin da gudu ya nufi hanyar fita daga parlourn.

Larai tana ganin haka da sauri ta shige bedroom d'in Suhaima ta sanya wasu abubuwa cikin drower ta fito.


Gudu kawai Sabeer yake shararawa akan hanya har ya k'arasa hospital d'in Mumy, a rikice yayi parking tare da bud'e bayan motar ya d'auko Suhaima yayi cikin asibitin da ita.


Da Mumy ya fara cin karo fitowar ta daga room d'in operation tana zame hand gloves d'in hannun ta, ganin d'an nata ne tare da Suhaima ya sanya ta kiran nurses suka kar6i Suhaima zuwa wani room na daban, yayin da Sabeer ya zube a k'asa yana kuka sosai, dafa kafad'ar shi tayi jiyowa yayi ya rungume ta had'e da fad'in
"Mumy ina rok'an ki kada ki bari na sake rasa cikin nan please Mumy ki taimaka min "

Tausayin d'an nata ne ya kamata amman tasan dab take da rabuwa su bazata bari tausayin shi yayi rinjaye cikin zuciyar ta ba.

Da kanta ta jagoranci su Dr Aishat da Dr Nabilah zuwa room d'in da aka kwantar da Suhaima don tana son su zame mata shaidu, sunyi nasarar tsayar da jinin sai dai kuma tun kafin suzo asibitin cikin ya zube allurar bacci akayi mata tare da sanya drip suka fito domin neman jinin da zasu sanya mata.

"Mumy ina fatan ban dad'a rasa shi a karo na biyu ba? "

"Yalla6ai yanzu jini muke buk'ata da za'a sanya mata "
Cewar Dr Aishat kenan, dole Sabeer ya hakura da tambayar yaje aka d'auki jinin shi duk yanda Mumy taso ta hanashi yak'i yarda ya biye mata.


Bayan awanni biyar a lokacin Suhaima ta farfad'o in banda kuka babu abin da take yi haka ma Sabeer wanda yayi kuka ya more yana zaune agefen Suhaima ya kasa rarrashin nata.

Shigowa room d'in akayi Daddy ne da Mumy suka shigo sai Jiddah, ko zama basu yi ba suka fita daga d'akin gaba d'aya har Sabeer da Suhaima tare dasu Dr Aishat mota suka shiga sai gida.

Zama suka yi a parlour duk sunyi shiru kafin Daddy yace
"Muna son sanin mene ne musabbabin zubewar cikin Suhaima tun da kune kuka dubata".

"Yalla6ai mun gano inda matsalar take tablet d'in zubar da ciki akesha shine dalilin zubewar cikin "

Ba Suhaima da Sabeer ba hatta Daddy sai da ya d'ago a matuk'ar razane yana kallon Dr Aishat,

"Tabbas kuwa anyi hakan ko zubewar cikin farko ma shan maganin akayi Dr Faridah ce tace kada na fad'a a bari sai ta sake zubar da wani "

"Okay mun gode kuna iya tafiya "
Cewar Daddy kenan, tashi suka yi suka tafi, yayin da Suhaima, Sabeer, Jiddah da Daddy sun kasa cewa komai musamman Sabeer da Suhaima da suka ji abun wani iri.

Cikin kuka Mumy tace
"Innallilahi wa'inna ilaihi raji'un daman nasan za'a rina talaka bai iya samu wuri ba sai yayi rashin mutunci, daman bason Sabeer d'in take ba tun da har bazata iya had'a zuri'a dashi ba take zubar mishi da ciki "

Girgiza kai tayi tana tafa hannu tace
"Aikuwa tun da haka ne wallahi sai Sabeer ya rabu dake rabuwa ta har abada, yanda Allah shi kadai ya bani inason ganin ya tara min jikoki shine don bakinciki da munafarci irin naki kike zubar da cikin har sau biyu to wallahi baki isa...... "

Bata gama maganar ba Daddy ya d'aga mata hannu dole tayi shiru cikin nutsuwa Daddy yace
"Suhaima ki fad'a mana gaskiya shin wannan abin da ya faru da had'in hannun ki aciki?"

Cikin wani irin kuka na tashin hankali tace
"Wallahi Allah Daddy bansan komai akai ba ban ta6a shan wani magani ba na rantse da Allah "

"Daddy Allah Suhaima bazata sha magani ba don ta zubar da ciki tana son Sabeer bazata iya aikata haka ba sai dai idan sharri akayi mata wallahi a fad'i wanda yake bata abu taci a lokacin sai cikin ya zube anan za'a gano munafikin da ya...... "

Kafin Jiddah ta k'arasa maganar ta Dr Faridah ta kwad'a mata mari tare da cewa
"Daman Jiddah baki da hankali yanzu sai ki bi bayan wata bare bayan kina ganin d'an uwanki take cuta tana zaluntar shi amman kin ban kunya wallahi"

Basu ankara ba sai ganin Sabeer suka yi da sauri ya tashi a sukunye ya nufi bedroom d'in Suhaima ya fara hargitsa d'akin don yasan indai gaskiyar magana ne Suhaima na zubar mishi da ciki zai samu wani k'arin haske akai.

Birkita d'akin yake komai sai da ya hargitsa cikin wardrobe duk ya zubo mata kayanta k'asa har katifa ya d'aga cikin toilet drawer d'in gefen gado duk ya duba bai ga komai ba a lokacin zuciyar shi ta fara aminta da maganar da Jiddah tayi sharri akayiwa Suhaima daman shi bai gama yarda ba.

Har zai fito daga d'akin idanun shi suka sauka kan drower d'in jikin mirror da sauri ya k'arasa wajen yana bud'e su har ya janyo ta k'asan, lokaci d'aya jikin shi yayi wani irin sanyi ga66an jikin shi suka saki wata irin tsanar Suhaima ta fara mamaye cikin zuciyar shi ganin abin da idanun shi suka gane mishi.

Kwaso kwalin maganin yayi gaba d'aya ya fito daga d'akin a fusace kamar wani zaki yana zuwa ya watsawa Suhaima maganin akanta cikin kzakkausar murya yace
"Suhaima! Wannan mene? "

Suhaima wadda sauran k'iris fitsari ya zubo ta ta zubawa maganin ido duk da batayi karatun likita ba jikinta ya bata wannan maganin shine wanda ake magana akan shi.

"Alhamdullilah da Allah ya toni asirin munafuka"
Cewar Mumy kenan tana jijjiga kafa hatta Daddy mamaki ne ya hanashi magana.

"Yaya wallahi Suhaima bazata aikata haka ba "
Cewar Jiddah tana faman kuka kamar zata shid'e, cikin 6acin rai yace
"Jiddah close your mouth or I'll slap U wallahi "

Juyowa yayi wajen Suhaima tare da cewa
"Nagode Suhaima akan duk abin da kika yi min wannan shine sakayyar da zaki min A SANADIN SON KI mene banyi ba nayi fad'a da family na iyayena na bar inda suke na tafi wajen ki nasha wahala kafin ki kar6i soyayya ta ashe duk kallon wawa kike min bansan me nake ba, kin zubar min da cikin jikin ki sau biyu nasan baki sona dama don haka get out from my house i hate you Suhaima i hate you so much nasan bazan yi regretting wannan abin da nayi ba kuma da sannu Allah zai saka min "

Yana gama fad'in ya nufi upstairs zuciyar shi na wani irin zafi, tashi Suhaima tayi tana faman kukan tashin hankali zata fita daga parlour tabar gidan taji muryar Daddy yana cewa
"Suhaima kada ki tafi zansa ayi bincike ban yarda da wannan abun ba"

Girgiza kai take tana cewa
"A'a Daddy kabar na tafi bazan zauna ba "
Tana gama fad'in haka ta fice daga gidan da gudu tana kuka, Jiddah ce tayi kok'arin bin ta amman Mumy ta rik'e ta gam tana faman hararar ta..................




Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[4/11, 11:38 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ


♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*



*PAGE 93-94*






Suhaima gudu take tana kuka har ta samu ta fito daga gidan, sannan ta d'an tsaya tana yiwa gidan kallon k'arshe don tasan bazata ta6a komawa cikin shi ba har abada kuwa.

Fara tafiya tayi tana goge hawaye da hijab d'in jikinta ko takalmi babu a k'afar ta, wani mai taxi taga ya sauke wata mata bata tsaya tambayar shi ta fad'a cikin motar tana kuka kawai, daga matar har mai taxi d'in suka bita da kallo kowanne fuskar shi ta d'auki alhini suna tunanin ko mutuwa akayi mata mai zafi yasanya ta haka dad'in dad'awa da suka ga ko takalmi babu a k'afar nata, canjin matar mai taxi ya bata sannan ya tada motar suka fara tafiya sai da suka hau kan titi sannan yace
"Baiwar Allah ina zan kai ki? "
Dakyar ta iya tsayar da kukan tayiwa mai taxi bayanin inda zai kaita, mai taxi bai zaci wajen da nisa ba sai da ta fad'a mishi sunan kauyen da zai kaita yaso yi mata maganar ba nan zai je ba but ganin irin halin da take ciki ne kawa yayi niyyar taimaka mata.


*****

"Faridah ina jiye miki duk ranar da gaskiya tayi halinta, idan har da sanya hannun ki cikin wannan abun to kiyi gaggawar warwarewa tun kafin kizo kina nadama "

Turo baki tayi kan tace
"Wai ni duk kun tattara laifi akaina ina ruwana da ita da har zanyi yunkurin zubar mata da ciki kawai ta samu sake ne kasan halin talakan mutum bai iya samun waje ba, kuma nagodewa Allah da ya sanya suka rabu da d'ana yaje ya auri wadda zata haifa min 'yan jikoki na, yanzu kawai saki nake so naji yayi mata yanda zasu rabu har abada"

"Allah ya shirya ki Faridah "
Cikin wani irin murmishi tace
"Amin my Dear "

Tashi Daddy yayi zai fita itama ta mik'e tana cewa
"My Dear ka tsaya mu tafi da Son mana kada mu tafi mu barshi shi d'aya "
Cikin jin haushin abin da Sabeer yayi wa Suhaima tunda bai tsaya yayi bincike ba kawai ya yanke hukunci yace
"Ai ba yaro bane shi kuma yasan hanyar gida "
Yana gama fad'in haka ya wuce ya fita daga palon, Jiddah ma d'aukan Islam tayi ta wuce da sauri ta bi bayan Daddy da harara Dr Faridah ta bita tukunna ta wuce upstairs inda Sabeer yake.

Agefen gado ta ganshi yayi ruf da jiki rabin jikin shi a saman bed rabin a k'asa sai wani irin shashshak'a yayi na kuka idanun nashi sunyi ja sun kumbura hatta face nashi tayi ja sai maimaita kalmar
"Why! Why! Suhaima zaki yi min haka na tsane ki i hate U "
. wani sanyin dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar Dr Faridah jin yanda Sabeer yake furta ya tsani Suhaima kamar tayi tsalle da ihun murna haka take ji amman sai ta danne, zama tayi akan gadon ta tare da d'aukan kanshi ta d'ora kan k'afafun ta shafa mishi gashin kanshi take a hankali tana rarrashin shi but still Sabeer eyes nashi basu bar zubar da tears ba.

"My Son kayi hak'uri mu tafi gida kaji bazan iya barin ka anan kai d'aya ba "
"No! Mumy ki tafi ki barni zuciya ta yana daf da tarwatse wa, ina jin zafi acikin zuciya na idan na tuna Suhaima ta cuce ni taci amanata ta yaudare ni tayi min butulci Mumy! "

Dafe saitin zuciyar shi yayi da hannun shi d'aya yana jan wani irin numfashi, wani irin zabura Dr Faridah tayi ganin yanda eyes d'in Sabeer suka kakkafe.

Hannu ta d'ora saman kanta tana kuka tace
"Wayyo Allah nah na shiga uku zan kashe d'ana da kaina! "

******


Sai bayan sallahr ishsha ne suka k'arasa kauyen su Suhaima har k'ofar gida mai taxi ya kaita har zuwa yanzu Suhaima bata bar kukan bak'inciki da takaicin hukuncin da Sabeer ya yanke ba batare da bincike ba aure ko shekara baiyi ba ace har an rabu daman ashe ba sonta yake tsakani da Allah ba yaudare ce yake mata irin ta mazan yanzu nima na tsane ka kamar yanda ka tsane ni Sabeer!.

Maganar da d'an taxi yake mata ne ya dawo da ita daga duniyar tunani fitowa tayi daga motar cikin dushewar murya tace
"Bari na kar6o maka kud'in ka "

Ko taku uku bata yi ba taji ta bige mutum d'agowar da kanta da zatayi suka had'a ido da Yah Aliyu cikin tsakanin mamaki yace

"Suhaima! "

ai Suhaima batasan lokacin da ta fad'a jikin shi ba ta saki wani irin marayan kuka, wani irin tashin hankali da fad'uwar gaba ne ya ziyarci Yah Aliyu tuni fuskar shi ta fara canja yanayi.

"Yay... Yaya ka biyashi kud.... kud'in shi "
Ta fad'a cikin kuka tana nuna mai taxi da hannun ta, zuciyar Yah Aliyu tana tafasa yace
"Malam nawa ne kud'in ka? "
Nan d'an taxi d'in ya fad'a hannu Yah Aliyu ya zura a aljihu ya d'auko kud'in shi ya bashi yana bashi ya rik'o hannun Suhaima suka shiga cikin gida.

Aunty Aliyah da take zaune tana jijjiga Ameer yayi bacci taga shigowar mijin nata batasan lokacin da ta kwantar da Ameer saman katifa ba ta mik'e a razane tana cewa
"Suhaima kece da daren nan? "
Jikinta Suhaima ta fad'a tare da fashewa da kuka da k'arfi, ruwa Yah Aliyu ya d'ebo mai sanyi a randa zama yayi tare da zaunar da Suhaima akusa da shi ya bata ruwan da hannun shi, bayan ya gama bata ne sannan cikin nutsuwa yace
"Suhaima fad'a min me yafaru kada ki 6oye min komai don baki da kamata a duniyar nan "

Kallon Yah Aliyu tayi kafin ta sauke ajiyar zuciya ta fara zayyana mishi abubuwan da suke faruwa gaba d'aya bata 6oye musu komai ba tana gama fad'in ta sake fashewa da kuka, Aunty Aliyah wadda take kukan tausayin Suhaima ta janyo ta jikin ta tana rarrashin ta.

Yah Aliyu kuwa wani zafi zuciyar yake yi sai wani huci mai zafi da yake fitarwa zagaye tsakar gidan yake hannun shi goye a bayan shi ya ma rasa abin cewa can ya bud'e baki cikin kakkausar murya yace

"Yau ni Aliyu za'a wulak'anta aci mana mutunci don kawai muna talaka, abin da Sabeer zai aikata mana kenan lallai yau koda bai sake ki ba ni ni Aliyu na sanya almakashi na datse igiyoyin da suke tsakanin ku dashi bake bashi har abadaaaa..........





Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[4/12, 10:39 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ


♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*



*PAGE 95-96*





Yana sauke wani irin huci Yah Aliyu ya k'arasa maganar ga wasu hawaye na bak'inciki da suke zubo mishi idan ya tuna yanda aka zubar wa k'anwar shi ciki har sau biyu, an cuci k'anwar shi cuta ba k'arama idan ya tuna idan kuma shine iya k'wanta aduniya fa, idan ya kasance iyakar 'ya'yan da zata haifa ne a iya duniya fah shikenan angama cutar k'anwar shi ba ita ba ganin 'ya'yan da zata haifa wasu can daban sun zubar mata dashi.

"Inaaa! Bazai yiwu ba dole sai na d'auki fansar abin da akayi wa k'anwata koda zai kasance abu na k'arshe a rayuwashi, an cuce mu don abin da akayi wa Suhaima tamkar shi aka yiwa.

Komawa yayi ya zauna tare da janyo Suhaima kusa dashi ya sanya hannun shi ya d'ago kanta suna kallon juna yace
"Suhaima baki da kowa sama dani don haka wannan abin da akayi miki sai na d'auki fansar shi koda duk abin da na mallaka a duniyar nan zai k'are "

Girgiza kanta Suhaima kawai take cikin kuka take cewa
"Nooo! Yaya kada ka kula su na bar mutum da Allah duk wanda yayi min wannan

Please Login or Register in order to submit comment