Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zata wuce kenan.

"Mumy! "
Taji saukar muryar d'an nata mafi soyuwa cikin zuciyar ta, runtse ido tayi wasu hawaye na kok'arin zubo mata amman sai ta had'iye su ta wuce toilet da sauri ta ajiye bowl d'in da towel kafin ta fito tabar d'akin da sauri.

"Kada kayi kuka Son zan rarrashi Mumyn ka"
"Daddy Mumy tana fushi da ni "
Cikin rarrashi Daddy yace "Mumyn ka bazata iya fushi da d'anta ba abin da yake sone baiyi mata shi yasanya ta 6acin rai but nasan zata huce bazata iya jure fushi da yaron ta ba kamar yanda nima na kasa jurewa"
Gid'a kai Sabeer yayi kawai, suna cikin haka Alhj Ahmad d'an fillo ya shigo d'akin sannu yake yiwa Sabeer amman bai kalli inda yake ba da yaga yana kok'arin ta6a shi ma sai ya tashi yana d'ingishi ya bud'e kofar baya ya fita ko kallon shi bai yi ba.

Da kallo duk suka bishi na mamaki kafin Alhj Ahmad ya zauna yana goge gumi na tashin hankali yace
"Hussein anya yarinyar nan ba asiri tayiwa Sabeer ba? "
D'an murmishi Daddy yayi kafin yace
"Abba ba wani asiri asali ma yarinyar bata son shi "
D'an zaro ido Alhj Ahmad yayi kafin yace
"Batason shi kamar yaya? Kana nufin Sabeer ne kawai yake son ta? "
"Ehh Abba so yake yaje neman soyayyar ta "
Cire hular kanshi d'an fillo yayi yana firfita da ita don wani gumi da ya keto mishi na tashin hankali, daman ashe Sabeer son maso wani yake wanda ake ce mishi k'oshin wahala innallahi, tuni jikin Alhj Ahmad yayi mugun sanyi da yaji jarrabar da Allah ya d'orawa jikan shi na son maso wani gashi yarinyar 'yar k'auye shi yanzu mene mafita?.

Shiru suka yi gaba d'aya babu mai yin magana a tsakanin su har wurin 10:30 suna zaune jigum jigum suna jiran shigowar Sabeer amman bai shigo ba haka suka tashi suka bar bedroom d'in kowanne zuciyar shi cike da tunani kala kala.

Wasa wasa yanzu gaba d'aya Sabeer baya kula Alhj Ahmad d'an fillo da Hajjah, Daddy kawai yake kulawa kawai Mumy kuma bata shiga harkar shi sai dai zata zo ta gasa mishi k'afa sau biyu ta sanya mishi magani, tsakanin ita da Sabeer bansan wanda yafi wani ramewa ba a tsakanin su, ta 6angaren Daddy kuma yana ta kok'arin shawo kan Mumy ta amince don samin farincikin tilon d'an su amma tak'i yarda da maganar tashi ko baccin kirki bata iyayi saboda tunanin tilon d'anta ta rasa samun mafita don mafitar ta d'aya ta bari Sabeer auren Suhaima kuma sam abin da bazai ta6a yiwu ba.

Alhj Ahmad d'an fillo kuwa ya rasa samun sukuni don Sabeer bayayi mishi koda shi yayi mishi magana bazai kalli inda yake ba balle ya amsa mishi k'arshe ma sai Sabeer ya bar mishi wurin, duk yanda ya so Sabeer ya saurare shi yak'i bashi had'in kai da wani cikin jikokin shi da tuni yayi watsi da al'amarin amman Sabeer kuwa na daban ne son shi cikin zuciyar shi mara adadi ne, tun kafin a haifi Sabeer yake nuna wa cikin so har aka haife shi a kullum son Sabeer k'ara yawa yake cikin zuciyar shi.

Duk yabi ya rame ya fad'a ga mafarkin da yake da Sabeer da wata kyakkyawar yarinya duk mafarkin da zai yi da wannan yarinyar yake ganin su da Sabeer, gashi Sabeer yana kuka yana rok'an ta da ta so shi amman sai tayi tafiyar ta, gaba d'aya d'an fillo ya hankalin shi a matuk'ar tase yake don ganin irin mafarkin da yake.

A haka aka d'ibi sati biyu cikin wannan yanayin alokacin Sabeer k'afar shi ta warke sosai duk babu kumburin ya koma tafiyar shi normal babu d'ingishi, har zuwa lokacin Mumy bata yi magana ba Daddy kullum cikin lalla6a ta yake.

"Daddy tun da na warke kayi min izinin tafiya wajen Suhaima "
Sabeer ya fad'i hakan cikin marairaice fuska, d'an shiru Daddy yayi yana tunani don rasa ta inda zai fahimtar da Sabeer cewa Mumyn shi bata amince da hakan ba da kuma Abbah da Hajjah, yana shirin bud'e baki yayi magana yaji ance
"Hussein basai kayi tunani ba ni na bawa Sabeer izinin tafiya wajen masoyiyar shi neman soyayyar ta na amince Sabeer ya tafi domin samun farincikin shi "

Da sauri suka jiyo suna kallon D'an fillo a tsaye yana murmishi daga ni na yak'e ne ba'a son ranshi ya fad'i hakan ba, ba har cikin zuciyar shi ya furta hakan ba amman Sabeer da Daddy saboda farinciki sam basu d'ago shi ba, da gudu Sabeer yaje ya rungume D'an fillo yana dariyar farinciki wata ajiyar zuciya ta kwanciyar hankali D'an fillo ya sauke jin Sabeer rungume dashi yaushe rabon da Sabeer ya rungume shi, yaushe rabon da yaga dariyar shi haka duk so ya canja shi tamkar ba Sabeer d'in da ya sani ba.



"Thank U so much kakanah! "
Ya k'arasa fad'i yana bashi peck a kumatun shi, dad'i ya ishi D'an fillo jin Sabeer d'in shi cikin farinciki kamo hannun shi yayi ya rik'e tare da cewa
"Ka yafe min marin da nayi maka Sabeer nayi regretting akan haka"
Girgiza kai Sabeer yayi yana murmushi yace
"Kada ka damu Abbah ya wuce "
Sake rungume Sabeer yayi yana bubbuga bayan shi.
"Ni an mance da ni da.... "
Daddy ya k'arasa maganar da hannun shi na alamar shima ayi hugging nashi, da sauri d'an fillo ya janyo shi ya had'asu ya rungume su acikin jikin shi.

Sun jima a haka kafin su rabu da juna nan Sabeer ya mak'ale jikin D'an fillo yana zuba mishi shagwa6a son ranshi shi kuma yana lalla6a shi, dariyar yak'e kawai D'an fillo yake yi, sun jima suna hira kafin kowa ya tafi ya kwanta zuciyar Sabeer fal farinciki a wannan daren yayi baccin da ya jima bai yi ba.

Washe gari da safe ya tashi saboda d'oki da kanshi yake had'a kayan shi cikin trolley bags nashi saboda zumud'i saboda a yau yake son tafiya zuwa k'auyen su Suhaima ya fara fayyace mata abin da yake damun shi.

Bayan ya gama had'a kayan ne ya d'auki phone nashi ya kirawo Jiddah maganar mintuna biyar yayi da ita ya kashe wayar, saboda tsananin mamaki Jiddah kusan sumen zaune tayi na jin inda Sabeer yake neman address a wurin ta na gidan su Suhaima, tura mishi tayi ta message saboda ita ma sauri take a yau jirgin su zai tashi zuwa yawan honeymoon wanda gama wayar ta da Suhaima kenan Sabeer ya kirawo ta kanta ya d'aure sosai amman ta bar komai sai sun dawo tukunna.

Zaune Sabeer yake durk'ushe gaban Mumy cikin bedroom nata, gwiwar shi a k'asa ya sanya hannun shi saman k'afar ta idanun shi hawaye ne yake fitar wa, gama shiryawar shi kenan zai tafi ya shigo bedroom d'in ta cikin rawar murya ta kuka yace

"Mumy nah! Ki yafe min kisa min albarka tare da yi min addu'ar samun nasara tafiya da fushin ki ba k'aramin barazana zai zame min ba"

Juyar da kanta gefe tana share hawayen fuskar ta, Daddy da shigowar shi kenan shima yabi sahun yanda Sabeer yayi yana cewa
"Sweetheart kiyi hak'uri ba laifin Sabeer ba ne so ne kiyi mishi fatan samun nasara please "
Jiyowa tayi ta kalli Sabeer da Daddy da suke durk'ushe a gaban ta wani kwarjini da cika ido d'a da uban suka yi mata ta rasa me zata ce bakin ta yayi mata nauyi ta kasa bud'e shi tayi magana.

Rarrashin ta da lalla6awa Daddy ya dunga yi wa Mumy sun dad'e a haka kafin Sabeer cikin dashashshiyar murya yace
"Mumy ki taimaka wa rayuwata please kada na mutu"

Kallon shi tayi da sauri gaban ta yana fad'uwa idanun shi sun yi ja suna fitar da hawaye, "please Mumy nah! "
Ya fad'a can k'asan mak'oshi, Mumy ta gaji da jin wannan maganar a wurin Sabeer ta gaji da ganin fitar hawaye a idanun d'anta, hannun ta yana rawa kamar mai jin tsoron ta6a abu ta d'ora hannunta saman gashin kan Sabeer tace
"Ka tafi Sabeer kaje Allah ya kare min kai "

Basu yi tsammanin jin wannan maganar a bakin ta ba don haka sai suka tsaya suna kallonta kamar was7 sokaye, d'an murmishin yak'e tayi hawaye na fita a idanun ta tace
"Ka tafi kada yamma tayi maka ka kula da kanka "

Rungume ta yayi cikin farinciki shi da Daddy suna zuba godiya kafin Daddy ya rik'o hannun ta zuwa compound d'in gidan Sabeer na rik'e da d'ayan hannun Mumyn, gaba d'aya family na D'an fillo sun fito suna sallama da Sabeer, sai da Sabeer ya bisu one by one yana rungume na sallama, sannan daga k'arshe driver ya bud'e mishi kofa ya shiga mota idanun shi akan iyayen shi yana kallon yanda Mumy ta fad'a jikin Daddy tana kuka.

Kauda kanshi yayi suna nan tsaye driver yaja motar suka fita daga gidan, kowa yana mamakin saukowar Alhj Ahmad d'an fillo har ya amince da buk'atar Sabeer wasu sun tausayawa Sabeer don sunsan Sabeer bazai jure zaman k'auye ba yayin da wasu kuma suka cika da farinciki daman a rayuwa dole ka samu mai tausaya maka idan kana cikin damuwa wasu kuma a lokacin zasu yi farinciki da ganin ka cikin haka.....



Hmmm fan's ya kuka ga wannan page d'in?
Anya Mumy da D'an fillo da Hajjah har cikin zuciyar su suka aminta da tafiyar Sabeer kuwa?.
Sai ku biyo ni next chapter don jin yanda zaman shagwa6a66en nan zai kasance cikin karkarar k'auye koya zata kasance?




Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/8, 7:15 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

EXCLUSIVE WRITER'S FORUM


Dedicated to my Sadeey SaNaz


Ina kike Khadijah Neenah cool wannan shafin naki ne kyauta na murnar taya ki kammala littafin ki mai suna WASU MAZAN.. Hak'ik'a kin fad'akar damu ya kuma nishad'antar Allah ya k'ara basirah da k'arfin ido, ina miki fatan Alkhairi! ❣




PAGE 49-50




Bayan tafiyar Sabeer Mumy kasa danne kukan ta tayi da gudu ta wuce side d'in su bedroom ta shige ta hau kuka sosai na tausayin halin da Sabeer zai shiga da kuma kukan takaici da bak'in ciki akan wata banza 'yar k'auye d'anta kamar Sabeer zai tafi neman soyayyar ta.

Da haka Daddy ya shigo ya fara rarrashin ta bayan ya janyo ta jikin shi, dakyar ta shiru tana sauke ajiyar zuciya, sai da Daddy yaga tayi bacci sannan ya kwantar da ita ya fita duk jinshi yake babu dad'i na tafiyar Sabeer.

Daddy yana fita daga bedroom d'in Mumy ta bud'e idanunta tare da sakkowa daga saman bed dama tayi hakan ne don Daddy ya fita ya bata waje, tana son ta samu nutsuwar da zatayi tunani na d'aukan mataki akan shegiyar yarinyar nan da zuri'ar ta don sam bazata ta6a amince wa Sabeer ya auro mata d'iyar talakawa ba, talakawan ma na k'auye wanda basusan komai ba sai nemo da kiwo inaaa abin da bazai ta6a yiwuwa ba, daman ta barshi ne don kafin ace za'a yi auren tasamu mafita haka ta tsunduma a tunani sosai na samun mafita kuma bazata yi abin da Sabeer da Daddyn shi zasu zargeta da hana wannan auren ba.


***** ***** *****


Suna tafiya a mota Sabeer kuma ya kwanta tare da tukunkune jikin shi waje d'aya tamkar mai jin bacci, hawaye ne suke fita a idon shi yana kewar iyayen shi yana kuma tunanin yanda zaman shi anan zai kasance shin Suhaima zata kar6e shi matsayin masoyin ta sannan ya 'yan uwanta zasu kar6e shi matsayin mai son 'yarsu, wannan tunanin shi yake dad'a dagula lissafin Sabeer kada su kore shi su hanashi Suhaima tsoron shi d'aya kada su hanashi neman soyayyar Suhaima.

Sai da driver yazo wurin da suka ta6a had'uwa da Suhaima anan Sabeer ya bashi umarnin tsayawa, bayan yayi parking ne sosai Sabeer ya tsaya yana kallon wurin yana tuna wani al'amari da ya ta6a faruwa a wajen har wani murmishi ne ya su6uce mishi.

Nan Sabeer ya yiwa driver magana akan ya fito mishi da kayan shi, bayan driver ya fito dashi ne nan Sabeer yace mishi ya koma gida, yana nan tsaye driver yaja motar ya tafi zuciyar shi fal tausayin Sabeer don yasan bazai ta6a iya zaman wannan k'auyen mai kama da daji ba nan cikin zuciyar shi yayi mishi addu'ar fatan dacewa.

Sabeer ya d'an jima a wajen yana dad'a nazarin wajen gaban shi na fad'uwa saboda ganin garin ya fara d'an duhu don dab ake da akirawo sallahr mangarib.

Wani d'an saurayi ne yazo zai shige Sabeer ya rasa ta yaya zai mishi magana da yaga yana kok'arin wuce shi ne yasa shi yin kar6in hali yace

"Assalamu Alaikum"
D'an jiyowa yayi ya kalli Sabeer kafin ya tsaya nesa kad'an dashi yace
"Waalaikumussalam "

"Ammm inason zan yi mata tambaya please "
Saurayin cikin mamaki ya ke kallon shi don bai zaci Sabeer yana jin hausa ba ya d'auka bature ne ko balarabe yazo yin wani abin a k'auyen nasu.

"Allah yasa na sani"
D'an sauke numfashi Sabeer yayi tare da cewa
"Don Allah ko kasan gidan wani uhm... "
Ya d'an yi shiru kad'an yana tuna sunan Yayan Suhaima da Jiddah ta sanar dashi d'an murmishi ya saki tare da ya tuna sunan yace

"Yawwa sunan shi Aliyu yana da k'anwa Suhaima kuma manomi ne "

D'an murmishi saurayin yayi kafin yace
"Na gane shi nasan gidan "

Wani sanyin dad'i ne ya kwararanya cikin zuciyar Sabeer cikin murna yace
"Yawwa don Allah taimaka min ka kaini gidan "
"To shikenan "

Nan saurayin yayi gaba Sabeer kuwa sai ya tsaya kamar an dasa shi ta ina zai iya d'aukar trolley d'in nan, ganin Sabeer ya tsaya yasa saurayin dawowa yace
"Lafiya? ".

"Ko zaka iya taimaka min da trolley d'in bazan iya d'auka ba please "

Saurayin bai yi mamaki ba don kallo d'aya zaka yiwa Sabeer kasan cewa d'an hutu ne, d'an murmishi yayi tare da kinkimar jakar, nan Sabeer ya rataya jakar laptop d'in shi suka tafi, tun ana tafiya ba'ayi nisa ba Sabeer ya fara gajiya ga wani uban tsoro da ya mamaye zuciyat shi ganin babu gidaje sosai, amman suna dad'a gaba sai ya cika da mamaki da yaga sun shiga wata unguwa duk gidaje sosai ba kamar inda suka baro ba.

A k'ofar wani gida yaga sun tsaya saurayin yace
"Ga gidan nan "
"Yawwa sannu thank U so much "
Nan ya shigar mishi da trolley d'in cikin zaure ya ajiye, laluba aljihun shi Sabeer yayi na jeans ya zaro 1k ya mik'a mishi tare da cewa
"Gashi abokina na gode sosai but ka kar6a don Allah "

Hannu biyu saurayin yasa ya kar6a tare da zuba godiya har zai wuce da sauri Sabeer yace
"Hmm jimana abokina ya sunan ka? "

D'an murmishi yayi tare da cewa
"Sunana Ashiru kuma ga gidan mu nan "
Ya k'arasa fad'i yana nunawa Sabeer gidan su wanda gida d'aya ne tsakanin su da na Suhaima.
"Ni kuma Sabeer "
"Sunan ka mai dad'i irin na 'yan birni "
Dariya ya bawa Sabeer wanda ya sanya sai da ya d'an yi murmishin dariya saboda ya kula zai yi abin dariya, daganan ya wuce ya tafi Sabeer kuwa babu neman isowa ya kutsa kai cikin gidan tamkar irin gidan nan nasu.



Suhaima tana zaune kan wani dutse tana alwala ta sallahr mangarib, ga Aunty Aliya kuma tana kok'arin sauke miyar abincin dare kenan daga saman murhu suka yi wata sanyayyar murya tayi musu sallama.

Amsawa Aunty Aliya tayi yayin da Suhaima ta tsinci kanta da bugawar zuciya na lokaci d'aya, kafin su ankare sunga mutum a filin tsakar gida a tsorace Aunty Aliya ta kalle shi yayin da Suhaima ta kusan zubewa a k'asa saboda tsabar kid'ima da tsorata na wanda ta gani a k'auyen su kuma cikin gidan su.

"Malam lafiya wa kake nema "
D'an murmishi yayi tare da d'auke idanun shi daga kallon Suhaima ya dawo dasu kan Aunty Aliya yace
"Nazo neman Suhaima ne sunana Sabeer "

"Suhaima kuma? "
Aunty Aliya ta furta hakan tana kallon Sabeer kafin ta jiyo da kanta zuwa kallon Suhaima wadda jikin ta yake rawa na tsorata.

"Eh Suhaima nake nazo nema, idan babu damuwa zanyi sallah sai nayi miki bayanin ko ni waye? "

Aunty Aliya sai tsoron nata ya ragu don kallon da tayi wa Suhaima ta karance ta tsaf alamar tasan shi amman tayi mamaki sosai na yanda Suhaima ta iya 6oye mata abu, don haka sai tace
"Toh ai babu damuwa "
Nan ta je inda suke ajiye botocin gidan ta d'auko babbar butar Yaya Aliyu da bata rabo da ruwa aciki ta ajiyewa Sabeer a gaban shi, d'an murmishi yayi tare da cewa
"Na gode "
Murmishin yak'e Aunty Aliya tayi, tana nan tsaye ya ajiye jakar laptop d'in shi dake rataye a kafad'ar shi saman wani dutse sannan ya tsugunna yayi alwala, abin sallah Aunty Aliya ta bashi sabida masallacin da nisa daga gidan ba lalle ya gane ba yana bak'o, kar6a yayi ya shimfid'a ya fara sallahr har zuwa yanzu Suhaima na tsaye tamkar wadda aka dasa a wajen ko kwakkwaran motsi bata yi, ganin haka ya sanya Aunty Aliya janyo hannun Suhaima suka wuce d'akin ta.

Cikin tsoro tace
"Suhaima wane ne wannan? "

Suhaima itama a tsorace tace
"Na shiga uku Aunty yanzu sai da Sabeer ya biyo ni "

"Ki fad'a min wane shi kafin Yayan ku ya dawo daga masallaci "

Murya na rawa ta bud'e baki zata yi magana suka ji sallamar Yaya Aliyu daga tsakar gida, kallon kallo aka tsaya yi tsakanin Aunty Aliya da Suhaima ko motsin kirki sun kasa......



Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/10, 5:16 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




PAGE 51-52




Murya na rawa ta bud'e baki zata yiwa Aunty Aliya bayani suka ji sallamar Yaya Aliyu daga tsakar gidan, kallon kallo aka tsaya yi tsakanin Aunty Aliya da Suhaima ko motsin kirki sun kasa gaban su sai dukan uku uku yake na tsoron yanda Aliyu zai saurare su na shigowar wani kai tsaye gidan.


A haka ma a tsakar gida kallon kallo aka tsaya yi da Aliyu da Sabeer wanda idar da sallahr mangarib d'in shi kenan, da fara'a Aliyu ya shigo gidan anman had'a idon da suka yi da Sabeer ya sanya fara'ar fuskar shi ta d'auke lokaci daya ya 6ata fuska gefe d'aya na cikin zuciyar shi yana mamakin wannan wane ya shigo mishi gida haka kai tsaye haka har yana sallah.


Sabeer ganin Aliyu ya d'aure fuska sosai yasa shi tsorata gaban shi ya fad'i kada ya kore shi daga gidan, murya na rawa yace

"Sannun ka ina yini? "
Cewar Sabeer kanshi a k'asa don ya fara tsarguwa da wannan kallon da Aliyu yake mishi, tamkar bayason amsawa yace
"Lafiya k'alau "

D'an matsawa yayi kusa da k'ofar d'akin Aliyah yana mamakin da har yanzu babu wanda ya fito ya amsa mishi sallama tsakanin ta da Suhaima tunda ba haka suke mishi ba matuk'ar suna gidan kuwa.

"Aliyah, Suhaima kuna ina? "

Muk'ut Suhaima da Aliyah suka had'iye yawu lokaci d'aya, idanun ta saman fuskar Suhaima tace
"Gamu a d'aki mun yi sallah ne "
Alhalin babu wanda yayi yunk'urin yin sallahr har gwara Suhaima tayi alwala.

"Ku fito ina son ganin ku "
"Toh gamu nan "
Fad'in Aliyah cikin dakiya don ita tafi ma Suhaima jarumtar amsawa, sun d'an d'auki mintuna biyu sannan suka yi shahadar fitowa gaba d'ayan su.


Yaya Aliyu yana zaune saman tabarma kusa da k'ofar d'akin Aliyah, yayi da Sabeer yake zaune saman abin sallah a tak'ure hankalin shi a matuk'ar tashe saboda uban cizon da sauro yake galla mishi a hannu da k'afar shi ga kukan shi da ya dameshi cikin kunnuwan shi ga zafi don sai had'a gumi yake.

Fitowa suka yi tare da zama kusa da Yaya Aliyu sai da ya kalle su na 'yan mintuna kafin yace
"Na shigo gida sai na tarar da wani abin mamaki dana gani, shin wane? Kuma me ya kawo shi cikin gidana ba tare da yarda ta ba? "

K'uwwww cikin Suhaima da Aliyah ya fitar da wannan sautin ganin yanda Aliyu ya d'aure fuska tamkar bai ta6a dariya, basu ta6a ganin shi cikin wannan had'e fuskar ba sai yau don haka suka tsorata.

"Ku nake saurare ku yi min bayani "
Fad'in Aliyu kenan ganin sunyi shiru kansu a sunkuye.

Aliyah ce tayi k'arfin halin cewa "Uhm da....daman yanzu mu... muke son kiraka a... a waya mu fad'a maka, ya dai... dai ce sunan shi... shi Sabeer "

Kallon baku da hankali yayi musu da sauri Aliyah ta sunkuyar da kanta ganin irin kallon da Aliyu yake jefan ta dashi, idan ba wannan kallon yayi musu me zaiyi taya ya kawai bakasan mutum ba ka barshi ya shigo cikin gidan ka kai tsaye namiji ma ba mace ba a yanda zamanin yanzu abubuwa suka ta6ar6are.

Bai k'ara bi takansu ba ya juya wajen Sabeer da lokacin hankalin shi ya gama tashi saboda cizon sauro tamkar zai fashe da kuka ko yayi ta ihu ko yaji dad'i, Suhaima tana ankare dashi cikin zuciyar ta tace "Allah ya k'ara da uban wani iyayi ne ya kawo ka inda bazaka iya rayuwa mai dad'i ba kamar yanda ka saba rayuwar jin dad'i da hutu maganin iyayin mutum kad'an ma ka gani" duk da a d'an tsorace take sai da ta saki murmishi mugunta sauran kad'an dariya ta kubce mata ta mugunta.


"Malam Sabeer muna son sanin kai waye? Me ya kawo ka kuma nan gidan? "

Sabeer d'an had'iyar yawu yayi kafin ya motso kusa da Yaya Aliyu cikin sanyin muryar shi yace
"Kamar yanda ka sani Sunana Sabeer Hussein d'an fillo Yaya ga k'awar Suhaima wato Jiddah "

Nan take Yaya Aliyu yayi murmishi da jin Yayan Jiddah ne ko ba komai d'an uwan Jiddah bai cancanci wulak'anci a wajen su ba.

"Masha Allah ashe d'an uwan Jiddah ne kai yarinya mai hankali da nutsuwa, toh Malam Sabeer muna son sanin lafiya kazo inda muke?".


Sai da yayi shi na d'an minutes kafin ya bud'e baki yace
"So da k'aunar Suhaima ne yasa ni zuwa nan domin na sami soyayyar ta, na kasance tun lokacin da na ganta naji inason ta so na tsakani da Allah kuma ba yaudarar ta zanyi ba wallahi auren ta zanyi "

"Ikon Allah! "
Fad'in Aliyu kenan, Suhaima da Aunty Aliya kuma sun baza kunnuwan su suna sauraren abin da yake fad'a.

"Shine idan baza ku damuwa ba ina son ku koma can birni zan baku gida, mota da kuma aikin yi sannan zan...... "

Kasa k'arasa maganar shi yayi ta mak'ale a fatar bakin shi ganin irin yanda fuskar Aliyu ta rikid'a ta koma wata iri na yanayin fusata ga wani d'an iskan kallo da yake jifan Sabeer jin yazo mishi da wani banzan magana.

Sabeer kuwa kasa magana yayi yana kallon Aliyu yanda yake mishi wani irin kallo alhalin a girmi bazai girme shi sai ma watak'il ya bashi shekara biyu.

"Gaskiya tun da ka biyo ta wannan hanyar ba lallai Suhaima taso ka koda ta so ka ni kuma bazan yarda ta aure ka, mu ba makwad'aita bane duk da mu talakawa ne muna rayuwa a karkara muna jin dad'i yanda muke rayuwar mu bama hangen wani abin don haka ka sake tunani Sabeer baza mu ta6a yarda da wannan maganar taka ba "

Nan Aliyu ya cigaba da masifa don ya d'auka Sabeer ya raina musu arzik'in su ne, baisan Sabeer ko kad'an

Please Login or Register in order to submit comment