Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba haka bane cikin zuciyar shi da yasan yayi wannan tunanin amman sai ya watsar daga baya tun da iyayen shi sun amince da auren Suhaima a haka amman sai Daddy ya sanya shi furta hakan wanda yayi dana sanin fad'in haka.

Ana cikin haka sai ga Babaa Lantana nan da Baba Adamu sun shigo domin kwana biyu basu lek'o ganin jikin Aliyah ba, suka tarar da wannan hatsaniyar har Aliyu yana cewa Sabeer ya kwashi kayanshi ya koma inda ya fito, sosai hankalin Sabeer ya tashi tuni hawaye sun fara zuba a idanun shi.

Aunty Aliya ya bata tausayi sosai Suhaima kuwa ko a jikin ta, nan Babaa Lantana da Baba Adamu suka shiga zancen dakyar Aliyu ya hak'ura sai lokacin kuma yaga hawayen da Sabeer yake fitarwa sai kuma jikin shi yayi sosai, bai kamata ya wulak'anta jinin Jiddah ba yanda taso su ba tare da kyamatar su ba. Suhaima kuwa dad'i ya kamata tasan yanzu Yaya Aliyu zai kore shi addu'a take cikin zuciyar ta Allah yasa kada Yaya Aliyu ya amince da dad'in bakinshi.

"Kayi hak'uri idan ka bani dama zan zauna a gidan ka na nemi soyayyar Suhaima "
Fad'in Sabeer yana goge hawayen fuskar shi.

Nan jikin Aliyu ya Kara sanyi sosai mene laifin Sabeer anan Allah ne ya jarrabe shi da son Suhaima bai kamata yayi mishi haka ba kodan 'yar uwar shi Jiddah wadda ko d'azu da safe sai da sukayi waya da ita gaba d'ayan su don haka cikin sanyin murya yace

"Nima kayi hak'uri da abin da nayi maka kuma na amince da hakan Allah ya taimaka"

Wani sanyi dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar Sabeer wanda har sai da ya rungume Aliyu yana godiya, yayin da Aliyu, Aliyah, Babaa Lantana da Baba Adamu suka yi dariyar farinciki, Suhaima kuwa wani bak'in ciki ne ya turnik'e ta sai kawai taja tsaki ta wuce d'akin ta da sauri duk suka bi ta da kallon mamaki.


"To kai gaka d'an birni anya zaka iya cin abincin mu ka kwanta a irin d'akunan mu kuwa "
Cewar Babaa Lantana, dariya Sabeer yayi kafin yace.
"Me zai hana kuwa Babaa "
Nan aka d'an ta6a hira cikin farinciki wanda a lokacin Sabeer ya shiga ransu saboda sauk'in kanshi.

Tashi Babaa Lantana da Baba Adamu suka yi da zummar tafiya nan Aliyu ya dage sai sun ci abinci aikuwa k'in yarda suka yi tare da tafiya.

Bayan sun tafi Aliyu ya umarci Aliyah da ta kawo musu abinci, babu dad'ewa ta shirya musu sannan ta wuce d'aki don yin sallah.

Bud'e kwanon Aliyu yayi tuwan biskin gero ne da miyar taushe tasha gyad'a da manshanu sai tashin k'amshi yake, nan Aliyu yayiwa Sabeer Bismillah ba don Sabeer ko yasan mene ba ya tsunduma hannun shi ya fara ci dakyar ya iya had'iye lomar da yayi saboda rashin sabo da cin irin wannan abincin .

Kasa cigaba da ci yayi fahimtar hakan da Aliyu yayi yasa shi girgiza kai yana tausayin Sabeer yasan wahala ce sai yasha don birni da karkara akwai banbanci musamman a irin gidajen da Sabeer ya taso.

Ruwan Sabeer ya runtse ido yasa ba don yayi mishi irin yanda yake so ba gashi cikin shi sai k'arar yunwa yake don rabon shi da abinci tun breakfast na safe saboda zumud'i ma bai ci abinci sosai ba.

"Zaka iya shan fura? "
Cewar Aliyu yana kallon shi d'an sosa k'eya yayi kafin yace
"Eh zan sha kasan mu ma family's d'in mu Fulani ne muna sha amman ni ba sosai ba "

Gid'a kai Aliyu yayi yana cewa "yanzu don duhu yayi zuwa gobe sai mu fita kaga yanda garin namu yake "

Tashi yayi ya shiga d'aki babu jimawa ya fito shi da Aliyah nan ta wuce kitchen tana kok'arin damawa Sabeer fura, babu dad'e wa ta dama shi ta kawo mishi a cikin k'ok'o da ludayi had'e da kofin roba ta ajiye mishi.

"Sannu Aunty Aliyah na had'a ki da aiki "
Murmushi tayi tare da cewa "laaa ba komai wallahi dafatan zaka iya shan wannan furar "

"Zan iya mana "
Murmishi tayi ta wuce d'aki, nan Sabeer ya janyo furar ya fara sha da ludayin gard'in gero da kindirmon nono ya ratsa shi sosai furar tayi mishi dad'i.

"Da ka zuba a kofi koh"
Yana lumshe ido yace
"Barni kawai Yaya nasha a haka don na saba "
Dariya kawai Aliyu yayi, bayan sun gama ne Aliyu ya shiga wani d'aki na kusa da zaure ya fara gyarawa nan Aunty Aliya ta fito itama ta bishi d'akin tana tayashi aikin, Sabeer najin dariyar su da magana suna yi k'asa k'asa lumshe idanun shi yayi sun birge shi sosai yana fatan su yi irin wannan zaman da Suhaima idan ya shawo kanta ta kar6i soyayyar shi.

Tsaf suka gyara d'akin bayan sun share sun bud'e window na d'akin nan suka sanya labule na k'ofa dana window kafin su fito kuma su shiga d'akin Aliyah sai ga Aliyu ya fito da k'aramar katifa ta k'aramin gado ya sanya d'akin Aliyah kuma ta shimfid'a mishi zanin gado a jikin katifar ta kunna turaren wata na tsinke sai d'akin ya fito fes dashi, Aliyu ya d'auki jakar Sabeer ya shigar mishi da ita kafin kuma su d'unguma shi da Sabeer su tafi masallaci don yin sallahr ishsha....


Aishat A Muh'd 💃🏻
[2/18, 5:01 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




PAGE 53-54




Bud'e labulen d'akin Aliyah tayi tare da shigowa zama tayi kusa da Suhaim wadda ta kwanta rub da ciki a saman gadon ta, dafa bayan ta tayi kafin tace
"Suhaima tashi mu yi magana "
Tashi Suhaima tayi zaune tana goge hawayen fuskar ta da hannunta, kallon mamaki Aliyah take mata kafin tace
"Me yasa kika yi mishi haka Suhaima?, haba Suhaima bansan ki da halayyar wulak'anta mutane ba, ki tuna saboda sanadin son ki fah ya bar gatan shi da komai nashi na jin dad'i ya dawo nan k'auye wanda bai ta6a rayuwa acikin irin wannan yankin ba ya aminta zai jure kowacce wahala indai zai same ki, koda da iya abincin mu ma kafin ya saba aiki ne zai hak'ura ya jure duk don A SANADIN SON KI, haba Suhaima ki tausaya mishi kada ki bashi wahala don na tabbatar Sabeer son ki yake tsakani da Allah ba yaudarar ki yake, idan yaudara ce ma bazai zo har nan ba don haka kiyi tunanin kafin ki yanke hukunci tukunna "

Zum6ura baki Suhaima tayi tare da cewa
"Ni gaskiya Aunty bana son Sabeer hasalima kinsan na tsani auren mai kud'i saboda gujewa wulak'anci, musamman gidan su Sabeer tunda na baki labarin abin da suka yi min"

D'an shiru Aliyah tayi tana d'an tunani kafin tace
"Kina da gaskiya don wannan amman ni ina mai baki shawara kiyi tunani sosai kafin ki yanke hukunci,tare da addu'ar neman za6in Allah kada ki yanke hukunci da gaggawa"

Gid'a kai Suhaima tayi kawai tare da cewa
"Ni bama zan so shi ba"
"Hmmm na dai ji ki Suhaima kawai amman wannan zakad'ed'en sauryin ne kece bakya sonshi kawai ra'ayin ki ne ya hana ki tsayawa kiyi tunanin kin fad'a son Sabeer daga irin kallon da kike mishi d'azu "

Wayyo aikuwa Suhaima ji take kamar ta rusa kuka jin abin da Aunty Aliyah ta fad'a mata, zum6arar baki tayi tare da kwanciya ta juyawa Aliyah baya, abin ya bata dariya tashi tsaye tayi tare da cewa
"Abincin ki yana kitchen fah kije ki ci kada ya huce "

Tana gama fad'in haka ta fito daga d'akin, nan ta tarar da Sabeer da Aliyu sun dawo bayan tayi musu sannu da dawowa ta yiwa Sabeer sai da safe ta wuce cikin d'aki.

Sun d'an jima suna hira kafin Sabeer ya wuce d'akin da aka sauke shi bayan yayi wa Aliyu sai da safe, yana tafiya yana waiwayar d'akin Suhaima ko Allah zai sanya ya hango ta don kuwa yana son sake sakata cikin idanun shi kafin yayi bacci, Aliyu yana kallon yanda yake kallon d'akin Suhaima nan ya sake tabbatar wa Sabeer yana son Suhaima bana wasa ba, amman mene dalilin k'in amincewar Suhaima na ta kar6i soyayyar Sabeer?.


Sabeer yana shiga d'akin sai yaji shi kamar wanda aka sanya shi a akurki duk da d'akin yana da d'an girma kuwa hakan bai hana sa Sabeer ganin k'ank'antar shi ba irin wanda ya saba kwanciya da shi ba.

Zama yayi gefen katifar yaji ta tik'irk'ir tauri sosai, ga wani hucin zafi da d'akin yake fitarwa alamar dai ba'a yin amfani dashi a rufe yake sai shegen kukan sauro da ya addabi kunnen shi, ga ba wadataccen haske wata 'yar k'aramar fitila ce kawai a rataye jikin k'usa a bango mai irin mai batir d'in nan, zabga tagumi Sabeer yayi yana tunanin yanda ya tsinci kanshi inda bai ta6a tsammanin ganin a haka ba koda a mafarki sai gashi kwatsam lokaci d'aya ya tsinci kanshi aciki ikon Allah kenan.


Zumbur ya mik'e kamar wanda aka tsikara sakamakon wani fitsari da ya matse shi, wayyo Allah nah yanzu ta ina zan fara shiga toilet d'in su, fad'in haka cikin zuciyar Sabeer yana faman matse k'afa, fuskar nan tashi tayi kalar tausayi tamkar wanda zai fashe da kuka kasa jurewa yayi kawai ya tashi da sauri ya fito daga d'akin zuwa tsakar gidan.

Ba kowa a tsakar gidan ga duhu yayi tsit kake ji, yana nan tsaye sai ga Suhaima ta fito a d'aki zata shiga kitchen d'ebo ruwa suka kusan cin karo da Sabeer saboda duhu gashi babu wadataccen hasken farin wata, ba k'aramin tsorata tayi ba ta d'auka ko wani aljanin ne amman lokacin da ta fuskanci Sabeer ne sai kawai ta dake tare da d'aure fuska zata wuce daga sauri yasha gabanta ya tsaya

"Malam lafiya? "
"Uhm ina son ki nuna min toilet "

Da hannu ta nuna mishi ba tare da tayi magana ba ta wuce shi ta d'auko ruwan ta shige d'aki ko kallon inda yake bata sake yi ba, buta ya d'auka ya wuce cikin toilet d'in a d'an tsorace, duk da a duhu ne hakan bai sanya shi gane tsabtar da band'akin yake dashi ba a tsorace yayi abin da zai yi ya fito yana share gumi sai kace wanda yayi tseren gudu duk gumin tsoro ne, da sauri ya wuce d'akin ya rufe kafin ya kwanta saman katifar.


A cikin wannan daren ya zame wa Sabeer daren da bai ta6a tsammanin zai irin shi a wannan duniyar ba saboda yanda zafi da sauro suka hanashi runtsawa, idan zafin ya isheshi sai ya cire kayan jikin shi iya vest da 3quater ne kawai a jikin shi sai buge bugen sauro yake yi ko baccin kirki ya kasa samu ga wani tsananin ciwon kai da ya kamashi saboda gajiya ga rashin bacci.

Washe gari kuwa jikin Sabeer yayi luhu luhu da cizon sauro abin ka da d'an hutu kuma farar fata duk tayi ja tundaga fuskarshi kuwa har jikin shi inda kaya bai rufe ba, idanun shi sun yi ja sosai ga wani zazza6i da ciwon kan ya saukar mishi dashi wajen asubah, har gari ya waye yana kwance a d'aki bai iya fitowa ba sai da Aliyu ya shiga ya ganshi kwance sai rawar sanyi yake ya tukunkune waje d'aya.

Cikin tashin hankali Aliyu ya k'arasa tare da cewa
"Subhanallah! Sabeer baka da lafiya ne? "

D'an murmishin yak'e yayi hawaye na zuba a idanun shi na zafin ciwo yace
"Zazza6i ne yake damuna da ciwon kai ko zaka taimaka min da paracetamol? "

"Sannu Allah ya baka lafiya, bari na d'auko maka amman ka d'aure ka fito sai kayi brush kaci wani abin kafin ka sha maganin "

D'aga kai kawai Sabeer ya iya yi sannan Aliyu ya taimaka mishi suka fito tsakar gidan bayan ya d'auko mishi maclean da brush nashi cikin bag d'in da ya taho da ita.

Aunty Aliya da Suhaima suna zaune a kan tabarma ga breakfast a saman tabarmar da yake tare suke karyawa, Aunty Aliya batasan sand ta mik'e tsaye ba tana zaro ido tare da cewa
"Innallilahi Aliyu mai ya cije haka "

Zaunar da Sabeer yayi saman kujera kafin yace
"Cizon sauro ne wallahi"
"Allah sarki sannu Sabeer Allah ya baka lafiya "

D'an murmishin yak'e yayi mata yana d'aga kanshi alamar amsawa, tun lokacin da Aunty Aliyah ta fara magana Suhaima ta d'ora idanun ta kan Sabeer ta k'ura mishi ido cikin wani yanayi wanda ni kaina na kasa tantancewa, sai da suka had'a ido tukunna ta janye nata idon daga kallon shi ta sunkuyar da kanta.

"Suhaima zo ki samo ruwan d'umi a kitchen yayi brush dashi "

Tashi tayi ta d'auki buta ta d'ebo ruwan d'umin ta kawo maimakon ta sirka shi sai kawai ta dire a gaban shi a haka gaba d'aya jinta take wata iri kamar ba ita ba.

"Wash Allah! "
Taji muryar Sabeer ya fad'a da sauri ta kallo inda yake sai taga yana yarfe hannun shi tare da yatsina fuska ga hannun yayi ja sai lokacin hankalin ta ya dawo jikinta ta mance bata surka ruwan da na sanyi ba.

"Suhaima baki da hankali da zaki kawo mishi ruwan zafi ba tare da kin surka ba"
Fad'in Yaya Aliyu kenan yana hararar ta bayan sun had'a ido.

"Laaa Yaya na mance ne Allah kayi hak'uri "

Da sauri ta mik'e ta d'auki butar ta nufi wajen da suke ajiye ruwa ta surka ta kawo mishi tukunna ta koma ta zauna, duk inda tayi idanun Sabeer suna kanta suna shawagi gaba d'aya ta kasa sakewa.

A haka ya lalla6a yayi brush sannan ya dawo saman tabarmar zama yayi kusa da Suhaima sai ya jingina da bango, sannu Aunty Aliya da Yaya Aliyu suka yi mishi ya amsa muryar shi can k'asa, koko ne mai kauri yasha gasara Aliyu ya mik'a wa Sabeer hannun shi yasa ya kar6a tare da kaiwa baki ya kur6a.

Ba shiri ya furzo dashi waje sai a jikin Suhaima ya 6ata mata jiki don duk ya tsatstsalu a jikin ta har da saman fuskarta, sannu suka k'ara yi mishi yayin da Suhaima ta cukune fuska takaici da 6acin rai fal zuciyar ta har a saman fuskar ta ya nuna.

"Am sorry please "
Ya fad'i cikin sanyin murya fuskar shi d'auke da damuwa dagani kasan ba'a son ranshi yayi mata ba.

"Je ki canja kayan ki wanke fuskar ki"
Fad'in Aliyu kenan ganin irin yanda Suhaima take jifan Sabeer da kallon tsiwa.

A fusace kuwa ta mik'e ta wuce d'akin ta bata dad'e ba ta fito d'aure da zanin wanka tare da hijab a jikinta ruwan wanka ta had'a tare da wucewa toilet.

Duk wannan abin da take Sabeer yana kallon ta ji yake tamkar ya tashi ya rungume ta cikin jikin shi ya rarrashi ta ya nuna mata hakan da ya faru ba'a son ranshi ba ne tsautsayi ne amman babu damar yin haka.


"Me zaka ci a dafa maka tunda baka son kokon? "
Fad'in Aunty Aliya kenan
"Aunty idan na samu ruwan tea ma ya isheni don bana sha'awar cin komai"

"Haba haba ruwan tea me zai maka ka fad'in abin da kake so kawai nan kamar gida ne "

"Kin ga wuce kitchen mu je "
Cewar Aliyu nan suka tashi suka tafi kitchen suna shiga Aliyu ya fita bai dad'e ba ya dawo, cikin mintuna kad'an Aunty Aliya ta dafawa Sabeer tea da yasha kayan kamshi citta da kaninfari sannan aka soya kwai suka kawo mishi.

"Sannu da kok'ari Auntyn mu"
D'an murmishi kawai tayi. A lokacin Suhaima ta fito daga toilet da harara tabi Sabeer kafin ta wuce d'akin ta.

Nan suka karya har suka gama Suhaima bata fito ba nan Aliyu ya tafi siyowa Sabeer paracetamol, yayin da Aunty Aliyah ta wuce d'akin ta.


Sabeer yana kok'arin mik'ewa don wuce wa d'aki ya kwanta Suhaima ta fito kallon shi tayi tare da cewa
"Malam ba lallai ba dole idan baza ka iya zaman nan ba ka tarkata ka koma inda ka fito tunda babu wanda ya gayyace ka anan don bazai yiwu kana had'a mutane da wahala ba "
Tana gama fad'in haka ta fice daga gidan gaba d'aya, nan tsaye take Sabeer yaji wani zazza6in yana neman rufe shi dakyar ya iya kai kanshi d'aki ya zube akan katifa yana wani irin numfashi......



Kuyi hak'uri da ni fan's, kun ji ni kwana 2 shiru abubuwa ne sai a slow but insha Allah zan nayi kok'ari wajen typing.



Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/22, 8:55 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz



Dis page is dedicated to Faridah Bashir (Ummu Safwan) marubuciyar Tambarin sarautah, wannan shafin naki ne kyauta Allah ya raya mana Safwan ya k'ara zumunci Amin ❣



PAGE 55-56





Yana cikin wannan haline Aliyu ya shigo d'akin hannun shi rik'e da paracetamol da ruwa a cup na roba, ganin halin da Sabeer yake ciki ne yasa Aliyu ajiye maganin a gefe ya k'arasa wajen shi da sauri ya rik'o shi tare da cewa
"Sabeer jikin ne? "
Jan wani numfashi yayi wanda ya sanya Aliyu mugun tsorata, a hankali kuma ya sauke numfashin nashi tare da zaunawa saman katifar ya jingina bayan shi da bango kallon Aliyu yayi da idanun shi jawur dasu wanda yake afkin yi mishi sannu fuskarshi da tarin damuwa yace

"Kada ka tashin hankalin ka bani maganin nasha "
"Kodai zamu je asibitin nan na kusa damu su duba ka "
Cewar Aliyu d'an murmishin yak'e yayi kafin yace
"Basai mun je ba naji zazza6in ya sauka yanzu sauran ciwon kai bacci zanyi yanzu "

Sannu Aliyu ya k'ara yi mishi kafin ya fita ya bashi gurin dob ya samu damar yin bacci, tunani kawai Sabeer ya fad'a na yanda Suhaima take wulak'anta shi ina laifin shi anan don kawai yace yana sonta da wannan tunanin bacci mai nauyi ya d'auki Sabeer.


Tunda Sabeer ya farka daga baccin yaji da sauk'i ciwon kan ya ragu, tun daga lokacin Sabeer yake kok'arin koyan cin abincin su yana kuma bin Aliyu gona duk da baya kok'arin yin aiki idan sun je zai zauna yana kallon yanda yake yi ko kuma ya dunga zagaye gonar ko kuma Ashiru wanda ya taimake shi ya kawo shi gidan su Suhaima da yamma wani lokacin zai zo su tattaka zuwa cikin k'auyen, gashi yana kiran iyayen shi su gaisa sannan Aliyu, Aliyah da Babaa Lantana da Baba Adamu suna kok'ari wajen janshi a jiki ya sake dasu tamkar 'yan uwan na jini.


Sai dai ta 6angaren Suhaima ne har yanzu babu wani cigaba don har yanzu tak'i bawa Sabeer fuskar da zai bayyana mata yanda yake sonta.


Aunty Aliya kuma tayi nauyi sosai sai ya kasance duk wani aiki na cikin gidan Suhaima ke yi, yayin da Aliyu wani lokacin yake taimaka mata idan ayyukan sunyi mata yawa.


Suhaima ce zaune saman kujera tana yankan salad tana sauraron freedom redio cikin shirin su na duniyar mu a yau wanda Usman Usman yake gabatar wa tana son shirin sosai batason ya wuce ta, Sabeer ne yayi sallama ya shigo gidan tun kafin ta amsa mishi, haushi ya turnik'e ta don haka sai ta fara gunguni tana cewa
"Mutum sai kawai ya shigowa mutane gida kai tsaye tun kafin a amsa mishi sallamar a bashi izinin shigowa sai kace a gidan arna "

D'an murmishi yayi yana girgiza kai don yaji ta tsaf sai kawai ya tashi ya koma zaure sannan yayi sallama mamaki sosai Suhaima taji da taji ya koma sai da ta d'an jima kafin ta amsa mishi sallamar sannan ya shigo yaja kujera ya zauna lokacin har ta gama yankan salad d'in.

Shiru taji bai yi magana ba sai ta d'an d'ago kad'an ta kalleshi duk ya rame yayi d'an bak'i kad'an kamar ba Sabeer ba, gani tayi zai kallo inda take ya sanya ta kauda idonta da sauri zata tashi kenan taji muryar shi cikin sanyi yace

"Baby taimaka min da abinci I'm very hungry wallahi please "

Yi tayi kamar bata ji shi ba ta wuce kitchen kafin ta fito ta wanke salad d'in duk yana kallon ta don tayi mishi kyau cikin wata gown ta atampha duk da basu kamata ba d'inkin amman sun zauna cif a jikin ji yake kamar ya sanyata cikin jikin shi ya dunga fad'a mata irin son da yake mata ko ya samu sassaucin da yake ciki.

Ya fad'a dogon tunani yana yi yaji kamshin turaren Suhaima a kanshi da sauri ya d'ago kanshi ya kalle ta tana tsaye hannun ta d'auke da plate na abinci tana mik'a mishi, hannun shi ya sanya ya kar6a hadda ta6o mata 'yan yatsun ta saboda tsokana yak'i kar6ar plate d'in aikuwa wani irin shock Suhaima taji ajikinta wanda bata ta6a jin irin shi ba da sauri ta saki plate d'in nan yayi saurin tarewa yana sakin murmishi ganin irin yanayin da ta shiga ajiye abincin yayi yana kallon shi shinkafa da wake ne sai salad da mai da yaji gefe d'aya a saman abincin ga kifi nan an sanya sosai abincin ya bashi sha'awa.

"Uhm sauran ruwa Baby "
Ya fad'i hakan a lokacin da Suhaima take kok'arin shiga d'akin ta ta huta don ta gaji tun safe take aiki, haushi ne yake kamata tun lokacin da Sabeer ya koyi ce mata Baby kuma ko a gaban su Yaya Aliyu haka yake fad'a mata, komawa tayi kitchen ta samu jug k'arami mai murfi ta d'ebo mishi na randa mai sanyi ta kawo ta dangwarar mishi a gaban shi.

"Sannun ki Baby nah Allah ya bani ke "
Ko kallon shi bata yi ba ta juya ta wuce d'aki sai kawai taji zuciyar ta tak'i aminta ta furta ba Amin ba daga addu'ar da Sabeer yayi.

Cikin kwanciyar hankali ya fara cin abincin yayi mishi dad'i sai dai ko rabi bai ci ba ya ture shi saboda yayi mishi yawa yasan da gayya ta zubo mishi da yawa, yana nan zaune ya fara jiyo muryar Aliyah k'asa k'asa tana kiran Suhaima daman yinin yau a d'aki ta yini bata jin dad'in jikinta.

Jin wannan kiran yasan Suhaima bazata ji ba ya sanya shi tashi ya nufi d'akin Suhaima ya shiga ba tare da neman izinin ta ba tana kwance saman bed tayi kwanciyar ringingine tana duba littafin addu'o'i.

Tsayawa kallonta kawai ya tsaya yi don wannan kwanciyar ba k'aramin sanya shi a wani yanayi na daban, Suhaima ji take kamar ana kallon ta sai ta kawar da littafin daga saitin fuskar ta fuska a d'aure tace
"Malam lafiya zaka shigo min d'aki ba neman izinin? "
D'an sosa kai yayi kafin yace
"Aunty Aliyah tana kiran ki "
Yana gama fad'in haka ya fita, d'an tsaki taja kafin ta mik'e ta fita d'akin Aliyah ta shiga sai ta tarar da ita cikin wani hali don nak'uda ce ganga ganga ta taho mata da sauri ta k'arasa inda take durk'ushe ta rik'o ta tana kuka.

Sabeer zai fita kenan yaji kukan Suhaima nan ya fara kiran sunan ta hankalin tashe gashi bashi da damar shiga d'akin, nan Aliyah dakyar ta fad'awa Suhaima taje ta kirawo mata Babaa Lantana.

Tana fitowa taci karo da Sabeer wanda yake tsaye a bakin k'ofar hankalin shi a tashe kamar ya fad'a d'akin haka yake jin shi.

Ganin Suhaima zata fita yasa shu rik'o hannun ta yace
"Baby what wrong with U? "
Kamar ta share shi sai kuma tace
"Aunty ce zata haihu tana shan wahala "
"Innalillahi bari naje na kirawo Yaya da Babaa Lantana ki zauna kusa da ita "

Da sauri ya juya ya fita yayin da Suhaima ta koma cikin d'akin, babu dad'e wa da fitar shi sai ga Babaa Lantana da Aliyu sun shigo gidan tare da Sabeer nan suka shiga cikin d'akin ban da Sabeer wanda yake tsaye zuciyar fal tausayin Aliyah.

Yana nan tsaye Suhaima ta fito tana kuka da

Please Login or Register in order to submit comment