Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Aliyu wanda idanun shi suka yi ja na tausayin halin da matar shi take ciki akabar Babaa Lantana a cikin d'akin
"Ya kamata mu tafi hospital "
Cewar Sabeer da ya matso kusa da Yaya Aliyu, d'an girgiza kai Aliyu yayi kafin ya bud'e baki yayi magana sun ji kukan jariri.

"Alhamdullilah "
Suka furta gaba d'aya suna nan tsaye Babaa Lantana ta fito fuskarta d'auke da farinciki tace
"An sauka lafiya mun samu namiji "
Nan fuskar su ta fad'ad'a da fara'ar farinciki, Suhaima mai kuka ta dawo dariya har da buga tsallen murna ta rungume Yayanta, kallon su Sabeer yake cike da sha'awa daman shima yana da k'anwa ko Yaya wanda suka fito ciki d'aya da shima ya nuna mishi irin son da yaga Aliyu da Suhaima da suke yiwa junan su.

Suhaima ruwa ta d'ora kan wuta bayan ta hura itace bayan yayi zafi ne ta kwashe takai toilet sannan ta d'ebo wanda za'a yiwa jariri wanka ta kai d'akin Aliyah inda har Babaa Lantana ta gyara ko'ina fes ta sanya turaren wuta na kamshin d'akin.

"Sannu Aunty Aliya "
Suhaima ta furta tana rik'o hannunta fuskarta d'auke da murmishi,
"Yawwa kanwata ke ma sannun ki "
Kamata Babaa Lantana tayi ta kaita band'aki wanka tayi mata suka fito sannan tayi wa jariri lokacin da suka gama tsaf suka shirya sai ga Yaya Aliyu nan da taxi ya taro zasu je asibitin da Jiddah ta kaisu lokacin tana laulayin ciki.

Suka tafi aka bar iya Suhaima a gidan tana dad'a gyarawa, bayan ta gama ne sai tayi wanka ita ma ta fito d'aure da zanin wanka ko hijab bata sanya ba da yake tasan a tunaninta Sabeer ya bi su hospital ne.

Tsayawa tayi bayan ta fito daga wankan tana taje dogon gashin kanta ta sunkuyar da kan gashin yayi gaba tana taje shi, bayan ta gama irin ta d'ago kanta gashin yayi baya sai a fuskar Sabeer wanda shigowar shi kenan gidan, ya hango ta tana taje kanta.

"Wash! kin sanya min gashi a ido da bakina fah"
A d'an tsorace Suhaima ta jiyo jin muryar Sabeer a kusa da ita, suna had'a ido nan gabanta ya hau fad'uwa ganin irin kallon da yake jifanta dashi idanun shi har sun fara canja launi, na shiga uku ni Suhaima daman wannan mutumin bai bi su ba, ta fad'i hakan cikin zuciyar ta tana mai ja da baya shima yana bin ta da haka har bayanta ya jingina da bangon d'akin ta sai kawai ta runtse ido tare da k'ank'ame jikinta waje d'aya.

Hannun shi ya sanya ya d'auke gashin da ya rufe mata face nata ya zuba mata ido musamman pink lips nata wanda ta d'an danne na k'asan kad'an da hak'orinta na k'asa ji yake kamar yayi ta kissing d'in su sai dai ba yanzu ba da sauran lokaci amman duk lokacin da ya mallake su sai ta gane kurenta sai ya ladaftar dasu ta tsiwar da suke mishi.


"Baby open your eyes please "
A hankali ta bud'e idanunta gabanta na cigaba da fad'uwa ta zube idanunta saman fuskar Sabeer wanda batasan lokacin da suka d'auki mintuna 2 tana kallon cikin idanun shi wanda daga k'arshe kasa jure kallonsu tayi sai kawai ta sunkuyar da kanta k'asa jikinta yayi sanyi wani irin abu ne yake fisgarta game da Sabeer amman tana kok'arin yaki ce shi don batason yayi mata tasiri akanta.

"Baby mene aibuna da baki sona why Suhaima? "
Shiru tayi babu amsa hannun shi ya sanya ya d'ago face nata cikin muryar shi da ta soma rawa tamkar wanda zai fashe da kuka yace
"Saboda me baki sona ni d'an iska ne ko kuma ban cancanta a so ni ba? "
Girgiza kanta tayi don bakinta yayi mata nauyi ta kasa magana.
"Toh kina sona? "
Nan ma ta girgiza kai, wani abu ne ya tokare wuyan Sabeer wanda ya sanya wasu hawaye fita daga idon shi.

A hankali ya saki fuskarta jikin shi yayi sanyi sosai goge hawayen face nashi yayi tare da sakin murmishin yak'e yace
"Ni kuma ina son ki kuma insha Allah zai kin zama tawa, ina son ki Baby "

Yana gama fad'in haka ya juya ya tafi har yana cin tuntu6e da abu sauran kad'an ya fad'i saboda gaba d'aya ba'a hayyacin yake ba.

Hankali Suhaima ya tashi da sauri ta ce
"Sabeer kayi hankali kada kaji ciwo"
D'an jiyowa yayi ya kalleta kafin ya juya ya bar gidan gaba d'aya zuciyar shi sam babu dad'i.


Jikinta a sanyaye ta shige d'aki ta kwanta rub da ciki a saman bed wasu hawaye ne suka fara zuba a idanunta me yasa bata ta6a jin tausayin Sabeer irin na yau, me yasa ta fara jin wani yanayi game da Sabeer wanda bata ta6a jin irin shi ba, anya kuwa zuciyar ta bata fara son Sabeer ba kuwa?......



Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/24, 9:00 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




PAGE 57-58




Ta dad'e kwance a hakan don batasan iyakacin lokacin da ta d'auka ba jin dawowar su Yaya Aliyu taji daga hospital, nan ta tashi da sauri tana zira kaya tana mai mamakin dad'ewar da tayi don ma ta gama dukka ayyukanta, wani siket ta sanya pink colour mai turuwa sai T-shirt in black colour mai k'aramin hannu tana da tattara daga gaban rigar sai ta gyara gashin kanta tayi rolling da pink d'in veil kalar siket d'in batayi wani make-up ba daga powder da ta sanya sai lips gloss mai kamshin apple tayi kyau sosai duk da batayi kwalliya ba.

Nan ta fito tsakar gidan babu kowa d'akin Aliyah ta wuce sai ta tarar da Babaa Lantana da Aliyu sai Sabeer a palour babyn na hannun Sabeer yana faman kallon shi addu'a yake cikin zuciyar shi Allah ya nuna mishi auren shi da Suhaima ta haifa mishi kyakkyawan babyn yanda yake shi d'aya yana rok'an Allah yasa ya haifi yara da yawa don bazai sassautawa Suhaima ba duk shekara yake son tana haifa mishi baby shi zaina yin zaman rainon su.

Yana cikin wannan tunanin yaji sassanyar kamshin turaren ta sai da ya lumshe ido kafin ya bud'e su ya sauke su saman beautiful face d'in Suhaima sai akayi dace ita ma ta d'ago idanunta ta kalleshi nan suka fara kallon junan su, dakyar Suhaima ta iya controlling d'in kanta ta janye idanunta ta wuce ta samu ta zauna kusa da Aunty Aliyah, shima Sabeer d'auke idon nashi yayi yana wani shan kamshi ji yake tamkar ya lasheta don tayi mishi kyau.

Duk wannan kallon da suke yiwa junan su Aliyah da Aliyu suna kallon su suna kyautata zaton Suhaima an fad'a tarkon Sabeer, wayar shi ya d'auko ya d'auki babyn pic's yana d'an yin hira da Babaa Lantana wadda yake zaune kusa da ita, sun jima a zaune a haka Suhaima tana son d'aukan babyn don bata ganshi ba gashi Sabeer yak'i ajiye shi gajiya tayi don haka cikin muryar shagwa6a tace

"Wai ni Aunty Aliya baza'a ban na d'auki babyn ba ni fah tun da aka haife shi ban d'auke shi ba sosai "

Rik'e ha6a Aliyah tayi tare da cewa
"Ni zan hana ki d'auka ne ai gashi hannun mutumin na ki sai kije ki kar6a "

D'an jim tayi kamar bazata je ba sai kuma ta kasa jurewa don haka sai ta mik'e a nutse ta nufi inda Sabeer yake zaune, kamar an tsikare shi ya mik'e tsaye da sauri ya mik'awa Babaa Lantana babyn tare da cewa
"Nayi mantuwa Babaa rik'e minshi ina zuwa "
Yana mik'a mata ya fice da sauri har yana mance wayar shi, baki sake Suhaima take bin shi da kallo tabbas akwai wani abin d'an ta6e bakinta tayi ko maye ruwanta ma, kar6ar babyn tayi ta rungume shi a jikinta k'aunar shi na ratsa cikin zuciyar ta.


Wayar Sabeer ce take k'ara kira na biyu kenan da ake yi mishi gashi tun da ya fita bai dawo ba.

"Suhaima ajiye babyn ki kai mishi wayar tunda bai dawo ba "
Cewar Yaya Aliyu, Babaa Lantana ta mik'awa babyn ta mik'e tare da d'aukar phone d'in nashi ta fita daga parlorn, kallon phone d'in take sosai tayi mata kyau da gani mai tsada ce sosai bana kad'an ba.

Bata ganshi a tsakar gida ba don haka tayi sallama d'akin shi sau uku ba'a amsa ba, sai kawai ta tura kanta cikin d'akin wayam bata ga Sabeer, abin ya d'aure mata kai ina ya shiga ne.

Fitowa tayi ta duba don ta duba kofar gida tana lek'awa ta hango abin da ya kusan sumar da ita saboda tsanannin tashin hankali, tuni jikinta ya hau rawa zuciyar ta na bugawa da k'arfi nan da nan idanun ta suka rikid'a daga farare sol zuwa ja, ba komai ta hango ba sai Sabeer da yake zaune saman wani d'an reshen bishiya da ya karye ya fad'o k'asa sai ake zama a kanshi sai wata budurwa wadda bata gane fuskarta ba tasha uwar d'amara a kugunta a tsaye gaban Sabeer suna dariya hankalin su kwance ita kuma tana wani jan mayafi tana rufe fuskarta tamkar mai jin kunya.

Shi kuma yana mata magana, tuni Suhaima taji wani mugun kishi ya tokareta wanda batasan tana da irin kishin nan ba, batasan lokacin da ta k'arasa inda suke ba ta tsaya ranta a mugun 6ace.

Tun tahowar ta Sabeer ya hango ta yana kallonta ta gefen idon shi ganin yanda fuskarta ta koma yasa shi narke murya yana dad'a jan budurwar da hira wadda kasance k'anwa ce ga Ashiru.


Ganin ta d'auki tsayin seconds a tsaye babu wanda ya kulata yasa taja wani mugun tsaki tamkar zata tsinke harshenta, da sauri suka jiyo suka kalleta.

"Laaa Suhaima ashe kece "
Cewar budurwar yarinyar tana washe baki, wata harara ta gallawa buduwar wanda batasan ta iyata ba, sauran kad'an dariya ta kubcewa Sabeer ganin abin da tayi.

D'an wani tunani Suhaima tayi sai kawai ta k'ak'alo yak'en dole tace
"Eh ni ce Sadiya ya kike? "
Tana washe hakora tace
"Lahiya lau wallahi yanzu tahowar da zanyi gidan ku zan shigo ganin jaririn Aunty Aliya sai wannan d'an binni ya tsayar da ni "


"Hmmm "
Abin da Suhaima ta fad'a kenan, sannan ta mayar da hankalin ta kan Sabeer ta mik'a mishi wayar shi ba tare da sun had'a ido ba tace
"Kiran ka akai "
Bata bari ma ya kar6a ba ta sakar mishi ita Allah ya sanya yayi saurin cafewa ba don haka ba da ta kwankwatse sai kawai ya bita da kallo har ta wuce cikin gida kafin ya sauke ajiyar zuciya ya mik'e shima ba tare da ya kula Sadiya ba ya wuce cikin gidan d'akin shi ya shiga ya rufe k'ofa tare da kwanciya saman katifa yana son fassara abin da yake kan fuskar Suhaima amman ya kasa tantacewa nan ya fara juyi kawai.

Suhaima kuwa tana shiga gidan ta wuce zuwa cikin d'akin ta idanun ta sun rufe da wani irin abu da ta tabbatar da ba komai ba ne sai kishin Sabeer, fad'a wa tayi kan gadon ta tare da fashewa da wani irin kuka, tasan idan ka fara son mutum dole kayi kishin sa kenan ya ita ta fara son Sabeer tunda gashi daga nin shi da wata batasan dalilin tsayuwarta ba ta ji wani abu ya tokare mata wanda tasan ba komai ba ne sai kishin Sabeer!......



_ku cigaba da hak'uri fan's da ni, ga wannan ku yi manage da shi please_


Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/28, 5:42 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




*PAGE 59-60*




Tana kwance kawai taji an dafa bayanta a d'an tsorace ta d'ago kanta sauke ajiyar zuciya tayi don ganin Aunty Aliya ce ta dafata.

"Tashi mu yi magana Suhaima"
Tashi zaune tayi tana mai sunkuyar da kanta tana murza 'yantsunta batason ta kalli Aunty Aliya su had'a ido kada ta karanci wani abin akan fuskarta.

"Hala Suhaima kin fara son Sabeer ne kike kishi dashi? "
A razane ta d'ago kanta tana kallonta, gid'a kanta Aliyah tayi tare da cewa
"Idan baka son mutum taya zaki fara jin haushi don kin ganshi a tsaye da wata?"

"Ni fah Aunty bason Sabeer nake ba ni ba haushi naji ba fah dana ganshi da wata a tsaye"

"Shikenan tun da ni ban isa ki fada min matsalar ki ba amman tabbas kwanaki biyun nan kin canja don ba haka kike ba, amman tun da kin ce ba haka ba"
Tana gama fad'in haka ta juya zata tafi da sauri Suhaima ta sanya hannun ta ta rik'o na Aunty Aliya da D'an k'arfi ta matse hannunta

"Ni kada ki ji min ciwo kawai ki cikani na tafi tunda ni baki d'auke ni matsayin Yayar ki ba kuma abokiyar shawarar ki, ni da nasan Suhaimar dana sani ba haka take ba bata iya 6oye min komai nata"

"Aunty kiyi hak'uri ki zauna zan fad'a miki koma mene "
Zama Aunty Aliya tayi kusa da Suhaima.

Kamar bazata yi magana ba tayi shiru sai mutsu mutsu take da baki, d'an kallonta Aliyah tayi tare da girgiza kai kawai wani lokacin Suhaima tana bata mamaki idan tana wasu abubuwan.

"Idan baza ki magana ba zan tafi ".
Cikin rawar murya kamar mai shirin fashewa da kuka tace
"Uhm... Uhm Aunty ni kaina na rasa mai yake damuna haka, cikin kwanaki biyun nan idan Sabeer yayi min magana ko muka had'u sai naji gabana yana fad'uwa, sannan kuma kawai d'azu dana ganshi da wata sai naji wani takaici wanda ya sanya ni kuka"

"Kin fara son Sabeer kenan ".
Waro ido waje tayi tare da dafe kirjinta da hannu kafin tace
"Taya na fara son Sabeer Aunty bayan ni kuma sam baya gabana? ".

"Ta yanda kika fara kishi dashi, Suhaima ina mai k'ara tunasar da ke da kada kiyi abin da zai sanya ki dana sani daga baya saboda na tabbatar idan kak'i Sabeer zaki zo kina nadama mara amfani don kafin ki samu wanda zai so ki kamar Sabeer zaki dad'e kina nema, kiyi amfani da damar ki Suhaima kafin ta kubce miki "

Tana gama fad'in haka ta tashi ta fita saboda kiran da Babaa Lantana tayi mata, ta bar Suhaima cikin wani yanayi mai wuyar fassaruwa.

"Nayi amfani da dama ta kafin ta kubce min, me Aunty take nufi.....! "

Dafe kanta take wanda ya fara yi mata ciwo gaba d'aya ta rasa me ya kamata tayi shin zata bi shawarar Aunty Aliya ne ko kuwa zata bi abin da zuciyar ta yake kitsa mata na kada ta bari son Sabeer ya zauna mata cikin zuciya idan ba haka ba zatayi nadama don family d'in Sabeer baza su so ta ba a matsayin surukar su duba da wulak'ancin da tasha lokacin bikin Jiddah.




*_After two weeks_*


Acikin wannan satin ne bayan an sha sunan d'an Yaya Aliyu wanda aka sanya mishi sunan Baba Adamu, su Babaa Lantana sun so ya sanya sunan mahaifin shi Umaru amman Aliyu da Suhaima suka k'i aminta da hakan k'ememe don baza su ta6a mance abubuwan da mahaifin su ya aikata musu ba, Ameer Suhaima ta sanya yaron suna fad'a mishi saboda 6oye sunan shi da suka yi.

Zuwa wannan lokacin Sabeer ya dad'a ramewa sosai sakamakon tunani da ya sanyawa kanshi gashi yaja baya da al'amarin Suhaima da yana da ikon da zai cire sonta cikin zuciyar shi da yayi, duk wanda yasan Sabeer a baya yanzu ya ganshi sai ya tausaya mishi musamman akasan A SANADIN SO ya zama hakan gaba d'aya ya fita hanyar Suhaima tunda ko ya kulata ba wani sauraren shi take ba, sosai Aunty Aliya da Yaya Aliyu suke tausaya mishi don yayi alkawarin bazai yiwa Suhaima auren dole ba sai dai kawai taji ana d'aura auren ta da Sabeer sosai Aliyu yana bashi tausayi.


Ta 6angaren Suhaima ma duk ta wani rame saboda son Sabeer da kullum yake shiga cikin zuciyar ta yana nuk'urk'usa kowanne sashi na cikin zuciyarta, sai dai ta kasa bawa zuciyar ta aminta har takai da ta furtawa Sabeer cewa tana son shi zata aure shi sannan zata iya jure duk wani wulak'anci na family d'in shi zata jure shi indai Sabeer zai rik'e ta cikin mutunci bazai juya mata baya.

Da wannan tunanin take kwana take tashi tana jiran Sabeer ya k'ara furta mata kalmar so a time d'in take son sanar dashi ita ma ta kamu da son shi, a lokacin da take kok'arin fad'a mishi ta kamu da sonshi a lokacin kuma ya canja mata ko magana bata had'a su yanzu ya zatayi kenan.

Zaune take a d'aki tana wannan tunanin da ya zame mata kamar karatu don a kullum makamancin tunanin take yi, runtse ido tayi hawaye masu zafi suka samu sauka asaman face nata, zafi zuciyar take mata.


Zumbur ta mik'e tsaye da zaunen da take ta fito tsakar gida nan ta fara shara gyara gidan tsaf tayi sannan tayi wanke wanke da wanke toilet kafin ta wuce d'akin Aunty Aliyah ta gyara mata shi tsaf ta sanya turaren wuta, kallonta kawai Aunty Aliya take saboda ganin yanda take rama gashi kana kallon face nata zakasan tana d'auke da damuwa, har ta gama sanya turaren wuta ta fita daga d'akin tana kallonta ajiyar zuciya ta sauke tana mai taya Suhaima da addu'a Allah ya yaye mata abin da yake damunta.

Agurguje tayi wanka ta shirya cikin wasu kaya pakistan dogon wando white ne sai rigar da tsayinta wajen gwiwar ta ne itama farace rigar sai touch d'in flower's blue ajikin gaban rigar body spray ta fesa bayan ta shafa powder da man le6e, tayi kyau duk da ba wani make up tayi ba.

Hijab dogo mai hannu blue colour ta sanya sannan ta zura flat shoes akafanta white ta fito ko d'akin Aunty Aliya bata shiga ba ta fita, a k'ofar d'akin da Sabeer yake ta tsaya tana son shiga tana kuma tsoro gabanta sai fad'uwa yake, ta dad'e a haka kafin dakyar ta iya d'aga kafarta ta shiga d'akin sai dai kuma wayam babu kowa sai dai da alama bai dad'e da fita ba don ga kaya a zube a k'asa wanda ta ganshi ya sanya da safe.

Da sauri ta k'arasa shiga ta tattara d'akin ta gyara ta share shi tas sannan ta hango wani diary nashi akusa da pillow d'auka tayi ta fara karanta wa.

Tun da ta fara karantawa take kuka a hankali har takai da ta bud'e baki sosai tana kukan tausayin Sabeer daman ashe haka yake sonta, me yasa ta wulak'anta shi da tasan haka yake sonta da a lokacin da ya furta mata so ta amince dashi, me yasa bata tsaya ta fahimce shi ba ita wacce iri ce da bata tsaya tayi nazari akanshi ba.

"Wayyo Allah nah...! "
Fad'in Suhaima hawaye na zuba a idanunta.

"Allah sarki Sabeer ashe kai masoyina na gaskiya dole a yau ba gobe ba na bayyana maka zuciyata ta dad'e da kamuwa da son ka!, i luv U Sabeer with oll my heart! "

Tashi tayi tsaye bayan ta ajiye mishi diary d'in ta fita daga gidan gaba d'aya ma, a k'ofar gidan ta tsaya tana kalle kalle ta inda zata hango Sabeer, amman ko mai kama dashi bata hango ba sosai tayi mamaki don bai fiye yawo sosai ba sai dai idan Yaya Aliyu zai je wani wajen ya rakashi shima ba koyaushe ba sai abokin shi Ashiru da suke d'an fita amman basa nisa kuma basa dad'ewa sosai.

"To ina yaje!? "
Cewar Suhaima a fili ta furta hakan tana furzar da iskar bakinta, cikin sanyin jiki ta juya zata koma cikin gida kenan ta hango Ashiru, wata ajiyar zuciya ta sauke kafin ta k'arasa kusa dashi da sauri tace
"Ashiru don Allah ko kaga Sabeer? "

Da murmishi a fuskar shi yace
"Eh yana cikin gonar Yaya Aliyu a zaune yanzu na barshi acan na taho d'auko abu "
ajiyar heart Suhaima ta sauke tare da hamdala jikin zuciyar ta kafin tace
"Yawwa nagode Ashiru"

Tana gama fad'in haka ta wuce da sauri zuwa cikin gonar Yaya Aliyu, yayin da Ashiru ya wuce cikin gida.

Tana k'arasa gonar ta fara dube duben inda yake ta d'an jima tana dubawa kafin ta hango shi kan wani dutse mai d'an girma a zaune, kallo d'aya zaka yi mishi ka fuskanci yana cikin damuwa.

Ta jima tana kallon shi hawaye na zuba a idanunta na tausayin Sabeer kasa k'arasa wa inda yake tayi kawai ta tsaya tana kallon shi, jikinshi ne ya bashi ana kallon shi yasa shi d'ago kanshi yana dubawa ya hango Suhaima a tsaye ta zuba mishi ido, d'an murmishi ya saki na yak'e kafin kuma lokaci d'aya ya zaro ido waje fuskarshi d'auke da tsantsar tashin hankali da k'arfi ya furta

"Suhaima! "
Bazato Suhaima taji ya kirawo sunanta fuskarta d'auke da murmushi itama ta furta
"Sabeer! "
Ganin batasan abin da ya hango ba ne bane yasa shi zabura ya mik'e da wani irin gudu da zafin nama ya k'arasa inda take tsaye bai yi wata wata ba ya ture ta gefe guda ta fad'i k'asa.

Arud'e ta d'ago kanta ta kalle shi inda kuma a daidai lokacin Sabeer ya saki wata k'ara da k'arfin gaske ya fad'i k'asa yana wani irin abu kafin kuma jikin shi ya sandare kamar matacce ya zama, cikin hargitsi Suhaima ta mik'e tsaye ta taho inda Sabeer yake kwance, sauran taku d'aya tayi ta k'arasa wajen ta hango abun da ya matuk'ar firgitata ya tsorata ta lokaci d'aya jikinta ya hau rawa na tsoro ko kwakkwaran motsi ta kasa balle ta nemi agaji.......



Uhm ga Sabeer a kwance kamar matacce ko mene ya same shi sai ku biyo ni don jin abin da ya faru, mu had'u a next page don jin yanda zata kasance, ku cigaba da hak'uri fan's.


Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/28, 9:04 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*


Written by
Aishat A Muh'd

Dedicated to my Sadeey SaNaz




*PAGE 61-62*




Ba wani abu Suhaima ta gani ba wanda yayi matuk'ar razana ta sai wani k'aton snake baki wuluk dashi wanda batayi tantama ba shine ya harbi Sabeer, ganin yayi kanta ne yasa ta bud'e muryar ta gaba d'aya ta zuba wata k'ara ta firgita, gaba d'aya jikinta rawa yake yi saboda tsabar firgita rufe idanunta tayi kawai ta sadakar kasheta zai yi.

Kafin ya k'arasa inda take ne Aliyu da Ashiru wanda suka taho gonar suka jiyo k'arar Sabeer a rud'e suka taho da gudu suna gaf da k'arasa inda suke ne suka sake jin k'arar ihun Suhaima da gudu suka k'araso ganin abin da yake kok'arin cutar da ita ne ya sanya su nufar inda yake nan Ashiru da Yaya Aliyu suka far masa da duka sai da suka kasheshi tsab tukunna suka k'arasa wajen da Sabeer yake kwance Suhaima tana rik'e dashi tana kuka kamar ta shid'e.


Hankali a tashe suka k'arasa wajen sannan Yaya Aliyu da Ashiru suka d'auki Sabeer suka nufi gida, Suhaima tana biye dasu kamar tayi hauka saboda tashin hankali.

Suna k'arasa gida suka shigar dashi gida nan aka kirawo mai magani na gargajiya ya fara aikin shi har ya cire dafin a k'afar Sabeer inda macijin ya cijeshi, sannan ya sanya magani a wurin nan yace musu zai iya farkawa a koda yaushe don ya auna arzik'i saboda macijin da ya harbe shi yana da dafi sosai, sannan ya ba da maganin da zai yi amfani dashi daga k'arshe kuma yace idan ya farka a kirawo shi sannan yayi musu sallama ya tafi.


Aliyu da Aunty Aliyah hankalin su ba k'aramin tashi

Please Login or Register in order to submit comment