Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shi zama a kan carpet ya k'ura mata ido cikin wani yanayi daban, d'an hararar shi tayi tare da murgud'a mishi baki ta mik'e ta wuce toilet da kallo ya bita yana murmishi sannan ya girgiza kanshi har yanzu tsiwar tana nan ba'a daina ba.


Bayan ta idar da sallah ne agurguje ta wanke toilet tsaf tazo ta gyara bedroom d'in amman ban da kan bed saboda Sabeer da yake kwance akai yana bin ta da mayataccen kallon shi, bayan ta gama ta fita zuwa tsakar gida ta tarar har Yah Aliyu ya wuce schl Aunty Aliyah kuma ta gama komai ta gyara gidan tsaf.


Gaida ta Suhaima tayi tana tambayar ta mai jiki bata amsa ba ta wuce kitchen tana cewa
"Aunty da akwai ruwan zafi zanyi wanka? "

Murmishi tayi kafin tace
"Da akwai na dafa muku don nasan zaku nema "

D'an zaro ido kad'an Suhaima tayi gabanta ya fad'i kada Aunty Aliyah ta zargi ko sunyi wani abun bayan babu abin da ya faru tsakanin su, sai kuma ta share kawai ta d'ebo wanda zai ishesu wanka ta wuce d'akin bata k'ara bi takan Aunty Aliyah ba don ta bata kunya.


"Idan ki kai ruwan ga abin karyawa nan kizo ki d'aukar muku "

"Toh "
Kawai tace ta shige d'akin, had'a mishi ruwan wanka tayi sannan ta fito tana kok'arin yi mishi magana yace
"Baby nah kin tashi lafiya?"

Kauda kanta tayi bata amsa ba sai kawai tace mishi
"Na had'a maka ruwan wanka "
Tana gama fad'in haka ta wuce ta fita zuwa waje, kayan breakfast d'in ta d'auko musu ta kawo d'akin ta tarar dashi har ya shiga wanka, gyaran kan bed tayi ta d'ameshi sosai yayi kyau.


Kayan shi ta duba taga duk sunyi datti da squeezing sai iya wanda ya sanya jiya da dare masu kyau daman kayan gaba d'ayan su kala 4 ne ya taho dasu, tana nan tsaye tana tunanin mafitar wanne kaya zai sanya sai gashi ya fito daga toilet d'in yana daure da towel d'in Suhaima wanda dakyar ya ritsa shi d'ayan hannun shi kuma rik'e da kayan da ya cire su.


Kallo d'aya Suhaima tayi mishi ta d'auke kanta kawai ta tattaro kayan shi masu datti ta k'arasa inda yake ta fisge masu dattin wanda ya cire tayi fita daga d'akin da sauri, da kallo ya bita yana murmishi kawai.


Tana fita kayan ta had'a ta fara wanke mishi tana gama wanke su ta koma cikin d'akin har zuwa lokacin yana zaune gefen gado dashi da towel d'in kanshi a sunkuye yana ciccila k'afa.


Had'a mishi tea tayi sannan ta zuba mishi jellop d'in da akayi na taliya a plate, kusa dashi ta ajiye mishi tare da maganin shi dakyar ta iya cewa

"Ga breakfast d'in ka nan "

Tana gama fad'in haka ta wuce toilet don yin wanka, a nutse yake shan tea d'in har yasha rabin cup sannan ya d'auki taliyar kad'an ya iya ci ya ajiye yasha maganin shi da ragowar tea d'in.


Fitowa tayi daga toilet tana daure da zani ta dubi dressing mirror k'ara had'e fuska tayi ganin yana bin ta da mayataccen kallon shi, tana tsaka da shafa mai ne taji lallausan hannun Sabeer yana yawo a jikinta da sauri ta sanya hannun ta tana kok'arin cire hannun shi amman sai taga ya zube saman gwiwowin shi ya kama hannunta dukka biyun ya had'e dana shi yana kallon cikin idonta yace

"Baby nah da farko ina neman yafiyar ki akan abin da nayi miki, ina rok'an ki da ki yafe min nasan nayi kuskure ban kyauta miki ba da na kasa gane makirci aka had'a mana don kawai a raba mu nayi nadamar hakan, wallahi Baby ina son ki sosai kullum sonki k'ara shiga zuciyata yake i luv U with oll my heart "

Shiru tayi mishi hawaye ne zasu zuba daga idonta da sauri ya girgiza mata kanta kan yace
"No Baby kada kiyi kuka please, kukan ya isa haka bana buk'atar sake ganin zubar hawayen nan "
Dole ta had'iye kukan amman duk da haka sai da wad'annan hawayen da suka fara fitowa suka zubo, hannun shi ya sanya ya goge su yana cewa
"Baby kice kin hakura kin yafe min zamu koma zama da junan mu kamar da "

Rungume shi Suhaima tayi tana cewa
"Komai ya wuce a wurina, sai dai ina tsoron komawa gidan ka "
Ta k'arasa fad'a duk alamar tsoro ya bayyana a face nata, wani tausayin ta ne ya kamashi yasan da gaske take fad'in haka har cikin zuciyar ta, bubbuga bayan ta ya fara yi yana cewa

"Baby anan zamu zauna baza mu tafi ko'ina ba har sai kin amince da kanki zaki koma gidan ki, kin yarda da haka? "

Cikin jin dad'i ta saki murmishi wanda shine na farko da tayi mishi tun zuwan shi kauyen su tace
"Na yarda da hakan sosai "
Jan hancin ta yayi kad'an yace
"Naji dad'in haka Baby nah zan kasance mai faranta miki rai har k'arshe rayuwata insha Allah "

Ya k'arasa fad'a yana matse ta ajikin shi har sai da tace
"Wash! You are hurting me "
Sannan ya sassauta ruk'an da yayi mata kafin tace
"Kaje ka kwanta tunda baka da lafiya "

"Waya fad'a miki aini na warke daman ciwon so ne ya kwantar dani gashi kuma na samu maganin shi "

D'an hararar shi tayi tana turo baki bata ankara ba taji lips d'in shi kan nata, sun d'auki wajen 5 minute a haka kafin su rabu da junan su suna sauke ajiyar zuciya kallon junan su suke cikin wani shauk'i.



***********


Hango Dr Faridah nayi cikin katafaren palourn ta tana faman safa da marwa kallo d'aya zaka yi mata kasan hankalin ta a matuk'ar tashe yake, don yau kimanin wajen sati 3 bata samun wayar Sabeer daga dukannin number's d'in na k'asar waje wanda yake amfani dasu.


Kullum tayi try numbers d'in a kashe harda ta gida 9ja ma, abin yayi matuk'ar d'aga mata hankali don kuwa hakan bai ta6a faruwa dasu ba, tananin wanne hali Sabeer yake ciki don ta tabbatar Sabeer baya cikin Nigeria tun da har da ita aka raka shi airport.

To ina ya shiga?, dum gaban ta ya fad'i da tuna ko yana tare da wannan shegiyar yarinyar, amman kuma tasan Sabeer baya k'asar, da sauri cikin rawar jiki ta d'auko phone nata ta shiga searching d'in numbers d'in shi na Nigeria domin ta bibbiyi layin nashi ko yana nan Nigeria bai tafi ba yaudarar ta yayi.

Sai dai har taga ma searching nata bata ga wata alama ba don nuna mata ake layukan suna kashe, jefar da wayar tayi tare da d'ora hannunta saman kanta gaba d'aya ta tallafi kan nata, gashi har zuwa yanzu Daddy baya bata fuskar tayi mishi magana balle ta fad'a mishi matsalar ta ina d'anta ya shiga, wasu hawaye ne masu zafi suka fara sauka kan fuskar ta na tsabar kewar d'annata da tayi ji take kamar ta shekara 3 bata ganshi ba............




Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[4/27, 9:39 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ


♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*



*PAGE 110*









Tana zaune a palourn tana wannan tunanin tunanin ga hawaye kaca kaca a face nata Daddy ya shigo parlourn kallo d'aya yayi mata ya d'auke kanshi kada ta karya mishi gwiwa don kwanakin biyun nan tana bashi tausayi ta sanya damuwa akanta saboda rashin jin muryar d'an nata, duk ta rame ta fara zama silent sosai, kok'arin hawa steps na bene yake yaji muryar ta na cewa

"Daddyn Sabeer ina son magana da kai please "

Ko kallonta Daddy bai yi ba ya fara hawa steps don har yanzu bai ga tayi laushi sosai ba na yanda zai sanar mata inda Sabeer yake.

Ganin Daddy ya shareta ne ya sanya ta tashi da sauri ta bi bayan shi, har zai shiga side d'in shi tayi saurin rik'o hannun shi cikin muryar kuka tace

"Don girman Allah Dear ka fad'a min inda Son yake? "

Hannun shi ya sanya wanda bata rik'e nashin ba ya zame nata hannun yayi gaba kawai ya shige side d'in shi, nan Mumy aka durk'ushe tare da sakin kuka na tashin hankali.

Daddy jingina bayan shi yayi da bayan door tare da runtse eyes nashi tausayin ta ne yake neman rinjayar zuciyar shi don yasan yana son Dr Faridah so bana kad'an ba, ba k'aramin wahala yake sha ba na wannan zaman da suke yi tare amman bashi da yanda za yi dole ya nuna mata kuskurenta na zubar mishi da en jikokin shi da tayi so yake tayu nadama sosai yanda a lokacin zai sanar mata da inda d'anta yake, amman fah kukan ta yana ta6a mishi zuciya sosai.


Sai da tasha kukanta ta more sannan ta mik'e ta wuce side d'in ta hawaye na zuba a eyes nata, kamar wata mahaukaciya sabon kamu take faman gwada kiran number's d'in Sabeer na dukkan k'asar da tasan yake zuwa har da ta gida Nigeria amman dukka abu d'aya nau'ora take sanar da ita a kashe suke, zaman tayi kan bed tare da rafka tagumi dole ta fara binciken inda Sabeer ya tafi bazata zauna ba batasan halin da Sabeer yake ciki ba.



***********


Zaune Suhaima take kusa da Aunty Aliyah suna aikin girki na dare suna er hirar su cikin nishad'i, Yah Aliyu ya fito daga palon Aunty Aliyah hannun shi rik'e da phone nashi kallon su yayi tare da girgiza kai kullum haka suke kamar abokanan juna ya fad'i hakan cikin zuciyar shi, mik'awa Suhaima wayar yayi ba tare da yace mata komai ba ya juya zuwa cikin palon.

Da kallo ta bishi cikin mamaki wane yake kiranta haka, kawai sai ta sanya wayar a kunnen ta jin ana magana, wani zabura tayi tare da tashi tsaye ta buga tsalle da ihu murna tana furta

"Jiddahhhh"

Sabeer da yake kwance kan bed cikin d'akin Suhaima da sauri ya taso jin muryar Suhaima tana ihu, turus yaja ya tsaya da yaji ta ambaci sunan Jiddah, tsayawa yayi bai k'arasa fitowa ba daga d'akin tare da hard'e hannun shi dukka biyun yana kallonta yanda take tsallen murna, murmishi ya saki cikin zuciyar shi yana cewa

"Baby nah har yanzu yarinta na damun ki halin nan yana nan bai canja ba "
Ya fad'i hakan cikin zuciyar shi yana kok'arin komawa cikin d'akin suka had'a ido da ita hura mata kiss yayi sannan ya shige cikin d'akin.



Murmishi Suhaima tayi da taga abin da Sabeer yayi mata nan ta cigaba da waya da Jiddah cikin farinciki taji dad'in sakkowar Yah Aliyu sosai kodan kewar Jiddah tayi sosai, bayan sun sha hirar su Jidda cikin d'oki take fad'a mata gobe zata zo daga k'arshe suka yi sallama cikin kewar junan su.

Aunty Aliyah na zaune tana kallon ta murmishi kawai take ganin yanda Suhaima suke waya cikin d'oki, zama tayi tana cewa

"Wallahi Aunty nayi kewar Jiddah sosai naji dad'in yanda Yah Aliyu shi ya kirawo ta da kanshi ya had'a mu "

"Nima kaina naji dad'in hakan Suhaima Allah ya bar wannan kauna dai"

"Amin Aunty, gobe ma tace zata zo "

"Allah ya kaimu sai kiyi shirin yin dambu ko d'an wake don nasan halin Jiddah da son cin su idan tazo gashi an kwana 2 bata zo nan ba "

Cikin murmishi Suhaima tace
"Haka ne kuwa Aunty nah kin ma tuna min gobe da wuri zan tashi na fara hidimar taryan ta kinsan Jiddah da d'oki da wuri zaki ganta"


D'an hararar wasa tayi mata kan tace
"Wanne tashi wuri kuma kimsan dai mijin ki na nan gashi baya jin dad'i zama zaki ki kula dashi naji da hidimar Jiddah "

Kwa6e fuska Suhaima tayi tare da shagwa6e wa har da karyar da wuya tace
"Kaiii Aunty bayan ya warke kuma gaskiya ni zan yi "

Girgiza kai Aunty tayi kafin tace
"A'a Suhaima ki bawa mijin ki kulawa yafi koma ni zanji da komai"


Bata son yin musa da ita don haka tace
"Toh Aunty "

"Yawwa tawan dad'i na dake bakya jayayya Allah ya bamu jikoki twins "

Wata kunya ce ta rufe Suhaima musamman da taji Yah Aliyu ya amsa da
"Amin Mata ta "
Wanda ya fito zai fita yaji Aunty Aliyah tana wannan addu'ar, da gudu Suhaima ta mik'e ta wuce cikin d'aki kunya sosai ta rufe ta kamar ta nutse, yayin da Yah Aliyu da Aunty Aliyah suka sanya dariya har da tafawa da hannun su.


Bayan ta yana jingine a bayan k'ofa eyes nata a lumshe tana murmishi bata ankara ba taji saukar kissing a wuyan wanda ya haddasa mata sauke ajiyar zuciya tare da bud'e idonta sauke su tayi kan na Sabeer wanda daman kallonta yake.


Da sauri tayi niyyar wuce wa cikin d'akin ya sanya hannu tare da rik'e nata kafin kuma ya janyo ta gaba d'ayan ta jikinshi ya rungume ta tsam, wata wawiyar ajiyar zuciya ya sauke cikin kunnen ta ya rad'a mata
" i luv U Baby nah "

Murmishin jin dad'i tayi bata ankara ba taji ya d'auke ta gaba d'ayan ta bai ajiye ta ko'ina ba sai saman bed kwanciya a jikinta yayi hannun ta yana saman kanshi tana wasa da gashin yayin da shi kuma yake fad'a mata irin matsayin da take cikin zuciyar shi yana bayyana sirrin zuciyar shi wanda wasu abubuwan baza su fad'u a baki tsakanin shi da DANGARTAKAR ZUCIN shi ne wanda yana godiya ga Allah da bai sanya YAYI SAKEN sakin Suhaima ba wanda yasan sai ya fad'a kogin tsantsar nadama amman Allah ya takaita mishi K'ARSHEN WAHALAR shi, zai kasance mai godewa Allah har karshen rayuwar shi akan bashi Suhaima da yayi kamilar mace wadda ta had'a komai kuma wadda kowanne namiji yake fatan ajiye irinta a gida, yasan yasha wahala duk A SANADIN SON ta amman gashi komai ya wuce K'ARSHEN WAHALAR shi yazo yana fatan insha Allah babu abin da zai sake rabashi da Babyn shi sai mutuwa.



Kiran sallahr mangarib ne ya katse su Sabeer ya tashi yayi alwala ya wuce masjid ya bar Suhaima na kok'arin shiga toilet don yin alwala.

Bayan ta idar da sallahr ne ta tsaya karatun Qur'an har zuwa sallahr ishsha bayan tayi addu'o'in ta ne sannan ta sake gyara d'akin sosai ta fita ta sami garwashi ta kunna turaren wuta, sannan ta koma wajen Aunty Aliyah suna d'an ta6a hira duk da har yanzu tana jin kunyar ta akan maganar d'azu.


Sai wurin 9 na dare suka shigo gidan Yah Aliyu da Sabeer nan inda suke zaune a saman tabarma suka zauna kowanne kusa da matar shi, nan Suhaima ta zuba abincin aka fara ci bayan an gama ci aka zauna er hira zuwa 10 na dare suka yi sallama kowa yaja matar shi suka wuce d'akin su.


Duk yanda Sabeer ya so kasancewa da Babyn shi tak'i bashi had'in kai saboda tak'i mance ya tsane ta da ya furta mata, k'arshe da zai takura mata ta sakar mishi kuka dole ya hakura ya fara lalla6a ta har ya samu bacci ya d'auke ta, zuba mata ido yayi bayan bacci ya d'auke ta Baby rigima ya furta hakan kan ya sake rungume ta ajikin shi wani sonta na sake ratsa mishi cikin zuciya da haka shima bacci yayi awon gaba dashi.




*_WASHE GARI DA SAFE_*

Suna zaune gaba d'ayan su a tsakar gidan suna breakfast da yake Yah Aliyu sai da rana yake da lecture sai hira suke cikin jin dad'i da annushuwa.


Sallama suka ji ana yi lokaci d'aya gaban Aliyu da Suhaima yayi mugun fad'uwa wanda har ya kasa yunkurar tashi don yaga wane, sai da aka kuma yi har sau biyu amman ya kasa tashi har sai da Sabeer yace

"Babban Yaya ko naje na duba? "

Da sauri Aliyu ya mik'e tare da cewa
"Barshi bari naje "

Fita yayi jikin shi a matuk'ar sanyaye, yana bud'e k'ofa ya fita ras ras gaban shi ya fad'i ganin wani tsohon mutum duk kanshi da gemun shi furfura ta mamaye su gashi kamar ka hure shi ya fad'i d'an siriri dashi duk yayi bak'i ya zama wani kala gashi yana rik'e da sanda da ita yake dogarawa kallo d'aya zaka yi mishi kasan bai dad'e da tashi daga wannan muguwar cutar ba ta paralyzed ba, jiyowa mutumin yayi suka had'a ido da Aliyu lokaci d'aya Aliyu ya d'ago hannun shi yana nuna shi bakin shi na rawa dakyar bakin shi ya iya had'a kalmar
"Ba... Bab..... Babaaaa! "




Sorry Fan's na kusan gama muku ku cigaba da yi min uxiri.





Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[5/1, 7:52 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ


♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*



*PAGE 111*










Cikin tsananin mamaki da razani Aliyu ya sake furta
"Baba me ya kawo ka wajen mu kuma yanzu?"

Dattijon ya fashe da wani irin kuka yana cewa
"D'ana kayi hak'uri ku yafe min abubuwan da nayi kuma ciki har da tafiyar da nayi na barku sama da shekaru masu yawa ban waiwaye ku ba "

Ran Aliyu ne ya k'ara 6aci da ya tuna saboda bak'incikin shi mahaifiyar su ta rasu da irin wulak'ancin da ya dunga yi musu, sam bazai ta6a yafe mishi akan abubuwan da ya aikata a gare su, don haka ya bud'e baki cikin rawar murya yace

"Baba ni da k'anwata bama buk'atar sake ganin ka kamar yanda mu ma ka gudu ka barmu don haka kawai ka kyale mu zamu k'arasa rayuwar mu babu uba "

Yana gama fad'in haka ya juya zai koma gida, yayin da Baba yake faman kuka yana furta
"Ku yafe min Aliyu hakk'in ku ne yake bibiyata ku yafe min ko na ji dad'in rayuwata "

Amman ina Aliyu bai saurare shi ba ya wuce gida tare da rufe k'ofar ya jingina bayan shi kan k'ofar duk dauriya irinta Aliyu sai da ya kasa rik'e kukan shi ya fashe da wani irin kuka mai ban tausayi har yanzu yana jin amon murya Baban nashi yana furta su yafe mishi.

"Lafiya kake kuka? "
Yaji saukar muryar Sabeer kusa dashi yana mai rik'e shi hankalin shi a tashe don a iya sanin shi Aliyu jarumi ne ba kamar shi ba dole akwai wani babban abu da ya d'aga mishi hankali.

Girgiza kanshi yake kawai ya kasa magana, suna cikin haka Suhaima da Aunty Aliyah suka shigo zauren jin kamar sautin kuka, hankalin su ba k'aramin tashi yayi ba ganin yanda Aliyu yake kuka, nan take suka fara kukan ita Aliyah zuciyar ta ce ta bata Baban ta ko Babaar tane wani daga cikin su ya rasu.

Da sauri Suhaima ta k'arasa wajen Yah Aliyu ta shige jikin shi tana kuka tace
"Yaya me.... me ya faru kake kuka? "

Ganin yanda hankalin su ne ya tashi sosai ya sanya shi bud'e baki dakyar cikin muryar kuka a shak'e yace

"Suhaima Bab..... Baban mu ne ya dawo "

Awani firgice Suhaima ta d'ago kanta ta kalli Yah Aliyu cikin tsananin tashin hankali da rud'ani kafin ta rushe da kuka tace
"Yaya don Allah kace ya tafi ina tsoran shi wallahi kada ya kashe mu kamar yanda ya fad'a, Yaya zai dawo yana dukan mu da zagin mu ina tsoran shi..... "

Ganin abin nata ya had'ar mata da tsoro, firgici da kuma sumbatu har ta rasa me zata ce ya sanya Sabeer ya janyo ta jikin shi ya rungume ta yana bubbuga bayan ta alamar rarrashi yayin da Aliyah ma ta k'arasa wajen mijinta tana bashi baki da ya bud'e k'ofar duk da kuwa da irin kallon da yake wurgata, gashi sai wani sauke huci yake kamar wani tsohon zaki.

Suna tsaka da haka ne suka ji ana bubbuga k'ofar cikin sauri Aliyah ta sanya hannu zata bud'e k'ofar amman kafin ta bud'e Aliyu ya sakar mata wata harara bashiri ta hakura kawai ta zubawa mijin nata ido yanda ya rikid'a ya koma mata wani daban kamar ba Aliyun ta ba.


"Aliyu, Aliyah, Suhaima, Sabeer ku bud'e k'ofar nan nasan kuna jin na"
Suka jiyo amon muryar Baba Adamu yana kwalla musu kira, Sabeer ne yayi kok'arin janye Suhaima daga jikin shi ya samu ya bud'e k'ofar, yana bud'e wa Baba Adamu da Babaa Lantana suka shigo bayan su kuma mahaifin su Aliyu ne yana dogara sanda.

Suna had'a ido da Suhaima ta wani saki k'ara mai rud'ewa wanda sauran kad'an ta wuntsila tsabar firgita da tsoran shi da sauri Sabeer ya taro ta ya rik'e ta k'am itama rik'eshi tashi sosai suka shige cikin gidan jikinta na 6ari don masifar tsoron shi take.


Daman tabarmar da suka karya akanta tana nan a shimfid'e zama suka yi dukkanin su ban da Suhaima da ta gudu d'aki tana kuka sai Yah Aliyu da yake tsaye ya kasa zama.


Tashi Sabeer yayi ya nufi d'akin ya tarar da Suhaima tana kwance a ruf da ciki tana kuka sosai, cikin sanyin jiki Sabeer ya k'arasa inda take ya zauna tare da janyota jikin shi ya d'orata saman k'afafun shi share mata hawayen face nata yake yi cikin sanyin murya yake rarrashin ta, dakyar ya samu tayi shiru sannan ya d'auko ruwa ya bata tasha, kad'an ta iya sha sannan yace

"Baby nah ki nutsu mu je, amman na rok'e ki kada kiyi kuka ji yanda idanun ki da fuskar ki suka yi ja gashi sun kumbura saboda kukan da kika yi"

Cikin sanyin jiki ta d'aga kanta alamar toh daga haka yaja hannunta suka fito zuwa tsakar gidan inda suke zaune jugum jugum kamar gidan makoki sautin kukan Baban su Suhaima ne kawai yake tashi, damk'e hannun Sabeer Suhaima tayi jikinta ya fara rawa don masifar tsoron Mahaifin ta take kallonta Sabeer yayi cikin zuciyar shi yana tunanin mai Mahaifin su yayi musu da har Suhaima take jin tsoron shi haka gashi ya karanto tsananin tsanar shi kan fuskar Aliyu da Suhaima.


Gefe suka samu suka zauna sannan Baba Adamu yayi gyaran murya tare da cewa

"Alhamdullilah dukkan godiya sun tabbata ga Allah subhanahu wata'ala da ya bamu aron rai har zuwa wannan lokacin da ya sanya ni ganin wai Umaru ne ya dawo gida"

Baba Adamu ya k'arasa maganar tashi cikin tsananin mamaki da jimamin yanayin da suka ganshi aciki, cikin sanyin murya da tsantsar nadama Baban su Aliyu yace

"Bani da bakin kare kaina a wajen ku don hak'ik'a na cika azzalumi mara imani kuma butulu a wajen iyalina, nayi nadama dana sani mara adadi nasan na cika mara tausayi wajen mata ta Fatima da yarana Aliyu da Suhaima, bansan ta inda zan fara neman gafarar ku ba ku tausaya min duk wani jin dad'i na rayuwa bana jin shi kuma nasan duk hakk'in ku ne ku yafe min 'ya'ya n........ "

Bai k'arasa fad'in maganar ba saboda wani kuka da ya kubce mishi na nadama, duk wajen shiru akayi ana sauraren shi sai da ya tsayar da kukan dakyar yace
"Ina Fatima ku kaini inda take na nemi yafiyar ta don Allah, Aliyu Suhaima ku yafe min ba don ni ba don girman Allah "

Baba Adamu ne yace
"Umaru sai dai kayi hak'uri amman Allah yayi wa Fatima rasuwa tun washegarin da ka tafi cikin ma dake jikinta shima ya rasu "

Neman mik'ewa yake amman jikin shi babu k'arfi ya k'asa tashi sai kawai ya fashe da kuka yana cewa
"Na shiga uku yanzu ya zanyi da d'unbin tarin hakk'in Fatima da yake kaina me yasa ma na tafi na barku Fatima ki yafe min "

Babaa Lantana tana zubar da hawaye tace
"Umaru ka godewa Allah kafin Fatima ta rasu ta yafe maka duk abin da kayi mata"

Kallon Babaa Lantana yayi tare da kura mata ido kamar yau ya fara ganin ta yace
"Da gaske kike Fatima ta yafe min? "

"Tabbas Umman mu ta yafe maka don ita ba macuciya bace kuma ba azzaluma bace ta kasance mai hak'uri da yafe

Please Login or Register in order to submit comment