Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shi da basa tare dashi yanzu yanda ya kwana 2 kawai bai ga yaran nashi ba yana tsananin kewar su ina kuma Mumy da ta shafe wajen 2yrs bata sanya shi a idonta ba ko taji muryar shi dole ya gaggauta komawa gida wajen Mumyn shi.


Yana cikin wannan tunanin ne Suhaima ta shigo d'akin ta jima tana kallon shi baisan ma ta shigo d'akin ba, cikin kwanakin nan tana kula dashi da yanda yake cikin damuwa, cikin sanyin jiki ta k'arasa inda yake ta kwanta cikin jikinshi lokaci d'aya suka saki ajiyar zuciya, k'ara k'ank'ame ta yayi cikin jikin shi, kallon face d'in shi Suhaima tayi tace

"My dear har yanzu tunanin ne, ka fad'a min abin da yake damun ka please "

Shafa face nata yayi kafin yace
"Baby ina son ganin Mumy nah ne "
Murmishi ta saki mai sanyi kan tace
"My dear abu mai sauk'i kawai gobe ka shirya ka tafi, nima kaina ina son kaje kaga Mumy don nasan hankalin ta yanzu yana tashe "

"Yawwa Baby nah ki shirya mu je zan yiwa Daddy waya kada a kawo su twin's gobe muka je sai mu taho dasu "

"Lokaci yayi da zaka koma ka cigaba da rik'on company d'in ka my Dear kabar Daddy da nashi shima "

"Allah Baby da gaske kike zamu koma gidan mu? "

Mak'e kafad'a tayi cikin sigar wasa tace
"A'a ni dai zamu zauna anan duk weekend sai kazo kana ganin mu "

Ta6e fuska yayi yana son yin kukan shagwa6ar da aka kwana 2 ba'a yi ba yace
"Haba Baby baza ki tausaya wa d'an mijin ki ba, idan muka zauna waje d'aya sai yafi min kwanciyar hankali please please Baby nah"

"Uhm uhm wayo kake son yi min nak'i yarda "

Da ya gane tsokanar shi take nan ya cafkota tare da cewa
"Baby kin rainani da yawa don kin ga kwana 2 kin huta baki samawa su twin's k'annen su ba koh, bari yanzu zan baki ajiyar Baby nah "

Dariya sosai Suhaima take yi ganin yanda yayi, tashi yayi da sauri ya rufe k'ofar d'akin sannan ya dawo kusa da ita ya shiga aika mata da sak'onnin shi bata yi musu ba itama ta shiga mai da mishi da martani, sun jima suna faranta ran junan su kafin su yi wanka kuma ya shirya ya tafi masjid don sallahr la'asar yayin da Suhaima kuma ta zauna gyara jikinta.


Su Daddy na hanya dawo da Na'eem da Shaheed ne Sabeer ya kirawo shi a waya akan suyi zaman su gobe suna tafe zuwa gida don yaga Mumyn shi, sosai Daddy yaji dad'in haka nan ya shiga sanyawa Sabeer albarka daman da wannan niyyar ya taho na wajen rarrashin shi ya zo Mahaifiyar shi ta ganshi, bayan sun gama waya ne Daddy ya sanya driver ya koma gida sai ganin su kawai Mumy tayi cikin jin dad'i ta rungume Na'eem da Shaheed suma sai murna suke da ganin sun dawo wajen ta sai da ta gama murnar dawowar su sannan ta kalli Daddy tace

"Yana ga kun dawo sun bar min su ne? "

"A'a gobe iyayen su zasu zo sai su tafi dasu basanan yau ne "

Yana gama fad'in haka ya wuce ya fita, dad'i sosai Mumy taji idan sun zo zata nemi alfarmar su barmata su don Allah idan yaso ta sanya su schl duk hutu sai suna zuwar musu hutu wajen iyayen su.



Da daren ranar Sabeer yake yiwa Aliyu maganar zuwan su gobe gida nan Aliyu yayi mishi fatan alkhairi shi da Aunty Aliyah, cikin daren nan Sabeer kasa bacci mai nauyi yayi yana zumud'in gari ya waye ya ganshi a jikin Mumyn shi yana zuba mata shagwa6a son ranshi.


Washe gari bayan sun gama breakfast ne Aliyu ya sanya aka taro musu taxi har k'ofar gida, basu dad'e ba suka fito cikin shirin tafiya Sabeer na sanye da wata shadda ash colour yayin da Suhaima take sanye da wani lace ash&pink d'in flower's sunyi kyau sosai nan suka yi sallama da kowa kafin su shiga motar mai taxi yaja su tafi, Suhaima murmishin yak'e kawai take amman gabanta sai fad'uwa yake batasan me zata je ta tarar acan ba don haka duk a tsorace take.


Tun safe da Mumy ta tashi take faman zirga zirga a tsakanin kitchen da dining area tana shirya abincin bak'i, dariya ta bawa Daddy ma sosai ganin ko baccin kirki ta kasa don tana son kyautata musu Sosai su ji dad'i, don su ji dad'in bar mata Na'eem da Shaheed cikin zuciyar Daddy cewa yayi yaran ki ne zasu zo ba wasu bak'i daban ba.


Sai da ta gama shirya komai sannan ta barwa en aikin ta gyaran palon da na kitchen, tattara Na'eem da Shaheed tayi suka tafi Upstairs d'akin ta suka shiga nan tayi musu wanka tsaf tare da shirya su cikin kayan su irin d'aya jean ne blue sai pink d'in T-shirt sunyi kyau sosai takalman su ma pink ne ta fesa musu perfumes masu k'amshi, zaunar dasu tayi saman bed tare da basu iPad d'inta bayan ta kamo musu game tace
"Oya ayi game ban da fita kuma ban da rigima yanzu zanyi wanka "

Gid'a mata kai suka yi don hankalin su nakan wayar murmishi tayi ta shafa kansu sannan ta wuce toilet, agurguje tayi wanka ta fito ta shirya cikin wata gown black mai adon silver tayi rolling kanta da veil d'in rigar sosai tayi kyau bakace ita ta haifi Sabeer ba bayan ta fesa perfumes ne ta kamo hannun su Na'eem da Shaheed suka fito zuwa downstairs a palourn suka zauna tana zaune ta zubawa k'ofar palo ido so take kawai taga iyayen Na'eem da Shaheed.


Motar na tsayawa agaban gate d'in gidan sai da gaban Suhaima ya fad'i sosai fiye da lokutan bayan, hannun ta Sabeer ya rik'o ya rik'e k'am tare da cewa

"Relax Baby na ki kwantar da hankali babu abin da zai faru insha Allah ina tare da ke "

Jikinta a sanyaye ta gid'a kanta kawai don bakin ta yayi mata nauyi, fitowa suka yi daga cikin mota daman Yah Aliyu ya biya kud'in duk kuwa da Sabeer yak'i yarda da hakan amman sai da biya, mai taxi ya juya ya tafi kallon gidan Sabeer ya tsaya yi yana nan yanda yake sai gyaran shi da akayi sosai, tura k'ofar jikin gate yayi suka shiga hannun shi rik'e dana Suhaima jikinta ko'ina rawa yake na tsoro.

Da yake atime d'in rana tayi sosai kowa yana part d'in shi, maigadi sakin baki yayi yana kallon d'an lelen gidan d'an fillo, murmishi Sabeer yayi mishi aikuwa nan ya k'araso wajen Sabeer zai tsugunna ya hanashi bakin shi yak'i rufuwa yake gaida Sabeer da Suhaima yana murnar dawowar shi.

Sallamar maigadi yayi sannan suka wuce cikin gidan kai tsaye part d'in su ya shige dasu, door bell ya danna sau biyu zai danna na ukun ne aka bud'e k'ofar parlourn.


Kallon junan su suka tsayi cikin wani irin shauk'in so na tsakanin uwa da d'anta kowannen su idanun shi taf da hawaye, ji suke tamkar a mafarki hawayen eyes d'in Mumy ne ya sakko kan face d'in ta tana cewa
"My Son kai nake gani da gaske? "

K'arasa shiga cikin parlourn yayi still hands d'in shi cikin na Suhaima, d'ayan hannun shi ya sanya yana goge mata face d'in ta cikin rawar murya yace
"Mumy ni ne Sabeer d'in ki ba mafarki kike ba "
D'aga hannun ta sama tayi tare da cewa
"Allah Yah Allah nagode maka da ka dawo min da yaro na cikin koshin lafiya "

Tsugunnawa k'asa suka yi daga Sabeer har Suhaima wadda bata kula da ita ba yace
"Mumy I'm so sorry nasan na 6ata miki rai da yawa kiyi hak'uri ki yafe min please "

Dafa kanshi tayi kafin tace
"Son ni ce wadda ya kamata na rok'i ka yafe min don ni na aikata maka abubuwa da dama ka yafe min d'ana"

Ta k'arasa maganar tana had'a ido da Suhaima, da sauri Suhaima tayi k'asa da kanta gabanta na fad'uwa jikinta na rawa sosai don batasan me zata yi mata ba.

Cikin mamaki sosai Mumy tace
"Son daman kana tare da Suhaima "

"Yes! Mumy ina tare da Mata ta "
"Alhamdullilah Allah nagode maka da ka dawowa da d'ana farincikin shi "

Tashin Suhaima tayi ta rungume ta k'am ajikinta lokaci d'aya ta fashe da wani irin kuka tana fad'in Suhaima ta yafe mata, cikin hawayen farinciki da na tausayin Mumy Suhaima tace

"Mumy komai ya wuce wallahi na yafe miki tuntuni, mu ma ki yafe mana "

"Na yafe muku duk da babu abin da kuka yi min ni ce na zalunce ku"

"No Mumy ki daina fad'in haka komai ya wuce please "

Had'a su tayi ta rungume su sosai suna zubar da hawayen farinciki, Daddy ne yayi clapping hand's nashi duk suka jiyo suka kalle shi face nashi fal farinciki yace
"Alhamdullilah wannan rana itace nake addu'a koda yaushe Allah ya nuna min ita ina raye, hak'ik'a naji dad'i sosai nayi farinciki da haka "

Murmishi Mumy take duk da kuwa tears ne ke zuba daga eyes nata, nan Sabeer ya nemi yafiyar iyayen su suka yafe mishi tare da yi musu addu'o'i na fatan alkhairi acikin rayuwar su kowannen su cikin zuciyar shi fal farinciki.

"Abbah! Mamee! "

Suka jiyo voice d'in su twin's suna kwala musu kira da sauri suka taho inda suke da gudu suka rungume iyayen nasu suna masu farincikin ganin su, kusan suman tsaye Mumy tayi kallon Daddy tayi tana neman k'arin bayani a wajen shi.

Murmishi yayi kafin yace
"Jikokin ki ne yaran Son d'in ki ne da Suhaima "

Wayyo dad'i Mumy rasa inda zata sanya kanta tayi don farinciki da tsabar murna kawai zuwa tayi ta rungume Daddy tana kuka, tapping hands nashi yayi kan bayanta yana cewa

"Is okay Mata ta kukan ya isa hakan godewa Allah zaka yi "

"Daddy bansan me zance ba "
"Godewa Allah zaki yi kawai "



Suna cikin haka ne suka ji anyi magana da bakin k'ofar parlour ana cewa

"Hussein da gaske maigadi yake cewa Sabeer ya dawo gida "

Da sauri Sabeer ya juya ganin kakan shi Dr Ahmad d'an fillo ne yake maganar daganin shi kasan bashi da cikakkiyar lafiya, da gudu Sabeer ya k'arasa wajen shi ya rungume shi yana cewa

"Ni ne Sabeer d'an lelen ka na dawo gare ku kakanah "

"Alhamdullilah naji dad'in haka sosai Allah yayi maka albarka da ka dawo gare mu kada ka sake yi mana irin haka d'an lele don ka tasar mana da hankali sosai "

Cikin kaunar d'an tsohon da tausayin shi Sabeer yace
"Insha Allah bazan sake ba "

Ana cikin haka Hajjah Hauwaa tazo itama ta gama d'an kukanta na dawowar Sabeer, anan suke ganin Na'eem da Shaheed wai duk yaran Sabeer ne, Dr Ahmad d'an fillo baisan lokacin da ya rik'e hannun Suhaima yana zuba mata godiya ba Hajjah Hauwaa kuwa rungume ta tayi, nan family's na cikin gidan suka dunga shigowa zuwa ganin twin's da taya su Mumy murnar dawowar Sabeer gida.

Dr Ahmad d'an fillo kwasar twins yayi suka wuce part d'in su dasu don bazai iya barin su ba son yaran yake har ma ya zarta son da yake yiwa Baban su, sai after la'asar ne su Suhaima da Sabeer suka samu zaman cin abinci bayan sunyi wanka, suna gama ci Mumy takai Suhaima bedroom d'in ta don ta huta komai ganin shi Suhaima take tamkar a mafarki wai yau itace Dr Faridah take rungumeta ajikinta tana mata godiya sannan kuma family's d'in Sabeer suke murnar kasancewar ta acikin su kowanne yana farincikin ganin ta lallai komai da lokacin shi duk tsanani yana tare da sauk'i hak'uri yana da riba babba a rayuwa haka kuma ka rik'e addu'a baza ka ta6a ta6ewa ba a rayuwar ka............




_Masu yi min addu'a ta samun sauk'i Alhmdllh na samu lafiya, nagode sosai Allah ya bar zumunci_Ameen

Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[5/11, 12:16 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*




Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ


ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ


♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*




*THE END*




_Na sadaukar da dukannin shafin nan ga dukkanin masoya na da fan's d'in A SANADIN SON KI, ina gaida ku aduk inda kuke tare da yi muku fatan alkhairi cikin rayuwar ku_❣




*PAGE 115*





Kwanakin su biyu agidan suna zaune cikin farinciki Mumy tattalin Suhaima sosai tana bata kulawa haka sauran en uwan Sabeer ma haka duk wad'anda suka yi mata abubuwa marasa dad'i sunzo sun bata hak'uri kuma ta hak'ura daman bata rik'e su ba cikin zuciyar ta, Jiddah tayi farinciki yanda en uwanta suka kar6i Suhaima a yanzu matsayin suruka ta gaban goshi kowa tattalin ta yake.


Kwana su biyu agidan da dare Sabeer ya shigo side d'in Mumy ya gaji da kewar matar shi, kunya ce take sanya ta k'in zuwa side d'in shi koda ya nemi da ta zo inda yake, gajiya yayi da wannan abun ya tahi d'akin, yana shigowa d'akin tana fitowa daga bathroom d'aure da towel duk gashin kanta ya watsu a fuskar ta da wuyanta duk sun manne saboda ruwan dake jikinsu.

Suna had'a eyes ne suka tsaya kallon junan su cikin tsananin kewa da shauk'in junan su, kallon ta yake kamar ya had'iye ta anutse ya k'arasa inda take tsaye ya zuba hands nashi cikin aljihun jeans d'in dake jikin shi, lumshe eyes tayi tana mai jin fad'uwar gaba kamar yau ta fara kasancewa dashi, kamshin perfumes d'in shi ya cika mata hanci yana k'arasa wa wajen ya cire hannun shi daga aljihun ya zuba su saman kafadun ta cikin tattausar murya yace

"Baby haka zaki yi min koh? "
Cikin shagwa6a tace
"Me nayi maka kuma? "
"Lallai Baby har kin mance koh, idan na kirawo ki kizo bedroom d'ina bakya son zuwa why? "
"Ni Allah kunyar Daddy da Mumy nake ji amman kayi hak'uri "
Murmishi yayi kafin yace
"Okay tun da haka ne yau zamu koma gidan mu "
D'an waro eyes tayi sannan tace
"Wayyo my Dear dare yayi fah ka bari sai gobe please ".

"Okay naji amman sai na rage zafi tukunna ".
Kafin ta sake magana taji ya had'e ta da jikin shi sannan ya sanya lips nashi cikin nata wani soft kiss yake mata wanda yake ratsa kowanne jijiyar jikinta, kok'arin cire towel d'in yake ya mance ma a inda suke gaba d'aya ya tafi wata duniya ta daban sai ji yayi Suhaima ta kwace bakinta da gudu ta shige ta rufe, yayin da Sabeer ya bita da wani irin kallo jikin shi asanyaye ya k'arasa kan bed ya kwanta yana mayar da ajiyar zuciya.

Kwanciyar kenan Mumy ta shigo bedroom d'in agajiye daga hospital take kallon d'an nata take cikin kulawa tace
"Son ya haka lafiya? "
Cikin shagwa6a yace
"Mumy bakin rik'e min mata ba kunyar ku tasa ko side d'ina bata zuwa gaskiya gobe kisa a gyara mana gidan mu zamu koma nagaji "

Kallon shi Mumy take har sai da ya k'arasa maganar sannan tace
"Toh sarkin mara kunya kai kuma koh, babu inda zata je sai ta huta nan da koh 1month ne "
Azabure ya tashi kamar wanda kunama ta d'ana yace
"What! Mumy kashe ni zaki yi ne "

"Ba'a mutuwa sai kwanan mutum ya k'are mara kunya "
Juya kanshi yayi gefe yana k'unk'uni tare da turo baki, dariya sosai ya bawa Mumy don sauran kad'an ta kubce mata amman ta danne ta.
Ana cikin haka Daddy ya shigo d'akin lokacin Mumy tana kok'arin cire lapcot d'inta, taimaka mata yayi yana tayata cirewa sai kuma ya hango Sabeer yana 6a66ata fuska yace
"Ah! Son what wrong with U? "
Kauda kai yayi bai yi magana ba kallon Mumy yayi yace
"Sweetie nah me akayi wa Son ne? "

Bashi labarin komai Mumy tayi ta k'arasa da fad'in
"Shine fah ina gama fad'a mishi ya tsaya yana wani 6ata fuska "

"Gaskiya Mumy baki kyautawa Son ba a bashi matarshi please ina rok'an mishi wannan alfarmar "

Murmishi Mumy tayi kan tace
"Okay Daddyn Sabeer an gama gobe sai su koma gidan amman gaskiya za'a bar mana twin's "

Wani tsallen murna Sabeer ya doka tare da rungume Mumy yana cewa
"Indai twin's ne Mumy mun bar miki nasan zamu samu wasu very soon "

D'an bige bakin shi kadan Mumy tayi tare da cewa
"Baka da kunya wannan yaron "

Sosa kai yayi da d'an gudu ya bar bedroom d'in, dariya Mumy da Daddy kawai suka yi zuciyar su fal farinciki, Suhaima ma da take cikin toilet murmishi kawai tayi da yake duk tana jin su wani sabon son mijinta taji yana ratsa kowanne lungu da sak'o na zuciyar ta, sai da taji fitar Mumy da Daddy daga bedroom d'in sannan ta fito ta shirya.


Washe gari kuwa da safe Mumy ta tura en aikinta tare da Jiddah suka gyara gidan tsaf Jiddah na kula da yanda suke gyaran gidan, zuwa bayan sallah issha suka koma gidan nasu amman ban da su Na'eem da Shaheed don su Mumy sun kar6e su sun zama nasu.


Kula tattalin juna da kuma soyayya ta gaskiya ita tace jigon zaman lafiyar da Suhaima da Sabeer suka ginata cikin gidan su, zaman su suke cikin jin dad'i da kwanciyar hankali, Suhaima yanzu bata da wata matsala yanzu sai tason cigaba da karatun ta kuma tasan komai lokaci ne idan Allah ya nufa zata yi ne.




*AFTER 2 YEAR'S*



Abubuwa da dama sun faru acikin wad'annan shekarun ta 6angaren Yah Aliyu ya kammala karatun shi na mass com har ya samu aiki a freedom radio a 6angaren labarai, Sabeer kyautar gida yayi mishi don yafi samun sauk'in zuwa wajen aikin da kuma sabuwar mota amman sam Yah Aliyu yak'i kar6a sai dakyar aka shawo kanshi ya kar6a, tuni suka tashi suka dawo cikin gari wannan gidan nasu na kauye kuma suka barwa Mahaifin su bayan Sabeer ya k'ara gyarashi tare da gidan su Babaa Lantana da Baba Adamu, anan aka matsawa mahaifin su Suhaima da yayi aure babu 6ata lokaci ya sami wata mata wadda auren ta d'aya mijin ya rasu ko haihuwa bata yi ba don haka ya aureta suna zaman su cikin kwanciyar hankali.


Haka kuma sun samu en uwan Umman su (Fatima) wad'anda suka zo kauyen suna neman su har suka dace wajen samun Baba Umaru, a lokacin aka nemo su Aliyu da Suhaima suka zo don ganawa da family d'in su wad'anda basu ta6a gani ba, sunyi mamaki sosai na ganin irin manyan mutanen da suka zo a matsayin en uwan Umman su, labari aka zauna yi bayan ansha koke koke da neman gafarar juna inda suke ba da labarin su en asalin garin kd ne, ashe Mahaifin su ne maraya ne Mahaifin Fatima ya d'auke shi aiki matsayin drivern shi so daga nan suka fara soyayya babu wanda ya sani bayan ta gama schl ne aka had'a ta aure da wani d'an uwanta wanda bama a k'asar 9ja yake aiki ba tak'i yarda sai tace sai Umar shine kadai wanda zata aura a k'arshe suka gudu sai neman su akayi aka rasa, shine en uwanta suka yi fushi da ita sosai har suka k'i neman ta sai kuma daga baya zuciyoyin su suka yi sanyi aka fara neman su amman ba'a gansu ba sai yanzu Allah ya tak'aita musu wahalar su.

Atime d'in da suka ji Fatima ta mutu sunyi kuka sosai iyayen ta sun yafe mata abin da tayi musu, nan fah aka gabatar musu da Suhaima da Aliyu saboda tsabar murna rungume su suka yi, Suhaima da Aliyu sunji dad'in ganin family d'in su sosai, sai yamma suka fara shirin tafiya Aliyu yayi musu alkawarin zasu zo har kd d'in, nan suka tafi kamar kada a tafi haka suke ji.



Daren ranar Suhaima take bawa Sabeer labarin komai ya tayata murna sosai, bayan sati d'aya suka shirya suka tafi kd sosai suka yi mugun mamakin ganin irin had'add'un gidajen su ashe manyan en boko ne, en siyasa da kuma en kasuwa da yake Umman su ita kadai ce mace duk maza ne yayyannin ta wajen su bakwai kuma suna raye har da yaran su manya ma.

Tar6a sosai suka yi musu ji suke kamar su had'iye su don so tattalin su suke sosai har sukayi kwanak biyu aka zagaya dangi sosai sannan suka dawo gida Suhaima har da kuka ta na rabuwa dasu sun shak'u da Hajia mahaifiyar Umman su sosai.



Bayan dawowar su ne Jiddah ta haifi d'anta namiji ansha suna sosai su Suhaima, acikin lokacin ne ita ma Suhaima ta samu ciki sai dai mai sauk'in laulayi ne ba kamar cikin Na'eem da Shaheed ba, Sabeer yaji dad'i sosai sai kula yake bata da tattali kamar shine cikin farko haka ma su Dr Faridah ba'a barsu a baya ba suma sosai suke kulata, haka ta cigaba da rainon cikinta cikin kwanciyar hankali.


After 9 months ne Allah ya sauki Suhaima lafiya ta haifi twince d'inta dukka mata tsakanin Sabeer, Mumy, Daddy da Dr Ahmad d'an fillo bansan wanda yafi murna ba acikin su, bayan sun dawo gida nan fah gida ya cika da en uwa da abokanan arzik'i sai taya murna ake na samun wannan karuwar da akayi, washe garin haihuwar ne mutan kd suka taho da abubuwan arziki sosai sai lokacin Mumy take ganin en uwan Suhaima sosai tasha jinin jikinta don tasan bazasu nuna musu komai ba nan zuciyar ta ya dad'a kyashin halinta tabbas ba'a son wulakanta d'an adam don bakasan irin baiwar da Allah yayi mishi ba.


Ranar suna yaran suka ci sunan Dr Faridah da kuma Fatima suna kiran su da Shaheeda da kuma Afnan, sosai ansha suna da walima an kashe kud'i sosai a wannan sunan sai fatan Allah ya rayasu.


Haka lokaci ya cigaba da tafiya har sukayi arba'in duk family na Suhaima sai da suka je sosai sai da sukayi wurin 1week a kd Hajia sai da ta gyara jikarta sosai sannan suka dawo gida, twince na da 5months Aunty Aliyah ta sake haihuwar mace wadda taci Sunan Suhaima Yah Aliyu ya mayar da sunan k'anwar shi nan aka sha suna aka watse.


Duk wani jin dad'i da kwanciyar hankali Suhaima tana samun shi wajen gwarzon mijinta Sabeer, itama ta bashi duk wata kulawa da ta kama zaman su suke cikin jin dad'i, Na'eem da Shaheed tuni Dr Faridah ta sanya su a tsadaddiyar wata prvt schl sai hutu suke zuwa gidan iyayen su don har islamia da tahfiz duk an sanya su ban da extra lesson da ake musu a gidan masha Allah kuma yaran brain nasu naja gasu nutsattsu basu da hayaniya sosai.



Bayan wasu en shekaru Shaheeda da Afnan sunyi wayo sosai har an yaye su, a lokacin Sabeer ya samawa Suhaima schl a Buk tana karantar medicine sosai Suhaima ta nuna farincikin ta haka ma Yah Aliyu yaji dad'in barin Suhaima da Sabeer yayi ta cigaba da karatu har godiya yayi wa Sabeer.

Ta 6angaren Yah Aliyu kuwa Alhmdllh duk wani bud'i yana samu ta 6angaren aikin shi, gashi sun had'a hannu da Sabeer sun bud'e wani tafkeken gidan gona a kauyen nasu Suhaima da kuma wurin hutawar su inda sunje sosai wajen yayi kyau sun d'ibi ma'aikata suna biyan su, sosai en kauyen sun ji dad'i hakan don an rage masu zaman banza babu sana'a.


Duk sunje sunyi aikin hajji da Omarah sun yawata k'asashe sosai musamman Suhaima ma don Sabeer yace honeymoon d'in da basu yi ba suna farkon auren auren yanzu zasu yi shi nan suka zube Shaheedah da Afnan hannun su Dr Faridah suka wuce honeymoon d'in su, sai da sukayi wajen wata hud'u sannan suka dawo gida har da tsarabar ciki.


Tun safe take faman zirga zirga a tsakanin kitchen saboda yau Sabeer zai dawo daga tafiyar da yayi ta tsayin wata 1, ta gama had'a mishi abubuwan ci dana sha ta gyara ko'ina sannan ta barwa er aikinta wanke wanke, upstairs ta haye ta shiga d'akin su Shaheedah wanka tayi musu ta shirya su cikin wasu English wears na gown sai dai tsayin ta iyakar gwiwar

Please Login or Register in order to submit comment