Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Aliyu zan tafi gida ana nema na, zan dawo gobe da safe na mayar da ku gida Allah ya bawa Aunty Aliyah lafiya "

Kallon ta Aliyu yake gaba d'aya ya rasa ma mai zai ce mata dakyar ya iya bud'e bakin shi yace
"Amin Jiddah nagode sosai da karamcin ki gare mu, nasan kina son tafiya da Suhaima koh? "

D'an murmishi tayi tare da cewa
"Haba Yaya Aliyu taya zan tafi da ita bayan itace ke kula da Aunty babu komai wlh nasan lalura ce taja hakan "

Girgiza Aliyu yayi kafin yace
"Idan lokaci bai k'ure ba ki d'auki Suhaima kuje gida ta d'ebi kayan da zata yi amfani dasu, sai ku taho da Babaa Lantana ta zauna da mu anan zuwa gobe "

Duk da Jiddah taji dad'in abin da Aliyu yace mata amman sai da ta sake cewa
"Ka barshi Yaya yanzu babu lokaci sauri nake sai kirana ake lokacin kamu yayi amman insha Allah gobe zan dawo sai mu tafi tare "

"Shikenan Jiddah Allah ya biya ki, Allah ya sanya alkhairi "
"Amin Yaya, amman godiyar ta isa haka "

Murmishi suka yiwa junan su kafin Suhaima da Aliyu su tashi rakiyar Jiddah har zuwa compound d'in hospital d'in suka sake yin sallama kafin ta shiga mota driver yaja motar su tafi, Aliyu da Suhaima suka dawo cikin room d'in da aka kwantar da Aunty Aliyah har yanzu dai bacci take bata farka ba zama suka yi jigum jigum, sai jefi jefi suke d'an ta6a hira sannan nurses suna shigowa duba Aliyah, da dare sai da Jiddah ta aiko driven da suka zo tare da takeaway na abinci sai kayan tea acikin leda bak'a 'yar babba, sosai Aliyu da Suhaima suka ji dad'in haka daman a lokacin yake tunanin fita neman masu abin da zasu ci sai gashi, nan Aliyu ya sake jinjina k'aunar da Jiddah take yiwa Suhaima dasu kansu basu da abin da zasu biyata abin da tayi musu sai dai addu'ar fatan alkhairi.


Washe gari da safe Aliyah ta tashi jikin ta da sauk'i sosai ta samu k'arfin jikin ta, tana cin abinci sai dai wani ya zauna wani ya fito amman sosai sun ga sauk'i fiye da lokacin da suka zo jiya tun da tana tashi da kanta ba tare da an taimaka mata ba.


Ganin haka ya sanya likita basu sallama tare da rubuta mata maganin da zata nayin amfani dashi, sannan ya fad'a musu idan taji wani canjin yanayi a jikinta ta dawo hospital d'in tun da file Jiddah ta sanya aka bud'e mata.

K'arfe 11:25 na safe sai ga Jiddah ta shigo room d'in sosai taji dad'in ganin Aunty Aliyah jikin da sauk'i, bayan an gaisa kuma suka fito daga cikin asibitin zuwa inda motar da Jiddah tazo da ita, yau babu driver ita d'aya tazo da kanta tayi driving, bayan sun shiga motar ne suka d'auki hanyar zuwa k'auyen nasu.

Bayan sun isa gida ne a gurguje Suhaima ta gyara gidan tsaf tana kok'arin d'ora girki Babaa Lantana ta shigo gidan ta kar6in aikin tare da ce mata ta shirya su tafi, aikuwa nan ta shiga wanka bayan ta fito ne ta shirya jikin ta a lokacin Jiddah har ta gama had'a mata kaya a cikin bag d'in da ta bata suka fito zuwa tsakar gidan.

Inda Yaya Aliyu da Aunty Aliyah suke zaune zama suka yi suma a k'asan tabarmar da suke kai, nasiha sosai mai ratsa jiki Yaya Aliyu yayi wa Jiddah na irin rayuwar da zata shiga nan da kwana d'aya, haka Babaa Lantana ma tayi mata nasiha sosai Aunty Aliyah ce babu k'arfin yin magana sai murmishi da take mata cikin zuciyar ta tana mata addu'a.

Daga k'arshe Jiddah ta fito daga gidan da bag d'in Suhaima a hannun ta, saboda taga alamar kamar akwai abin da suke son fad'a wa Suhaima, aikuwa tana fita Yaya Aliyu da Babaa Lantana suka yi mata nasiha na ta tsare mutunci kanta ban da kula samari da rawar kai komai ta gani ta kawar da kai tana yin alkunya kodan saboda Jiddah sannan Yaya Aliyu daga k'arshe ya gargad'i ta da babbar murya kada tayi shiga matsatstsiya na sutura, ta suturce jikin ta matsayin ta na 'ya mace.

Bayan sun gama mata nasihar ne Yaya Aliyu ya bawa Suhaima kud'i masu dama sannan yace
"Wannan kud'in ki nemi abin da zaki siyawa Jiddah gift's dashi ki rage wasu kuma don ki rik'e a hannun ki "

Aunty Aliyah cikin muryar marasa lafiya tayi wa Suhaima magana da ta shiga d'akin ta ta d'auko mata wani box cikin drower d'in gadon ta, nan Suhaima taje ta d'auko ta mik'a mata kar6a tayi ta bud'e sai ga wata sark'a, d'an kunne, zobe da warwaro guda uku sai sark'ar k'afa masu kyau sai kyalli suke da d'aukan ido farare ne.

"Ki bawa Jiddah kice mata ba yawa tayi hak'uri "
Cewar Aunty Aliyah kenan cikin sanyin murya, rik'e hannun ta Suhaima tayi tana murmishi tace
"Toh Aunty zan bata insha Allah "


Daga haka Suhaima ta tashi haka ma Yaya Aliyu suka fito zuwa nan kofar gida inda Jiddah take zaune cikin mota, shiga seat d'in gaba Suhaima tayi tare da rufe k'ofa, nan Jiddah tayi wa motar key suka fara tafiya sannan Yaya Aliyu ya buga machine d'in shi yana binsu a baya don ganin gidan su Jiddah saboda zuwa d'auko Suhaima.

"Malama da haka zamu tafi kina min hawaye salon ace na sato ki "
Fad'in Jiddah cikin sigar tsokana,
"Kewar gida na fara yi Jiddah tun da nake ban ta6a zuwa wani wajen kwana ba sai yau"
Cewar Suhaima tana kwantar da kanta a jikin kujera.
"Lallai da drama duk lokacin da kika yi aure za'a kai ki gidan miji kenan, tun da shi fatan zama na har abada ake "
D'an zaro ido Suhaima tayi tare da cewa
"Tabbb ni fah auren ma baya gaba na Jiddah, har yanzu ban ta6a tsayawa da wani ba da sunan zance ba "
"Lallai yarinya da sauran ki kina tunanin Yaya Aliyu zasu zuba miki ido babu aure? "
D'an marairaice fuska Suhaima tayi tana cewa
"Ni fah da za'a bi tason ra'ayi na karatu zan cigaba da yi wlh tun da gaba d'aya ni yarinya ce nawa na ke "

Hararar wasa Jiddah tayi wa Suhaima kafin tace
"Ai yanzu tsab za'a yi miki aure ki zauna akwai wad'anda basu kai ki ba ake musu su zauna lafiya ma "

D'an shiru suka yi na 'yan minute's kafin Jiddah tace
"Ni kuwa Suhaima wane irin Namiji kike son aura i mean halayyar shi, yanayin shi and everything da kike son mijin ki ya kasance? "

Shiru Suhaima tayi na tunani kafin ta sauke ajiyar numfashi tace
"Ni a tsarin rayuwa ta bana son auren miji mai kudi da yawa nafi son auren talaka dai dai ni wanda bazai wulak'anta ni ba da 'yan uwana ba ko dangin shi su na wulakanta mu ba, kuma bana son auren miji mai irin kyan nan da yawa ina da kishi wallahi bazan iya jure ganin 'yammata suna kai mishi farmaki ba, sannan bana son mai saurin fushi,ina son kuma mijina ya kasance mai ilimi both side addini da boko kuma...... "

"Kaiii Suhaima idan kuma Allah ya baki handsome mai kyau da kudi fah, kamar yanda kike da kyau ke ma? "

"Hmmm bana fatan haka Jiddah na fison talaka d'an uwana, ni koda misali wani mai kud'in zaice yana sona bazan amince mishi ba wulak'anci zan tayi mishi har ya hak'ura ya bar ni, nasan ma bazai jure wulakanci ba zai rabu da ni "

Dariya sosai Jiddah tayi kafin tace
"Koda wanda kika watsa mishi ruwa ne idan ya dawo yace yana son ki fah ya zaki yi? "

"Tabbb ai korar shi zanyi balle nasan bazan sake ganin shi ba har abada ma"

Cikin zolaya Jiddah tace
"Kika sani ko shine mijin naki Allah ya kawo miki "
Dukan wasa Suhaima ta kaiwa Jiddah da sauri ta goce tana dariya tare da cewa
"Haba Besty daga wasa sai duka kin mance ni amarya ce zan had'a ki da my sweet darling fah"

D'an murmishi Suhaima tayi kawai ta d'auki phone d'in Jiddah tana kallon pic's d'in ciki, da haka har suka k'arasa gidan su Jiddah amman daga waje tayi parking bata shiga cikin gidan ba, Wow! abin da Suhaima tace kenan ganin irin unguwar su Jiddah ta manyan masu kud'i ce ganin gidan su Jiddah kuwa sai da gaban Suhaima da na Yaya Aliyu ya fad'i.

Anya basu yi gangancin sake wa da Jiddah ba irin wannan k'aton gidan daga ni Iyayen ta ba k'aramin masu kud'i bane, lokaci d'aya jikin su yayi sanyi sosai, nan Jiddah ta k'arasa wajen Yaya Aliyu suka yi sallama bayan ta tabbatar mishi da jibi da yamma yazo d'aukan Suhaima idan yazo ya kirawo ta a waya daga haka suka yi sallama ya buga machine d'in shi ya tafi jiki a sanyaye yana dana sanin sakewa da Jiddah da suka yi har haka, kada a wulak'anta mishi k'anwa ko kuma su bud'e mata ido da rayuwa amman da ya tuna irin tarbiyyar Jiddah sai ya d'an ji sanyi cikin zuciyar shi but still jikin shi a sanyay dakyar yake tuk'a machine d'in yana addu'a cikin zuciyar shi Allah ya tsare mishi Suhaima har taje ta dawo lafiya...



Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz

Dis page is dedicated to
Ayusher Ilias my Namecy
Biebie dee tawa
My Zeee yabour
Asy khaleel, kirkin ku daban ne ina yin ku sosai sister's Allah ya bar zumunci a tsakanin mu ❣



PAGE 32-33




Bayan tafiyar Yaya Aliyu ne Jiddah ta shigo motar tayi mata key maimakon su shiga gidan sai Suhaima taga ta juya sun bar unguwar gaba d'aya, cikin tsokana Jiddah tace
"Baki ji tsoro ba kada na siyar da ke naga baki tambaye mu ina zamu je ba "

D'an murmishi Suhaima tayi tare da cewa
"Na yarda da ke ne sosai Jiddah nasan son da kike min bazai sa ki cutar da ni ba "

"Haka ne tawan Allah ya bar mu tare har 'ya'ya da jikoki, waiii ya kaga Suhaima da jikoki suna cewa goggo Suhaima "
Dariya kawai suka yi adaidai lokacin Jiddah ta k'araso inda zasu je wani katafaren shagon yin gyaran jiki, saloon, manicure and pedicure da kuma make-up sai lalle, parking Jiddah ta samu tayi suka fito zuwa cikin shagon sosai wajen ya burge Suhaima, matar wajen tana ganin Jiddah ta fara washe baki da alama ta saba zuwa wajen.

Babu 6ata lokaci Jiddah ta fad'a wa matar abin da za'a yi wa Suhaima, aikuwa nan suka shigar da Suhaima wani room suka farayi mata gyaran jiki na dilka sosai suka tsaya suka gyara Suhaima sun san zasu samu kudi masu tsoka, bayan an gama gyaran jikin aka yi mata gyaran su farce sannan aka dawo kan lalle daga k'arshe kuma aka gyara mata gashi wanda basu sanya mata relaxer ba cos gashin Suhaima yana da tsantsi irin na asalin fulani sai suka wanke mata kan da kalolin shampoos and conditioner different color's, sannan suka busar mata da dogon gashin ta da hand dryer tukunna suka gyara mata in style.

Kyan da Suhaima tayi 6ata lokaci ne wajen fad'ar shi tayi kyau sosai tamkar ba ita ba, har wasu kayan Jiddah ta bata ta sanya wata milk d'in gown mai adon light green sai veil light green shima nan ta sanya kayan aka yi mata light make up sosai tayi kyau, rolling d'in veil d'in suka yi mata akanta ba k'aramin had'uwa tayi ba idan kaga Suhaima ka d'auka irin mai kud'in nan ce ba daga k'auye ta fito ba.

Ita kanta Jiddah bata zata haka Suhaima take ba sai yanzu hankalin ta ya kwanta tasan dai ba lalle iyayen ta su gane daga inda Suhaima ta fito ba, kuma ba laifi kan Suhaima a waye yake bata da dahun kai, nan Jiddah ta biya kud'in suka fito daga shagon kai tsaye gida suka nufa.

Horn Jiddah tayi gateman ya bud'e mata kofa ta shigo ciki a parking lot tayi parking tukunna suka fito daga motar, sakin baki da hanci Suhaima tayi ganin irin girman gidan su Jiddah gashi part part ne sosai gidan ya birge Suhaima amman bata kuma aha'awar zaman irin cikin gidan nan don tasan dole a samu masu wulak'anta mutane, ta6o ta Jiddah tayi tana murmishi tace
"Alhamdulillah yau Allah ya nufa Suhaima zata zo gidan mu, ina cikin farinciki yau sosai, Suhaima ga gidan mu nan kina ciki yau anan aka haife ni na girma, daman na fad'a miki gidan mu muna da yawa don kakan mu da iyayen mu duk a ciki muke zaune "

Gid'a kai Suhaima tayi tana k'ak'alo murmishin yak'e kafin tace
"Masha Allah wannan gidan naku yayi kyau sosai Jiddah "
Kamo hannun Suhaima tayi tare da cewa
"Thank U my dear "
D'auko bag d'in Suhaima tayi suka nufi wani part, duk taku d'aya da Suhaima take sai gabanta ya fad'i sosai gaba d'aya a tsorace take kamar wadda za'a sace haka take jin ta.


Suna shiga cikin k'aton parlourn wani sanyin Ac da k'amshin turare ya bugi hancin Suhaima ko'ina tsab dashi duk da mutanen da suke zazzaune cikin parlourn kuwa, kusan gaba d'aya mutanen kallon Jiddah da Suhaima suke.

Tuni Suhaima ta fara tsarguwa da kallon, wata matashiyar budurwa ce kamar sa'ar Jiddah ta taso da gudu ta rungume Jiddah tana cewa
"Ga amarya ga amarya nan ta dawo, ina kika shige muna ta neman ki? "
D'an murmishi Jiddah tayi tare da cewa
"Na d'an fita ne wani wajen "
Kallon budurwar tayi tare da cewa
"Zahra meet my friend Suhaima Omar, Suhaima meet my sister Zahra 'yar gidan K'anin Abban mu ce "

Cikin murmishi Suhaima tace
"Ina yini? "
Wani banzan kallo da Zahra tayi wa Suhaima sai da ta kusan zubewa a k'asa saboda rawar da jikin ta ya fara, wani banzan tsaki Zahra ta saki tare da hararar Jiddah tace
"Kefa tsiyata kwashe kwashe ne dake ina kuma kika samo wannan villagers girl d'in? "

Dumm gaban Suhaima da Jiddah ya fad'i, duk gyaran da ta kashe kudi tayiwa Suhaima don kada su gane daga inda ta fito sai da Zahra ta gane, wannan maganar a cikin zuciyar ta Jiddah tayi bayan ta gama k'arewa Suhaima kallo inda taga ita bata hango makusa ba sai ma kyan da Suhaima tayi, amman sai ta dake ta harari Zahra tare da cewa
"Ni fah bana son iskanci Zahra wannan fa friend d'ina ce tare muka yi schl itace fa Suhaiman da nake baku labari"

Wata shegiyar dariya Zahra ta saki tare da nuna Suhaima da d'an yatsa tace
"Dis villagers girl ce kuka yi schl tare kin ma raina min hankali nafa sanki da kwashe kwashe "

Haushi ne ya turnik'e Jiddah a fusace taja hannun Suhaima wanda idanun ta sun ciko da kwalla taf suka nufi hanyar da zata kai Jiddah part d'in Umman ta yayin da Zahra da sauran mutane wanda suka karkata hankalin su da jin hirar tasu tuntsire wa da wata irin dariyar ta rainin hankali.

Wani parlour suka dad'a shiga tsayawa Jiddah tayi tare da jiyowa ta kalli Suhaima tace
"Don Allah Suhaima kiyi hak'uri da abin da Zahra tayi miki bata kirki ne "

Mayar da kwallar Suhaima tayi tare da kwakwalo murmishi yak'e tace
"Kada ki damu Jiddah duk abin da akayi min zan d'auke kai saboda ke "
Rungume ta Jiddah tayi cikin farinciki da jin abin da Suhaima tace mata
"Thank U so much dear "


"Jiddah ke da wane? "
Da sauri Jidd ta saki Suhaima jin maganar Umman ta wani kallo Umman take yiwa Suhaima kamar irin kallon da Zahra tayi mata.

Da murmishi akan fuskar Jiddah taja hannun Suhaima zuwa kusa da Umma tace
"Umma ni da Suhaima ne, itace wadda nake baki labari, Suhaima wannan ce Ummana"

Da sauri Suhaima ta durk'usa k'asa cikin girmama wa tace
"Umma ina yini? "
"Lafiya "
Cewar Umma cikin halin ko inkula daga k'arshe ma cewa tayi
"Jiddah kiyi sauri ki wanka yanzu mai makeup zata zo kinsan yau ne dinner wadda Hajia Faridah ta shirya na family koh"

Tana gama fad'in haka ta wuce ko kallon inda Suhaima take bata sake yi ba ta wuc abinta cikin tak'aici Jiddah tabi bayan Umma da kallo kafin ta dawo hankalin ta kan Suhaima da har yanzu take durk'ushe ta kasa tashi saboda mugun sanyin da jikinta yayi na abin da ta fara cin karo dashi tun shigowar ta gidan su k'awarta Jiddah.


A lokacin hankalin Suhaima ya tashi sosai ta d'auka Umman Jiddah zata kar6e ta da fara'a ba kamar Zahra ba, shi yasa tayi wa Jiddah alk'awarin kauda kai daga abin da akayi mata, amman fah Jiddah tayi mata abubuwan da zata iya jure duk wani cin kashin su akanta na tsayin kwana biyu daga lokacin da tafi gidan su babu wanda zai sake ganin ta balle har yayi mata kallon banza.

"Kiyi hakur..... "
Jiddah ta fad'i hakan tana d'ago Suhaima fuskar ta da tarin damuwa sosai, da sauri Suhaima ta toshe mata baki da tafin hannun ta tare da k'ak'alo murmishin dole tace
"Kada ki bani hak'uri Jiddah me akayi min babu komai kada ki damu please "

Girgiza kai Jiddah kawai tayi tare da rik'o hannun ta tana cewa
"Mu tafi bedroom d'ina ki huta kiyi hak'uri da halin 'yan gidan mu kusan haka suke "
Gaban Suhaima ya sake fad'uwa da jin abin da Jiddah ta fad'a anya zata iya zaman gidan nan kuwa...



Aishat A Muh'd 🏌🏻‍♀
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz




PAGE 34-35




Hannun ta d'auke da cup wanda coffee ne aciki ta shigo cikin bedroom d'in turus ta tsaya ganin shi a zaune ya zabga tagumi, ta rasa abin da yake damun d'an nata gaba d'aya ya canja tun ranar da ya doki Fadilah, ajiye cup d'in tayi saman center table d'in k'arasa wa inda yake tayi har zuwa lokacin Sabeer baisan da zuwan Mumyn nashi kusa dashi ba, girgiza kawai tayi tana kallon shi kafin ta sanya hannun ta d'ora shi tayi saman kafad'ar shi tace

"Son tunanin me kake? Me yake damun ka ne kwananan "
Girgiza kai yayi tare da cewa
"Nothing Mumy "
Zama tayi kusa dashi tana mai kamo hannun shi cikin nata kallon shi take cikin kulawa tace
"Son baka da wanda zaka fad'a wa damuwar ka duk duniyar nan sama da ni, ka sanar dani ko zan iya baka shawara please "

Cikin gajiya da maganar Mumy yace
"Nace miki babu komai ki rabu da ni please "
Ya k'arasa maganar da d'an tsawa kad'an.
"Shikenan Son koma mene Allah ya yaye maka "
Cikin zuciyar shi ya amsa da Amin.
"Ga coffee kasa na lura tun breakfast baka k'ara cin wani abin ba, idan ka gama ka shirya ka kayan ka saman bed kasan yau ne dinner na sister d'in ka Jiddah kuma kowa na family zai je don haka ina buk'atar ganin ka please Son "

Shiru yayi mata bai kulata ba itama bata sake bi ta kanshi ba ta wuce ta fita don idan da sabo ta saba da shariyar Sabeer wani lokacin musamman idan yana cikin damuwa bai fiye son magana ba.

Mumy tana fita ya zame ya kwanta kan sofa yayi matashin kai da hannayen shi, idanun shi lumshe su yana tunanin Suhaima sosai yake mamakin yanda yarinyar ta tsaya mishi cikin zuciyar shi, shi baisan so ba amman da alama ya fad'a son wannan yarinyar, dummm gaban shi ya fad'i da ya tuna yanda 'yan uwanshi da iyayen shi suka tsani talaka balle ita a k'auye ma take, yanzu shi ya zai yi zuwan shi wajen uku k'auyen ko mai kama da ita bai gani ba ya rasa yanda zai yi.

Son da yake mata bazai iya hak'ura da ita dole ne yasan yanda zai 6ullowa al'amarin, bayan bikin Jiddah dole ya koma k'auyen ya neme ta, zai nuna mata so sannan zai bawa iyayen ta kud'i sosai ya basu gida da mota da jari sosai yanda bazai samu matsala ba ta 6angaren iyayen shi idan suka ga iyayen ta masu kud'i ne, wani murmishi ya saki na kamar wanda ya samu nasara ma sai lokacin hankalin shi ya kwanta, kiran sallahr mangarib ne ya katse mishi tunani, toilet ya shiga yayi alwala ya fito kai tsaye masallaci ya wuce.


Babban hall ne wanda ya k'ayatu da decorations masu kyau da k'ayatuwa wajen ya tsaru yayi kyau sosai, ga haske tamkar ba dare ba sanyi Ac ta ko'ina ban da k'amshin tsadaddun turaren jikin manyan masu kud'in da suke zaune a wajen kamar anyi 6arin turare a wajen.

Manyan hamshak'an mutane ne masu kud'i sosai a wajen ansha kwalliya ta kece raini ga tsadaddun sutturu da aka sanya mutane suna zazzaune a wajen da aka tanadar musu, slow music ne ke tashi kawai a wajen duk mutane an hallara, family d'in Jiddah gasu nan ga friends na iyaye dana amarya sai na yayyanin amarya dana k'anen ta abin dai ya tsaru gwanin sha'awa kowanne da kalar ankwan su, haka 6angaren dangin ango gasu nan da nasu ankon daban suma sunyi kyau sosai.


Amarya da ango ake jiran shigowar su babu dad'e wa mc ya fara sanar wa shigowar ango da amarya kowa ya nutsu ya zubawa kofar shigowa kallo don ganin shigowar amarya da ango.

Cikin takun k'asaita da nutsuwa Jiddah da angon ta khaleel suka shigo hannun su sark'e da junan su, Jiddah tana sanye da wata farar gown har tana jan k'asa sai ash head da ta sanya yana da kwalliyar flowers silver ajiki pose da hill nata dukka ash ne masu kwalliyar silver ajiki tayi kyau sosai abin ta, haka angon ma Khaleel yasha shadda ash colour sun yi matukar kyau da dacewa da junan su, sai watsa musu wasu fararen furanni da red ake yi.

Bayan su kuma Suhaima ce tasha light pink na gown sai head nata pink mai d'an duhu tasha makeup tayi matukar kyau tamkar ba Suhaima ba, ba wanda zai ganta ya zaci daga k'auye ta fito tama fi 'yan birnin kyau a wajen don ba k'aramin haskawa tayi ba tamkar itace ma amaryar ba Jiddah, don kallo dawowa yayi kanta abin da yasa duk ta dibirbice ta rasa inda zata yi saboda idanun mutanen da suke kanta sai murmishin yak'e take.


Da haka ta samu waje ta zauna bayan ango da amarya sun wuce wajen zaman su, nan aka fara gabatar da dinner cikin nutsuwa da wayewa, gaba d'aya Suhaima a tak'ure take saboda bata saba zuwa irin wad'annan wuraren ba, har zuwa lokacin da amarya da ango suka fito domin taka rawa nan 'yan uwa da abokanan arzik'i suka fito domin yi musu lik'i.

Dr Faridah ce ta fito filin wajen nan mutane suka bata hanya ta wuce zuwa inda su Jiddah suke tsaye ita da angonta suna taka rawa a nutse, bag d'in hannun ta ta bud'e ta fito da bandir d'in 1k ta fara watsa musu tamkar bata san zafin kud'i ba sai da ta gaji tukunna ta bar wajen.

D'ago kan Suhaima yayi dai dai da barin Dr Faridah wajen aikuwa suka had'a ido wani irin bugawa zuciyar Suhaima tayi da k'arfin gaske haka ma a 6angaren Dr Faridah d same abin da Suhaima taji haka taji itama, amman sai ta kawar da kanta daga barin kallon ta cikin zuciyar tana tunanin irin wannan kyan na yarinyar da bata ta6a ganin ta ba sai yau, gashi ta d'an birgeta kad'an da taga duk da kyan da take dashi but bata da rawar kai irin na 'yammatan da suka waye sosai kafin kuma watsar da tunanin ganin Suhaima ta cigaba da sha'anin gaban ta.

Har zuwa lokacin da aka buk'aci amarya da ango su yanka wedding cake nasu, nan 'yan uwan amarya

Please Login or Register in order to submit comment