Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da gyad'a ga ainahin man k'uli da kuma yajin da aka daka da kayan k'amshi da tafarnuwa, muk'ut Jiddah ta had'iyi yawu saboda tana son dambu sosai, dariya ce ta kubce wa Suhaima ganin yanda Jiddah take had'iyar yawu don kawai taga dambu.

Hararar wasa Jiddah tayi mata tare da cewa
"Tun da dariya kike min na fasa baki cup cakes d'in da nayi miki Aunty Aliyah da Yaya Aliyu zan bawa "

Danne dariyar ta Suhaima tayi tare da rik'o hannun Jiddah tana cewa
"Haba tawan just kin ban dariya ne ganin yanda kike had'iyar yawu but na daina"

Gid'a kai Jiddah tayi kawai saboda ta cika bakin ta da dambu ba damar tayi magana har wani lumshe ido take saboda dad'in da yayi mata, hannu Suhaima takai kan jug ta zuba mata so6on a cikin cup ta ajiye mata kusa da ita, sannan ta koma wajen wardrobe tana cigaba da gyaran kayan suna d'an hira da Jiddah jefe jefe har ta kammala cin abincin ta taya Suhaima k'arasa gyaran kayan, bayan sun gama suka fita zuwa tsakar gidan inda Aunty Aliyah da Yaya Aliyu suke zaune a saman tabarma shigowar shi kenan babu dad'e wa, nan suka gaisa da Jiddah tare da yi mata fatan alkhairin auren da zatayi tare da 'yar nasiha, sosai Jiddah taji dad'in haka tare da yi mishi godiya duk jikin ta yayi sanyi.

Suna nan zaune akayi kiran sallahr mangarib nan Yaya Aliyu yayi alwala ya wuce masjid, yayin da Suhaima, Jiddah da Aunty Aliyah suka yi nasu alwalan tare da gabatar da tasu sallahn.


Bayan sun idar ne da sallahr Jiddah tayi wa driver d'in ta waya, babu dad'e wa yayi sallama a kofar gidan Jiddah ta tashi taje inda yake tsaye kofar gida ta kar6i abin da ta buk'aci ya kawo mata wata 'yar bag ce black mai kyau madaidaiciya wadda zata cinye kayan mutum set 5 a ciki.

Shigowa gidan tayi tare da ajiye bag d'in gaban Suhaima tace
"Besty ga ankon ki fah ki duba ki ga yayi miki "

Sakin baki Aunty Aliyah da Suhaima suka yi suna kallon ta cike da mamaki, bayan d'azu da safe Yaya Aliyu yace gobe zai bata kud'in ankon da na gifts d'in da zata siya mata sai gashi kuma Jiddah ta zo mata dasu.

Murmishi Jiddah tayi ganin yanda suke kallon ta kafin tace
"Aunty wannan kallon fah, ni ku duba kuga yayi? "
Ta k'arasa magana cikin shagwa6a ganin sun k'i bud'e bag d'in tamkar masu jin tsoron akwai wani mugun abun aciki, ya sanya Jiddah ta janyo bag d'in kusa da ita ta bud'e, sai ga wasu tsadaddun kaya kala hud'u ta fito dasu masu matuk'ar kyau da tsada, swiss atampha, lace guda biyu da kuma wa wani material Light pink mai haske da abin nad'in kai pink shima amman mai duhu, anyi d'inkin gown ajiki yayi masifar yin kyau, sai shoes and hang bag set d'aya da su watch k'irar gucci na mata da kuma abin hannu, sark'a d'an kunne kai abubuwan kyalakyale sosai Jiddah ta zuba wa Suhaima.

Rasa bakin godiya Suhaima da Aunty Aliyah suka yi har sun bud'e baki zasu fara godiya Jiddah ta hana su dole suka hak'ura amman gaskiya Jiddah mutum ce tayi musu hallaci tayi musu abin da baza su ta6a mance wa da ita ba har abada, abun kyautata wa take musu tamkar wasu shak'ik'an 'yan uwanta na jini, babu tsangwama ko kyankyamin su da take duba daga inda ta fito, su kansu sun san Jiddah iyayen ta masu kud'i ne sosai bana wasa ba.

A haka Yaya Aliyu ya shigo ya same su sam ya nuna wa Jiddah bai ji dad'in abin da tayi ba da ta bari shi zai bata kud'i taje ta siyowa Suhaima kayayyakin ko nawa ne, nan Jiddah ta nuna mishi ita fah yanda ta d'auki Suhaima tamkar 'yar uwarta ta jini zata iya yi mata komai har idan tana dashi dole yasa Yaya Aliyu hak'ura yayi mata godiya daga k'arshe kuma ta tashi zata tafi har bakin motar su Suhaima da Yaya Aliyu suka rakata suna godiya tana nuna musu batasan godiyar nan, anan Aliyu yayi mata alk'awarin zuwa ta tafi da Suhaima idan ta dawo sosai Jiddah da Suhaima suka ji dad'in hakan, Kafin suyi sallama kuma ta shiga motar driver yaja suka tafi suna masu d'agawa junan su hannu har sai da motar ta k'ule tukunna Yaya Aliyu ya rik'o hannun Suhaima suka wuce gida.



****** ********** ********


Kwance yake saman kujera cikin garden ya zurfafa a cikin tunanin yarinyar da suka had'u, tsawon wajen kwanaki 5 da had'uwar su amman ya kasa manta ta koyaushe cikin tuna beautiful Face nata yake, cikin mafarkin shi da farke yake tunanin yarinyar da baisan sunan ta had'uwar su ta farko da junan su.

Shi yasan ba sonta yake ba duk da bai ta6a son wata mace ba, but why ya damu da ita har haka, duk san da ya tuna ta yana jin bugun heart nashi na k'ara k'arfi yana son tunano muryar ta da kyakkyawar surar ta yana son Allah ya k'ara had'a su koda sau d'aya ne ya ganta ya sake jin daddad'ar muryar ta.

Sake gyara kwanciyar yayi yana mai lumshe ido hango kyakkyawar face nata yayi lokacin da take mishi tsiwa tare da yanda cute lips nata suke motsawa kamar a lokacin take mishi tsiwar haka yake ji.

Ji yake bazai iya jure ba zumbur ya mik'e tsaye tare da nufar side d'in su da saurin shi kamar ba Sabeer ba, yana tashi a wajen Fadilah ta fito daga ma6oyarta ta zauna kan kujerar da ya tashi tana mai shinshina kan kujarer tamkar Sabeer ne zaune a wajen tsabar fitinar ta, d'ago eye's nata tayi wanda suka yi ja cikin wata irin murya tace
"I luv U Sabeer, ina maka son da bazan iya zuba ido ka so wata mace a rayuwar ka ba dole nasan ta yanda zanyi na karkato hankalin ka gare ni "
Tana gama fad'in haka ta tashi tare da wuce wa side d'in su Sabeer...



Aishat A Muh'd ✍🏻
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz


PAGE 26-27




Yana k'arasa wa part d'in su bedroom nashi ya shiga yayi wanka tare da shirya cikin wani blue jeans da T-shirt red yayi kyau cikin sauri sauri ya fesa perfumes tare da d'aukan phone's nashi ya fito zuwa parlour.

Akan dinning table ya hango Mumy, Daddy da Fadilah suna yin lunch abin su, ganin shi da Mumy tayi yasa ta cewa
"Son k'araso kaci abinci "
Yana nufar hanyar fita a parlourn yake cewa
"Mumy sauri nake zan fita sai na dawo "
Kafin wani ya k'ara magana ya fice da sauri, da ido suka raka shi cikin zuciyar Mumy tana mai mamakin abin da ya canja mata yaro lokaci d'aya don da ba haka Sabeer yake mata ba.


Yana fitowa harabar gidan ya hango driver da hannu yayi mishi alamar yazo da sauri driver ya k'araso inda Sabeer yake tsaye, key d'in motar dake hannun shi ya mik'a mishi hannu ya sanya ya kar6a tare da nufar inda motar take ya shiga key yayi mata tare da jan ta zuwa gaban Sabeer, kafin driver ya fito ya bud'e mishi k'ofa tuni Sabeer ya shiga cikin motar, don haka kawai driver tuk'i ya fara gate man ya bud'e musu gate suka fita.

"Yalla6ai ina zamu je? "
Driver ya tambaya, ba tare da Sabeer ya kalli inda yake ba yace
"D'an k'auyen nan da muka je zaka mayar da ni "
"Toh Yalla6ai "
Driver ya fad'a cikin mamakin mai Sabeer zai je yayi a wannan k'auyen kuma, gashi babu fuskar tambaya sai kawai yaja bakin shi yayi shiru ya mayar da hankalin shi kan tuk'in da yake.


Bayan sun isa k'auyen ne inda Sabeer ya had'u da Suhaima nan driver yayi parking a wurin, fitowa Sabeer yayi daga motar yana faman kalle kallen wajen da kuma hanyar da Suhaima tabi ranar ko zai ganta, amman har ya gama wurwurga idanun shi baiga ko mai kama da Suahima ko wannan yaron, gajiya yayi da tsayuwa ya shige mota ya zauna but still eyes nashi na jikin window yana kallon waje, driver dai kawai ido ne nashi.

Tun rana wajen k'arfe 2 suke wajen har yammaci wajen 5 na yammaci Sabeer bai ga mai kama da Suhaima ba, sosai abun ya dame shi ya rasa yanda zai yi yana son sake ganin yarinyar ne, sallahr la'asar anan suka yi ta cin abinci ne babu batun yin shi, Sabeer ko yunwar baya ji ma rabon shi da abinci tun breakfast na safe driver kuwa daurewa kawai yake don kuwa yunwa ce take kwakwalar 'ya'yan cikin shi, yana tunanin abin da ya tsayar dasu anan waje tsaya wajen awa 4, addu'a yake cikin zuciyar shi Allaj yasa Sabeer yace su tafi gida.

"Driver mu tafi gida "
Abin da Ado driver ya ji kenan wani sanyi dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar shi ko ba komai yasan nan ba da dad'e wa ba zai samu abinci ya ci, key yayi motar suka bar wajen amman idanun Sabeer akan hanyar da Suhaima ta wuce da gudu gaba d'aya wata damuwa ce cikin zuciyar shi, jinshi yake wani iri daban yaso sake ganin beautiful face nata a yau, haka suka k'arasa gida jiki ba k'arfi Sabeer ya shige bedroom nashi ya kwanta kan bed zuciyar shi cike da tunani kala kala duk akan Suhaima.



**** ****** *******



Aunty Aliyah ce durk'urshe a bakin makwarara tana faman kelaya amai sosai hannun ta dafe da da cikin ta d'ayan kuma dafe da k'asa, Suhaima da Yaya Aliyu sai sannu suke mata tamkar zasu yi kuka yanda fuskokin su ya nuna musamman ma Suhaima ganin yanda take shan wahala, sai da ta gama aman tsaf Yaya Aliyu ya wanke mata bakin ta tare da kamata suka wuce rumfar ya zaunar da ita kan tabarma, yayin da Suhaima kuma take gyara wajen da aka 6ata.

"Sannu Aliyah bari na fito da machine mu tafi asibiti tun jiya da yamma kike aman nan gashi har gari ya waye kina yi duk abin da kika ci sai ya fito koda ruwa ne ya kamata mu je kiga likita "

Yaya Aliyu ya fad'i hakan yana mik'a mata hijab d'in ta, bata yi musu ba ta sanya hannu ta kar6a tare da sanya wa, daidai lokacin Suhaima ta gama gyaran wajen ta k'araso rumfar, kallon ta Aliyu yayi tare da cewa
"Ki tafi gidan Babaa Lantana ki zauna zamu je asibiti ne "
Fuskar Suhaima d'auke da tsantsar damuwa tace
"Toh Yaya Allah ya dawo daku lafiya, Aunty Aliyah sannu Allah ya baki lafiya "

"Amin ya rabbi "
Cewar Aliyu don Aliyah bata iya magana saboda jin jikin da take yi, d'aki Suhaima ta shiga ta d'auko hijab d'in ta sannan ta fito hannu Aliyah ta rik'e suka fito zuwa kofar gida, inda Yaya Aliyu ya fito da machine d'in, sai da ya kulle gidan tukunna ya hau machine d'in dakyar Aliyah ta iya hawa saboda rashin jin dad'in jikin ta, sai da Suhaima ta ga tafiyar su sannna ta k'arasa gidan Babaa Lantana.


Da sallama ta shiga gidan Babaa Lantana da take wajen marhu tana soya gyad'a ta siyar wa ta amsawa Suhaima sallamar tana cewa
"Tabbb yau wa nake gani a gidan nan ba dai Suhaima ba?"
Ta fad'a cikin sigar wasa, d'an murmusawa Suhaima tayi tare da cewa
"Ni ce nan Babaa Lantana ina d'an tsohon ki? "
Suhaima ta k'arasa fad'i tana zama kusa da Babaa Lantana.
"D'an tsoho ya fita can gidan mai unguwa zasu tattauna matsalalon mu na garin nan musamman akan al'amarin matasa"
"Yayi kyau hakan "
Cewar Suhaima kenan
"Lafiya dai kike koh? "
Cewar Babaa Lantana tana sauke kaskon suyar gyadar, kallon ta Suhaima tayi tare da cewa
"Me kika gani? "
"Ganin ki nayi kamar fuskar ki da damuwa ne "
"Uhm Babaa Aunty Aliyah ce bata da lafiya yanzu haka sun tafi asibiti da Yaya "
Da sauri Babaa Lantana tace
"Me yasame ta? "
"Tun jiya take kwara amai har yau bai tsaya ba ko ruwa tasha sai ya dawo duk ta rame "
D'an shiru Babaa Lantana tayi kafin kuma ta saki murmishi akan fuskar ta daman tayi hasashen haka don taga alamomi sosai a jikin d'iyar ta ta magana ce bata yi ba.


Kallon mamaki Suhaima take yiwa Babaa Lantana ganin tana murmishi kamar wadda tayi mata wani babban albishir ba lalura ta fad'a mata ba kasa hak'ura tayi Babaa Lantana tayi magana tace
"Wai Babaa lafiyar ki kalau ina fad'a miki rashin lafiyar Aunty kina murmishi? "

"Uhm Suhaima ai abin farinciki ne ya samu shi yasa kika ga ina murmishi "
Cikin rashin fahimta Suhaima tace
"Rashin lafiyar Auntyn ne abin farinciki? "
'Yar dariya Babaa Lantana tayi tare da cewa
"Matsala ta da ke Suhaima rashin gane wa ina nufin Auntyn ki ciki ne da ita wannan lalurar da take yi ta laulayin ciki ne kin fahimta? "

Wani sanyin dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar Suhaima daman burin Aunty Aliyah ta samu ciki ta haihu kusan kullum sai ta fad'a wa Suhaima ta taya ta da addu'a Allah ya bata 'ya'ya, sai gashi Allah maji rik'on bawan shi ya bata, lallai yau Aunty Aliyah da Yaya Aliyu akwai murna an samu abin da ake so, amman duk da haka sai da Suhaima tace
"Da gaske kike Babaa? "
"Insha Allahu kuwa Suhaima "
Washe baki Suhaima tayi tana mai jin dad'i farinciki fal cikin zuciyar ta tana jiran dawowar su Yaya Aliyu.

Suna nan zaune Suhaima na taya Babaa Lantana d'aurin gyad'ar a leda suka ji tsayuwar machine d'in Aliyu a kofar gida, da gudu Suhaima ta fita har tana wancakali da faratin gyad'ar ya watsowa Babaa Lantana a fuska amman Suhaima bata tsaya ba tayi waje da gudu.

"Oh ni 'yasu Allah ya shiryi Suhaima ji yanda ta zubar min da gyadar nan "
Cewar Babaa Lantana tana tsince gyadar da ta zube a k'asa.

Suhaima tana fitowa kofar gida ta hango su har ma Yaya Aliyu ya bud'e gidan sun shiga, da sauri Suhaima ta k'arasa gidan ta shiga kallon fuskar Yaya Aliyu tayi taga sai washe baki yake haka ma Aunty Aliyah duk da kuwa jin jikin da take hakan bazai sa mutum ya kasa fahimtar farincikin dake shimfid'e a fuskar ta ba, nan Suhaima ta tabbatar da ciki ne dai da ita zancen Babaa Lantana ya zama gaskiya.

"Albishirin ki "
Cewar Yaya Aliyu yana kamo hannun Suhaima, cikin murmishi tace
"Goro fari tas Yaya "
'Yar dariya yayi kafin yace
"Auntyn ki ciki ne da ita zata haifar miki d'a "
Wani tsalle Suhaima ta daka ta rungume Yaya Aliyu tana dariya kafin ta cika shi ta rungume Aunty Aliyah tana cewa
"Wayyo dad'i Allah mun gode maka "
Hannun Yaya Aliyu ta rik'o dana Aunty Aliyah tace
"Yaya Aunty na taya ku murna sosai Allah ya fito mana dashi lafiya "
"Amin Thumma Amin "
Suka fad'i fuskar su k'unshe da murmishin farinciki, ana haka Babaa Lantana ma ta shigo ita da Baba Adamu don dawowar shi kenan Babaa Lantana take sanar mishi shine suka taho duba jikin Aliyah.

Anan Baba Adamu yaji abin farinciki daman Babaa Lantana ta hasaso hakan, nan suka taya juna murnar samun k'aruwar da zasu samu kafin daga baya su yi musu sallama su tafi......




Aishat A Muh'd 🏌🏻‍♀
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz


PAGE 28-29




Tun daga lokacin ya kasance Aunty Aliyah bata da ishashshiyar lafiya a jikin ta yau lafiya gobe ciwo, duk ta rame sosai saboda laulayin da ya sanya ta a gaba, aiyukan gidan kuwa Suhaima ce mai yin su don Aliyah bata iya komai sai kwanciya saboda rashin k'arfin jikin ta dakyar take iya tashi zaune, ga baccin da take sosai abinci ma ba kowanne take iya ci ba ba k'aramin walaha take sha ba.


Da haka aka cinye kwanaki biyar Aunty Aliyah tana fama da azababben laulayi, ya rage sauran kwanaki biyu a fara bikin Jiddah kuma ayau ne ranar da Jiddah ta fad'a zata zo ta dauk'i Suhaima su tafi gidan su don fara hidimar biki, gashi Aunty Aliyah ba lafiya Suhaima ma ta fitar da ran zuwa bikin Jiddah saboda ganin yanda jikin Aunty Aliyah yak'i sauk'i duk hidiman gidan ita kad'ai ce mai yi don ma wani lokacin Babaa Lantana na zuwa taya ta 'yan ayyuka.

Wajen k'arfe biyun ranar laraba Jiddah ta zo lokacin Suhaima ta kammala girkin rana tana share gidan taji da sallamar ta aikuwa yar da tsintsiyar hannun tayi da gudu ta k'arasa inda take suka rungume junan su cikim tsananin jin dad'i.
"Amarya kinsha k'amshi sai wani kyalli kike tun kafin a fara jin amarcin "
Cewar Suhaima cikin murya k'asa k'asa tana dariya, dukan wasa Jiddah ta kawo hannu zata yi mata da sauri Suhaima ta goce suna dariya.
"Allah Suhaima kin fara zama mara kunya, zan fad'a wa Yaya Aliyu yayi miki aure ke ma "
Rik'e bakin ta Suhaima tayi da hannun ta d'aya kafin tace
"Wooh rufa min asiri ni har yanzu yarinya ce da saura "
Hararar wasa Jiddah tayi mata tare da cewa
"Uhm a hakan kike yarinya ai kuwa ki zuba ido ina aure zan ziga Yaya Aliyu yayi miki ke ma nace ke kika fad'a min na fad'a mishi aure kike so kina jin kunyar sanar dashi shi yasa kika aiko ni "
Jiddah ta k'arasa magana tana dariyar mugunta, kwa6e fuska Suhaima tayi tare da cewa
"Wayyo Allah nah Jiddah ki rufa min asiri, waiii idan Yaya yaji hakan ina tunanin 6a66ala ni zai yi "
"6a66alawar lafiya, ai ba wani mugun abu kika yi "
"Besty albishirin? "
"Goro fari tas mai ya faru k'awata? "
"Aunty Aliyah tana da ciki taawon 3 month's "
Wani uban tsallen murna Jiddah ta doka tare da rungume Suhaima tana cewa
"Da gaske kike Suhaima don Allah? "
Cikin tabbatar wa Suhaima tace
"Da gaske ne wlh Jiddah, sai dai yana bata wahala baki ga yanda ta koma ba duk ta rame ko abincin kirki bata iya ci "
Suhaima ta k'arasa maganar cikin yanayim damuwa, nan take Jiddah ita ma fuskarta ta koma kalar damuwa, hannun Suhaima ta rik'o suka nufi d'akin Aunty Aliyah tana cewa
"Kada ki damu Suhaima Aunty Aliyah zata samu lafiya, kinsan wani cikin yana bawa mace wahala sosai kafin ya girma, da zarar ya girma insha Allah zata samu sauk'i addu'a zamu cigaba da yi mata "
Gid'a kai Suhaima tayi kawai a lokacin suka k'araso kofar d'akin Aunty Aliyah sallama suka yi mata, dakyar ta iya amsa musu sallamr k'asa k'asa cikin irin sanyin muryar mara lafiyar nan wanda yake jin jiki sosai, d'aga labulen d'akin suka yi tare da shiga ciki tana kwance a falo saman sallaya da hijab a jikin ta alamar yanzu ta idar da sallahr azahar.

Zama suka yi kusa da ita sosai Jiddah hankalin ta ya tashi ganin yanda Aunty Aliyah ta koma wata iri duk ta rame sosai ta fita a hayyacin ta tamkar ba ita ba.

"Sannu Aunty Aliyah Allah ya baki lafiya "
Cewar Jiddah kenan, murmishin yak'e Aunty Aliyah tayi tare da cewa
"Yawwa Jiddah, Amin "
Dakyar take maganar tana jan numfashi irin wanda yake idan mutum yana jin ciwo sosai idan yayi magana yake yi.

"An kaita hospital kuwa Suhaima? "
Jiddah ta tambayi Suhaima tana kallon ta.
"Eh Yaya ya kaita amman magani suka bata "
"Wanne hospital ne wannan da ko drip baza su sanya mata, jiki babu kwari ga ba cin abinci, yanzu da sun sanya mata drip zata ji k'arfin jikin ta "

Tana gama fad'in haka ta ciro wayar ta dialing d'in digit na Yaya Aliyu tayi bayan sun gaisa ta fad'a mishi tazo tana son ganin shi, babu dad'e wa sai ga Yaya Aliyu ya shigo bayan sun dad'a gaisawa ne tace

"Yaya Aliyu don Allah ina son kayi min alfarma mu kai Aunty Aliyah hospital d'in da muke zuwa, ba don na raina kulawar da kake bata ina son zan kaita inda zasu duba ta sosai "

Girgiza kai Yaya Aliyu yayi tare da cewa
"Baza'a yi haka ba Jiddah wahalar zata yi yawa, ki fad'a min sunan hospital d'in gobe zan kaita da kaina a duba ta "

"Don Allah Yaya ka daure mu je na roke ka "

Nan Jiddah tayi ta rok'an shi dakyar daga k'arshe ya amince don har Jiddah ta fitar da ran zai barsu, nan da nan suka shirya tafiya hospital a motar da Jiddah tazo, Yaya Aliyu da driver a gaba Jiddah, Suhaima da Aunty Aliyah a baya su bayan sun yiwa Babaa Lantana sallama, sai addu'ar fatan alkhairi Babaa Lantana take yiwa Jiddah.


Wani had'add'en private hospital wanda Jiddah da families d'in ta suke zuwa nan ta sanya driver ya kaisu, babu 6ata lokaci aka kar6i Aunty Aliyah saboda sunsan wace Jiddah, nan aka shigar da Aunty Aliyah special room ita d'aya sai doctor da kuma nurse guda biyu.

Sun d'auki tsawon lokacin suna checking nata kafin daga k'arshe su sanya mata drip tare da yi mata injection na bacci kafin su fito a room bacci mai nauyi ya d'auke ta.

Bayan sun fito ne likita ya buk'aci ganin su cikin office d'in sa bayan sun shiga sun zauna ne, sai da yayi rubutu cikin file sannan ya fara cewa
"Ciki ne da ita na tsayin 3 months so kunsan kowacce mace da irin halittar ta na laulayi ciki kafin yayi kwari, shine yake bata wahala baya ga wannan babu wani abu babba sai malaria, zamu yi iya kok'arin mu na ganin koda cikin kashi biyar ne ta samu saukin kashi uku sauran kuwa sai a hankali don haka mun bata gado zamu rik'e ta har zuwa gobe insh Allah "

"Okaya doctor thank U very much, yanzu zamu iya ganin ta?
"Why not sai dai ban da hayaniya please and kuma ga maganin da za'a yi amfani dashi na rubuta ana buk'atar shi da wuri don tana tashi zata sha "

"Okay doctor ba damuwa"
Nan doctor ya bawa Aliyu suka yi musabiha tare da cewa
"Allah ya bata lafiya ya kuma raba su lafiya congrats Yalla6ai "
"Amin nagode likita "
Sam doctor yayi tuanin cousins d'in Jiddah ne ganin su suma kyawawa dasu tamkar family d'in su Jiddah shi yasa bai kawo komai a ranshi ba, sai dai yanayin su da ya nuna basu da kud'i kamar su Jiddah.

Bayan sun shiga room d'in da aka kwantar da Aunty Aliyah ne suka zauna shiru kowa da nashi tunani ta 6angaren Aliyu yana tunanin da kunya ya iya kallon idon Jiddah yace bazai bar Suhaima ta tafi bikin ta ba ganin irin d'umbin hallacin da tayi musu bai kamata ya hana Suhaima zuwa ba, gashi kuma Aliyah na buk'atar kulawa sosai gashi idan suka koma gida gobe Suhaima ce k'arfin ayyukan gidan idan ya barta ta tafi ya zasu yi?...




Kuyi hak'uri da wannan fan's sai gobe kuma insha Allah.


Aishat A Muh'd 🏌🏻‍♀
[2/4, 11:28 AM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: 💝 A SANADIN SON KI 💝


Written by
Aishat A Muh'd

♻EXCLUSIVE WRITERS FORUM

Dedicated to my Sadeey saNaz



This page is for U my Ramlat ar manga (Real mai dambu 🥗) thanks for luv nd everything Allah ya bar zumunci ya raya zuri'a, ina matukar alfahari dake wannan shafin naki ne kyauta 👄




PAGE 30-31




Tashi Jiddah tayi tsaye tare da d'aukan bag d'in ta gida take son tafiya saboda yau ne ranar kamu sai faman kiran ta ake a waya ana tambayar ta inda take, kallon ta Aliyu da Suhaima suka yi, ita ma kallon su tayi tare da cewa

"Yaya

Please Login or Register in order to submit comment