Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Aymah wai yau kodai bakyajin dadine naga idon ki ya kumbura ko zazzabi kike?.

Da sauri Jameel ya ɗago kai ya zubamata ido baya ko kyaftawa sai zujiyar sa dake tsalle tsoron shi daya kar ace wani abu ke damunta .

Cikin sanyin ta tace banajin komi kaka kawai dai hakanan naji sauyin jikina.

To ko muje Asibiti. cewar jameel yana zubamata ido cikin kulawa.

Dan murmushi tamai tace A'a bai kai nan ba.

Fuska ya ɓata ya mike ya zura takalman sa yace" Deedee bata mayafi muje Asibiti Amma Hijjob ba gyale ba.

Deedee tace kwaraiko kuje! Hijjob kuma wannan baka isaba abinda take so shixata sanya.

Ido ta zaro sadda taga ta mike cikin shagwaɓa da takema Deedee datake gani kamar uwarta tace" nifa gaskiya bazanjeba amun allura, kana bake ce kikace ya koma aikin sa na daba dan ya samomun kudi ,nikuma baki fadaman miye aikin ba ko na wahalane oho ta karasa tana turo baki da Dire kafa kamar yar 17yrs...

Sassanya Murmushi ya saki yana yin kasa da kai da sauke ajiyar zuciya jin dadi da tace ba komi ke damun taba .

A'Hankali yace "madallah da wannan halitta mai dumbin Alkhairi..

Deedee kau haba ta rike tace ƙudura sama liman da wawan zama ! Yanzu dama duk akan wannan karama matsala kika saki lokaci daya? yo nace in bai nema mikiba wazai ba?.

Murmushi tayi suka hada ido dashi ta d'agamai gira kana tace shi din nan kanena ne Deedee,Hakkina ne na tashi tsaye wajen neman nawa na kaina dan samar mishi abinda zan gina shi.
Kai wai kai mene ma matakin karatunka ta karasa tana zaro mai ido da daure fuska irin ita Babba nan.

Kai ya shafa yana murmushi dan ya lura so take ta kasheshi da salan ta kamin yace "ai mace bata girman namiji som, Yanzu haka da wani abu xai shigo gidan nan ita kanta wannan Deedee data baje anan aguje zatai ciki nine dai zakin da zan tsaya naji mike shirin farauta Iyali...datse harshen sa yayi da karfin masifa tinowa dayayi da katoɓarar da zayyi.

Deedee kau dariya tashigayi yayin da Aymah bata gane hausar tashi ba .
Deedee ta dauki ɓawon gyaɗa ta hau jefamasa yana caɓewa.
Tace Allah ka shiryaka yaron nan ..

Aymah kau murmushi kawai tayi tana wani nazari.

Anan unguwar Yayi sallah mangariba da isha kamin yaci abinci ya masu sallama ya tashi.

Washe gari ana gama Asuba bayan yagama duk kan azakar nashi yama su Baba sallama ya fita.
Kai tsaye tasha ya nufa wajen abokan sa na da.

Sun kau yi farin ciki matuka da ganin shi dan tinda ogan shi yayi accident shima yabar zuwa.

Jiki na rawa aka hau bashi key na motoci dan kowa yason shi da zafin nama gashi baya wasa da Hakkin kowa.

Motar Dutsama kawai ya karbi key dinta dan bayaso yana nisa dasu yafiso yaje garin dake kusa da nasuya dawo cikin ikon Allah.

Karfe tara akama motar lodi ya hau ta da addu'a.

Cikin kwarewa yake murza sitiyarin ya kaisu lfy ya sake yin wani lodin na katsina ya dawo .

Bayyi kasa a gwiwaba ya sake hadawa ya koma.
A takaice saida yayi tsawu ukku kamin aka raba kudin ukku akabama mota daya, shi daya , Mai mota ɗaya .

Ba laifi ya samu kudi a ƙallah dubu 8k

Koda ya dawo gida ya zubema Inna su shi sosai suka samai Albarka sukamai murna.

Yace su ɗauki nasu ya kaima su Deedee sauran.

Baba dake gefe yace A'a bazaayi hakaba gaskiya.
Ka kaimasu sai kaima ka rike wani abu ni Alhamdulillah wanda nike samu Ya ishemu .

Aa yace yana mikewa yace babu abinda zanyi nida gobema in sha Allah fita zanyi wannan ai na farko ne dan Allah ku dauko wani Abu..

Albarka suka sake samai Inna su tace to ga 5k ka kaimasu mu bari mu dauki biyu kai kuma ka dauki daya kayi kalaci.

Godiya ya masu kamin yace wai Inna mu ina wannan Halima dake zuwa gidan nan ne.

Malam ya harare shi yace sai yau ka tinota yarinya datama bauta da iyayen ka kamar zata mutu ta gaji ta koma garin su.

Baki ya dan tabe kamin ya shige dakin shi ya dakko kayan wankan shi ya dibi ruwa yayi wanka ya daura alwallah mangariba.

Bayan ya zira kananun kaya masu baylain kyau ya fesa turare kana ya dauki hanya gidan Aymah.

Da sallama ya shiga gidan bayan an'bashi izini ya shiga palon kasancewar akwai wuta firar su kawai suke wayoyin Adnan gaban Aymah tana dan lallatsawa Akai akai .

Ido ta dago tace kanena sannu da shigowa.

Wata harara ya dan ballamata yana faɗin. gaskiya zan daina zuwa kinacemun haka Deedee kimata magana.

Tom'tom sorry Yayana na daina sannu tace tana murmushi.

Yawwa lovely sst tnx u.

Deedee tace cen dai ta matsemaku kai gyambo da san girma ita kuma tana biyema taɓarar ka.

Karkacewa yayi ya zaro 5k din yace gashi ku fara sayen abinda babu dan Allah zuwa gobe.

Aymah ta zaro ido tace kai Jameel miye kayi ka samu kudi.

Sata nayi.
Ya bata amsa kai tsaye yana zubamata shanyayyun idon shi.

Ido ta zaro tare da hada hannaye tace" bance ba! Amma Dan Allah wane aikin wahala kayi yabaka wannan kudin .
.
Deedee tayi murmushi tace mota fa yafaraja yanabin garuruwa dama aishine sana'ar shi.

Sosai Aymah ta mayar da attention dinta kaf kanshi tare da zubamai fararan idanun ta da a hankali hawaye keta kwanciya ciki.

Shima din kallon ta yake amma irin kallon nan na tsoro da bazaice ga nufinta a zuciba shin kudin ta raina koko oho dai.

Tsawon lokaci kamin cikin sanyi tace" Duk akaina ka fara wannan wahala?

Deedee tayi Murmushi tana fadin' bari dai in watsa ruwa inzo mungode Allah ya tsare ka daga sharrin abin hawa.

Ameen yace yana gyara zamanshi har lokacin zuciyar shi bugawa take dan baison hukuncin Tambaya da Aymah ta masaba.

Tana ganin wucewar Deedee ta rarrafo inda yake gab da junan su kamin tace" Jameel.

Dan kallon ta yayi yace" na'am.

Miyasa ka zabi komawa abinda ka bari saboda ni?

Kafada ya daga kamin yace kawai hakanan sabida kasancewar ki marainiya ayanzu baki da gatan kowa saina Allah dani,to gani ai bazan amince ki fita nema ba,Kana karki manta saboda nine kikayi missing kaf abinda kika mallaka,So in ban tashi na nemar miki ba waye zaibaki ?.

Hawaye suka zubomata kamin tace.
Jameel dan Allah da manzon sa in dai nice ka daina ,kabani lokaci kalilan dan Allah,Kana wallahi badan kai na rasa komi ba,Yana cikin ƙaddarata,Karka manta komi a rubuce yake a kaddara bawa fatan mu dai Allah kabamu ikon cinye jarabawoyin mu...

Ameen Ameen..

Amma in'dai Hakane kinga kenan nima komawata wannan aikin yana cikin ƙaddarata so kimun Addu'a kawai.

Murmushi tayi tana dan kallon shi tace" kai ko,nizakawa wayo?.

Shima murmushin ya mata yace" A'a kawai dai inq bisa sunnar maganar kine komi kaddarane a rayuwar bawa.

Tom Allah ya mana zabin Alkhairi,amma ni yanzu nafiso koda neman zakai ka tattalawa kanka kaga ka dan fara girma kyanshi ace nan da shekara ukku zuwa biyar in aurar dakai, kana bikin ka ba irin na kowa bane dole muyi dogon tanaji..

Ido ya zaro kamin ya k'ank'ance ɗaya akanta yace Biyar?,dan bakya sona, sai nayi shekara biyar ba aure,in sha Allah nan da shekara biyar yaron mu ko yarin yamu sun kai shekara hudu.

Kaf fara'a fuskarta ta dauke jin furunci shi cikin wani alhini tace " Kenan dama kana da wacce kake so amma baka fadamana ba.

Murmushi yyi yana shafa kanshi yace" Allah mas@ni ,muna dai lalubune a duhu.

Deedee ce ta fito tana baza kamshi tace "wai har yau firar bata kareba ni inacen har nayi nazarin Abinda zai fishe mu.

Aymah tace kaka miye kika nazar ta?.

Deedee tace "bazamu zubamasa ido kullum Yaje ya nemo ya bamu muga Randuna sai dai mu girke ana zubamamu muna lashewa.

Dan haka nida yar jikallena tsaye zamu tashi wajen neman na kanmu sana'a zamu fara in sha Allah , Gobe goben nan zanje kasuwa Naga abinda ya dace nayi.

Dariya ya hauyi harda rike ciki abinda bai fiye yiba.

Sosai Aymah ta shagala da kallon baiwar kyan dake tattare da matashin bawan Allah nan mai jini ajika.

Deedee kau rai ɓace tace" ai dole kayiman dariya ka daukan mahaukaciya nadai gama ma komi tinda na kawo ubanka duniya.

Cikin danne dariyar sa yace "kema Deedee daga shiga har kinyi bacci da mafalki saiki hango abu har ya tabbata.

Takalman kafarta ta cire tana fadin tashi kabar gidan nan gwauron banza ko in'bugama aka.

Mikewa yayi yana bude hannu da fadin "ko baki koramba tafiya zanyi nan ya masu sallama yatafi.

Ajiyar zuciya AYMAH ta sauke tana lumshe ido.

Washe gari Jameel karfe takwas ya bar gida sadda ya isa tasha shine kawai ake jira .
Kamar yanda ya zama akidarsa fara addu'a kamin hawan karfe haka yayi kana ya kunna suka dauki hanya sai fatan dawowa lfy.

Deedee kau tana tashi ta damamasu kunun tsamiya da kosai suka zauna suna kalaci Aymah kau sai santi take dan ita duk bata iya wannan kayan galgajiyar ba gata da son su shiyasa in Didi nayi kamar kunnan ta ya tsinke.
Bayan sun gana tashiga gyaran palon Dede tamata sallama ta fita kai tsaye kasuwa ta nufa.

Zobo ta auna kwano biyu da aya kwano biyu da citta da kanunfari na 500.

Wajen masu fruit ta nufa suka hadamata
kwakwa
Dabino
cocumber
kankana
Kashu
Abarba
kana tayi gida zuciyarta fess.

Koda Aymah taganta da kayan itama dariya tayi tace .
miza'ayi da wannan Deedee karki manta G.R.A muke batasu ake ba kar abinki Yayi kwantai.

Cikin bama kai kwarin gwiwa Dede tace in sha Allah bazaiba na fadamiki tsaya dai kiga ta karasa tan aje mayafi ta ɗauki Ayarta ta surfa ta wanke sosai ta cire tsakuwar kana ta samata ruwa ta aje ta hau tafasa zobon dayaji citta da kanunfari da bawon abarbar data saya.
Cocumber da kankana da Kashu da sauran Abarba tasa Aymah ta mata blending nasu.

Zoɓon na tafasa ta tace tare da juye kayan fruit din ciki ta ɗauki sugar da foster dinta mai kwakwa da gwaiba ta juye aciki wani ni'imtaccen kamshi ya fara tashi kota ina.

Aymah ta ɗibi wani a roba tace" tun kamin yayi Sanyi yawuna ya tsinke tasa a fridge.

Deedee tace ja'ira kyama sake fada ta dauki markadan Ayarta da kwakwa da dabino ne kawai aciki sai citta da kanunfari tace .
Natafi kai markaɗe.

Aymah tace kawo nakaimaki tace A'a bashi dai na fita.

Da kwatance ta gane wajen mai markaɗan nan tayi tsaye ta wanke injin din tass da kusan rabin jarka ruwa.
Mai markadan natamata dumin ta karar da ruwan taa.

Shuru Deedee tayi tana kissima yanda zataimata .

Ana'mata fashi ukku tace.
Baiba saida akayi biyar kana ta dauki goma ta bata tace ungo kyasai ruwan wannan kuma darin markade ne gobe in zandawo nazo da ruwana kazamar banza.

Takaici ya kashe matar ta bita da kallo Deedee ta mata murmushi tace bye inji Anna (Arna)

Koda taje gida ƙanƙara tasamu takai biyar ta dinga fasawa tana juyewa kamim ta samu suyi ta tace ta xuba shiga tare da kulla abinta tsaf ga leda da duk ta saya tashiga sawa a fridge.

Karfe biyar na yamma komi yayi sanyi sosai.

Tayi wanka, ta shirya Tare da fesa turare ta dauki karamin boket ta zuba komi goma goma yace aymah xanje in dawo.

Ido Aymah ta zaro tace badai tallaba.

Aa haba sadaka zanyi ina zuwa.

Fita tayi ta fara shiga makwaftan dake kusa dasu duk in an'gaisa zatayi kwatancen gidan da take suyi barkwanci da masu gidan kamin tace to sana'a nike gashi a a ɗan Ɗana kamin azo asaya.

Duk kau gidan data ba sai sunsha gabanta suna santi wasu subata kudi da niyyar zasu bita su kara saye wasu kuma suce zasuzo saye ahaka dai tashiga gida goma cur kamin tadawo gidan su Yara biye da ita da zasu karɓa nan ta shiga zubama kowa abinda yake so.

Karfe shidda yayi sallama ya shigo gidan hannusa rike da leda.
Wani milk din yadine jikin sa mai saukin kudi an'mai ɗinki zamani ɗan madaidaici yamasa masifar kyau. madaidaiciyar sumar sa tasha gyara sai kamshi yake.

Sannu da zuwa sukaimai Aymah ta tashi ta kwasomai kunun Aya da zobon Deedee ta kawo da jallop din taliya da suka dafa.

Allah yasakamiki da Aljannah yace yafara Bissimillah yanaci suna dan fira da Deedee dan Aymah kau hankalinta naga wayar Adnan.


Suna zaune akaita shigowa sayen zobo kan kace mi abu yayi kasa saida Deedee tace babu kana aka kyalesu tace kai kaji gantalallu an'saba shan lemu mai karas yau anji nawa ana so azuke man koni banshaba.

Dariya yayi yace wannan ne kike Sayarwar ?

Eh mana yayi dadi Ko.

Sai magana yaga Aymah tayi maza ta mike tare da daukar Hijjob din Deedee sauri sauri tace ina zuwa Kaka ta fita da sauri...

Kallon juna sukai Kamin Deedee tace "lfy kuwa? to ina zata waye ta sani .

Kamar tunamai tayi da sauri ya mike ya mara mata Baya.

Yana fita get din ya hango wani mai Machine ya juya baya ita kuma tayo ciki tana ɓoye abu.

Waye shi yace idon shi na sauyawa zuciyar sa namai mugun zafi kamar zata fasa kirji ta fito.

❤️MATAR OGA NA ❤️
MALLAKI
UMMY AYSHA

LITTAFINAN NA KUDI NE KIBIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI HAJIYA
ACCOUNT NUMBER 9064260199 AMINA DAHIRU OPAY BANK
SHEDAR BIYANKI TA WANNAN LAYIN 07038423451

Page 14


"Kallon shi tayi na lokaci kamin ta ɗaure fuska gam babu alamar fara'a ko wani wasa a tattare da ita ta nemi raɓashi zata wuce batare data bashi Amsa tambayar sa ba.

Aymah maganafa Nike miki Jameel yace yana bin bayanta.

Juyowa tayi itama idonta sunyi jawur tace.
Kaga Jameel bai'dace kanamun haka ba dan kaga na baka fuska,Kana da Babban matsayi a Rayuwata kaida iyalinka amma wannan bashine zaisa nabaka fuska kana tuhumata kamar yar cikin kaba,karka manta a shekarun da nike dashi zan iya tantance gyara zan kuma iya tantance b'arna,karka matsama Rayuwarka da tuhumata akan Duk abinda kaga nayi,kazuba ido kayi kallo,kana karkacika matsaman da son jin abinda bani na buɗe baki na fadama ba,in har mukatafi akan haka sai kafi kowa jin dadin zama dani ina fatan ka fahimceni ta karasa tana juyawa tayi tafiyar ta .

Jameel kau da kallo yabita.
kallo mai cike da mamaki da maɗaukakin tashin Hankali.
Yanzu har akwai abinda zai iya zama sirrinta wanda bazata fadamaiba,shine take kallo take fadama wannan bakar magana akan kawai yanaso karemata mutunci!
Aiko saiya gwadamata namijin duniyane shi, kana shekarun shi bazai zama Hujjar da zata iya rainshi ba.

Wannan dalilin ya ɓatamai rai sosai ko sallama bayyi da DeeDee ba yayi tafiyar shi gida ranshi na suya.

Aymah kau tana shiga ta Haura sama kamin ta dawo kasa ta cire Hijjob ta aje.
DeeDee ta bita da ido ganin ba walwala fuskarta sai batacemata komaiba illah ruwa datace taje tasha.

Ruwan kau ta ɗauka tasha sosai kamin ta ajiye tayi sama da kanta ta fara nazari.

"Son Jameel yamata shigar bazata A zuciyar ta bayan tasanya makullin kiyayyar Ɗa namiji ta rufe, Amma Dole soyayyar da takemai tasa ta karfin tsiya ta bude ta bashi babban matsayi a zuciyarta.
Ita kanta har mamaki take yanda lokaci ɗaya son yaro ƙarami yayi ma zuciyarta shigar farmaki haka cikin sauki.

Tana da burin Alkhairi wa Jameel da Family nasa amma kuma lokaci baiba da zata bayyana amatsayi hasken rayuwar sa.
Tana kyautata mishi zaton Alkhairi amma kuma bazata bashi damar Sanin abinda batai niyya ba ayanzu.
Cikin rauni tace''
Am so sorry My Jameel karkayi Fushi kaji. .

Jameel kau kamin ya isa gida wani zazzafan zazzaɓi ya saukar mai dan shi halittar shi muddum aka ɓatamai rai ko bakar magana sai ya kwanta ciwo tamkar mace.
Da sallama yashiga gidan nasu yana Layi.

Inna su ta kamashi tana fadin "Kai lfy?.

Kaina ke ciwo yace dakyal yana sauke numfashi.

Sannu tamai tare da rakashi daki ta kira kabeer akan yaje ya taimakamasa ya cire rigar.

Kamin ma ya shiga ya iske ya cire kayan daga shi sai vest da wando yayi kwance ya lumshe ido.

Ganin hakan yasa Kabeer din fita dan bashi waje yayi bccin sa.

Yana ganin fitar sa ya gyara kwanciyar sa kanshi na kallon kwanon ɗakin.
Wasu hawaye masu masifar zafi suka zubomai.

Ya Yadda son Aymah A jinin shi yake.
Ya yarda da kaunar ta aka halicce shi,Baitaɓa tinanin soyayya A rayuwar sa ba.
Yana ganin ɓata lokacine da shirme,amma yau ɗaya Ta ɓatamasa rai akan wani gantalallan tsamurmurin saurayin da tayi wanda ko yayi rantsuwa bazai kaffaraba babu abinda zai kaishi.
Shine Dan'yayi kishinta zatamai faɗa,koko tana ganin dan yayi zama kalkashin su bai cancanci ya tsaurara tsaronshi akanta ba bayan amanar shi yake ganinta ahalin yanzu Tinda yana da Babban buri akanta.

Cikin rawar murya ya fara magana.
"Aymah ina son ki ,ina kuma matukar Kaunar ki wlh, Duk da ina tsoron bayyanamiki hakan dan nima nason bandace da keba Gaba da baya kinfi karfina,,To Amma shi so ba ruwan sa.
Karkiyi amfani da girman shekarun da kika fini ki'ki bin umarnina hakan zai iya jefani tashin Hankali da bashi da magani,Dan Allah AYMAH ki fahimceni,ba nufina nayi takura wake ba,Inaso ne dai na kare maki mutuncinki,aganina ayanzu baki da dan uwan dayafini , bai'dace ace akwai abinda kike ɓoyeman ba nazama ke kinzama ni in abun Alkhairi ne zan baki goyon baya, wanda naga zai cutamiki zan nisantaki dashi haba man Aymah ya karasa haƙoran shi na haɗewa dana juna tsabar masifar zazzabi .

Malam ne ya shigo yana fadin sannu jamilun Deedee ashe bakaji daɗe ba Allah yabaka Lfy ga Paracitimol na siyoma.

Mikewa yayi ya karɓar yasha ya koma ya kwanta.

Cikin lokaci bacci yayi gaba dashi .

*Kauyen Abukur*.


Tsintsiyar kwakwace Hannun Wata mata tana shara ranta ɓace ta juyo ta fallama mutumin da kan shi ke ƙasa mari.

Cikin fushi tace.
"Jakin inane kai akan ana bamu 5k na kula dakai shikenan saika zauna kai tamana kazanta yanzufa na gyara wajen nan sai kuma ka sake ɓatawa dan ubanla.
Bance in kana da buƙata kayimana Haushi akira Malam ya kaika ba tinda baka magana,Katon banzakai ka sake ka gani yanda zanma.


Kanshi ya ɗago anan nima na zaro ido ganin yanda lokaci kankane yanda halittar Adnan ta juye yayi wani masifaffan baki idon shi duk sunyi zuru zuru alamar yunwa ta faramai illah.

Kai yashiga d'agawa dan ko magana baya iyayi.

Kunnen shi ta rike sosai tana murɗawa tace zaka sake.

Da sauri yashiga jujjuyamata kai Hawaye na sakkomai bana komiba sai na bakin ciki.

Kanshi ta dungure tace Ɗan wahala kawai kimanin wata daya amma jibi yanda siffarka ta dawo kamar ta ifritu mina jinni, in sake ganin yaman kazanta wajen turken awakina yaga yanda zan yimai sabuwar kaciya ta karasa tana xaro wuka da zaro mai ido...

Sosai kau ya furgita dan zaman da yayi da Ladidi ya fahimci duk abinda tace zatai mai yimai take dan batada tausayi balle imani ko kaɗan a ranta.
Aranshi kau Ya ɗauki Alwashin yanda zai samu kakkafar wukar da zayyi mitsi mitsi da naman jikinta Duk ranar daya ganshi tsaye da kafarsa.
Hmm akwai daba ,Dole ya haɗa kogo guda na jinin makiyansa na fili dana ɓoye..

Washe gari.

Aymah ce waya akunnan ta cikin tashin Hankali tace" Dr ga Yan wajen aikin sanan zuwa yanzu gidan nan Duba shi ina cikin matsala ya zamuyi?


Deedee ce ta dawo daga kasuwa bayan tayo sayayya kayan kununta da zoɓo.
Dan Asuba fark kuɗaɗan mutane sukazo hannuta tace.
Lafiya kike Safa da marwa Aymah?.

Hawaye ta sharce tace Deedee "
Mutanan wajen aikin sune zasuzo duba shi gashi nacemasu yana gida yanzu haka suna hanya na kira Dr yace bari yazo.

Tsaki Deedee tayi tace dallah nasama wani abune.

"Kice basai yazo nan ba yasanya a dakko Adnan din inda aka kaishi akawo nan.
maza azo da wayan nan mazajen da suka kaishi suma.

Ihu Aymah ta fasa tana rungume Deedee da sumbatar goshinta kamin ta ɗauki waya ta kira Dr ta shedamai.

Shima rikicewar da Yayi baisa wannan tinanin yazomai ba saida ta faɗamai.

Cikin farin ciki ya juya akalar motar sa kuwa zuwa gidan bulo din daya dakko matasan.

Ganin motarsa yasa suka taso suna ihu.

Bai tsaya komi ba yace su shiga kawai.

Kai tsaye suk faɗa ya fara kwasar gudu kamar zasu tashi sama.

Cikin lokaci suka isa kauyen .

Inda yake suka isa suka iske ba'a dade damai wanka ba dan ya tika kashin safe.

Basu tsaya komiba yace su kwaso shi aka sanya mota yana ta harara Su.

Bayan sun shigo Cikin gari suka kaishi akai mai Aski tass aka gyara mai fuska kana sukayo gida.


Umarni ya basu akan su sake mai wanka.

Wanka sukamai mai kyau .

Deedee tace su samai Harda malum malum saiga Adnan kamar ƙadangare cikin Babba riga duk yayi wani iri.

Shinkafa da miya da Nama Deedee ta zubo ta aje kusa dashi sai zaro ido yake.

Murmushi Deedee tayi tace Noo inji turawa wannan duk cikin basajane irin wadda kake ma mutane.

Hon suka fara ji kamar za'a fasa gidan ashigi hakan yasanya Deedee aguje matsawa kusa dashi ta fara bashi abincin yanaci da sauri sauri.

Matasan nan suka fita suka budemasu get din tare da zama cen wajen, Yayin da Dr ya kara gyara zaman glass din sa da abin aune aunen dake sargafe wuyan sa .

Aymah ce cikin shiga ta kamala Hijjob har kasa ta fita ta masu jagora harda manyan shi suka shigo palon da ko kujeru Babu.

Wulcum shanaye inji Deedee tana murmushi.

Ɗaya daga cikin su ne yayi dariya da alama yajita yace Mama shanaye kuma.

Tace to ai naji tana ta cemaku wulcum sir nikuma ai ƙara inyi jimla karwani yaji zafin bancemai ba .
Sannu ku dai mala'ikun Duniya ga Abokin kunan Bakaken aljannu sun shanyemai Dukkan gaɓɓai yanzu haka bamu da komi agidan duk ta sayar wajen neman masa magani...

❤️ MATAR OGA NA ❤️

Mallaki
Ummy Aysha

Domin mallaka naki ki biya kudin ki ta account Number nah kamar haka
9064260199 Amina dahiru OPAY BANK saiki turo shedar biyan ki ta Whatsapp number nah 07038423451

Page 15

"Wani da ya hakimce tsaye Saboda rashin mazauni da alama ogan su ne ya kalli Dede ya gaidata cikin hausar shi data ke zau ta sakota wa yace "Mama ya mai jiki.

Deedee ta karkace saiga hawaye tace" Kabari kawai Yallabai abun babu sauki ciwon anne (Arne).

Lami lafiya fa yazo daga wajen aiki nima nazo ganin yar kanwata wato matar sa.
Yaji anata dukan kofa kason soja da fusata ya fita yaga wata mata tace ya sammata abinci batada abinda zataci.

Maimakon ya bata hakuri Aa saiya hau tsulamata mari dai yanda Wani makwabcin su ke faɗaman dayake yana wajen Abun ya faru.
Tom yana cikin dukan natane ta ɓacce shima ya faɗi nan Yana Rawar Banjo .
Haka dai Aka kawomana shi nan ciki muna kuka da tinanin ko pamalise ce Inji yan boko wato dai shanyewar Ɓaran jiki ya samai.

Wannan likitan shine nan Babba Asibiti yake aiki wato Asibitin kwarari .
Duk aune aune dai da Akai basu nunamana komi ba yadaice afitar dashi waje.
Yanzu haka yau kwanan mu biyu da dawowa dan gajiya sukayi suka koromu ko silifas bamu saba suka furgaɗomu.
Gashi ko magana Bayayi ma yanzu gabaki ɗaya kwara da Yana Haniniya irin Ta Doki,To yanzu ko Haniniyar sauro Bayyi hakadai Yake tamkar butum butumi na India.
Tom Yanzu dai sana'a na fara da zansamu murafawa kai Asiri aita nema masa Magani kaga sheda cen yanzu nadawo kasuwa Ah toh maula zanyi kwara inyi da karfina..

Dukkan su saida tausayin Dattijuwar ya tsargasu Dan sun hango mugun alhini a fuskarta gata da shiga rai.

Adnan kau soi rarraba ido yake yanajin kafurar karya da Wacce baison ko wace ba take keto mai.
Ya rabbi ka budeman koda bakina ne in karyata tsohuwar nan yace aranshi yanajin kamar ya fashe da kuka,Shida ko Chemis basu kaishiba amma Ance yaje kasar waje Yah Allah.

Ɗaya daga cikin sune ya kallai yace "Kuma kamar yanason yace wani abu Mama.

Deedee data dakko kayan sana'a ta tace" Yo ai haka yake wata rana ma gani zakai Yana zillo Kamar tsohuwar motar dataci Cikusoba.
To dai Ina ganin Aljanar ce kemai Cakulkulo..
Gashi fa Nan gani yake duk kun'mai tsaye kamar masu gadin jahannama yaganku Cikin kaya masu Ruwan ganye.
Yanzu bala'in tsoron mutane yake balle ku da zai ganku da yawa.
Kuma ina laifin ku shigo da dai-dai amma kamar zaku Rakiyar kansilan kauye ku shigo daki duka sai kace an'tadaku daga Asambali.

Dadama daga cikin su dariya suka hauyi dan akwai hausawa Sosai wayan da Basajin Hausar kaɗan ne.

Nan dai sukaita Alhini suna kuma jerama Dr tambaya yana basu amsa cikin natsuwa.

Babban ogan sune yace da DeeDee" Mama ko kina ganin mu maidashi Bariki cen kalkashin kulawar

Please Login or Register in order to submit comment