Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kaida ɓarawo hukuncinku ɗaya dan kayi satar maganata. kara cakaman wukar A ciki Yayi yakuma sata ya datseman Wannan hannu ya karasa yana gwadamasu guntun hannusa dake cikin riga..

Kuka Sosai Aymah keyi yayin da manager ke share hawaye Anya Adnan mutum ne kuwa..

Yacigaba da fadin..ganina cikin Wannan halin ya tabbatar mai da bazan sake rayuwaba nan ya jani har gab da gidan gonar Mahaifinki ya ajiyeni kamin ya kama gabansa tafiyar da yayi mai dogon zango.

Ni dai kam a labarin da naji nan wasu manoma suka tsinceni aka fadama mahaifinki nan aka zo aka kawoni Asibiti Cikin garin katsina. Babu wamd yabani ran tashi sai gashi cikin hukunci rabbi Allah yasa ina da tsawon kwana a gaba..wani zuwa da mahaifinki yayi ganina naita gamashi da Allah akan banaso Abokin sa yasan ina raye..

Yaso yaji dalili na fadamai dai ba komi in lokaci yayi zan fadamai.
Amamatu kinson bashi da matsala son jin abinda bakai niyya faɗamai ba.
Bai matsaman ba hakama bai faɗamasu ba, koda na warke gidan shi aka mayar dani ya sanya masu kula dani ana gadina.

Bayan naji sauki sosai mahaifinki yasa aka dawo dani cikin iyalaina saidai hankalina a tashe yake ina tinanin taya zan iya sanar dashi manufar wayan nan azzaluman akansa.
Wani lokaci nayi shiri asace nabi dare dan zuwa in samu mahaifin ki Muyi magana aka shedaman bakwa kasar naji zafi sosai dan sabon mai gadin nasama dakeman kallon kamar mugu abinda yaceman bazaku sake dawowaba sai nan da shekara goma.
Nakauji dadi nakumaji na natsu da hakan na dawo cikin iyalina na cigaba da aikin gonata nida yan uwana hankalina akwance dan nason bakwanan ko Adnan ya dawo bazai iskeku ba.
Bayan shekara biyar wani wanda nike ɗan samun labarin gidan mahaifin ki yakeceman wai an ɗaura Auran ki da Adnan kana kina shekara 20 Amamatu nayi kuka nashiga tashin hankali nayi jinya duk akan wannan Auran naki da bantaɓa tinaniba.

A binciken da nayi na gano cewa Ashe saida Adnan yayo Babban shiri ya tun kari mahaifinki .

Shikam Baban ki a sannan Babban burin shi kar ya sake ɓatama Adnan shiyasa duk abinda ya nema yake mai jiki na ɓari har auranvki duk mahaifinki baya hayyacin sa, ke karshema rabashi yayi da danginsa baki daya sai shi kawai, Alh hamzama watsar dashi sukai baƙi daya basu sake bi takan shiba.

Saida ya tabbatar ya ginu da dukiyar mahaifin ki kana ya fara tinanin kawar dashi dan ya ida mallake komi.

Sadda kika kammala karatunki mahaifinki ya fara shelar son kowa yaje mishi Walimar buɗe Asibitin ki, bayan naji labari nabi dare dan zuwa wajen shi sai dai banson wake lura dani ba wasu suka kamani suka kulle tsawon kwana biyu baci ba sha ajikin bishiya.

Da yammacin da nike niyyar kwana na farajin ihu dana saurara da kyau naji kuka Yarana ne biyu da Allah yabani mace da namiji sai mahaifiyar su nan aka kawosu gabana aka yar, Adnan ya bayyana da zafgegiyar wuka yana murmushi yace" Ali kenan babu abinda bansaniba agame da binciken da kake domin ni , Sai dai awannan karon bazan ma ko kwarzaneba bakin ciki zai sanya zuciyar ka bugawa suma wayanda kakeyi dominsu gobe war haka ana shirin kaisu kushewa koma an binne su.

Gama wannan maganar keda wuya ya sanya wuka yama matata yankan rago da yarana biyu yasa aka binnesu ko wanka ba amasu ba.

Aiko maganar shi tayi tasiri dan nima nan wutata ta ɗauke sawon lokaci ashe har taɓin hankali ya sameni dana dawo hayyacina ake faɗaman mutuwar Iyayen ki Aymah nayi kuka nashiga tashin hankali.

Ganin ba sarki sai Allah na dawo nan dajin ina rayuwa ba wanda na sani babu wanda ya sanni.
Kayan itace sune abincina.

Wani lokacin kuma in hakura in kwanta gabaki daya duniya ta juyaman baya Aymah Allah ya sakamana dan Adnan ya mana tabon da bazai goge ba...

Wani irin kuka Aymah keyi jikinta kau wane na Jameel ya riga da yayi zafi.

Manager ma kuka yake Sosai yace Baba naji dadi da taji daga bakinka ada tana ganin wani abun bazai yiyu Adnan ya mataba.
Dukiyar tama tace wai ta barmashi dan kawai tayi Alkawari yanzu irin wannan mutanan za'a barwa ƙaruwa?.

Murmushi Yayi yace wane shi Amamatu.

Manager ya kalla yace waya faɗama inda nike???

Kuka sosai Manager yayi kamin yace Baba nayi kuskure a baya amma a yanzu ina son gyara laifina watakil ku yafeman kai ko baka yafeman ba nima zankai kaina court ..
Nine wanda.....

❤️ *MATAR OGA NA* ❤️
UMMY AYSHA
PAID BOOK

PAGE 19


""Nine wanda ya dakkoma Adnan iyalin ka har inda aka daure ka, amma wallahi azeem bai faɗaman kashe su zaiba, ya dai sanar dani cewa Aima barazana dasu wacce zatasaka guduwa daga garin baki ɗaya..Baba ni yaron sane babu abinda ban saniba na Adnan, amma daga lokacin dayama wannan zalincin naji na tsane shi ina neman kuma hanyar da zanbi in gyra kuskurena,nasha wahala sosai kamin in samo inda kake dakyal wani mutun Almajirine yanzu daya kasance Aminin ka a lokacin shike baka labarin rayuwar gidan su Aymah ya bani wannan address din naka,Shima yace a nemamasa gafarar ka domin kuwa Rashin kudi ya kamashi ya zagaye yaci amanarka wajen sanar da Adnan bibiyarsa da kake Har abinda ya faru ya faru dakai..

Murmushi sosai Baba Ali yayi kamin yace" ba komi Allah ya yafemana ,kai kuma na yafema suma kuma dasuka rigamu gidan gaskiya Allah ya gafartama su ya yafemasu kura kuran su. Amma tabbas Aymah yau ba gobe ba sai dukiyar ki ta dawo hannu ki dan gumin mahaifin kine,Hakki kuma naki ne bana Adnan ba..

Dakyal ta iya ɗago idonta dan kanta da kirjinta masifar ciwo yake ta zubamasu ta kasa cewa komi.

Ganin haka yasa hankalin su tashi manager ya tashi yana faɗin ta taso sutafi amma jikinta yayi bala'in sanyin da ko yatsanta bata iya mikewa.

Addu'a sosai baba Ali yashiga yimata kamin A'hankali ta fara sauke ajiyar zuciya.
Cikin maganar ta da bata fita sosai tace" Baba dan Allah kabini muje gida ina so mu ida magana ne acen Banajin daɗi.

Sosai ya nuna rashin amincewar sa saida tasamasa kuka tare da bashi labarin su Deedee tace''.
ina so kai ka zameman uba inaso ka gyara Alaƙar dake tsakanina da yan uwan Baba na,har yanzu zaune tsaye bata kareba tsakanina da Adnan, ga matar sa dake shirin shigowa danma manager na dakatar da ita banaso ta fara zargin wani abu ayanzu kaine hujjana na karshe Baba dan Allah ta karasa tana rike kirjinta Sosai dake barazana rabewa..

Cikin gamsuwa da kalamanta ya mike zai dauki kayan sa kala guda wayanda biyune dama yake rayuwa dasu ,yau in yasa wannn gobe ya wankesu da ƙafa tinda ba hannu ya shanya.
Hanashi tayi da faɗin muje kawai Baba.

Dakyal suka fito daga Wannan jejin، sadda suka kawo bakin mota Aymah ko gani sosai batayi saboda bala'in jirin datakeji daga jiya zuwa yai taji abinda yafi ƙarfin tinaninta shiyasa duka yanayin ta ya sauya.

Hanya suka ɗauka tafiya kamar ba gobe Baban kanshi saida ya gaji.
***
Jameel kau farin ciki hana shi bacci yayi Asubar fari ya samu Mahaifinsa da maganar, Sosai kuwa yaji daɗi da fadin ta wannan hanyar kawai zaka sakama Aymah dan Allah ka rikeman ita a mana Jameel kaga yanda ta sadaukar da farin cikin ta akan naku.. .

In sha Allah yace yana dukar da kanshi.

Inna su ce tafito daga ɗaki.
Da sauri ya tashi ya koma daki tabishi da kallo dan duk taji abinda suka tattauna Murmushi kawai tayi ta zauna tace" yanzu Baban su kana ganin taya zai iya Auran Hajiya Aymah? mace yar gayu data tashi gidan hutu Jameel ko gidan da zasu zauna babu ,gashi babu abinda zai mata koda lefe ..

Shuru Malam Habu yayi yace .
Duka abin Aure na Allah ne , Insha Allah kuma nima gobe zanje nasamu Deedee muyi magana,in yaso gonar nan inje kauye da kaina asake sata kasuwa muga abinda Allah zayyi.

Amince mai tayi da addu'a Allah ya zaɓamasu Alkhairi...

Duk abinda suke faɗa akan kunnan Jameel sosai yaji dadi haka kuma sun bashi tausayi shawarar Dr Abba ta fadomai .
Nan ya ɗauki wayar shi ya kirashi akan yanaso su hadu su tattauna akan batun kasuwancin da yace...
Sosai kam Abbah yayi farin ciki inda yabashi izinin ya iskeshi officer dinsa yanzu.

Ba ɓata lokaci yayi wanka ya shirya ya kira Abokan sa ya shedamasu bazai samu damar zuwaba sai washe gari.
Fatan Alkhairi suka mai shikuma ya sallami iyayensa ya doshi hanya Asibiti.

Bayan sun gaisa yake sheda mai Amincewar sa akan bukatar da yataɓa zomai da ita dan yanaso da kanshi yayi hidimarsa ba tare da ya dorama iyayen sa nawie ba.

Yaji dadi sosai nan ya kira dan uwansa yashedamai harkar da Jameel keso ya fara amma bayaso abashi driver kai tsaye yake so ya tsundumashi cikin Harkar, ga 500k ya bashi gudumuwarsa halak malak Allah yasa masu Albarka.

Faɗamaku halin farin cikin da Jameel ya shiga awannan gaɓar ɓata lokacine domin kuwa har hawayen farin ciki yayi kyautar irin wannan zazzafan kudi lokaci daya ba dangin iya bare na Baba.

Dr Abbah kau lallashin sa kawai yake yana nunamasa muhimmancin taimakama wanda bashi dashi.
Tare sukaje gidan ɗan uwan Dr Abbah nan suka zauna suka fara gaisawa kamin ya fara masu magana.

"kaga yanzu man petur muke kaiwa Nijer sukuma su bamu gas.

Dr Abbah yace to kamar ya ake harkar Yaya Nura?

Gyara zama Ya Nura yayi ya fuskance su sosai yace a ƙallah million biyu zata iyamaka wannan harkar.
Na farko dai sai kasai mota ka kuma sai jarkoki uwa uba zaka sai man petur din ..
Misali
Duk jarka biyu in kabasu zasu baka jarka guda ta gas kai kuma in kazo nan Najeriya ka saidata zaka iya samun ribar 5k duk ga wannan jarkar,to saika lissafaman in ka kai jarka dari nawa zaka samu riba.?

Sosai kam suka gigice dajin wannan uwar riba dake shigowa.

Murmushi yayi yace. Amma fa akwai kalubale, saidai kamin ya afkama zaka iya mayar da dukkan kudin da ka kashe cikin sati biyu zuwa ukku mussamman in'ka samu Driver Arziki ɗan amana da bashi da wasa.
kalubale kuma shine kamawa da Costume keyi.
In suka kamafa shikenan sai dai hakuri da fatan Allah ya mayar da Arziki.

Cikin gamsuwa da bayanin sa Dr Abba yace" Amma dai yaya ai ba kullum zasu kamaba ko?

Murmushi yayi yace haba Alh ai da kaima saika binciko aikin ka, in'kau akace kullum muma da bamuyi ba.

Cikin farin ciki sosai yace.
Yayah munji zan bashi aron Million daya da rabi ya fara ,Kaga dana yana da 500 a wajena in yaso sai a fara masa ko zuwa sati mai zuwane.

Murmushi yayi yace Babu damuwa Abbah duk yanda kuke so kuma nima in sha Allah zan dubamasa cikin amintattun drebobina in bashi wanda zasuyi harka tare..
Jameel yace "Yallabai ko ni zan iya wallahi.

Da sauri Dr Abbah yace" A'a kai dai abar shi hakan sune masana harkar tashi muje iyaka kai komi yayana zai maka ka ganshi nan yafini ilimi nesa ba kusaba amma kuma baya da ra'ayin aikin gomnati sai wannan harkar amma fa wlh shine Attajirin family namu kaima haka nike fata kaxama kaf Family naka.

Rungume shi Jameel yayi Yanajin wani mugun kaunar shi har cikin ranshi.

Mikewa Yaya Nura yayi yana dariya ya haɗasu ya rungume cikin wayewa yace.
kai dai munbari kai tama mutane Allura, mukuma munfison kullum Bugun Abuja suyita shigo wa.
Kai kuma kanena Allah yasanya ka fara asa'a,Ka gabatar da istakhara kamin farawa, kana ka yawaita Addu'a ka dinga sadaka zakaga haske in sha Allah,...

Godiya sosai suka mai suka tafi suka shiga motar Dr Abbah.

Jameel ya fara mishi godiya ya tsaidashi yace.
Jameel harkar sirri zamuyi dakai.

Saida gaban Jameel ya buga jin wannna magana cikin mamaki yace bangane ba?.

Dan murmushi Dr Abbah yayi yace" Jameel inaso karka bari Aymah ta sani,inaso ka aure tane kana cikin wannan yanayin naka na Driver mota,Ina so yazamana iyayenka kawai zaka sanarmawa a sirrance dan su sama Albarka, kana in kuka yi auran ko haya ka kama muku ku zauna.
Agefe ribar da kake samu kaje ka samu katon gida Lafiyayye ka gina kai atsayema in dai kanaso zaka iya samu.

Cikin Amincewa da bukatar shi Jameel ya rungumes hi tsamtsam yace" nagano manufarka Allah yasaka da Alkhairi, in sha Allah haka za'ayi ita kuma Aymah inaso nan da watanni kalilan amana Aure, ko bata tareba wallahi inaso najita ƙalƙashin inuwar aure na.

Wannan mai saukine yace yana tada mota.

Cikin jin daɗi yace" muje gidan ta inaso na ganta.

Motar ya tada yana zaulayarsa nan suka ɗauki hanya suna isa motar manager na tsayawa .
Gabaki daya suka fito motar shida Jameel inda manager kuma ya bude motar shi shima ya fito idonshi cikin na Jameel.

Wani mugun tsuma jikin Jameel ya fara dan rass ya gane shi.
Ranshi ɓace yake nuna shi da hannu yace" ubanmi kazo yimata anan? Ko ina dukiyar matata take munafuki yayi kanshi gadan gadan.

Dakyal Babb Ali ya iya buɗe gaban motar ya fito Yana daga sandarshi yace" Kayi hakuri yaro komi zai tafi daidia wannan ba macuci bane kamar yanda kayi zato kaji...

Cak Jameel ya tsaya yayin da manager da jikinshi ya dauki rawa yace "Wallahi babu niyyar cutar Aymah a Rayuwata, gatanan ka tambayeta ya faɗa yana bude bayan motar.
Nan ta bayyana kwance tana sauke numfashi kadan kadan da alama Athma ta ce ta tashi dan sai haki take.

Cikin wata tafiya ta mazajen zakuna Jameel din yayi bayan motar inda yaganta cikin wannan hali.

Ya subhanallahi, faɗar tashin hankali da yaron nan yashiga a dai-dai wannan lokacin ɓata lokaci ne...

Domin kuwa idon shi ganemai yaadingayi kamar bata numfashi.

Wani irin ihun kuka yasa yayi kanta gadan-gadan ya cakumota yana fadin.
Aymah dan girma Allah da manzon sa kitashi ki faɗaman misu kai maki,karkiman haka kar ki tozartani, karki yaudari zuciyar data ɗauka so da amana ta baki , Allah ne gatana sai iyayena ayanzu bani da gatan kowa sai naki, Wallahi rasaki a rayuwata tamkar rasa rainane, karkiman haka kibamu dama mu mallaki juna mu haifi yara inma tafiyarce sai mutafi dan Allah, kibari murayu a kalkashin inuwar aure, Aymah nah dan Allah yafada jikin shi ko ina na rawa zufa na ketomai hawaye kam kamar an bude pampo..

Dr Abbah ne yaja shi yace.
ka dubafa tana numfashi Jameel bafa mutuwa tayi ba ,a halin yanzu ma taimako take nema jibi yanda numfashinta ke barazana barin jikinta ko dai tana da Athma ne?.

Baba Ali yace.
Tabbas tana da ita dan ba shakka ta gadeta ne wajen mahaifin ta, ba abin mamaki bane ace itama bazata rasata ba.

Kagani ko maza dakkota muje Asibiti Jameel kukuma kushiga ciki Deedee na nan yace da manager.

Baba Ali yace.
A'a bazamu shigaba zamubiku munason sanin halin da take ciki..

Jameel kau tinda yaji tana da rai bai sake bin takan kowa ba ,aguje ya saɓeta kamar baby sukayi cikin mota Dr Abbah ya rifamasu baya. Kai tsaye FMC suka nufa Emergency ganin su da Babban Dr babu wanda ya tsaya neman katin su.

Likitoci ukku ne akanta dan ƙoƙarin ceto numfashinta, Yayin da Jameel kuma keta safa da marwa yana Addu'a,, Gefe kuma tinanin miyatasomata da wannan ciwon yake , kana miye alakar ta da wannan manager Abokin mijinta nefa maci amana ,abu na karshe waye Wannan Dattijon, kana ina sukaje haka sukadai da wannan ranar?..

Dr Abbah ne ya dafashi yana goge zufar fuskar sa yace.
Gaskiya akwai matsala Jameel,Banson wace irin damuwa Aymah tashiga ba wacce ta fara neman taɓa lafiyar zuciyar ta,A yanzu haka maganar da nikema ba Athma da muke tinani bace ta tashi kumburine zuciyarta yayi abin babu dadin ji.
Mafita daya shine ayi gaggawa yimata aiki..

Ya Salam.
Jameel yace.

Ya rabbi ka rabamu da shiga tsaka mai wuya yace yana dararashewa kasa.

Yau garana dukiya,da yana da ita babu wata fargaba da zayyi ,koda kai zasuce zasu fita wata kasa amma ahalin yanzu ko maradi akace yaje bashi da wannan halin.

Manager da suke jinshi ya taso yakara neman bayani Dr Abba ya masa yace babu Damuwa A fara shiri kawai.

Dr Abbah yace. Tom Babu damuwa,Sana gaskiya inaga Deedee bazata iya da wannan jinyar ba dan abune mai wahala.

Jameel dai shuru yayi yana binsu da ido dan bashi da ta cewa.

Manager ya kalli Jameel ya kalli Dr Abbah ya dan ja hannusa zuwa gefe nan suka shiga tattaunawa na wani lokaci kamim su dawo inda yake yayi tagumi zufa sai ketomai take.

Jameel in sha Allah yanzu da an'fito Sallah azahar zamu daura maku aure kaida Aymah ,Kana Aikin ta gobe da asuba ne Allah ya bata lfy zamuje wajen Baban ka yanzu.

Ido kawai Jameel ya zubamai dan bashi da abin fada a daidai wannan lokacin.
Ganin halin dayake ciki yasa Dr Abbah kamashi suka zauna akan kujera ya hau lallashin sa da nusar dashi mahimmancin aikin da za'amata , ba wani abu bane mai wahala, ai an maka kagani ko?

Kai kawai ya shiga ɗagamai, Tare da mikewa yaje inda window wajen yake yayi tsaye amma baya ganin ta.

Ganin haka Dr Abbah ya kama shi suka shiga Ciki inda take kwance tayi wani kyau tayi fresh gashinta duk a balbaje ga na'urar shakar iska makale a hancinta.

Gefen da take ya matsa yayi shuru, inama ace tana zaune da kafarta akamai albishir din wanna auran da kullum yake fata.

Dr Abba kau Hannu shi yaja suka fito tare da neman excuse suka sake hawa motoci sukayi gidan Deedee inda suka isketa zaune ta buga tagumi ga Uban zobo data gama hadawa amma batasa fridge ba.

Suna shiga ta taso tana binsu da kallo da leka bayansu ta kece da kuka tace" Dan Allah ku nemoman yar marainiyata wallahi tin safe ta fita banson inda ta tafi ba...

*Babu editing bana da charge*

❤️MATAR OGA NA ❤️
MALLAKI
UMMY AYSHA

PAID BOOK NE .
Page 20


""Dr Abba yace .
kwantar da Hankalin ki Deedee Aymah na tare damu , Yanzu haka akan maganarta muka zo miki..

Zama tayi tana zubamasu ido ta kasa cewa komi.

Cikin natsuwa ya shiga koramata bayanin ciwon Aymah da aikin da suke so amata.

Ya salam ! Deedee kamar ta shiɗe tsabar masifar kuka..
Dakyal tayi shiru tashiga kwararo Addu'a neman dace wa Aymah akan aikin da za'amata.
Suna cikin magana ne sukaji sallama baƙin kofa.
Dr Abba ne kawai ya fita yaga iyayen Jameel ne da kuma Baba Ali sai manager.

Sannu da zuwa Deedee ta masu tana sake matsamasu da carpet gefenta.
Yayin da Inna su Jameel kuma ta dawo kusa da ita ta zauna.

Bayan an gagggaisa nan ta kalli su manager tana fadin" ban wayeku ba?.

Bayan sun gaisa nan ya fara bata labarin rayuwar da sukai da Adnan, da Baba Ali, kamin ya kara da cewa .. Mama wallahi nayi nadama mafarin kenan sadda Adnan yajeman da batun son sa Aymah ta rattaɓa hannu akan takardun kaddarata na bata wasu takaddun na bogi dayake ba Allah a ransa som baima gane ba.
Ita kanta saida ta kalle ni a lokacin tsawa na dakamata akan ta sanya.
Alakata da Aymah ta farane sadda Adnan ya kwanta wannan jinyar, a binciken da take a wayar sa ne take gano wasu abubun dayake nufatar ta dasu da irin magana da yakeman nason yanda ya tsara kassara dukiyar ta ina kara ɗora shi akan hanyar da yakeso.
Anan ita kumaa ta ɗauki number nah taman magana akan son sanin manufar da Nike da ita akanta,Taya zan bama mijinta shawarar akanta sannan kuma naki yarda na bata Original ɗin takaddun kaddarata yah haka miye nufina akanta? .

Saida na gamsu da itace. Nan na koramata bayani asace da son taman Alkawari babu wanda zaiji har sai a fara bincike akan wasu abubuwan da har yanzu bamu gane ba..
.
To Wannan dalilin ne yasa nayi tsayuwar daka wajen gano wasu ɓoyayyin sirrikan nashi har muka gano video da yasanya akaje akamasa lokacin da mota kebin takan iyayen Aymah.

Dukkan su saida suka share hawaye Jameel kau bakin shi karkarwa yake sosai.
Kai dole Aymah tayi jinya masifar nan ta isa ace mijinka, Wanda kuke kwana tare ku tashi, shike da manufar sharri akan ka Da iyayen ka .

Baba Ali ya numfasa yace" Adnan Akwai Hakkin al'umma sosai akansa ,sai dai fatan in mai shiryuwane Allah ya shirya shi.

"Ba Ameen ba Dattijo... Deedee tace a fusace tana fadin "kai dole matsiyacin nan yaji hukuncin duniya kamin na lahira.

Murmushi Baba Ali yayi yace "A'a Hajiya ya daifi abar shi da mahaliccinsa,Kamar yanda yayi ba tare da sanin kowaba haka ya kamata abar shi ya koma wajen mai sama zaima kowa sakayya dai dai da hakkin sa...

Malam Habu yace" haka ne Deedee dan Allah kiyi hakuri.

Kwafa kawai tayi amma ranta ya ɓaci..
Manager yace .
Yanzu Deedee wannan jinyar ta Aymah akwai bukatar adinga kulawa da ita, kana dukkan mu babu wani makusancin daya dace ace an'barta dashi,shine muka yanke hukunci hada auran su da Jamilu tinda ya tabbatar ma Dr Abba da amincewarta a daran jiya.

Kuzo kuga washe baki kamar ba ita ke kuka ba.
Hannu ta taɓaa tace.
Shikenan na amince Allah subhanahu wa ta'ala ya tabbatar da Alkhairi.
Nan ta tashi tashiga daki sai gata da kudi ta aje gaban Malam Habu tace'' Abada sadakin Jameel, da wannan 50k din Allah ya tabbatar muna da Alkhairi.

Godiya sosai suka shiga yimata nan suka mike da niyyar zuwa suyi shiri su wuce Sallah Juma'a daganan za'a daura auran kamin su dawo dan akwai bukatar zama da Adnan.

Fatan Alkhairi tama su suka fita suna tafiya manager ya bayar aka kawo kaji da cefane da kananun kayan abinci akan Ayi girki dan rabama Muta ne .

Nan da DeeDee da Inna su Jameel dake ta murmushi jin daɗi da Almajiran Deedee aka zage suka shiga aiki bakama hannun yaro, wannan zoɓon datayi dama batayi kunun Ayaba aka saka a fridge aka hau bashi wuta.

Dr Abba kau waya yayi ya shedama su Yaya nura Auran gaggawa daya taso ma Jameel,.

Ya shedami zuwan su in sha Allah cikin lokaci..

Daganan yaja shi suka tafi wani katafaran shago ya sawo mai wata farar shadda mai masifar kyau mai tsada da hula da takalma da agwogo ya biya wajen masu aski aka gyarama Jameel din fuska..

Duk da fuska tashi ba walwala amma zanso kuga yanda baiwar kyau ta bayyana ga bawan Allah nan.

Kai tsaye gidan Dr Abba sukaje anan dakin saukar da baki yabama Jameel din umarnin ya shirya shima bari yashiga ciki ya kimtsa..

Ba kuzari amma haka ya shiga ya watsa ruwa ya haɗi da Alwallah ya fito, mai kawai ya ɗan murza yayi zaune ya zubama mirro ido..

Shifa ba Auran ne ya dameshi ba , Ya ga ta tashi zaune da mazaunan ta shine fatan shi,zuciyar shi namai sakar abubuwa marasa daɗi dakesa gaban shi
Bugawa.

Guntun hawayen daya zubo mai ya ɗauke A'hankali yace.
" My wife zakiyi farin ciki da ni in sha Allah,da yardar Allah sai na gusar da dukkan damuwar ki,na maye miki gurbin bakin cikin da kika tsinci kanki da farin ciki,Nayi Alkawari da sanina bazan taɓa saɓamaki ba,Zan bada farin cikina domin naki,banason komi naki kawai ke nikeso,farin cikin da kika rasa daga yau zaki fara samun sa in sha Allah,I love you so much Sweetheart.

Dr Abba ne ya Turo kofar ya shigo cikin wata dakekiyar shadda Milk sai zuba kamshi yake...
Turus yaja ya tsaya ganin Jameel nata sambatu.

Kai ya gilgiza cike da tausayinsa kamin ya matsa wajen shi ya hau lallashi da nusar dashi mahimmancin ɗaukar ƙaddarata aduk sadda tazoma.

Sosai kam hakan yayi tasiri a zuciyar Jameel din ba kadan ba ya samu saukin raɗaɗin da yakeji nan ya tashi ya shirya shape shape.

Ya subhanallahi.
Wallahi ba kadyan ba kayan nan suka karɓi fatar shi, sun mai mahaukacin kyau ga wani fresh da yayi ,ya fito Angon sa sak.

Turare Dr Abba ya dauka ya shiga fesamai ko ina kamin ya gama suka fito suka shiga Sabuwar motar Dr suka dauki hanya Yana ta sake ƙoda kyan da Jameel ɗin yayi...


"Hmm Wai yau zan mallaki Aymah matsayin mata yace yana lumshe ido.

Murmushi kawai Dr Yayi yace.
Al'amarin Allah ai ba abun wasa bane, kana kaima ayanzu zakai amfani da damarka ta fannin ƙaryata tinani da take na ganin ka yaro ,Ka nunamata Yaron ma namiji ne...

Akaro na farko ya saki murmushi yana dan cije lips ɗinsa da taune na k'asan da karfi ya daga gira guda sama yana ɗan turo halshe kamar zayyi fito.

Dr Abbah ya juyo

Please Login or Register in order to submit comment