Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

auran manufa yayi da ita.akwai abinda yakeso bana tinanin yanason matar nan dan zaman da suke som babu kulawa balle ayi batun soyayya.


Shuru yayi kamin yace Allah ka warwarr muna baki daya.

Ameen Ameen tace .

Wayar shi ce ta fara Ring ya ɗauka da sallama cikin mutunci yace.
Barka da dawowa Deedee nah fatan kin dawo lfy.

Alhamdulillah

Muna asibiti yace cikin ladabi.

Ido ya dan lumshe kamin yace.

Jameelu'n ki.

Kwatance ya mata ya kashe wayar tare da cewa tofa Deedee ta dawo Baraka, Nason zatayi fada sosai mussamman in taji Abinda ya faru.

Baraka tace A'a gaskiya zamu fadamata kawai, ai uwace muna buƙatar Addu'a ta.

Kimanin 20mnt suka farajin hayaniya Malam Habu ya leko da sauri dan yana da tabbacin mahaifiyar tasa ce dan batabarin sai ta kwana.

Da sauri ya isa wajen masu gadin da suka hanata shiga sai zazzaga masu bala'i take hannuta rike da buta.

Yace Deedee nah Lfy?

Afusace tace barni da yan iska da sukayi kama da masu gadin ɗakin macizzai,yo macizzai mana sai wani juye juye suke suna kaɗa kawuna kamar jikokin an'gulu,Yo ya za'ayi suce bazan shigaba ganin jikana,Jikana a kwance ace bazanje na ganshi ba,Wai sunce ko.l wani abu na kawo Nace a'a.
sunce yanzu wanda zai shiga sai dai mai kai abinci to tinda bani da abinci na ɗakko buta masallaci in kaima jikana yayi Alwallah ya gaida mahaliccin sa akwai abinda yafi wannan Fa'ida? Amma dayake kafuraine na farko wai basu yarda ba narantse da Allah saina shiga ko duk in'fasamaku kawuna ku kwanta jinya asamu masu hana har iyayen ku zuwa munafukai Yo daɗi ke kawo bawa Asibiti ta karasa tana ɗakko katon dutsi da gayya ta jefoshi gefem mai gadi daya aguje kau ya Ruga yana rike kanshi.

Ta sake ɗakkowa zata jefo shima dayan ya ruga ta sanya hannu ta turo kofar tana murmushi tare da cema zugar dake bayanta ku shishigo kuga dangin ku kunji ko sai nima kuma jikana addu'a.Ai nayi aikin Allah na sadaku da yan uwanku marasa Lfy nason zan'samu Lada.

Aiko kamar jira suke mata da maza haka sukaita turawa kowa yashiga kamin ta karasa wajen Malam Habu daya rike kanshi yana murmushi da kallon ikon Allah.

Tace kai kuma miye ko jikin jamalun ɗin ne yasaka murmushi in ce ya warke..


Murmushi Yayi yace.

Ina kallon jarumar uwata datafi ta kowan.Jameel ɗin ki da sauki,Fatana dai Allah ya kara miki lfy Deedee tah.

Ameen tace tana Ganin masu gadin da ransu ke ɓace suna surfamata harara.

Dan murmushi tayi tace .
Kuyi hakurin Dan uwayen ku kunji ko,Kunson rikicin tsufa! eh nace kunson rikicin Tsufa, Dan Allah kuzo ku garkame get din kar akawomuna farmaki tinda na shiga kuci gaba da aikin ku ta karasa tana wucewa Malam Habu biye da ita yana Murmushi.


Tunda ta shigo dakin ake Nunata ana cewa itace tasa aka shigo .
Nan fa akaita gaida Deedee tana hura hanci da amsawa cikin isa kamin ta farabin mutane tanamasu sannu har suka shiga ɗakin da Jameel yake..

Ganin yanda yake yasata fashewa da kuka tace shikenan jamalun Deedee,Abu yakai ka kass,gashi an'ki sayen gonar wallahi yanda naje abanza haka na dawo a wofi.
Kowa na korafin yanda aka matsama gonar nan da sace sacen mutane shiyasa kowa gani yake jalli joga zai saima kanshi.

Baraka tamata bayanin an'biya kudin aiki.

Haɓa ta rike tace wannan wane dan aljanna ne ya biyasu ?

Nan fa Baraka ta karkace tana kuka tana fadamata abinda ta sani game da Aymah.


Koda ta gama Gabaki daya saitaga Deedee tayi shuru tsawon dogon lokaci kamin tace inane gidan nasu?

Nan baraka ta bata.kwatancen wajen.

Deedee tace karki damu Allah na tare da ita, kuma nima zanje har inda take in'sha Allah, Allah yasanya wannan taimakon datamana yazams silar warwarewar damuwar ta,Kukuma Allah ya maku zaɓin Alkhairi.

Ameen suka amsa Baraka ta tashi tayi gida dan samo masu abinda zasuci duk da babu kudi sosai hannunta ta riga tayi sayayya kayan abinci .

Ana gama sallah mangariba tayi Asibitin inda ta iske jameel ya tashi amma ko zama baya iyayi sai gadon da aka ɗan dago masa.

Kallonta yayi ta kalle shi tare da mai ya jiki.

A'Hankali ya amaa yace "tana ina?

Gabaki ɗaya suka kalle shi Deedee tace'' wa?

Ita
Yace yana cije baki.

Deedee tace'' Subhanallahi har anzo nan wajajen jamalu,Yaushe aljana ta aure ka da kake jajenta bamu saniba ?kodai zafin ciwo ne ?.

Kallon ta yayi yana cije baki kamin ya dan harareta ya kawar da kanshi yana lumshe ido ,gaba ki daya tinaninta ya addabi zuciyar sa,wannan ciwon ya mugun kwafsamai ,Bayan shi wallahi azeem da sai ya gwadama Alh Adnan sabon jini ke yawo a jikin shi dan sai yamai mugun dukan da bazai iya numfashi ba.
Amma ko gobe ya ɗauki Alkawari sai ya rama mata dan ko ta yafe shi bazai yafe ba.


Hajiya Aymah kake tambaya ne Inna su tamai magana tana zubamai ido.

Da sauri ya dagamata kai yana zubamata ido.

Tana.nan Lfy bata jima da tfy ba.

Kai k awai ya d'aga yana furta Alhamdulillah a ranshi.

Fira suka danyi banda shi daya lumshe ido.

sai karfe tara Deedee da Inna su suka tafi aka barshi da.mahaifin sa kawai.

Aymah.

Zata iya cewa tinda take bata taba ganin mugun mutum ba kamar Adnan, Dan duk halin da take ciki ko alama bai tankamata ba, har aka yi Sallah mangariba akayi isha yana zaune sai wajen tara ya mike yayo Alwallah ya hadesu kamar yanda ya tashi ya sanya key a palon ya dawo ya kwanta .

Aymah Ma a haka bacci ya tafiya da ita sai wajen karfe ukku ta falka Tare da yun kurawa ta tashi cikin ikon Allah taji daɗin jikinta sosai.

Wanka tayi da ruwan zafi sosai ta gasa fuskar ta kamin ta dawo bisa gado ta kwanta ta lumshe ido tana tunanin juyin rayuwa.

Washe gari

Jameel

Karfe Shidda aka shiga dashi theater room sai mumafasa fatan fitowa Lfy.


Aymah kau wata fitinanniyar yunwa ce ta tayar da ita .
Dakyal tayi wanka ta sake gasa jikin ta ta dan fito palo dan samar wa cikinta abinda zataci.

A'Hankali take tafiya har ta iso palo.

Ido da ido suka hada ya kawar da kanshi gefe yana amsa waya da sake tsuke fuska..

Ina kwana tace cikin sanyi.

Baiko am'saba ya juya kai.

Bayan tashiga kiching din ta hada tea na ruwan sanyi dan bazata iya dafawaba tasha abinta.

Tana cikin wanke cup din ne taji shigowar katuwar motar tanka har inda daga shi sai ita ke shigowa .

Glass ta dan zuge taga katti na fitowa daga ciki ,su dukan su da shigar banza.

Gabaki daya suka Dumfaro palon.

Hakan yasata watsar da cup din ta fito da sauri daidai lokacin da suka banko Kofar suka shigo...


Hajiyoyin kamshi akwaifa UMSAD INCENSE na nan tana muki sabon shirin turarukn ta msu kyau da dadi kun san komi basai na fada.ba
.❤️ *MATAR OGA NA* ❤️
*MALLAKI*
*UMMY AYSH*
*PAGE* 9️⃣


* Sosai jikin ta ya ɗauki ɓari ganin duk jikin su a murɗe.

Adnan ya ɗago ido yana kallon su kamin ya mayar akan wayar shi yace" kun kyauta da kukazo kan lokaci ku fara dana sama tass kamin ku sakko nan ko ku rabasu biyu.

Da" to" suka amsa wasu suka haura dakin shi wasu sukayi nata duka biyun suka fara kwance kayan'ta suna sakkowa dasu.

Daga lokacin data fahimci ya san su sai hankalinta ya kwanta ta ɗauki Hijjob ta sanya tare da lafewa gefe tana kallon yanda Saketa kwashe mata kayan daki .

Saida suka cika motar gam kana sauran suka fitar dasu waje suka fara zuwa kai wasu su dawo.

Tana nan zaune shima yana saman kujera suka gama kwashewa tass suka zo zasu fara kwashe kayan palon.

Tass nan ma suka kwashe har labule basu bari ba .

Ido suka haɗa da Adnan ya saki murmushi ita dai batace komi ba.

Duka saida suka gama suka tafi bayan ya sallame su.

Lokaci ɗaya komi na gidan ya dawo wani iri kamar kango.

Masu gadin yama waya yace suzo.

Bayan sunzo nan yace ya dakatar dasu su koma Bariki zasuyi waya.

Gabaki ɗayan su Amsawa sukai suka tafi suka kwashe kayan su sukai tafiyan su ya rage dagashi sai ita.


Dan kallon ta yayi yana wani lumshe ido da sakin murmushi yace.
*Aymah Abdulkarim Mai Dala*.

Tom yau ina Abdul kareem din ina kuma kudin ina uwar ina uban ina kuma izzar mahaifin naki? ina dukiyar daya wulakantani kanta yakimin alfarma Ya barta yana taramiki?
Tom yau gashi an wayi gari bana tinanin abun biyar kina dashi a gidan nan.

Ko akwai?

Kai Kawai ta d'agamai tana sake bude idonta akan shi.

Murmushi yayi yace.
gabaki d'aya na canzamiki tsarin gidan nan da kuma rayuwar ki,Inaso kiji yanda naji,Kana ki ƙare a haka har abada,Ke ba mai Aure ba ke ba zawara ba.
Aymah zan baki umarni kai tsaye wallahi wallahi kika tsallake saina kasheki.

Ido ta zaro da karfi tana kallon shi.

Yess zan kashe ki kamar kiyashi ba ubanda ya sani,Ba kowa gidan nan dagani sai ke.
In kuma kikayi yunkurun guduwa ..Hmm ya fada yana murmushi da faɗin aka kamoman ke wallhi saikin sani domin nasamaki matakan tsaron da bazaki taɓa ganin suba sai sai su Su ganki..

Kana wannan yaron shine kawai zai dinga zama gidan nan shima Akwai dabbobon da zan aje wanda shine ya cancanta ya kula da su dake da abincin da zakici ,Dan daga sadda zai samu sauki Ya dawo bakin Aiki kin gama girki sai sai A siyomiko na bakin Hanya da yaran talakawa keci..

Murmushi tayi tace.
Adnan bazan gudu ba,ko baka aje kowa ba bazan gudu ba,Saboda nason daraja Alkawari karka manta alkawari nayi,Mudddum bakai ka koreni ba bazan bar gidan kaba,So wajen wama zani in nabar Nan.

Yace Kimma kanki taimako ya ƙarasa yana mikewa ya shiga dakin shi da ba ko gdo sai doguwar kujera. wanka yayi ya shirya ya zauna ya fara nazari rayuwar shi ta baya da Mahaifin Aymah da duk Duniya Yafi kowa tsanar shi,Dole ya fanshe bakin cikin sa akan Yarsa.

**
Alhamdulillah Jameel anyi aiki cikin nasara sai fatan Allah yasa karshen wahala kenan.

Deedee tayi murna tayi kukan farin ciki lokacin da akacemata aiki yayi kyau Masha Allah.

,**

A'Hankali sauyin rayuwa ya fara kawoma Aymah farmaki inda ta koma kamar wacce ta samu matsala kwalwa gabaki daya ta daina magana.
To dawama zatai. Saita kwana batace komi ba,Iyaka zakaga tana sallah tana addu'a sosai,Adnan baya gabanta dan loi kayan kamshin data saya gabaki daya ta mayar da abinta jikka ta ajiye dan tagama tusa kanta inda ba kwarjini ,Duk abinda zata faranta mai yanzu bata son sa.
Adnan ya mata abinda ko shine autan maza dole ta barshi yanda yake da manufa wulakanci akanta ,bazatace ga abinda tamai ba Hakama iyayen ta.
Amma ta son ya fito yanzu ya gwadamata kiyayya zahiri kana kamar yanda tayi alkawari muddum baibata takaddaba bazataje ko ina ba daj bazata fita da dakon igiyar sa dake kanta ba.

Gabaki ɗaya ya fiddamata kaunar Namiji cikin rayuwarta saboda tana ganin kamar duk wanda zata samu abinda yamata shima haka zai mata.

Adane take da burin ta fita gidan shi ta sake aure amma ayanzu kam som Babu wannan tunanin cikin ranta.

Jameel.

Tinda akai mai aikin nan ya susuce ya dawo so silent,Kullum tinaninta yake abin har tsoro yake bashi ,kullum zuba ido yake yaga ko zatazo kamar yanda Maman shi tace amma ina har ya fidda rai gashi har an'kwana biyar .
Kullum nazari yake akata,da Tinanin mitake? wani lokacin ma zuciyar sa takan bashi amsa da kilan tanacen ana dukan ta ,In kau ya tino haka burkicewa yake yace sai ya tashi ya koma gida ya warke.
sai sunyi da gaske yake komawa ya kwanta yana huci.

Yauma data kama sati daya damai aiki kuma yau ake shirin sallamar shi.
Kwance yake akam gado daga shi sai gajeron wando da farar vest.
Fatar nan tashi tayi lumi tayi kyau na maji yaci.
Hancinshi ya kara wani tsawo hakama pink lips dinshi sunyi yarrr dasu alamar jinya yake.

Kanshi a sama ya zubama silin ido.
Bai an'kareba ya farajin saukar hawaye .

DeeDee dake kusa dashi ta fasa kuka tace.
" Kai jama'a jamalu nah ka daina kuka ko baka warke ba?.

A'hankali ya karkato da kan shi akanta zuciyar sa na zugi da bala'in zafi yace "Deedee nah inaso na ganta wallahi,inajin zafi,inaso nasata idona, Deedee minai mata da bata sake waiwayana ba, DeeDee ko fushi tayi tana ganin da gangan na barsa yana dukan ta Bankwace taba?Ki faɗamata zan rama mata wallahi azeem zan rama mata Deedee nah. Dan Allah kice tazo yanzu ya ƙarasa hawaye sosai na ambaliya akan kyakyawar fuskar shi.

Deedee ta sake kallon gefe da gefe dan kara tabbatar ma da ba kowa dan Inna su da Baban su suntafi su huta kamin tace".

Wai jamalun Deedee anya allura nan bata tabama kwalwaba,Nifa so ne nike gani cikin kwayar idon ka,Jamalu son MATAR AURE?MATAR OGAN kaface anya akwai hankali anan ta karasa tana ɗora hannu aka da Rusa ihu.

Cak ya tsaya yana kallon'ta kamin da kyal ya yunkura ya mike ya ɗan kama hannuta cikin balain sanyi kamin yace.

DeeDee nah" SO fa?
Wayace miki ?
Ni nace miki Deedee?
Deedee ya ake gane so dan Allah?


Cikim tausayi tace Jamilu wallahi azeem ka kamu da son MATAR OGA ka
Tausayinta ne yayi tasiri aranka har ya rikide ya komama SO mai zafi.
Bakai murna ka rabu da wannan uban cuta dayakai robar wanke shinkafa girmaba ,Fatan ka kawai ka ganta anan gaban ka sannan zakaji daɗi,idan ba so ba to miye?.

Cikin Karaya yace *Tausayine*
Deedee.

Murmushi tayi tace. Hmm amma dai kam akwai ƙura anan sosai.
Amma ba ason Abinda Allah yayiba wannan matar kau tabbas mituniyar kirkice,Kaf wannan kudin da akama aiki ita ta biya, silar haka kuma ta rasa duka dukiyar ta mai yawa,Nan ta shiga koramai bayani .

Batama ƙarasaba ya mike tsaye cikin tashin hankali yana neman tafiya.

Jawo shi tayi ya fasa wani uba ihu.


Cikin rawar jiki tace ka natsu Jameel wallahi wallahi ko rana ɗaya ne saina Ramama Yarinya nan Dukan da yamata .

Jameel kau bayajin ta gabaki daya idon shi ya rufe har wani jijjiga bakin sa keyi.


Cikim ihu ta kwallah ma DOCTOR kira.


Aguje kam ya shigo dan dama zaizo bashi takadda sallama.

Dakyal ya maida shi bisa gadon dan burkice mai yayi yana ihu mai gunza da faɗin saiya ganta.

Y salam Deedee tace tana dafe kanta.

Mama dan Allah bamu wuri inji DR.

Tashi tayi ta fita ya mayar da natsuwar shi akan Jameel yace" Abokina natsu ka saurare ni man.

Kallon shi Jameel yayi yana cije baki.

Murmushi yayi yace" kana sonta ne?


Ido ya dan zaro kamin yace" Aa nifa tausayi take bani ai Babba ce Kuma marainiya Bata da kowa!.

Sake murmusawa Dr nan yayi yace.
Ƙarami baya Auran Babba ne,Annabin mu ya auri Nana khadija data bashi shekaru kuma sukai Aure ,Akwai magana da zan fadama wacce zata zame ma hujja,akwai kuma taimkon da zanma duka rayukan nan biyu ma'ana kai da ita in sha Allah,Fatana dai kayi hakuri,ka kuma iya takon ka,karka bayyana Asirin zuciyar ka kai tsaye ,Saboda irin wannan abin da Mutumin nan kema baiwar Allah nan zai sanya mata ganin bakin maza ciki kuwa har dakai,Tinda a yanda naga ta damu ranar data bada kudin nayi tinanin ita zatai zaman jinyar ka,Bana da masaniyar an barta ko ba abar ta ba amma dai tabbas da saita zo sake ganin ka koda so dayana Amma shuru..

Kayi hakuri ka ida warkewa duka miya rage ?Dan'ma fa baka shan magani bakacin abinci da kwana biyune ko ukku na sallame ka.


Shuru Jameel yayi yana nazarin maganar shi ina shi ina son mace mai kudi Mai kyan Aymah,MATAR OGA NA fa kai ina ya faɗa a fili yana jujjuya kai .

Murmushi Yayi yace Ni kuma inaji ajikina kwana kusa zaka mallaketa tazama ƙarkashin kulawar ka inda rabo ta haifama yan Babys masu kama daku,Azahirin gaskiya kundace da juna Abokina...

Kunya sosai ta kama Jameel wacce saida tasa shi juya baya ya wani saki sassanya murmushi nan nasa daya daɗe Baiba ya wani lumshe ido da fadin anya,To taya?

Dariya sosai Dr yayi. har cikin ranshi yake tausayin su su duka , Amma in sha Allah mafita nata ɓullowa kota ina .
Haɗa mai komi yayi na maganin sa kamin ya kamo shi kaɗan kaɗan suna takawa suka fito .

Deedee ta zaro ido tace lfy?

Murmushi Yayi yace Zan aje Abokina gida ne Baba ki dakko kayan amfanin ku.

Baki ta washe tace.
" Kai Allah yamaka Albarka Ɗan lukuti, inaga yau zaka karya sihirin Aljanin Abokin shi,Yo miskilancin jameel yasa ko Aboki bashi dashi tin na yarinta da ya fada Rijiya ya rassu har yau baisake ba, kullum yana daki kamar mai jego,Yau kau gaka dashi abinda na dade banba Ai sai godiya.

Dariya yayi yace Miskili kafi mahaukaci ban haushi zan gyara miki shi kwana kusa.

Allahu yasha Yasha Dan lukuti.

Murmushi kawai Yayi dan in tana wani abu sai tabashi dariya yana son zama da Tsahhi yasha dariya ya kuma ƙaru da wasu labaran nada..


Yan kayan su da ba yawa ta halhaɗo ta fito dasu anata kallon su da Babban likitan da Bakowa yake kulawa ba.

Motar sa ya buɗe ya sanya Jameel gaba kana ya Buɗema Deedee Yan Kayan ya watsa su boot kamin yaja da bismillah suka dauki hanya Deedee na kwatan tamai.


Gab da gidan Aymah Jameel ya Kalle shi yace Friend Dan Daraja Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama ku tsaya naganta na mata godiya karamcin ta gare ni.

Cak Dr ya tsaya yanabin gidan da kallo kamin yace DeeDee kimasa jagora ku shiga ku fito na ƙarasa daku.

A'Hankali ya fito ta kama shi yana tafiya sannu sannu.

Faɗa Deedee ta fara dataga yanda suke tafiya taki karewa kamin su iso bakin palo .

Akan kujerar robar barandar Aymah ya zauna yana sauke numfashi dan yagaji ba karya amma fatan shi yayi tozali da kyakyawar fuskar ta mai cike da karamci da Kamala.

Deedee ta kwankwasa kofar shuru tsawon 10mnt kamin taji an ɗan Budemata.

Aynah ce cikin shigar rigar atamfa hijjob dinta har kasa ga cazbaha a hannunta.

Kallon kallo sukai kamin kuma tace sannu Inna ina wuni.

Deedee dake mata kallon tausayi tace lfy klau sannu.
Ni Kaka Jamilu Baraka ce, Ni na haifi mahaifinsa to munzo Muyi godiya .

Ido Aymah ta ɗan zaro kamin ta ce sannu Kaka sannu fa shigo.

Aa ba sai na shigo Ba Allah ya miki Albarka Ya kuma yaye matsalaki ya baki mafita cikin gaggawa, Allah ya maki Albarka yajikan Magabata..

Ameen tace cikin rauni kamin tayi
Shuru Zuciyarta na bugawa dan so take ta tambayi jikin sa amma bakinta ya mata nawie ,bataso ta sake kullah alaƙa da kowane Namiji duk girman shi duk karantar shi.

Jameel kau da tin sadda ta fito yakejin wani masifaffan faduwar gaba, ga zuciyar sa sai tsinkewa yake yakuma kasa daina kallon ta..

Kallo ɗaya yamata ya gane ta bala'in rame kuma tana cikin damuwa fatan shi kawai yaji tayi tambayar inda yake dan ya lura som batagan shi ba .
Yana so yanda Ya damu da ita yaji koya ne ta damu dashi.

Deedee tace to mungode sosai Allah ya biyaki ya kuma baki lada kana ya warware Damuwar ki.

Cikin sanyi tanayin kasa da kanta tace "Ameen Kaka nagode,Dan Allah ki gaishemin da Baba Baraka sosai asake bata Hkr akan abinda ya faru Shii..m..a.. ace mai Allah ...ya .sa..wake..y..asa..anyi ...a Sa'a takarasa a rarrabe muryarta har rawa take idon ta na cika da Hawayen data kasa gane ko namiye..

Sassanya murmushi mai sauti ya saki da saida yasata dagowa da sauri idon su ya sarke dana juna.

Gabaki daya saida Zukatan su ya buga da bala'in ƙarfi, kowa ya zubama Ɗan uwan shi ido,sunama junan su kallo mai cike da kewa da kuma bege.

Aymah ce tayi saurin kawar da kanta gwfe tana dan wasa da yatsun hannuta dan wani girma ya karamata da kwarjini.

A'Hankali tace "ya jiki?

Alhamdulillah yace A'hankali Narkakkun idon sa akan ta .

Ɗan dagowa tayi suka hada ido da sauri ya kawar da kai gefe itama haka .

Kanshi ya ɗan shafa yace "Hidimar da ki kaiman Allah ya maye miki gurbinta da farin ciki na hr abada,Zan miki Addu'a allah yabaki tukwicin Aljannah,Ngd sosai nazone na miki gdy ya faɗa yana mikewa dakyal yana dan Cije baki.

Ido ta lumshe dan ba karya kalaman sa sun ratsa mata zuciya, sun kuma sanyata farin cikin Da take jin tayi bankwana dashi Abadan..

A'hankali tace Ameen tnx u.

Baice komi ba ya fara ƙoƙarin tashi da kanshi.
Da kyal ya mike ya fara tako Dan ƙafarshi tayi mugun sanyi .
Gab da ita yawani turguɗe zai faɗi.

Da Karfi ta kwallah ihu tana Rarumo shi jikin ta gabaki daya, dakuma dukkan ƙarfin ta hankali tashe.

Wani irin tsalle zukatan su keyi lokacin da suka zubama junan su ido Yana tallabe A hannuta.

Deedee kau kamar ɗiyar roba ta hau Kif-kifta ido dan gani tayi yanda yayi kwanciyar aka tallabe shi kamar wanda zaisha Mama😄


( Weyyyy Hajja Deedee nasu ba irin naku bane)

Last free page in sha Allah

❤️MATAR OGA NA❤️
Last free page

UMMY AYSHA.
PAGE 🔟



**Aymah kau cikin bala'in sanyi tace."Sannu kar ka fama raunin ka ta ƙarasa tana ɗagoshi A'Hankali.


Ido ya dan lumshe mata yana gyara zaman riga shi kamin A'Hankali yana ɗangyasawa Ya fara takawa.

Wani irin tausayin sa sosai ya dirar mata Ahankli tace.
" zaka dawo bayan ka warke?

Cak ya tsaya kamin ya juyo ya kalleta yace "kina buƙatar hakan?

Cikin wata shagwaɓaɓiyar murya da batason tana da itaba tace .
Babu kowa agidan kuma ina jin tsoro .

*Subhanallahi! A karon farko wannan magana tayi tasiri akwalwarsa har ta motsa lfyr sa ta ɗa namiji.

Ido ya lumshe mata kamin ya ɗan fara tafiya dan tsayawa kamar tonuwar Asirin sane.

DeeDee ta kalle ta cikin tausayi ta kama hannu ta tace.
Miyasa kike so ya tsaya Ummu bakya tsoron dokar mijinki yabi ta kanshi Kamar yanda yabi ta kan iyayen shi.

A'Hankali tace.

Kaka inajin tsoro sosai na zamana ni kadai agidan nan, Babu tsaro ga halin da ƙasar nan ke ciki,Kana dama yace shikadai xai bari yanamun sayayya dan Allah karkuyi fushi in ya warke ki barshi ya dawo gidan nan.

Deedee ta kama hannuta ido cikin ido tace..
Kinaso na taimakamiki ki fita kangin rayuwar da kike ciki cikin ikon Allah koko bakya so?.

Cikin rawar baki Aymah tace
Zanso haka amma Kaka na riga da nayi Alkawari wa Kaina bazanje ko ina Ba .
Saboda bana da inda yafi nan ,kana dangina duk sun gujeni bazasu karɓeni ba,Kaka Biyar dinma da zan hau mota bana da ita kibarni kawai inga iyakacin Adnan..

Murmushi Deedee tayi tana karema gidan kallo kamin tace.
Shidin banza shidin wofi.
su Makashima sunyi yayin su sun shuɗe balle shi da ko Rabin su baikai ba A hatsabiban ci ,gamawa dashi har wani abune bari dai jikana ya warke xan maki zuwan kanki kwana biyu, Yo kwana biyu Mana dan yakin bana dare ɗaya bane.

Murmushi sosai Aymah tayi tanajin soyayya kyakyawar tsohuwar har cikin ranta.

Murmushi tayi tace ngd Kaka Allah ya kiyaye.

Ameen tace cikin sauri ta cimmasa tare da kama shi suka fara tafiya.

Sadda zai Fita get din ne ya dan juyo a sanyaye yayin da sukai ido hudu da Aymah dake bin Faffaɗan bayan shi da aikin wahala yasa shi buɗewa da kallo.

Ɗan kauda kai tayi cikin aji yayin da shikuma ya ficce suka fada motar Dr suka tafi har kofar gidan su ya ajesu .

Deedee tace ya shigo yace A'a zaizo da mangariba.

Godiya sosai Jameel yama shi yana dagamai hannu suka shiga ɗan madaidaicin gidan nasu.

Da sallama suka shiga Inna su na tuka tuwo Malam Habu na daka Daddawa sai firan su suke, Yayin da Autan ta ke Wanke'wanken .
Gabaki daya sunyi farin cikin dawowar shi dan Kabeer rungume shi yayi yanata kuka dan akwaishi da karara zuciya gashi yanason Yayan nasa.

Bayan sun xauna sun natsu Deedee ta ƙanƙan ce ido tace .
Wallahi wallahi sai wannan auran ya mutu ina mai shedamaku kwana kusa , Saboda yarinyar nan akwai jini ajikinta na yarinta wannan azabar da zai'bata itace zatasa ta zama Kwarangwol kamin nan ya saketa sannan kuma ne duniya zata juyamata baya dan baka da wanda zai auri sauran mutuwa.
Kai nifa dana hango palon nan sai Naga kamar babu ko labule!koko idona ne oho.
Inaji ajikina Muzguna mata zayyi, to aiko yayi a banza wallahi dan sai yaji a jikin shi Yaseen xanta hurama cikin shege .

Gabaki daya suka sanya dariya malam yace .
A'a uwata kiyi hakuri karkimasa wannan aikin kinji,Ki barshi wallahii ki zuba ido tin duniya Allah ke sakayya yanzu.
Badai dukiyar marayaba Hmm! zai tantance hatsabibancin ta gare shi.

Hahahaha Deedee ta shiga dariya babu ko

Please Login or Register in order to submit comment