Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

banza ba ne , mun jima mu na jiran wannan damar yanzu ya bata komai "

wata shegiyar dariya Mohammed ya yi ya fara takawa ya yi gaba ya na fadin " kar ka damu , wannan ne na farko kuma na karshe , dan babu wanda zai dawo da ga Makka a cikin su , kai dai ka tsayar da maganar auren ka da RIANNA kafin Malik ya bar kassar nan "
haka dai su ka ci gaba da tafiyar su su na hirar su ta makirci


▪AMIR


Ya na jin su Miram sun fita , ya dawo cikin parlourn
Malik ya na zaune inda ya ke ko motsi bai yi ba

a hankali Amir ya karaso cikin parlourn ya nufi sofar da ya tashi ya koma ya zauna ya na fadin " Ina son mu yi wata Magana "

a hankali Malik ya juyo ya kale shi ya ce " wace magana ? "

" wanene ya nemi auren RIANNA lokacin da ba na nan "

" Miram ne ! amma ta ce ba ta son shi , yanzu dai Akwai Sarki Abdoul Mujeeb ya nema wa yaron shi babba , Aymane auren ta , kuma mahaifiyar ku ta ce ta yarda ka san Abdoul Mujeeb yayan ta ne "

cikin nitsuwa Amir ya katse shi da cewa " na san da wannan dukka , ina son na ga Yaron , MALIKAT INAS da ita RIANNA sun yarda ? "

" yanzu dai ba ya cikin saudiya , ya tafi wani aiki a kassar Turkey , bayan Azumi ya dawo , RIANNA ta ce sai ta gan shi kafin ta yanke shawara , ka san yar uwar ta ka da mugun son maza ma su kyau shi ya sa ta ki yarda da Miram wai ya yi mata tsufa " ya kai karshen ya na yar karamar dariya

" kennan babban yayan Diya ne ? " ya fada cikin zuciyar shi

ya yi nisa cikin duniyar shi ya jiyo Muryar Malik ya na fadin " ya kamata ka je ka yi wa matar ban kwana yadda ya dace "

slowly ya juyo da kan shi ya kali Malik ya daga mishi gera guda ya na fadin " What do you mean ? "

yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " ka na nufin ba za ka yi mata ban kwana ba , kar ka manta cikin daren gobe za mu tafi "

" goben idan ta yi na yi mata " ya kai karshen ya na tashi da ga saman sofar ya nufi corridor
da kallo Malik ya raka shi har sai da ya shiga sannan ya saki wani dan karamin murmushi



❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤


(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥




💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀





👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑



【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】




Marubuciyar littafin
【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】





【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】





____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________



PAGE 10 ❤🔥






Amir kuma bayan ya koma bedroom din shi kai tsaye toilet ya nufa
jim kadan ya fito sanye da bathrobe da Allamun wanka ya yi
ya na fitowa ya nufi dressing room ya shiga
ko two minutes ba bai yi ba , ya fito da ga shi sai short , kai tsaye ya nufi katafaren bed din shi ya Haye ya yi rub da ciki , ya kai hannu ya kashe wutar dakin baki daya sannan ya lumshe idanun shi

ya dauki wajen good 30 minutes a haka kafin ya jiyo wayar shi ta yi ruri allamun shigowar sako , daman ba barcin ya ke ba

da farko har ya so ya share , amma wata zuciyar ta ce ya duba kar a je abu mai mahimanci ne

dan karamin tsaki ya ja kafin ya bude idanun shi ya kai hannu ya dauki wayar ya kunna ya kali screen din

wata number ce da a ka yi saving da sunnan * MY BELOVED ❤💍*
🤔🤔🤔 ku tsaya beloved ya na nufin masoyina ko na yi batan kai ? tommm wacece wanan beloved kuma 🤔🤔

a hankali ya kai hannu ya cire password din wayar ya shiga wajen Text ya fara karanto sakon ta kamar * Good night yaya Zayd di na ❤😚 *

text din ta ba karamin sanyaya mishi zuciya ya yi ba , har sai da lips din shi su ka dan motsa allamun ya so ya yi murmushi amma ya danne

a hankali ya fara typing shi ma ya yi mata reply da * Thanks ❤ Good night *
ni na zata da ya tura mata zai kashe wayar , kawai sai ya tsaya ya na kallon screen din har sai da ta yi mishi reply kamar haka " Thanks 💋 *
reply ya yi mata da * Okay ajiye waya yanzu tafi ki yi barci *

ko one minute ba ta yi ba ta yi mishi reply da cewa * kai ma ka tafi ka yi barci 😑 *
* shikenan sai da safe *
* yaya Zayd gobe za ka zo mu yi breakfast tare ? 🥺🥺 *
* eh zan zo *
* 🥳🥳🥳 yawwa yaya Zayd ni da kai na zan shirya mana breakfast , na tafi ma dan na samu na tashi da wuri , I LOVE YOU byeeeeee ❤ *
* bye *
ya na gama rubuta hakan ya kashe wayar ya ajiye saman bedside drawer ya na kallon wayar
da allamun ya na jiran sakon ta
sannu sannu har barci mai dadi ya dauke shi bai sani ba


* WASHE GARI ( misalin karfe 10 )


" Amir ! tashi Ammien ka na son magana da kai " Malik ya fada ya na dan bubuga kafar Amir da ke ta faman sharar barcin shi

a hankali ya fara motsi ya na karato adu'ar tashi da ga barci sannan ya ware idanun shi a hankali sai saman Malik da ke tsaye ya tsare shi da wadanan Hazel eyes din na shi

cikin magagin barci Amir ya ce " wai malam lafiya ka tashe ni ? "
" iyeeeee , lalle idon ka ya bude Amir , yanzu ni ka ke wa wannan tambayar ? Shikenan Tashi ka tafi Ammie din ka ce ke son yin magana da kai , ni zan wuce fada " ya kai karshen ya na juyawa ya fice bedroom din

ya na fita Amir ya sauko da kafafun shi kassa ya mike tsaye ya fara takawa ya nufi Toilet
jim kadan ya fito daure da towel a kugunshi , ya nufi dressing room kai tsaye
nan ma bai wani dauki lokaci ba ya fito sanye da jeans brown color da T-shirt white color , kafafun shi kuma , cikin wasu sneakers farare kal , ya saki wannan smooth hair din na shi , gashin shi yanzu tubarikallah ya toho har ya kai shoulder din shi , sai tashin kamshi ya ke

bedside drawer ya nufa ya dauki wayar shi ko duba ta bai yi ba ya saka ta cikin aljihu ya fice dakin ya fito corridor ya shigo parlour , kai tsaye ya nufi lift ya shiga ya sauko kai tsaye ya baro building din

ya nufi part din MALIKAT INAS
duk inda ya wuce sai dogarai sun sunkuyar da kai su na yi mishi barka da safya
in kuma bayi ne , sai sun zube saman guyiwowin su , su na gaishe shi har ya wuce sannan su tashi su ci gaba da tafiyar su

shi ko daya bai bi ta kan gaisuwar su ba ya nufi part din MALIKAT INAS , hankalin shi na wata duniyar ji ya ke kamar ya manta da wani abu mai mahimanci

a hankali ya motsa lips din shi ya na sallama ya shigo parlourn MALIKAT INAS
nan ya tardo ta zaune , ita da RIANNA da Nesrine duk sun yi zugum waje guda
su na jiyo sallamar shi su ka dago kai a tare su ka kali saitin kofar su na amsa mishi sallamar shi sannan RIANNA ta daura da cewa " Amir ina ka tsaya wai tun dazu mu na ta kiran ka a waya "

karasowa ya yi cikin parlourn ya na fadin " What happening ku ke kira na tun da safe ? "
RIANNA na shirin magana MALIKAT INAS ta daga mata hannu ta yi shiru sannan MALIKAT INAS ta ce " Je ka , ka gani da idon ka " ta fada ta na nuna mishi hanyar corridor

a hankali ya juya ya kali corridor din sannan ya juyo ya kali MALIKAT INAS ya na son ya yi magana ya shanye ya nufi corridor din kamar yadda ta ce

kai tsaye bedroom din Inaya ya nufa
a hankali ya sa hannu ya tura kofar ya na sallama cen kassan makoshi

ya na shigowa ya gan ta zaune tsakiyar gadon ta juya wa kofar baya ta sunkuyar da kai
a hankali ya fara jiyo Muryar ta cen kassa kassa allamun waka ta ke
karasowa ya yi cikin dakin ya tsaya dab da gadon ya na rike da hannayan shi a baya

murya kassa kassa ya ce mata " Barka da safya "
ba tare da ta juyo ba ta ce mishi " barka " a takaice sannan ta ci gaba da wakar ta

tsaya wa ya yi ya na kallon ta na wani dan lokaci kafin ya juya a hankali ya fice dakin
kai tsaye parlour ya dawo , ya nufi MALIKAT INAS ya tambaye " lafiya wai ku ka kiro ni tun da safe haka ? "

cikin bacin rai MALIKAT INAS ta ce mishi " Amir yanzun ne tun da safe , karfe 11 har da mintina ? "

shiru ya yi ya tsaya ya na kallon ta , tabbas ta na cikin fushi ba kadan ba , ga Dukkan allamu kuma da shi ta ke fushin

cikin nitsuwa ya ce mata " Ammie please calm down , me ya ke faruwa ne ? "

nuna mishi Dining room ta yi ta na fadin " tun karfe 6 ta shiga kitchen dan ta shirya maka breakfast , amma ba ka zo ba " Ta na gama rufe bakin ta ta ga juya a hankali ya koma cikin corridor din

bedroom din Inaya ya koma shi har ga Allah wlh ya manta da zancen breakfast din da za su yi tare , bare yau wani barci mai dadi ya dauke shi , ba dan Malik ya tashe shi ba da wuya ya tashi yanzu

a hankali ya sa hannu ya tura kofar dakin ya shigo ya na sallama cen kassan makoshi
ko motsawa ba ta yi ba ta na nan yadda ya bar ta , ta na wakar ta kassa kassa

gaban gadon ya karaso ya tsaya kamar dai da farko bai ce mata komai ba ya na kallon ta
sai da ya dauki lokaci a haka kafin ya zauna bakin gadon ya kai hannu ya daura saman shoulder din ta ya na fadin " Cutie ! "

" uhm " ta fada ba tare da ta juyo ba
" ba za ki juyo ba " ya fada ya na janye hannun shi da ga saman shoulder din ta

a hankali ta girgiza mishi kai ba tare da ya ce komai ba
hannu ya sa ya cire sneakers din kafafun shi sannan ya Haye saman gadon shi ma , ya koma gaban ta su na fuskantar juna ya yi irin zaman cin tuwo shi ma

ya na kallon face din ta ya ga uban hawayen da ke konce sama , ga wasu nan na zubawa bibiyu ga shi kuma ba kukan ta ke ba hawayen ne kadai ke zubowa

a hankali ya kai ya goge mata hawayen ta ya na fadin " hawayen minene wannan ? "
" komai ! " ta fada a takaice ba tare da ta kale shi ba
sai da ya gama goge mata hawayen ta sannan ya janye hannun shi ya ce " kin yi breakfast ? "

a hankali ta gyada mishi kai allamun eh
" yaushe ki ka fara yi min ƙariya "
" ni gaskia ce na fada maka , ka tambayi Ammie "
" shikenan , minene matsalar to ? " ya fada ya na dan lekon face din ta

girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " babu komai "
" dago ki kale ni to "
ba tare da ta dago kai ba ta ce " yaya Zayd don Allah tashi ka yi tafiyar ka "

dan zaro idanu ya yi ya na kallon ya yi mamakin abun da ta fada
" kora ta ki ke yi ne ? " ya fada

ba ta ce mishi komai ba ta juya ta sauko da kafafun ta kassa ta tashi ta nufi toilet da gudu ta shige ta medo kofar ta rufe
ta na shiga ko ta saki kuka mai cin rai har sai da ya jiyo sautin kukan

da sauri ya diro da ga saman gadon ya nufi toilet din ya tura kofar ashe ba ta sa key ba
ya na shigowa ya tardo ta zaune bakin bath ta sunkuyar da kai ta na kuka

nufar ta ya yi bai ce mata komai ba ya sa hannu ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya bar toilet din
ta na jin ya dauke ta ta fara wuntsila kafafu ta na fadin " yaya Zayd ni ka sauke ni "
bai dire ta ko ina ba sai saman bed din ta
sannan ya juya ya nufi door ta dauka fita zai yi kafin sai ta ga ya tura kofar ya rufe ya juyo ya dawo cikin dakin ya nufi bed din

ta na ganin ya nufo ta , ta yi sauri ta mike zaune ta juya daya geffen ta na shirin sauka
kafin ma ta sauko da kafafun ta kassa ya karaso wajen bed din ya riko hannun ta da karfi ya meda ta konta
ya Haye saman gadon , ya riko hannayan duka biyu da hannu guda a saman kan ta saman ya sa dayan hannun ya ware kafafun ta ya shiga tsakiya sannan ya kawo face din shi saitin ta ta

tsuke gera ta yi ta na fadin " yaya Zayd ka sake ni , na tafi "
" yi min shiru , yaushe ki ka fara meda min magana ? " ya fada sam babu wassa a tare da shi

turo dan bakin nan nata ta yi ta kauda kai gefe dan ba ta jure kallon cikin idanun shi
a hankali ya kai bakin shi saitin kunen ta murya cen kassan makoshi ya ce mata " i'm sorry , ba zan sake ba "

ya na gama fadar haka ya ji ta sauke wata nanauyar ajiyar zuciya
slowly ya saki hannayan ta sannan ya sauka da ga saman ta , ya koma gefe ya zauna

ya na sauka ita ma ta mike zaune ta na sa hannu ta na goge face din ta ta ce " ka san ba za ka zo ba shi ne ka ce min za ka zo , tun safe na ke jiran ka , amma ka manta da ni "

" ban manta da ke ba " ya fada ya na riko hannun ta
a hankali ta ta fada jikin shi ta rungume shi ta na fadin " ni na ma yi fushi da kai "
zagayo da hannayan shi ya yi a bayan ta ya rungume ta shi ma sannan ya ce mata " Shikenan sake ni tun da kin yi fushi , ni ma na yi fushi "

yar karamar dariya ta yi ba tare da ta ce komai ba ta lumshe idanun ta
a hankali ya yi geffen damar shi ya konta da ita a jikin shi , a hankali ya fara shafa bayan ta ya lumshe idanun shi , shi ma

nan take kamar da wassa barci ya dauke su a tare a haka su na manne da juna


▪AFTER SOME HOURS


sannu sannu har sai da su ka share wajen good two hours su na barci a haka
a hankali Amir ya bude idanun shi ya na karanto kalmar shahada
ya na bude idanun shi su ka sauka kan Inaya da ke ta faman barcin ta cikin konciyar hankali

a hankali ya zame hannayan shi , ya mike zaune a hankali ya kai hannu ya dauki Sneakers din shi ya saka , sannan ya mike tsaye ya dan juya ya kale ta na dan lokaci kafin ya juya ya fara takawa ya fice dakin , ya na fitowa parlour ya ga babu kowa
bai tsaya neman su ba ya sa kafa ya fice part din

har ya nufi building din su , wata zuciyar ta ce mishi ya tafi wajen MALIKAT AL'UMU
a haka ko ya juya ya nufi part din MALIKAT AL'UMU

bakin shi dauke da sallama cen kassan makoshi ya shigo part din
a tare Rouksar da Tesnim su ka kai kallon su wajen kofar su na amsa mishi sallamar

wani kyawatencen murmushi Rouksar ta saki , ta na shirin yi mishi magana ya riga ta cewa " Tesnim where is mom ? " ya fada ya na kallon Tesnim

" ta na wajen Mamie " ta ba shi amsa
gyada kan shi ya yi a hankali kafin ya juya ya fara takawa

da sauri Rouksar ta mike ta bi bayan shi
Tesnim na kallon ta amma ba ta ce mata komai ba har sai da ta fice




❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤


(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥




💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀





👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑



【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】




Marubuciyar littafin
【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】





【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】





____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________





PAGE 11 ✍📚







ya na tsaka da tafiyar kawai ya jiyo Muryar Rouksar a bayan shi ta na fadin " Amir ! Amir ! "
ko juyo wa bai yi ba bare ya amsa ta , har yanzu bai manta abun da ta yi wa Inaya ba , ita ba ta san da ya ga komai ba

da sauri ta sha gaban shi ta tare mishi hanya ta na fadin " Amir tun dazu fa na ke biye da kai , ka na ji na ka kyale ni "

kallon ta ya yi na dan lokaci kafin ya ce " ban hanya na wuce " ya fada dan ya fi karfin ya raba ta geffen ta dan ya wuce

kashe mishi murya ta yi ta na cewa " Akhie ni fa kawai gaishe ka na taho yi , ba na samun damar ganin ka , kuma Tesnim ta ce min za ku yi tafiya ko ban kwana ba mu yi ba " ta kai karshen ta na marairaice murya

a hankali ya lumshe idanun shi ya na furza iska da ga bakin shi kafin ya bude idanun shi slowly ya kale ta ya ce " okay ! yanzu zan je na yi sallat , zuwa yamma ki same ni a garden "

dan zaro idanu ta yi ta na washe baki ta ce " Da gaske ? "
gyada mata kai ya yi kafin ya ce " eh , zan iya wucewa yanzu "

da sauri ta koma gefe ta ba shi hanya
" thanks " ya fada cen kassan makoshi kafin ya fara takawa ya bar ta nan tsaye
tsaya wa ta yi ta na bin shi da kallo har dai ya bacewa ganin ta sannan ta saki wani makirin murmushi ta juya ita ma ta koma part din MALIKAT AL'UMU

Shi kuma Amir kai tsaye Part din su ya nufa , bai tsaya ko ina ba sai a floor na uku
ya na shigowa parlour ya tardo Diya zaune tare Malik su na hirar su kamar abokan juna

Malik na ganin shi ya ce " Amir ina ka shiga kuma ban gan ka a mosque ba yau ? "

ko sannu Amir bai ce mishi ba ya nufi corridor ya shige Bedroom din shi
ya na shiga Diya ya bushe da dariya ya na fadin " ran ka shi dade , ai ba zai iya fada muku ba , amma ni na san da ga wajen babyn shi ya ke "

dan tabe baki Malik ya yi ya na fadin " tooooo , abun haka ne ? amma ka ga dan rainin sens ya ke ce min wai shi ba ya son ta "

" Ran ka shi dade wlh ba gaskiya ba ne , Tun lokacin da ya sauke ido saman yarinyar nan ya kamu da son ta tsawon shekara shidda biyar yanzu , ka san yadda Izza ta ke bare ta hadu da Mulki..... " da sauri Diya ya rufe bakin shi ya na dan zaro idanu ya ma manta da wa ya ke magana

yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " When LOVE MEETS POWER , ba za ka ji da sauki ba "
ya na kai karshen ya na sakin wani cool murmushi dan abun ya tuno mishi tarihin soyayyar shi da MALIKAT INAS , shi ma da farko haka ta dinga yi mishi irin wannan jan aji , ita ga ta daughter din Malik guda

ya yi nisa cikin tunanin shi ya jiyo Muryar Diya ya na fadin " har yanzu ya kassa yarda da abun da ke cikin zuciyar shi , amma so dai Amir ya na mutuwar son yarinyar nan , izza ce ta yi mishi yawa ba zai iya bude baki ya ce ya na son ta "

" kenan jira ya ke ta ce ta son shi ? "

a hankali Diya ya girgiza mishi kai ya na murmushi ya ce " ta jima da ta fada mishi wannan kalmar ta so , amma bai karba "

cikin nitsuwa Malik ya katse shi da cewa " nan gaba kadan zai karba , tun da har ya karbe ta a matsayin matar shi ta sunna , kuma ya na son ta cikin zuciyar shi , nan gaba kadan zai bude baki ya furta mata wannan kalmar "

" in sha Allah ran ka shi dade , nan gaba kadan za ka fara ganin jikokin ka "

yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya ce " haba Diya ina wannan babyn za ta iya daukar Amir , ai shi ya san dalilin da ya sa bai karbi soyayyar ta ba , ba dan ba ya son ta sai dan ya san kan shi , ya san halin kan shi in dai ta wannan fanin ne , ba karamin jarabbabe ba ne , na san haduwa guda za su yi , ku tafi jinyar watanni "

dariya sosai Malik da Diya su ka yi a tare , kai gulma dadi 🤣🤣
hayala yau dai Malik da Diya sai da su ka bude wa Amir na shi zaman


shi kuma Amir ya na Shiga Bedroom din shi ya wuce kai tsaye cikin toilet
jim kadan ya fito daure da towel a kugunshi ya wuce kai tsaye dressing room
nan ma bai wani dauki

Please Login or Register in order to submit comment