Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

min Amir lokacin bai yi ba , abun naki iskanci ne ma 🀣🀣 )

a hankali ya kai hannu ya warware Madauri bathrobe din ta , sannan ya fida mata ita ya ajiye gefe
ya kai hannu ya dauki box din da ke a tsakiya , ya bude ya fido wasu underwear pink color ma su mugun kyau , ya saka mata da kan shi

sai da ya saka mata su sannan ya tsaya ya na bin ta da kallo kamar bakuwar shi
cen kuma sai ya kai hannun shi saman cikin ta ya shafa a hankali cikin ran shi ya ce " wannan dan karamin cikin nata , zai iya daukar babys di na kuwa ? "

kamar ta san abun da ya ke fada , sai ta yi yar karamar dariya ta ce " babu komai a ciki "

slowly ya dago kan shi ya kali face din ta ya ce " amma na kusa saka wani abun a ciki "
daga mishi gera guda ta yi allamun minene

bai ce mata komai ba ya janye hannun shi a hankali ya fido wata gown da ga cikin box din
gown din Sky blue ce mai mugun kyau ta sha stone har da wasu sarkoki a wajen kugu kwanin burge
kamar ko an awna ta zauna mata cib cib a jiki

bayan ya saka mata gown din ya bude box din da ke a sama , ya fido wasu sneakers farare kal irin na mata masu ratsin blue
ya sunkuya ya dago kafar ta ya saka mata da kan shi , da allamun ya san lambar da babyn shi ke sakawa dan Sneakers din sun shige ta dai'dai

bayan ya saka mata sneakers din , ya bude box ta karshe , ya fido wata Alkyaba fara kal , an yi mata zanen flowers da zare mai launin gold , ya saka mata ita
sannan ya mike ya riko hannun ta , su ka fara takawa su ka nufi dressing mirror a tare
ya kai hannu ya dauki wani perfume ya feshe jikin ta da shi sannan ya meda shi ya ajiye saman dressing mirror din

dago kai ya yi ya na kallon ta , Masha Allah ta hadu gaskiya kamar na sace ta na gudu
sai da ya dauki lokaci ya na kallon ta , sannan ya kai hannu ya rufe mata kai da hular Alkyabar ta , sannan ya kai lips din shi ya manna mata kiss saman forehead din ta ya riko hannun ta ya ce " mu tafi ? "

gyada mishi kai ta yi kafin ta juya su ka fara takawa a tare su ka baro bedroom din
bari mu leko su Miram na san kafin nan sun iso part din MALIKAT AL'UMU



β–ͺMIRAM



Zaune ya ke shi da Mohammed a parlourn MALIKAT AL'UMU
MALIKAT AL'UMU kuma ta na zaune saman Sofa one seater ta zuba musu ido

cike da kissa Miram ya ce " Ranki shi dade , mun tunkari Amir da wata magana , kuma gaskiya amsar da ya bamu ban ji dadin ta ba "

cikin rudu MALIKAT AL'UMU ta ce " To micece wannan maganar kuma "

Mohammed ne ya amsa mata da cewa " maganar Hawan shi Mulkin Saudiya , ya ce ba za a nada shi ba a matsayin Malik sati me zuwa har sai kun Kamala Idda tare da MALIKAT INAS ranki shi dade "

cike da izza MALIKAT AL'UMU ta ce " bai isa ba , Malik ba shi da wani magaji bayan shi , Miram , Mohammed , ku je ku fara shirye shiryen Nada shi Malik , ba za a bar kujerar Malik babu kowa a sama har tsawon Wata hudu , babbar matsala za mu fuskanta da ga wajen al'uma "

wani makirin murmushi Miram ya saki kafin ya ce " hakan zai fi ranki shi dade , sannan magana ta gaba "

cikin rudu MALIKAT AL'UMU ta ce " to ku ce maganar mai tsayi ce ? "

yar karamar dariya Mohammed da Miram su ka yi a tare sannan Mohammed ya ce " to ranki shi dade , kin san Amir kamar yaro ya ke a waje na , duk da bai bani matsayin uncle din shi ba ni zan rike nawa , ranki shi dade kin san a rana guda a ke Nada Malik tare da MALIKAT , ni kuma a sani Amir ya isa aure , mai zai hana ya auri yarinyar waje na Hafsat "

wani cool murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta ce " ni ba zan matsa wa Amir a kan ya yi aure ba gaskiya , Ku nada shi kawai a matsayin Malik duk ranar da ya fitar da matar aure sai a nada mishi MALIKAT din shi , in kuma ya yarda da Batun auren fine sai a daura a rana guda "

cikin nitsuwa Miram ya katse ta da cewa " ranki shi dade zai fi a aura mishi ita da wuri , kar a zo a yi abun kunya , kun ga Amir ba yaro ba ne , ya na da nashi bukatun , kar a je ya janyo mana abun kunya "

cikin rudu MALIKAT AL'UMU ta ce mishi " kamar ya abun kunya ? "

dan jinkirtawa Mohammed ya yi kafin ya ce " to ranki shi dade ban so na fada miki ba amma dole zan fada miki , mun tarda Amir tare da wata yarinya a part din shi , yanzu ranki shi dade da wani a waje ne ya ga wannan abun , zai iya Ι“ata mishi suna "

dan zaro idanu MALIKAT AL'UMU ta yi kamar ba ita ta kai yarinyar part din nashi ba ta ce " Nawfel din nawa ? "

gyada mata kai Miram ya yi kafin ya ce " ki yi hakuri ranki shi dade , dalilin da ya sa mu ka ce a yi auren nan da wuri kar a...... "

bai kai karshen maganar shi ba MALIKAT AL'UMU ta katse shi da cewa " Ya isa haka , ku je ku fara shirye shiryen nada shi Malik , batun auren kuma ku bar ni da shi "

cikin girmamawa su ka yi mata Sallama , sannan su ka tashi su ka bar part din ransu fari kal burin su ya kusa cika

su na barin wajen wasu , mata guda Uku da ba su wuce shekara 33 ba su ka shigo parlourn kowace sanye da Gown off-White , sun yi Rowling wani veil green a kan su , kowace ta na rike da tray su ka nufi Dining room

da sauri MALIKAT AL'UMU ta tseda su da cewa " Dada , ku kawo su nan "
wadda ta kira da Dada ta ce " An gama ran ki shi dade "
ta fada ta na dawowa cikin parlourn su ka ajiye tray din , sannan Dada ta tashi da gudu ta koma kitchen
jim kadan ta dawo rike da wani tissu irin tablecloth haka ta shinfida saman Carpet din tsakiyar parlourn
sannan su ka shirya kayan breakfast din a sama ni bayan Fruits da Tea , da bread sauran abubuwan sam ban gane ko minene ba dan a irin abincin mu ba ne na hausawa

sai da su ka shirya wajen tsab gwanin burgewa sannan ku yi wa MALIKAT AL'UMU sallama su ka bar wajen



β–ͺAFTER SOME MINUTES



sai da ta dauki wajen good 30 minutes ta na zaune a haka kafin ta jiyo Muryar Amir ya na yi mata sallama

slowly ta dago da kan ta , ta na ganin su ta saki wani kyawatencen murmushi , ba karamin kyau su ka yi ba , ya na rike da hannun babyn shi

Cikin Fara'a MALIKAT AL'UMU ta ce " Sai yanzu ku ka yi niyar tahowa ? "

cikin girmamawa Amir ya karaso Wajen MALIKAT AL'UMU ya sunkuyar da kan shi ya manna mata kiss saman forehead din ta ya na cewa " Good morning momy "

da sauri Ita ma Inaya ta ce mata " Good morning Momy "
yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta ce " Good morning my pleasures , kun tashi lafiya ? "
Amir ya amsa mata da cewa " Fine momy , na same ki lafya ? "

mike tsaye MALIKAT AL'UMU ta yi ta riko hannun Inaya ta na cewa " Kamar dai yadda ka ke gani ina lafya , ku zo ku zauna tun dazu a ka shirya muku breakfast amma sai yanzu ku ka iso " ta kai karshen ta zaunar da Inaya a gaban tablecloth din , ta zauna geffen ta ita ma
a hankali Shi ma Amir ya juyo ya nufi wajen ya zauna a daya geffen MALIKAT AL'UMU , su ka saka ta a tsakiya shi da Inaya

cikin So da kauna MALIKAT AL'UMU ta ce saka Inaya a gaba ta fara Ι—ura mata fruits

sai da ta kusa shanye wajen Rabin fruits din saman tray din sannan Amir ya ce mata " momy kar ki fasa min ita " ya fada da larabci

yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta kali Inaya ta ce " baby , za ki sha Tea ? "

girgiza mata kai Inaya ta yi cikin shagwaba ta ce " Oun oun momy ni na fi son fruits sun fi gina jiki "

juyo wa Ta yi ta kali Amir irin kallon nan na ka gani ko
tsuke fuska ya yi ya na kauda kai gefe cikin zuciyar shi ya na cewa " wannan matar za ta fasa min ita da fruits "

kamar ko MALIKAT AL'UMU ta san abun da ya ke cewa sai ta amsa mishi da cewa " ka na dai ji ita ta ce ta fi son fruits "

ya san da shi ta ke amma sai ya shanye bai juyo ba , ya Ci gaba da shan Tea din shi cikin nitsuwa

sai da su ka dan jima a haka kafin Inaya ta kali MALIKAT AL'UMU ta ce " momy ina Aunty Tesnim ta ke ? "

" Su na garden ita da Friends din ta " MALIKAT AL'UMU ta ba ta amsa

cikin harshen larabci Amir ya ce ma MALIKAT AL'UMU " har yanzu yarinyar nan ba ta koma masarautar su ba ? "

" wace yarinya kuma ? "

cikin ko in kula Amir ya ce " wannan mai idanun maciji "

dan zaro idanu MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta ce " Allah ya tsare mu to , Amir na san Halin ka fa , wlh ka bawa Rouksar lafya , me ta yi maka ? "

shiru ya yi bai ce mata komai ba amma cikin ranshii har yanzu ya na jin haushin ture Inaya da ta yi har ta fadi gown din ta ta yage bai manta da ranar nan ba

ya yi nisa cikin tunanin tunanin shi ya jiyo Muryar MALIKAT AL'UMU ta na tambayar Inaya in ta koshi
cike da Shagwaba Inaya ta ce mata " momy ciki na na ya cika kamar zai fashe "

MALIKAT AL'UMU na shirin magana Amir ya riga ta cewa " Sai da na ce miki kar ki cika ta da Fruits " ya fada da larabci

salati MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta juya ta kali Amir ta ce " Nawfel ba na son shirme fa , shi ne za ka gwada min kai ma ka damu da matar ka "

" ni fa gaskiya ce na fada miki "

dan karamin tsaki MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta juya ta kali Inaya ta ce " Shikenan baby , tashi ki je wajen Ammie , na san ta yi kwana biyu ba ta gan ki ba "

gyada mata kai kawai Inaya ta yi ta na murmushi kafin ta mike tsaye ta fara takawa ta nufi kofar fita parlourn

har ta kai bakin kofar ta jiyo Muryar MALIKAT AL'UMU ta na cewa " ni gaishe min da ita idan kin je "

da to Inaya ta amsa mata ba tare da ta juyo ba ta ficewar ta
da kallo ya rakata har sai da ta fita sannan ya sunkuyar da kan shi ya ci gaba da shan Tea din shi ,
[28/09 Γ  09:35] +234 806 127 3970:




❀⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❀


(LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯




πŸ’”πŸ₯€ ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) πŸ’”πŸ₯€





πŸ‘‘β€ MALLAKIN MEERAH β€πŸ‘‘



【THE ROYALTY LOVE πŸ‘‘πŸ•ŠπŸ’–γ€‘




Marubuciyar littafin

【TAURIN ZUCIYA πŸ’–πŸ’πŸŒΊγ€‘





【 BOOK …………………… 2 ❀ πŸ‘‘γ€‘





____________________πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š___________________





PAGE 20 βœπŸ“š





babu wanda ya ce ma wani ufan har sai da Amir ya Kamala Breakfast din shi , MALIKAT AL'UMU ta kira su Dada su ka gyara wajen tsab

zaune ya ke saman doguwar Sofa , ya daura kafa daya bisa daya ya na latsa wayar shi

MALIKAT AL'UMU kuma ta koma saman sofar ta one seater ta zuba mishi ta na murmushi har ga Allah ta na mugun son gudan jinin ta , specially yanzu da mahaifin shi ba ya nan , sai ya yi mata mugun kama da Malik a lokacin da su ka yi aure

wani murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta ce " Amir Next week za ka hau kujerar Mahaifin ka , ka sani ko ? "

ba tare da ya dago kai ba ya ce mata " na sani , amma na ce su bari har ku Kamala Idda "

" why ? " MALIKAT AL'UMU ta tambayeshi

" ba na jin zan iya hawa kujerar Mulkin nan babu ke a kusa da ni "

wani cool murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta ce " Nawfel , duk lokacin da ka bukaci shawara ta ina nan mana , amma bai dace ba a ce Malik ya rasu kuma ya na da magaji amma a bar kujerar shi babu kowa a sama , hakan bai taba faruwa ba "

slowly ya dago kan shi ya marairaice fuska ya ce " yanzu momy ba za ku bari na kamo wanda ya yi wa Daddy haka ba , yanzu shikenan ya ci bilis kenan ? "

girgiza mishi kai MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta ce " kar ka damu General Abdellah ya na kan harkar yanzu haka , nan da lokaci kadan za su kamo shi , Idan ba ka hau Kujerar Mulkin ba , ko an kamo shi babu abun da za ka iya mishi saboda doka a hannun Malik ta ke "

ajiyar zuciya Ya sauke kafin ya ce mata " Shikenan Momy , a fara shirye shiryen na yarda zan karbi Mulkin "

" Alhamdoulilah " MALIKAT AL'UMU ta fada cikin zuciyar ta ta na murmushi
sannan ta ce mishi " Maganar MALIKAT kuma fa ? "
daga mata gera guda ya yi allamun bai gane ba

" ina nufin Yarinyar nan za a nada a matsayin MALIKAT ko kuma ka na son ka kara aure "

" why zan kara aure ? "
" ganin na yi yarinya ce , da wuya mutanan Fada su yarda a nada matsayin MALIKAT "

meda kallon shi ya yi kan wayar shi sannan ya ce mata " ba na bukatar amincewar su "

" Duk da hakan , me zai hana ka kara wani auren "

ba tai karshen maganar ta ba ya katse ta da cewa " momy ni fa babu aure a tsarin rayuwa ta , ko wannan kaddara ce kawai ta hada mu , kuma da ga ita ba zan kara wani ba " ya fada don shi har ga Allah ba ya tunanin zai iya auren wata macen a wannan rayuwar , ko ba dan ra'ayin shi ba , ba zai iya yi wa Inaya kishiya ba

( Ku ba shi hannu don Allah 😭😭 Gaskiya ka rike amanar malam , na san da wani ne sai ya yi hudu ma 🀧🀧 )

wani cool murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta ce " Na gode , ni ma ba na son maganar ka kara auren , da karancin shekarun ka ba zan so hankalin ka ya rabu tsakanin mata biyu ba , amma zan so yarinyar nan ta daina zuwa part din ka har ranar da za ka gabatar da ita a matsayin MALIKAT "

slowly ya dago kai ya kale ta ya ce " Why ? "

dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " ka ga ba mu kadai ba ne cikin masarautar , Kuma bayan mu ba wanda ya san ita matar ka ce , hakan zai iya janyo maka kananun magana , zan so ka bar ta a waje na har ranar da za a nada a matsayin MALIKAT sai ta tare a part din ka baki daya "

gyada mata kai kawai ya yi allamun to , ko shi zai so ta tare baki daya a part din shi

wani cool murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta ce " kafin nan fada min ka na son yarinyar nan ko kuwa ? "

" me ya sa ki ka min wannan tambayar "

" nothing , kawai na lura ne yadda ka damu da ita kamar rayuwar ka , shi ya sa na tambaye ka ko ka na son ta "

" momy dole na damu da ita saboda ita ce rayuwa ta , idan ba ni son ta zan aure ta ne ? "
yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta ce " Shikenan , ina jiran jikoki na tom "

dan zaro idanu ya yi ya na kallon ta wane jikoki kuma ? shi fa sam bai shirya haihuwa yanzu ba , at least nan da shekara biyar ya fi son har babyn shi ta kara girma yadda ba za ta samu matsala ba wajen haihuwa
ita dai MALIKAT AL'UMU shiru ta yi ta na kallon shi ta na murmushi



β–ͺINAYA



da sallama a bakin ta , ta shigo parlourn MALIKAT INAS
babu kowa a parlourn Sai Aymane ya na zaune ya na latsa wayar shi
kamar ba ta gan shi ba ta wuce kai tsaye corridor
ta na tsaka da tafiyar ta ta jiyo Muryar shi ya na fadin " Ke ina za ki je ? "

cak Inaya ta tsaya ta juyo a hankali ta kale shi saman da kassa sannan ta tsuke fuska
dan tabe baki ya yi kafin ya ce " ke ina za ki je ? " ya fada da larabci

turo dan bakin nan nata ta yi ta na ce mishi " ni ka min magana da turanci , ba na jin larabci ! "

dan karamin murmushi ya saki kafin ya ce " Okay come here "
dan karamin gunguni ta yi kafin ta dawo a hankali cikin parlourn ta tsaya gaban shi dan nesa kadan ta rike hannayan ta a baya ta ce " ga ni "

Tsaya wa ya yi ya na kallon ta da ga sama har kassa , ya saki wani makirin murmushi kafin yace " what is your name ? "

cikin shagwaba ta ce mishi " Inaya Ibrahim "

dan gyada kan shi ya yi kafin ya ce mata " me ki ke yi a nan ? "
dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " wajen Aunty RIANNA , da Ammie na zo , kai wanene ban taba ganin ka a nan ba "

kwatancen murmushi ya saki kafin ya ce " ni abokin RIANNA ne , zan iya zama abokin ki ? " ya kai karshen ya na mika mata hannu

gyada mishi kai ta yi ta na shirin mika mishi hannu ita ma ta ji an rufe mata idanu ta baya
yar karamar dariya ta saki kafin ta ce " Aunty RIANNA , na yi kewar ki sosai "

murmushi mai dan sauti RIANNA ta yi kafin ta saki idanun Inaya ta tako ta koma geffen Aymane ta zauna ta na cewa " sai yau ki ka tuno da Auntyn ki ko ? "

turo dan bakin nan nata ta yi kafin ta ce " Aunty fa duk shekaran jiya ne fa na tafi kuma ai ke ki ka ce na tafi "

yar karamar dariya RIANNA ta yi kafin ta ce " Shikenan na ji , shiga ciki Ammie ta na nan "

gyada mata kai Inaya ta yi ta na murmushi sannan ta juya ta nufi corridor ta shige abin ta
sai da ta shiga sannan Aymane ya juya ya kali RIANNA ya ce " Who is She ? "
dan karamin murmushi RIANNA ta yi kafin ta ce " she is my sister , Inaya "

" but a sani na Amira Tesnim ita kadai ce kanwar ki "
gyada mishi kai ta yi kafin ta ce " Eh " a takaice kafin ta sunkuyar da kai ta fara latsa wayar ta

dan karamin murmushi ya saki kafin ya ce " Mrs Aymane , batun auren mu kuma fa ? "

ba tare da ta dago kai ba ta ce " Duk lokacin da ku ka shirya "

" okay , me zai hana a yi auren ranar da a ke nada Malik ? ko ya ki ka gani "
" uhm no wonder " ta fada a takaice

cikin sanyin murya ya ce mata " please RIANNA , ki ban hankalin ki mu yi magana , Idan ba ki son auren nan ki fada min tun kafin mu yi nisa "

slowly ta dago kai ta kale shi ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " kar ka damu , kawai dai ba na jin dadi zan rabu da family na , zan rabu da Amir bayan tsawan shekarun da na yi ba ya tare da ni "

dan karamin murmushi ya yi kafin ya kai hannu ya riko nata ya ce " za ki samu Sabuwar Family , kuma zan kasance tare da ke , zan so na barki cikin ahalin ki , amma kin san ba dai'dai ba ne "

" please mu zauna a nan mana , akwai part dayawa cikin masarautar nan da har yanzu ba a bude su ba , me zai hana mu zauna a nan , ba na jin zan iya rabuwa da Amir , specially yanzu da zai hau mulkin Malik na san zai bukace ni a kusa shi "

marairaice fuska ya yi ya na fadin " masarautar tawa kuma fa ? Family na za su ga kamar ba za ki iya zama tare da su ba ne , ni na rassa ya zan yi wlh , auren nan sam ba ya cikin tsarin rayuwa ta , amma kuma da na gan ki na ji na kamu da son ki , kuma ba na jin zan iya janye maganar auren nan "

dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " shikenan ba komai " ta kai karshen ta na janye hannun ta da ga cikin nashi

wani cool murmushi ya saki kafin ya ce " ni zan tafi "

gyada mishi kai ta yi kafin ta ce " amma za ka dawo gobe ko ? "

daga mata gera guda ya yi ya na cewa " ba za ki iya yin kwana guda ba ki gan ni ba ko ? "

yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " shikenan tashi

Please Login or Register in order to submit comment