Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Gyada mata kai kawai ya yi da ga haka ya juya ya bar wajen
Dan karamin murmushi ta yi ta na sunkuyar da kai

Bangaran AMIR kuma ya na fitowa ya ci karo da Azim
Da sauri Azim ya Zube saman guyiwowin shi ya na fadin " gaisuwa na ke ya shugaba na , Allah karre mana yarima , dan sarki jikan sarki , duk mai taba ka mutuwa ce makomar shi "

Cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " ya isa haka Azim , me ke tafe da kai "
" ya shugaba na , MALIKAT AL'UMU na son magana da kai "
Takawa AMIR ya yi ya fara yin gaba , da sauri Azim ya mike ya bi bayan shi dan nesa kadan dan kar su zo dai'dai

Sai da su ka dan yi nisa da part din MALIKAT INAS , ya wuce part din MALIKAT AL'UMU sannan ya ce ma Azim " ka shirya min zama da ita a garden ina zuwa "
" an gama ya shugaba na " Azim ya fada ya na sunkuyar da kai kafin ya juya

Shi kuma AMIR ya nufi Building din shi , kai tsaye hawa na uku ya nufa ya koma bedroom din shi , ya na shiga ya wuce toilet dan ya yi wanka

After some minutes ya fito sanye da bathrobe , ya wuce dressing room
Jim kadan ya fito sanye da trouser Navy blue , da Shirt white color , ya daura wata alkyaba fara kal da ga sama , duk da bai da gashi dayawa a yanzu sai da ya sa wata yar pin ya daure shi a baya sannan ya daura hular Alkyabar shi , sai tashin fitinannan kamshi yake yi

A haka ya sa kafa ya fito bedroom din , kai tsaye part din ya fice baki daya
Duk inda ya wuce sai ma su tsaro sun zube saman guyiwowin su , su na gaishe da shi
Bai bi ta kan gaisuwar su ba ya nufi wani tanpasheshen garden
Cike ya ke da ciyayi da flowers , sai wata yar hanya da za ta sada ka da wata katuwar runfa dauke da wasu lamusasun sofas farare kal guda hudu uku two seaters , daya kuma three seaters , geffen kowa ce sofa akwai wata yar karamar table ta glass , da ga tsakiyar su kuma an shinfida wani kyakyawan carpet Fari kal mai ratsin ruwan gold gwanin burgewa
Duk wajen zagaye ya ke da dogarai , da guards rike da gun

A haka ya karaso kassan runfar inda ya tardo MALIKAT AL'UMU zaune saman sofa three seaters , ga yar karamar table gaban ta dauke da wani tray shake da fruits

A hankali ya motsa lips din shi ya na sallama , wadda shi kadai ya ji kayan shi
Sannan ya nufi sofa two seaters ya zauna ya na fadin " Good morning momy "
Daga mishi hannu ta yi ta na matse fuska ta ce " na yi fushi da kai "
Cikin sanyin murya ya ce mata " Momy me kuma na yi ? "
Hararrar wassa ta yi mishi kafin ta ce " where is My morning Hug ? "

Maganar ta ta , ta so ta ba shi dariya ma amma sai ya danne kayan shi ya tasso a hankali ya koma geffen ta zauna sannan ya rungume ta

Wani kyawatencen murmushi ta saki kafin ta ce " Na yi kewar sosai ka sani ko ? "
Ya na shirin dagowa da jikin ta , kawai ya ji an fado mishi a baya
Ko bai duba ba ya san ko wanene hakan ya sa shi cewa " tashi kar ki karaya min baya "

A hankali ta tashi ta na yar karamar dariya ta ce " ina kwana Akhie "
Raba jikin shi ya yi da na MALIKAT AL'UMU kafin ya tashi ya koma saman sofar da ya taso

" Akhie wai su wanene yaran nan da ka taho da su ? " TESNIM ta tambayeshi ta na gyara zaman ta saman sofar

Koma wa ya yi ya jingina bayan shi a jikin forehead din sofar ya daura kafa daya sama daya ya kale ta sannan ya ce " saman kan ki su ke ne ? "

Ta na shirin magana Diya ya shiga wajen ya na sallama Abdoul na tare da shi
Da sauri TESNIM ta mike tsaye ta na yar kara ta nufi wata yar budurwa da ke tsaye bayan Diya ta rungume ta ta na fadin " oyoyo , Rouksar , why ba ki fada min ba za ki zo "

Yarinyar da ta kira da Rouksar fara ce kal a shekaru za ta kai 22 haka , ta na da kyau dai'dai gorgaudo , ta so ta yi kama da Diya , amma fa kama ta jini da ga gani ka san kanwar shi ce
Rungume TESNIM ta yi ita ma ta na fadin " ni ma ban shirya tahowar ba , na ga Akhie ne zai tahowa shi ne na biyo shi dan na gan ki na yi kewar ki sosai my TESNIM "

Da ga haka su ka raba jikin su Rouksar ta nufi MALIKAT AL'UMU ta rungume ta ta na fadin " Barka da wannan lokaci Momy "
Dan bubuga bayan ta MALIKAT AL'UMU ta yi kafin su raba jikin su ta koma geffen ta ta zauna , TESNIM ita ma ta koma geffen ta ta zauna

Diya da Abdoul kuma su ka nufi dayar sofa two seaters su ka zauna
Abdoul dai tun da ya zo ya ke karewa AMIR kallo duk sai ya ga lokaci guda ya sauya mishi

Da haoussa Diya ya yi wa AMIR magana ya ce " AMIR ina ????? " ya kai karshen ya na daga mishi gera guda

A hankali AMIR ya juya kan shi ya kali TESNIM ya ce mata " TESNIM je ki kira min yaran nan "

Tsuke fuska ta yi ta na kauda kai gefe wai ita ba za ta je ba
" Idan ki ka bari na maimaita abun da na ce , jikin ki zai fada miki " ya fada cike da izza

Da sauri ta mike tsaye ta na dan gunguni ta fara takawa ta bar wajen ta na tafe ta na kunbura fuska wai ita ta ji haushi

Ta na barin wajen Rouksar ta saki wani kyawatencen murmushi ta na kallon AMIR ta ce " AMIR ba ka ganin ba ne tun dazu ka kyale ni "

" ke Rouksar ban son shirme AMIR din ne ki ke jira ya fara gaishe ki " Diya ya fada cikin tsare gida

Dan sunkuyar da kai ta yi ta na fadin " ka yi hakuri Akhie , ina kwana " ta fada cikin girmamawa
Gyada mata kai kawai ya yi ba tare da ya ce mata komai ba
Da ga haka ba wanda ya sake cewa komai har sai da TESNIM ta dawo tare da Inaya da Nesrine su ka shigo cikin runfar su na sallama

Da sauri Inaya da Nesrine su ka nufi Abdoul su ka rungume shi su na yar dariya
Rungume su shi ma ya yi ya na fadin " my sisters , da fatan na same ku lafya ? "
Inaya ce ta riga Nesrine cewa " Lafya lau yaya Abdoul , ina ka tafi ka bar mu jiya tun bayan fitowar mu jirgi ban gan ka ba " ta kai karshen ta na raba jikin ta da na shi ta koma saman sofar da AMIR ke zaune ta zauna geffen shi

Ita kuma Nesrine ta zauna kassa saman carpet geffen shi
A tare TESNIM da Rouksar su ka zaro idanu su na kallon Inaya ta na zaune saman sofar da AMIR ke zaune kuma bai ce mata komai ba , ko ita TESNIM yanzu in a ka ce mata ta yi hakan ba za ta iya ba
Ita dai MALIKAT AL'UMU ko a jikin ta sai ma tashi da ta yi ta bar wajen ta nufi part din ta

Ta na barin wajen AMIR ya juyo da kan shi ya kali Inaya kassa kassa ya ce mata " kun yi breakfast ? "

Juyowa ta yi ta kaleshi ita ma ta na murmushi ta gyada mishi kai
" za ki sha fruits " ya tambaye ta
Yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " no ni na koshi , sai dai in so ka ke ciki na fashe " ta fada cikin shagwaba

Girgiza mata kai ya yi kafin ya kali Nesrine ya ce mata " Nesrine ina son yin magana da ke " ya kai karshen ya na mikewa ya fara takawa ya fice runfar
Da sauri Nesrine ta tashi ta bi bayan shi

Su na barin wajen Rouksar ta kali Inaya sama da kassa kafin ta kali Diya ta ce " Akhie su wanene wannan ?" Ta kai karshen ta yi wa Inaya kallon kaskanci

Nuna ta da yan yatsa Diya ya yi kafin ya ce " saurare ni da kyau Rouksar na san abun da ya kawo ki masarautar nan , tun wuri ki sauke idanun ki da ga saman yarinyar nan , wlh ko gashin ta ki ka taba AMIR zai iya kashe ki , kuma ba abun da zai faru "

Da sauri TESNIM ta katse shi da cewa " Dalilin mi Akhie zai kashe ta saboda wannan dan babyn ? " ta kai karshen ta na nuna Inaya da dan yatsa

Yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " bari in ya dawo sai ki tambaye shi ai kun fi kusa "

Duk maganar nan da su ke yi a kunnen Abdoul dan shi ya na jin larabci ba kamar Inaya ba , abun da bai sani ba ita ma ta na jin larabcin amma sama sama , duk maganar nan da su ka yi ta dan gane rabin ta amma sai ta nuna kamar ba ta ji su ba , sai da ta bari sun Kamala sannan ta tashi ta dauki Apple guda da ke saman table din gaban sofar su TESNIM sannan ta koma ta zauna ta na cin Apple din ta


[16/09 à 09:57] M.N.M:



❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤


(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥




( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )




⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘



【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】




Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】




YOU CAN FOLLOW MY WHATSAPP CHANEL
👇👇👇👇👇👇👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i





BOOK .............. 2 🌹👑







________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________





PAGE ……………………6 ❤🔥







Bangaran AMIR kuma , a tare su ka baro wajen shi da Nesrine su ka sauka da ga saman Hanyar ya shiga cikin ciyayin sannan ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ita kuma ta na tsaye geffen shi


Sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce mata " kin san dalilin da ya sa na kira ki ?"
Girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " a'a yaya Zayd "
A hankali ya dan lumshe idanun shi ya bude kafin ya dan juyo da kan shi ya kale ta ya ce " da farko ki daina kira na da yaya Zayd , ki kira ni da Akhie ko kuma AMIR "
Da to ta amsa mishi

Shiru ya yi na dan lokaci kafin ya ce " na san malam ya fada miki auren da ke tsakanin da Diya kafin ya rasu "

Sunkuyar da kai ta yi kafin ta ce " Eh ya fada min , ranar da wadanan mutanan su ka zo gida su ka tafi da shi "

Gyada kan shi ya yi a hankali kafin ya ce " ina fatan ba ki da matsala da hakan "
Girgiza mishi kai ta yi allamun babu
" okay , Gabe za ki bi shi masarautar su ya gabatar da ke ga Familyn shi , Idan kuma a nan ki ke son zama ba matsala za a ware muku part "

Da sauri ta ce mishi " ni a nan zauna tare da Mama da Inaya , ba zan iya yin nesa da su ba " ta kai karshen kuka ya na kubce mata

A hankali AMIR ya hannu ya janyo ta jikin shi ya rungume ta dan ya san ba komai ba ta ke yi wa kuka ba face malam , ko shi hakan ya ji cikin zuciyar shi da ya kira sunan shi amma ba yadda zai yi dole ya danne

Sai da ya ji ta yi shiru sannan ya sake ta ya ja hannun ta su ka koma cikin runfar nan
Ya na zuwa ya mikawa Diya hannun ta
Murmushi Diya ya yi kafin ya riko hannun ta ya janyo ta ta zauna tsakiyar su shi da Abdoul ta na sunkuyar da kai

Shi kuma ya koma geffen Inaya ya zauna ,
Ya na zama Azim ya karaso wajen ya Zube gaban AMIR ya na fadin " gaisuwa na ke ya shugaba na , mai martaba na son ganin ka a Fada yanzun nan "

Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya ce " za ka iya tafiya "
" godiya na ke ya shugaba na " ya na gama fadar haka ya tashi da sauri ya bar wajen

Ya na barin wajen AMIR ya daga kan shi sama ya lumshe idanun shi
" AMIR ba za ka je ba ne " Diya ya fada mishi dan ya ga allamun ba ya da niyar tashi
Shiru AMIR ya yi bai ce mishi komai ba , bai kuma saukowa da kan shi ba
Ya na a haka ya ji kawai an kontar da kai saman cinyar shi
Slowly ya sauko da kan shi ya bude idanun shi , ya na kallon ta
Allamun barci ta ke ji dan har ta lumshe idanun ta , ta daura kafafun ta saman Sofar
Bai ce mata komai ba ya daga kan shi ya lumshe idanun shi

" Rouksar tashi mu tafi ko ? " TESNIM ta fada ta na mikewa tsaye
Karewa AMIR da Inaya kallo Rouksar ta yi kafin mike ta bi bayan TESNIM su ka bar wajen
Su na barin wajen shi ma Abdoul ya mike ya na fadin " Diya ina mama ta ke ina son ganin ta "

Cikin nitsuwa AMIR ya riga Diya cewa " ta na part din MALIKAT HOUDA "
Gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya mike ya riko hannun Nesrine ya ce su tafi Abdoul na biye da bayan su , su ka bar AMIR da Inaya a wajen

sannu sannu har AMIR da Inaya su ka share wajen good on hours a haka
ita ta yi barci shi kuma ya tafi duniyar tunanin shi , Allah kadai ya san abun da ya ke tunani

ya na a haka kawai ya sake jiyo Muryar Azim ya na yi mishi sallama
Dan karamin tsaki ya yi kafin ya sauko da kan shi , shii ya ma manta da cewa a na jiran shi a Fada

gaishe shi Azim ya yi kamar yadda ya saba sannan ɗaura da cewa Malik na son ganin shi a part din shi
"Okay " ya fada a takaice kafin ya sa hannu a hankali ya sauke kan Inaya da ga saman cinyar shi ya mike tsaye

sannan ya juya ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya fara takawa ya bar wajen Azim na biye da bayan shi dan wannan karan Malik ya ce kar ya dawo ba tare da AMIR ba

shi kuma AMIR kai tsaye part din MALIKAT INAS ya wuce da Inaya
da sallama cen kassan makoshi ya shigo parlourn MALIKAT INAS
nan ya tardo ta zauna ita da RIANNA su na hirar su

su na ganin shi dauke da Inaya su ka mike su ka nufe shi a rude su na tambayar me ya same ta
bai bi ta kan su ba ya wuce ya kontar da ita saman Sofa sannan ya juyo ya kale su ya ce " barci ne ta ke yi " ya na gama fadar haka ya raba ta geffen su ya wuce ya fice part din

wani cool murmushi RIANNA ta yi kafin ta tako ta zauna kusan Inaya ta ce " Ammie , ina ji a jiki na yarinyar nan she is so special for AMIR , duba ki yadda ya ke kula da ita kamar baby "

ita ma MALIKAT INAS wani dan karamin murmushi ta yi kafin ta koma inda ta taso ta zauna ta na fadin " dole ya kula da ita saboda ya na son ta , zalar so ya ke yi mata amma har yanzu ya kassa yarda da hakan , Idan har AMIR ya bude baki ya ce ya na son yarinyar nan zan fi kowa farin ciki , she is so innocent , abun da na lura da shi ta fi yar uwarta nitsuwa , za su dace sosai da juna , Sai dai kashh ya ki karbar soyayyar da ke cikin zuciyar shi "

" To yanzu Ammie ya ki ke so mu yi "

shiru MALIKAT INAS ta yi na dan lokaci kafin ta ce " ba abun da za mu yi , kawai za mu sakawa ikon Allah ido , Tun da har ya hada su , Haka zalika zai sa soyayyar da ke cikin zuciyar AMIR ta fito fili , na mu kawai mu taimaka musu idan za mu iya "

kara fadada murmushin ta RIANNA ta yi ta na fadin " Ammie Allah ma ya ce tashi na taimake ka , dole sai mun saka Hannu cikin lamarin su "

" To ya ki ke so mu yi , ni fa ban taba jin AMIR ya bude baki ya ce ga kalar matar da ya ke so bare har mu yi wani kokarin sauya ta "

" no Ammie ba wani sauyawa , a hakan ma ta yi , ni dai na san AMIR ya na son mace mai kwaliya , ba ki lura da irin kallon da ya ke yi mata dazu da safe , ni dai na san ko bai fada ba , kwaliyar ta ta burge shi "

yar karamar dariya MALIKAT INAS ta yi kafin ta ce " Oh dama kin san da wannan shi ya sa ki ka shirya ta tun da safe haka "

" me ki ke tunani na sani mana , ai duk fadin masarautar nan babu wanda ya san AMIR sama da ni , ke dai ki sha zama kawai za ki sha kallo " RIANNA ta fada cike da kwarin guyiwa allamun ta shirya wata a kassa

ita dai MALIKAT INAS ba ce komai ba kawai ta zuba wa Inaya idanu


▪AMIR


bayan ya fito part din MALIKAT INAS kai tsaye part din Malik ya wuce , kafin ya shiga sai da ya cire Alkyabar shi ya mikawa Azim da ke biye da shi sannan ya shiga building din
kai tsaye hawa na biyu ya nufa , nan ya tardo Malik tare da wasu manyan mutane biyu

ko gaishe su bai yi ba , sallamar shi ma shi kadai ya ji abu ne
kai tsaye ya nufi wata sofa ya zauna , zaman nan irin na gasaita

sai da ya zauna sannan Malik ya ce mishi " AMIR , Azim bai fada maka ka same ni a fada ba "

cikin ko in kula AMIR ya ce " ya fada min "
" Me ya sa ba ka je ba to , saboda kai musaman na shirya zama amma ba ka zo ba " Malik ya fada ya na nuna bacin ran shi
a hankali AMIR ya gyara zaman shi ya na fadin " Next time "

dan murmushi Malik ya yi ya na gyada kan shi kafin ya ce " okay na san ba za ka manta da wadanan nan ba , Sarkin Dogarai Hussein Bin Hashim da kuma Sarkin Bayi Mohammed Magid "

gyada kan shi a hankali AMIR ya yi kafin ya ce " Yes ban manta da su ba , ba wannan ne ba ya taba tsula min bulalar bayin shi ba " ya fada ya na nuna Sarkin bayi da ido

a tare duk su ka yi dariya sannan Sarkin bayi ya ce " To ina neman Afuwar Yarima , akasi ne a ka samu a ranar "

dan tabe baki AMIR ya yi ya na kauda kan shi gefe
sai da su ka tsagaita dariyar su sannan Malik ya ce " Kar ka manta matsayin uncle din ka su ke "

cikin nitsuwa AMIR ya katse shi da cewa " Abbi ba sai ka fada ba na sani , wannan shi ya ke auren MALIKAT MANISHA yarinyar MALIKAT HOUDA , Wannan kuma Yarinyar MALIKAT YOUSSRA " ya fada ya na nuna Sarkin bayi da ga karshe

Jinjina kan shi Hussein ya yi kafin ya ce " Ashe dai ba ka manta da mu ba "
" no " ya fada a takaice kafin ya mike ya nufi lift ya shiga ya nufi hawa na uku , ya na hawa ya wuce kai tsaye bedroom din shi

A cen kassa kuma inda ya baro Malik , sai da su ka Kamala tatauna war su a kan matsalolin da su ka shafi masarautar sannan ko wane ya tashi ya kama aikin gaban shi


▪NESRINE


bayan sun baro AMIR da Inaya kai tsaye part din MALIKAT HOUDA su ka nufa
A tare duk su ka yi sallama kafin su ka karaso cikin parlourn inda MALIKAT HOUDA ke zaune saman sofa ga table a gaban ta shake da fruits

a gaban ta su ka zube saman guyiwowin su sannan Diya ya ce " gaisuwa na ke ya shugaba ta "

dan karamin murmushi MALIKAT HOUDA ta yi kafin ta ce musu su tashi ita ba ta son wannan gaishe gaishen na shirme

yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " An gama ran ki shi dade , dama mun zo ganin mahaifiyar su ne "

" ka ce yaran Amina ne , Masha Allah , sannun ku to , tashi ku je ta na cikin daki na uku " MALIKAT HOUDA ta fada ta na murmushi , matar nan ba ta da matsala sam ita kowa na ta ne dalilin da ya sa ma AMIR ya ce a kawo mama wajen ta

ba musu su ka tashi su ka nufi corridor din bedrooms su ka shiga ta uku
nan su ka tardo mama zaune saman gadon ta , ta kurewa waje guda ido kamar mai tunanin wani abu

Nesrine na ganin ta yi gudu ta fada jikin ta na sakin kuka
sai a lokacin mama ta dawo cikin hayacin ta , ta daura hannun ta guda saman bayan Nesrine ta na fadin " lafiya ki ke kuka tun da safe haka "

a hankali Nesrine ta dago da ga jikin mama ta kai hannu ta fara goge hawayen ta , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " ba komai mama kawai na yi kewar ki ne "

dan karamin murmushi ita ma mama ta yi kafin ta juya

Please Login or Register in order to submit comment