Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kashe shi

a hankali ya Shigo Fadar , ya na taku cike da Izza , ya na sanye da wasu manya kaya irin na gidan Sarauta , da ga ganin kayan ka san miliyoyi a ka kashe musu Alkyabar jikin shi ma kadai ta kai wajen one hundred million , dan zaren da a ka yi mata zane ma na gold ne , duwatsun da ke cikin ta zallar diamond ne

tun da ya shigo , duk sojojin wajen su ka fara daga kafa su na sara mishi ji kawai ka ke dip dip dip kassar har girgiza ta ke

kai tsaye Kujerar Gold din nan ya nufa a hankali ya juya ya zauna saman kujerar
ya na zama ko sautin Algaita ya fara tashi cikin fadar , da sauri dogaran da su ka tare bangaran Maza su ka saki manyan rigunan su , su ka koma da ga baya gaba kadan da sojojin nan su ka tsaya

su na tsaya wa Wani dattijo Fari kal ya tara kyasumba har zuwa saman kirjin shi , da ga gani zai kai shekara 60 ko fi , ya na sanye da manyan kaya , ya na rike da wani Abu kamar box haka nade cikin wani farin Tissu
( Ina ga kamar Kur'ani ne πŸ€”πŸ€”πŸ€” a nawa tunanin )

a hankali ya fara takawa ya nufi gaban Amir ya tsaya
( Ni dai ban san ko wanene ba gaskiya πŸ˜‘πŸ˜‘, amma bari mu duba labarin shi kadan )

RAFIK BILAL wannan shi ne babban Wazirin Malik , da ga Malik sai shi indai a ciki Fada ne , shi da hannun shi ya nada Malik HICHAM bin JAABAR , kuma shi zai nada Malik Nawfel Bin Jaabar yanzu , duk cikin Fadar , da ga Sarkin bayi , Sarkin dogarai da sauran su duk a karshin shi su ke , duk wata shawara da Malik zai yanke tare da Rafik ya ke yanke ta , yanzu kuma Amir zai zabar nashi Wazirin , wanda ko Amir ba ya nan za a iya tunkarar shi , kuma idan ya yanke shawara ta zaune tamkar Malik ya yanke ta




[01/10 Γ  09:39] MEERAH πŸͺ·πŸ©·:



❀⚘ EXILED PRINCE ⚘❀
(LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯





( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )





STORY & WRITTEN BY : MEERAH πŸ‘‘πŸ”₯



Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA πŸ’–πŸ’πŸŒΊ




TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP CHANEL
πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i




_________________________β€»β€»β€»β€»β€»___________________________






BOOK .....................2 β€βœπŸ“š






β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘




PAGE 23 βœπŸ“š




Murya sama sama yadda kowa ke jin shi ya ce " Al-Amir Nawfel Hicham bin Jaabar , Ka yi rantsuwa da Kur'anin da ga ke cikin hannu na , za ka kula da masarautar Saudiya ? "

a hankali Amir ya daga Hannun shi ya daura saman Kur'anin murya cen kassan makoshi yadda Rafik ne kadai ya jiyo shi ya ce " Na yi rantsuwa da Alkur'ani mai girma zan kula da Masarautar Saudiya "

" Za ka rike Mulkin Saudiya cikin gaskiya "

a hankali Amir ya gyada kan shi kafin ya ce " Na yi Alkawari "

" za ka yanke hukunci kamar yadda Shari'ar mu ta musulimci ta tanada "

" Na yi Alkawari , zan kula da Saudiya tamkar rayuwa ta , Zan kare ta tare da Al'umar da ke cikin ta , Zan bawa me gaskiya gaskiyar shi , wanda ya yi laifi kuma zai fuskanci hukunci dai'dai laifin da ya aikata ko da kuwa Ni ne , na yarda zan fuskanci hukuncin da ya dace " ya fada dan ya fara gajiya da tambayoyin Rafik , shi so ya ke a yi da sauri ya bar wajen ya na da aikin yi

wani cool Murmushi Rafik ya saki kafin ya janye Kur'anin Ya juya ya kali dogaran da ke tsaye a baya ya gyada musu kai a hankali

juyawa ya yi ya ajiye kur'anin hannun shi saman table din da ke geffen Chair din Malik
dai'dai lokacin da dogaran nan su ka karaso wajen rike da wasu Tissu farare kal
hannu Rafik ya kai ya karbe su , ya bude ashe Rawani ne
cikin nitsuwa ya nadawa Amir Rawanin nan sannan ya ja hular Alkyabar ya rufe mishi kai , ba ka iya ganin komai sai wadanan Hazel eyes din nashi

ya na gama nadawa Amir rawanin shi ya koma wajen sofar da ya taso ya tsaya

ya na tsayuwa ko , dogaran da su ka tare bangaran Mata su ka sauko da rigunan su , su ka koma baya da sauri sauri

Slowly Inaya ta dago kan ta , ta kali Amir Dum ta ji gaban ta ya fadi , dan ba karamin kwarjini ya yi mata ba
ba ita kadai ba , duk matan wajen sai da su ka ji zuciyoyin su sun buga , gaskiya Mulki na kama Amir , specially irin zaman nan da ya yi na izza na Mulki , nan take Hafsat , Muntaz da Rouksar su ka ji wani mugun son shi cikin zuciyoyin su a tare ji su ke kamar su hadiye shi , ga kyau , ga kudi , ga Mulki ai kowace macen da ke wajen sai ta kamu da son shi , ita dama Inaya ta jima da son shi cikin zuciyar ta , ba abun da ya sauya kawai ta tsaya ta na kallon shi ta na sakin Wani cool murmushi

RIANNA ma murmushi kawai ta saki , gaskiya ta na alfahari da dan uwan ta , har kawo ruwa idanun ta su ka yi

su na a haka su ka Jiyo Muryar Rafik ya na fadin " Al-Malik Nawfel bin Jaabar "

a tare duk dogaran wajen su ka daga murya su na fadin " Allah ya ja zamanin mai martaba " har sau biyar
sojojin nan kuma su na ta sara mishi

sai da su ka Kamala sannan Rafik ya koma saman sofa din shi ya zauna
a tare duk mutanan wajen su ma su ka zauna saman sofar su , kowane ya zubawa Amir
( Kut Yanzu Malik ya ke 🀭🀭🀭🀭 )

kowane ya zubawa Malik ido , shi kuma ya kurewa Kofar fita Fadar ido ya na jiran kawai a Kammala ya tashi ya bar wajen da gudu , akwai wani abu na musaman da ya shirya yi

ya na a haka ya jiyo Muryar Rafik ya na fadin " Ranka shi dade mai grima Malik , lokaci ya yi da za ka zabar wanda zai maye maka gurbi na , bisa tsarin masarautar nan "

gyada kan shi Amir ya yi a hankali kafin ya nuna Diya da yatsa ko tunani bai tsaya yi ba
dan Zaro idanu Diya ya yi ya na kallon Malik ya saki wani cool murmushi kafin ya mike tsaye , ya karaso gaban Malik ya zube saman guyiwowin shi

a hankali Malik ya daga hannun shi ya daura saman kan Diya
ya na aza shi Diya ya ce " na yi Alkawari zan taya mai girma Malik rike Saudiya da hannun gaskiya "

ya na gama fadar haka Malik ya janye hannun shi
slowly Diya ya mike ya juya ya nufi gaban Rafik ya Zube saman guyiwowin shi
cikin nitsuwa Rafik ya zame rawanin kan shi , ya nadawa Diya
sai da ya Kamala nada mishi rawanin sannan Diya ya mike ya koma geffen daman Malik ya tsaya ya rike hannayan shi a baya ya ce " Bismillah "

a hankali kowane ya koma ya zauna , su ka fara kuskus kowane da abun da ya ke fada

a hankali Inaya ta rage sautin Muryar ta , ta ce " Aunty Tesnim , Me ya sa shi yaya Moussa bai zauna ba ? "

rage sautin Muryar ta ita ma Tesnim ta yi kafin ta ce " Da ga yanzu shi ne na hannun daman Malik , duk wata magana da Malik zai yi a bakin Diya za a ji ta "

yar karamar dariya Inaya ta yi kafin ta ce " kenan shi Malik ya koma kurma ? "

girgiza mata kai Tesnim ta yi cikin sanyin murya ta ce mata " a'a , kawai haka tsarin masarautar mu ya ke , ba a so a ji Muryar Malik , shi ya sa ki ka ga Diya ya tsaya a geffen shi ta yadda duk abun da zai fada Diya kadai zai ji shi "

" Shikenan yanzu an nada shi a matsayin Malik ? "

gyada mata kai Tesnim ta yi allamun eh

" shikenan ku tashi mu tafi ko ? "

RIANNA ta amsa mata da cewa " a'a babu inda za ku tafi , ba a nada MALIKAT ba "
slowly Inaya ta juyo ta kali RIANNA ta ce " Aunty RIANNA wace MALIKAT kuma ? "
wani cool murmushi RIANNA ta saki kafin ta ce " Za ki gani ke dai duk abun da a ka ce miki , ki yi shi kar ki yi magana "

da To Inaya ta amsa mata kafin ta juya ta kali Malik dai'dai lokacin da wani dogari ya shigo Fadar ya na rike da wata Box ta Gold ya nufi Rafik ya Zube saman guyiwowin shi ya mika mishi Box din

hannu Rafik ya kai ya karbi box din sannan ya mike tsaye cikin girmamawa ya ce " Ranka shi dade Malik , Lokaci ya yi da za a nada MALIKAT din ka , ga Alkyabar MALIKAT AL'UMU "

da sauri Sarkin bayi Mohammed ya mike ya ce " cikin Dukkan girmamawa ran ka shi dade Malik , kowa a nan ya sani ba ka da aure , ina ga ba sai an nada MALIKAT ba a yau "

slowly Rafik ya juya , ya kali Sarkin bayi ya ce " ba zai yi yu ba , rana guda a ke nada Malik tare da MALIKAT din shi , ga yan mata a nan zaune , ya zabi koma nawa ya ke so a aura mishi ita , a nada MALIKAT "

wani Makirin murmushi Mohammed ya saki dama da gangan ya yi hakan
dan sunkuyar da kai ya yi kafin ya ce " ran ka shi dade mai girma Malik , ga yar uwarka Hafsat , na baka auren ta a aura muku aure da ita , Idan har Mai girma Malik ya amince "

Gyada kan shi Rafik ya yi kafin ya ce " Masha Allah , hakan ya yi kyau "

slowly ya juya ya kali Malik ya ce " Mai girma Malik , zan kasance Waliyin ka , a aura maka ita a yanzu , a nada ta a matsayin Malikat "

shiru shi dai Malik ya yi bai ce komai ba bai ce musu komai ba
shi ko Rafik a tunanin shi Malik ya Amince kawai sai ya juya ya kali Mata ya ce " wacece Hafsat Mohammed a cikin ku "

da sauri Muntaz ta mike ta fice Fadar da gudu ta na kuka
da kallo duk su ka raka ta har sai da ta fice sannan Rafik ya sake maimaita tambayar shi

cikin kissa da kisisina Hafsat ta mike ta yi taku biyu gaba ta sunkuyar da kai ta na sakin Murmushi

Slowly Rafik ya juya ya kali Malik sai dai kafin ya yi magana Malik ya daga mishi hannu allamun ya yi shiru
ba musu Rafik ya yi shiru ya na kallon Malik

Da dan yatsar shi ya yi wa Diya allamun ya guso
da sauri Diya ya sunkuyo ya kai kunnen shi wajen face din Malik

cikin sanyin murya Malik ya ce mishi " ka yi abun da na ce maka "
wani kyawatencen murmushi Diya ya saki kafin ya gyada kan shi ya mike tsaye

kallon Hafsat ya yi ya ce mata " Za ki iya komawa ki zauna "
a tare duk mutanan wajen su ka zaro idanu Hafsat kuwa sai da ta dago kai ta kali cikin idanun Diya ba shiri nan take murmushin da ke saman face din ta bace

da sauri Mohammed ya ce " amma ranka shi d...... "

bai kai karshen maganar shi ba Diya ya katse shi da cewa " a'a Sarkin bayi , wannan shawarar ta Malik ce kadai , ba wanda ke da izinin fitar mishi da matar da zai aura "

cikin nitsuwa Rafik ya katse shi da cewa " amma ranka shi dade ka sani bisa tsarin masarautar nan a rana daya a ke nada Malik da MALIKAT "

gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya ce " mai girma Rafik mun sani baki daya , kun san a ka ce sabon sarki , sabon zamani , wannan tsarin Malik ya kawo shi , to Malik Nawfel ya sauya shi "

da sauri Miram ya mike ya ce " amma haka al'adar masarautar nan ta ke , ta ya za a ce rana guda an sauya ta "

kafin Diya ya yi magana RIANNA ta mike ta ce " cikin dukkan girmamawa Miram , zamani sauyawa ya ke , kamar yadda al'ada ke sauyawa , Idan har Malik ya ce ba shi da ra'ayin nada MALIKAT a yau , babu wanda ya isa cikin mu ya matsa mishi yin abun da ba ya so , a gafarce ni idan na fadi ba dai'dai ba " ta na gama fadar haka ta koma ta zauna

ita dai Inaya da ido kawai ta ke bin su dan da larabci su ke magana ita kuma ba gane larabci ta ke ba

A hankali Malik ya yi gyaran Murya
da sauri Diya ya koma ya dan sunkuyar da kan shi , ya na sauraron Abun da Malik ke fada mishi

mikewa tsaye ya yi , ya tako a hankali gaban Rafik ya mika mishi hannaye allamun ya ba shi box din
ba musu Rafik ya daura Box din saman hannayan Diya

juyawa ya yi ya ajiye box din saman table din Da Rafik ya ajiye kur'ani sannan ya karaso gaban Malik ya tsaya ya juya ya kali Rafik ya ce mishi " za ka iya komawa ka zauna "

ba musu Rafik ya koma ya zauna saman sofar shi
ya na zama Diya ya ce " kamar yadda Gimbiya RIANNA ta fada , zamani ya kan sauya tare da al'adun shi , Haka zalika Mulkin Malik Nawfel zai zo da nashi zamanin , da ga yau za mu kawo canji a cikin wannan masarautar , da ga yau mun janye dokar da ke cewa Rana guda za a nada Malik da MALIKAT , amma Malik ya yarda zai nada MALIKAT da hannayan shi ba na wani ba yanzu ba sai an jima ba "
nan take duk fadar su ka shiga yin hamdalah kowa ya saki murmushi

slowly Diya ya juya ya kali Malik
gyada mishi kai kawai Malik ya yi a hankali ba tare da ya ce komai ba

wani cool murmushi Diya ya saki kafin ya sauke ajiyar zuciya ya fara takawa a hankali ya nufi bangaran mata

kai tsaye wajen Inaya ya nufa , ya mika mata hannu ya na murmushi ya ce mata " baby tasso mu tafi " ya fada da hausa

cikin rudu Inaya ta ce mishi " yaya Moussa ina kuma za mu tafi ? "

girgiza mata kai kawai ya yi ya na murmushi ya ce mata " kar ki damu baby , ke dai tasso mu tafi duk abun da zai faru kar ki yi magana kin ji ko ? "

wani cool murmushi ta saki ta gyada mishi kai sannan ta daura hannun ta saman nashi , ta mike a hankali

a tare su ka fara takawa , har su ka karaso gaban Malik sannan ya saki hannun ta ya ce mata " yi kneel down "

ba musu ta Zube saman guyiwowin ta ta na kallon Malik fuskar ta cike da allamun tambaya

ta na tsugunawa Diya ya dauki yar box din nan ya bude ta

da sauri Mohammed ya ce " ranka shi dade ba dai yarinyar nan za a nada a matsayin MALIKAT ba , she is too small "

Malik bai ce mishi komai ba ya mike tsaye a hankali
da sauri duk mutanan wajen su ka mike tsaye

hannu Malik ya kai ya cire Alkyabar da ke jikin Inaya ya mikawa Diya
ya kai hannu ya fido Alkyabar da ke cikin box din da Diya ke rikeda

wata dankareriar Alkyaba ce , fara kal ta auduga , da ga gani wannan sakar ta hannu ce , musaman Zaren da a ka yi wa Alkyabar zane na gold ne , sai tashin qamshi ta ke yi

bai tsaya bata lokaci ba ya daurawa Inaya ita , ya saka mata hular , sannan ya mika mata hannu
slowly ta dago kai ta kali hannun shi ta saki wani cool murmushi sannan ta daura nata a sama ta mike tsaye
a hankali ya dago hannun ya kai saitin bakin shi ya manna mata kiss har sai da ya dan lumshe idanun shi a hankali

a hankali ya janye hannun ta cikin harshen hausa ya ce mata " zauna "
ya kai karshen ya na janyo ta wajen Kujerar MALIKAT

har za ta zauna Mohammed ya ce " ranka shi dade haka bai dace ba , ba ta isa zama MALIKAT ba "

ya na gama rufe bakin shi Miram ya ce " Mai girma Rafik ka yi magana mana , wannan ba za ta iya kula da harkokin MALIKAT ba , wannan doll ya kamata mu samo mata ai , ko ba haka ba " ya kai karshen ya na juyawa ya kali sauran mazan

babu wanda ya ce mishi ufan , dan ba wanda zai iya jayaya da umarnin Malik bare kuma wannan da ga gani bai zo da wassa ba

" Ranka shi dade , kar ka manta ita ma MALIKAT ta na da hannu cikin al'amarin masarautar nan " Rafik ya fada
[02/10 Γ  08:12] MEERAH πŸͺ·πŸ©·:


❀⚘ EXILED PRINCE ⚘❀
(LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯





( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )




STORY & WRITTEN BY : MEERAH πŸ‘‘πŸ”₯







_________________________β€»β€»β€»β€»β€»___________________________




BOOK .....................2 β€βœπŸ“š





β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘



P A G E 2 4 ✍ πŸ“š




ba tare da ya juyo ba Malik ya ce " ba na son na kara jin muryar kowa a cikin wajen nan " ya fada da dan karfi
nan take kowa ya shiga tayiΒ²n shi duk sai da su ka sunkuyar da kan su

ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce ma Inaya da ta tsare shi da idanu " Zauna cutie "
gyada mishi kai ta yi kafin ta zauna saman chair din a hankali ta na kallon shi, ta na zama shi ma Malik ya koma saman chair din shi ya zauna

ya na zama kowane ya koma saman sofar shi ya zauna
banda Hafsat da ta fice fadar da sauri

komawa Diya ya yi geffen Malik ya tsaya ya rike hannayan shi a baya a ya ce " za mu iya farawa "

ya na gama fadar haka General Abdallah ya mike ya karaso gaban Malik ya sara mishi sannan ya ce " ranka shi dade kamar yadda ka bada ubarni , mun kamo wanda ya harbi mai girma marigayi Malik "

a hankali Malik ya gyada kan shi , Allamun a kawo shi
dan sunkuyar da kai General ya yi kafin ya juya ya kali daya da ga cikin sojojin da ke tsatsaye cikin fadar

da sauri biyu da ga cikin su , su ka fice fadar da gudu

ba su wuce Five minutes ba , su ka dawo rike da wani saurayi da a shekaru ba zai wuce 24 years ba , ya na sanye da wasu kaya bakake an daure shi tsam kamar dauri goro

su ka karaso da shi geffen General su ka zubar da shi saman guyiwowin shi

kallon Malik General ya yi ya ce " Ga shi nan ranka shi dade , bisa bincike da mu ka yi , wannan shi ne Sniper din da ya harbi Malik "

kare mishi kallo da kyau Malik ya yi kafin ya juya ya kali Inaya ya kai dan bakin shi saitin kunnen ta ya rada mata " Cutie , kale shi da kyau , shi ne wanda ya kashe Abbi ? "

slowly Inaya ta juya ta kali saurayin nan da ga sama har kassa
sannan ta juya ta kali Malik ta ce " yaya Zayd , ba na ji wannan zai iya kashe mutum , sai dai idan matsa mishi a ka yi "

a hankali ya gyada kan shi kafin ya juya ya kali saurayin , shi ma haka ya ji cikin zuciyar shi , kamar wannan saurayin ba zai kashe mutum na haka kawai shi ya sa ya tambaye ta kuma ra'ayin su ya zo daya

kallon Diya ya yi , da sauri ya sunkuyo da kan shi Malik ya rada mishi " Ina son na yi bincike da kai na a kan wannan saurayin , ka ce a rufe shi kawai zan yanke mishi hukunci da ga baya "

gyada mishi kai kawai Diya ya yi kafin ya mike ya kali General ya ce " General za ku iya meda shi prison , Malik zai yi bincike da kan shi a kan wannan saurayin , sannan ku rage sasaucin daurin nan da ku ka yi mishi don Allah , sai ka ce mara imani "

yar karamar dariya General ya yi kafin ya juya ya kali sojojin da su ka kawo saurayin
ba musu su ka dauki saurayin su ka koma inda su ka fito
komawa General ya yi ya zauna saman sofar da ya taso

ya na zama Malik ya saki wani siririn Tsaki ya mike tsaye
da sauri su ma mutanan wajen su ka mike har da Inaya
bai ce musu komai ba ya fara takawa cike izza ya nufi kofar fita Fadar ya fice abun shi

ya na fita Rafik ya kali Diya ya ce " Diya , ya na ga kuma Malik ya tafi ba mu Kamala ba ? "

dan karamin murmushi Diya ya yi kafin ya ce " I'm sorry ina ga ba ya jin dadin jikin shi , in sha Allah gobe zai yanke shawara dan gane da sauran case din , yanzu kowa zai iya zuwa babban parlour domin wallimar da a ka shirya "

ya na gama fadar haka ya juya ya kali RIANNA
murmushi kawai ta yi kafin ta karaso ta rike hannun Inaya ta ce " mu tafi wajen momy ? "
gyada mata kai Inaya ta yi ta na murmushi kafin su fara takawa a hankali a tare su ka bar wajen

su na barin wajen Diya ya nufi Nesrine ya mika mata hannu ya ce " za mu iya tafiya madam ? "
dan karamin murmushi ta yi kafin ta daura hannun ta saman nashi , su ka fara takawa a tare su ka bar wajen
daya bayan daya duk mutanan fadar su ka watse



β–ͺMALIK


Kai tsaye part din shi ya koma , duk inda ya wuce sai dogarai sun zube har kassa su na gaishe shi

bai bi ta kan gaisuwar su ba kai tsaye ya nufi building din shi , ya haye floor na uku , ya na isa parlour ya nufi chair din shi ta Gold ya haye ya zauna , ya zame hular Alkyabar shi , tare da rawanin ya tila shi saman sofa , ya jingina bayan shi a jikin chair

Please Login or Register in order to submit comment