Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rude ya na fadin " My Cutie please Stop crying , ki fada min abun da ke damun ki , dubi duk kin tada min hankali "

bai gama rufe bakin shi ba ya ga ta yi tsit kamar yadda a ke dauke wutar nepa
Dum ya ji zuciyar shi ta buga , da sauri ya sa hannu ya na jijiga ta ya na kiran sunan ta , amma ina ko motsi ba ta yi

da gudu ya tashi ya fice dakin tun da ga cikin corridor din ya ke kwallawa MALIKAT INAS kira har ya fito parlour
RIANNA na ganin shi ta mike da sauri ta na fadin " Amir lafiya ka ke wa Ammie irin wannan kiran "

cikin fitar hayaci ya ke ce mata " please ina Ammie ta ke , Cutie ce , ban san abun da ke damun ta sai kuka ta ke na tambaye ta amma ta ki fada min "

da sauri ta raba ta geffen shi ta wuce ta nufi corridor ta shiga bedroom din Inaya
ta na shiga ta nufi bed din ta Haye ta riko shoulder din Inaya dukka biyu ta na jijiga ta ta na fadin " baby lafiya me ya same ki "

ba ta gama rufe bakin ta ba Amir da ke tsaye bayan ta ya ce " She is die ? "

shiru RIANNA ta yi ba ta ce mishi komai ba
cen kuma sai ta sauke ajiyar zuciya ta sauko da ga saman bed din ta kali Amir ta ce " Kar ka damu ina ga Period din ta su ka zo , ko last time haka muka sha fama da ita har suma ta dinga yi mana "

wata nanauyar ajiyar zuciya ya sauke har sai da ya dan lumshe idanun shi
wani cool murmushi RIANNA ta saki kafin ta ce mishi " To Romeo , sai ka tafi bari zan kula da ita "

girgiza mata kai ya yi kafin ya ce " no zan kula da ita "
"okay " ta fada a takaice kafin ta juya ta nufi dressing room
ta na shiga ya nufi bed ya zauna a hankali ya daura hannun shi saman cikin ta , ya na shafawa a hankali ya san shi ne ke yi mata zafi har ta dinga kuka

ya na a haka RIANNA ta fito da ga cikin dressing room ta na rike da wasu kananan kaya blue color da wasu underwear sai dai pant din ta saka mishi pad ta karaso ta ajiye daya geffen gadon sannan ta ce ma Amir " ga kaya nan na fido mata , idan ta farka sai ta yi wanka ta saka , ina kawo mata drug din da zai rage mata ciwon ciki "

gyada mata kai kawai ya yi , da ga haka kuma ta sa kai ta fice dakin
ta na fita , Amir ya mike ya nufi toilet ya shiga
jim kadan ya fito ya nufi Inaya ya sa hannayan shi biyu ya dauke cak kamar baby ya koma toilet da ita
tom ni dai bari na tsaya da ga waje

After some minutes ya fito ya na dauke da ita , ya nado ta cikin wani towel fari ta kankame shi sai kuka ta ke kassa kassa

kai tsaye saman bed ya nufa ya , ya zauna da ita saman cinyoyin shi
ya kai hannu ya dauko kayan da RIANNA ta fido mata ya saka mata da kan shi sannan ya kontar da ita saman gadon ya janyo Duvet ya rufe ta har zuwa ciki sannan ya koma bakin gadon ya zauna ya na kallon babyn shi

cikin sanyin murya ya ce mata " Cutie please stop crying "
girgiza mishi kai ta yi kafin ta ce " Zafi na ke ji "
" Shikenan Cutie zai daina yanzu konta ki huta zan tafi mosque lokacin sallat ya yi " ya na gama fadar haka ya kai dan bakin shi ya manna mata kiss saman forehead din ta sannan ya mike

da sauri ta riko hannun shi ta ce " za ka dawo ? "
a hankali ya gyada mata kai allamun eh
wani cool murmushi ta saki kafin ta saki hannun shi ta lumshe idanun ta ta na sauke ajiyar zuciya

sai da ya ga ya dan dauki lokaci ya na kallon ta kafin ya juya ya fice dakin ya janyo mata kofar
ya na fitowa parlour RIANNA ta ce mishi " har ka gama kula da babyn taka "
bai ce mata komai ya sa kafa ya fice parlourn ya bar part din
sai da ya fita sannan ta saki wata yar karamar dariya ta ci gaba da latsa wayar ta



β–ͺAFTER SOME HOURS


bayan ya Kamala Sallar shi , sai da ya koma part din shi ya yi wanka ya sauya kayan shi sannan ya fito ya nufi part din MALIKAT INAS , amma ta hanyar sirri babu wanda ya ga fitowar shi

bakin shi da sallama ya shigo parlourn , nan ya tardo MALIKAT INAS tare da RIANNA su na zaune a parlour
cikin girmamawa ya nufi Ammie ta shi ya gaishe ta

cikin zolaya ta ce mishi " yau dan Amaryar ka na waje na shi ne ka zo ko , tun bayan dawowar ka da ga Makkah ba ka leko ni ba "

bai ce mata komai ba ya nufi hanyar corridor
da sauri ta ce mishi " wlh kar ka taba min yarinya ta , ka bar ta ta huta " ta kai karshen ta dariya ita da RIANNA

Amir kuwa kai tsaye bedroom din Inaya ya wuce
bakin shi da sallama ya shigo bedroom din , ta na nan konce yadda ya bar ta ko motsi ba ta yi ba
a hankali ya karaso cikin dakin ya cire sneakers din shi , ya Haye saman gadon ya konta ya janyo duvet ya rufe kafafun shi har zuwa kugu sannan ya daura hannu saman cikin ta ya na shafawa a hankali ya na kallon face din ta
[30/09 Γ  04:24] MEERAH πŸͺ·πŸ©·:



❀⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❀


(LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯




πŸ’”πŸ₯€ ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) πŸ’”πŸ₯€





πŸ‘‘β€ MALLAKIN MEERAH β€πŸ‘‘



【THE ROYALTY LOVE πŸ‘‘πŸ•ŠπŸ’–γ€‘










【 BOOK …………………… 2 ❀ πŸ‘‘γ€‘





____________________πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š___________________







PAGE 22 βœπŸ“š




ya na tsaka da kallon ta ya ji wayar shi ta fara ringing
a hankali ya janye hannun ta da ga saman cikin ta , ya kai hannu ya fido wayar da ga cikin aljihun shi ya kali screen din

mikewa zaune ya yi ya gama bayan shi da forehead din gadon sannan ya dauki kiran ya saita wayar da face din shi

wata yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " Haba Amir ka yi min dan murmushi mana ? "

" lafiya ka kira ni , ba honey moon ka tafi ba , kyale ni " ya fada cikin tsare gida

" oh kar ka ji haushi fa , ba ni na hana ka tafiya ba , dama baby na ce ke son magana da sister din ta ni kuma ban da Number din ta shi ya sa na kira ka "

dan karamin tsaki Amir ya yi ya na shirin magana Ya jiyo Muryar Nesrine ta na fadin " ina wuni yaya Zayd "

gyada mata kai kawai ya yi amma ya ji dadin ganin ta cikin koshin lafya
wani kyawatencen murmushi ta saki kafin ta ce " yaya Zayd ina son ganin Inaya , ba mu yi sallama ba da ita "

bai ce mata komai ba ya juya wayar kan face din Inaya da ke faman kwana sannan ya dawo da wayar kan face din shi ya ce " ta na barci sai dai anjima ki kira ta "

" kai don Allah malam tashe ta " Diya ya fada cikin zolaya
" zo ka tashe ta idan ka isa " Amir ya fada cike da isa

yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " A yi min afuwa ran ka shi dade , dan sarki jikan Sarki , Malik din Saudiya baki daya , in sha Allah mu na tahowa Next week , idan baby na ta gama kula da ni " ya kai karshen ya na sumbatar kumatun Nesrine

yar karamar dariya ta yi ta sa hannayan ta biyu ta boye Face din ta wai ita ta ji kunya
shiru dai Amir ya yi ya na kallon su , ba karamin burge shi su ka yi , ya ji dadi ganin yadda su ke shaΖ™u da junan su lokaci guda haka , har cikin ran shi ya na musu adu'a Allah kar ya bar wani mugun abu ya ruguje musu wannan farin cikin nasu

ya yi nisa cikin duniyar tunanin shi ya jiyo Muryar Diya ya na fadin " Amir , ina son mu yi wata magana please "

gyada mishi kai Amir ya yi allamun ya na sauraron shi
kallon Nesrine Diya ya yi kafin ya ce " baby , za ki iya tafiya an jima zan sake kira miki ita "
gyada mishi kai ta yi kafin ta kali Amir ta ce mishi " sai an jima yaya Zayd , ka ce ma Inaya ina kewar ta sosai da sosai " ta na gama fadar haka ta juya ta bar wajen

ta na barin wajen Diya ya ce ma Amir " maganar auren Aymane ne da RIANNA "

" me ya faru ne ? " Amir ya tambaye shi

dan jinkirtawa Diya ya yi kafin ya ce " Amir auren nan bai konta min a rai ba , ina ji a jiki na wata muguwar manufa gare shi bayan auren nan , na san Aymane big bro di na ne , ban taba fada maka ba amma shi ne babban dalili na na baro Daular Ottoman , mu ka tafi Nigeria tare "

cikin rudu Amir ya ce mishi " me ka ke nufi ? "

ajiyar zuciya Diya ya sauke kafin ya ce " Aymane fa so ya ke ya zama Malik , dalilin ma da ya sa zai auri RIANNA , na san halin shi wlh ba son ta ya ke ba , kuma ni abun da ya fi tada min hankali shi ne ya na aiki da tsafi "

cikin nitsuwa Amir ya katse shi da cewa " wait ka na nufin dan tsubu ne shi ? "

" ban sani ba gaskiya , amma da na ke tasowa na sha ganin shi ya na wasu abubuwan da har yanzu ba zan iya fassare maka su ba , Yau din nan na yi wani mafarkin da ya girgiza tunani na , Amir duk abun da za ka yi ka sakawa Aymane Ido , duk da dan uwa na ne amma kar ka yarda da shi , wlh ya na da hatsari ba kadan ba "

ajiyar zuciya Amir ya sauke shi dama bai wani yarda da Aymane ba , dan tun lokacin da ya kama shi ya na yi wa Inaya irin kallon Sha'awa ya ji babu wanda ya tsana a duniyar nan sama da shi , in har abun da Diya ya fada mishi gaskiya ne , to kamata ya yi ya janyo Aymane a jiki yadda duk wani motsin shi zai kasance gaban idon shi , ko da kuwa ya yi kokarin kashe shi zai gano shi kafin ya aiwatar

" Diya , kar ka damu kai dai ka kula da matar ka , honey moon ku ka tafi , kar ka bari wannan tunanin ya bata muku....... "

bai kai karshen maganar shi Diya ya katse shi da cewa " Amir , maganar rayuwar ka da ta Inaya na ke maka magana a kai , zancen honey moon din mu kuma kar ka damu da ita , ba zan so silar ahali na ba wani abu ya same ka , ka sa a matso da ranar nadin ka please "

gyada mishi kai Amir ya yi kafin ya ce " shikenan , zan yi magana da Momy "

wani cool murmushi Diya ya saki kafin ya ce " yaushe ne ma da ranar nadin ni na manta "

" Ina ga ashirin ga wata ne "

dan zaro idanu Diya ya yi ya na cewa " Yau fa goma sha biyu mu ke "
Amir na shirin magana ya jiyo wata razananiyar kara da ga bayan Diya

ba shiri Diya ya mike da gudu dan ya san ba kowa ba ce sai Nesrine
Amir kuwa ya na ganin Diya ya bar gaban camera din ya katse kiran ya ajiye wayar shi saman bedside drawer ya na rokon Allah ya sa dai lafiya
bari mu leko su Nesrine mu ga


β–ͺDUBAÏ πŸ’¦


wani tanpasheshen Bedroom ne mai mugun kyau , komai na ciki white color ne , cen cikin dakin na hango wani wall na glass ka na iya hangen wani Teku Sky blue mai mugun kyau

cen na hango Nesrine zaune saman katafaren Bed din dakin ya na shinfide da wata bedsheet white color ta jingina bayan ta a jikin forehead din shi , ta na sanye da wata yar karamar riga dai'dai cinya blue colour mai mugun kyau

ta na a haka kawai Diya ya turo kofar dakin da karfi ya na fadin " Nesi "
" Na'am " ta fada mishi cikin sanyin murya

a rude ya karaso bakin gadon ya zauna ya na fadin " lafiya me ya same ki , ba ki dai ji ciwo ba "

girgiza mishi kai ta yi allamun a'a
ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce " to lafiya ki ka yi kara haka , kin san irin tsoron da na ji kuwa "

yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Film na ke kallo " ta kai karshen ta na nuna mishi Tv din da ke fuskantar bed din da remote din hannun ta

slowly ya juya ya kali Tv din kafin ya juyo ya kale ta baki sake ya ce " Nesi , kin san irin tsoron da ki ka ba ni kuwa ? "

girgiza mishi kai ta yi ba tare da ta ce komai ba ta na ci gaba da kallon Tv din ta
kare mata kallo da kyau ya yi cikin zuciyar shi ya na fadin " Zan yi maganin ki " ya na gama fadar haka ya saki wani makirin murmushi ya sa hannu ya kwace remote din hannun ta ya tila saman bedside drawer ya Haye saman gadon ya janyo kafafun ta ta konta ya Haye saman ta ya mata runfa da kirjin shi

wata yar karamar kara ta saki ta na cewa " yaya Moussa ka kyale ni Film na ke kallo "

da sauri ya ce mata " yi min shiru , shi ne za ki tsorata ni ? Nesi ni tsaran wassan ki ne wai , na ga kwana biyu duk kin raina ni "

wani cool murmushi ta saki kafin ta zagayo da hannayan ta a bayan shi ta ce " uhmm , ni ban raina ka ba "

" to minene ? " ya fada ya na daga mata gera guda ya daura hannun shi saman kumatun ta

wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Duk cikin L.O.V.E ne "
wani cool murmushi ya saki kafin ya ce " sai kin kashe ni ki huta "

a hankali ta dago kan ta ya hade forehead din su ta ce " zan kashe ka da soyayya ta "
ba ta kai karshen maganar ta ba ta ji saukar Lips din shi saman nata ya fara kissing ta ido rufe
( πŸ˜‘πŸ˜‘πŸ˜‘a'a bari na koma inda fito wadanan har yanzu ba su Kamala honey moon din su ba )



β–ͺDAULAR SAUDIYA πŸ”₯


β–ͺAMIR


ya na ajiye wayar shi saman bedside drawer ya juya ya kali Inaya dai'dai lokacin da ta bude idanun ta
ta na ganin shi ta saki wani cool murmushi kafin ta yi magana ya riga ta cewa " cikin ki , ya daina yi miki ciwo ? "

a hankali ta gyada mishi kai kafin ta ce " Eh , amma har yanzu ina jin zafi kadan "
" kar ki damu zai daina " ya fada mata cikin sanyi murya

wani cool murmushi ta saki kafin ta juya ta rungumo kugunshi ta na fadin " baby yaushe za mu tafi Honey moon wai ? "

a hankali ya zame hannayan ta da ga kugunshi , ya konta ya janyo ta jikin shi ya rungume ya na kallon face din ta ya ce " ba yanzu ba "

turo dan bakin nan nata ta yi ta na ce mishi " to sai yaushe ? "

" Idan ki na sarar turomin wannan dan bakin naki sai na cinye shi , rigimamiya kawai " ya kai karshen ya na ja mata kumatu

yar karamar dariya ta yi har sai da dimple din ta ya lotsa ta ce mishi " ina son mu samu baby "

" ni kuma ba ni so "

matse gera ta yi ta na cewa " Why ba ka so ? "
dan jinkirtawa ya yi kafin ya ce " Ban shirya kula da wani babyn ba "

dan zaro idanu ta yi ta na cewa " yaya Zayd dama ka na da baby ban sani ? "
gyada mata kai ya a hankali sannan ya ce " ba ga shi nan ba tare da ni "
daga mishi gera guda ta yi ta na fadin " Uhmmm ni ce babyn ka ? "

bakin shi ya kai ya sumbaci forehead din ta ya ce " yeah you're my baby "

wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " amma ni yaya Zayd ina son mu samu baby , me kama da kai , na saka shi a gaba na yi ta kallo "

" ki bar zancen baby , ke da samun baby sai dai wani ikon Allah "
cikin rudu ta ce mishi " yaya Zayd ban gane ba ? "
a hankali ya lumshe idanun shi bai ce mata komai ba , shi sam ba ya tunanin zai iya kula da baby cikin rayuwar shi , babyn ne ma sam ba ya so , ya na tsoron ya rasa ta wajen haihuwa , shi ya sa ya cire rai da ga samun baby cikin rayuwar shi

ya yi nisa cikin tunanin shi kawai ya ji ta kontar da kan ta saman kirjin shi ta na sauke ajiyar zuciya
bari dai mu dan tsagaita labarin



β–ͺAFTER SOME DAYS


yau dai ta kama ashirin ga wata , ranar nadin Amir a matsayin Malik

Tsaye Inaya ta ke cikin parlourn MALIKAT INAS , ta sanye cikin wata dankareriar gown Gold color mai mugun kyau har jan kassa ta ke , ta daura wata Alkyaba Fara kal da ga sama , an yi mata simple make up sai tashin qamshi ta ke , da ga gani kassan yau shirin na musaman ne

ta na tsaye a haka Nesrine ta shigo parlourn ta na sallama
Inaya na ganin ta ta saki kara ta nufe ta da gudu ta rungume ta ta na sakin kara
da gudu RIANNA ta fito da ga cikin corridor ta na fadin " baby lafiya me ya same ki ? "

cak ta tsaya tsakiyar parlourn ta na kallon Inaya da Nesrine rungume da juna
wani irin kyawatencen murmushi ta saki ta nufe su da sauri ta rungume su a tare ta na fadin " oyoyo Nesi ta dawo " ta kai karshen ta na raba jikin ta da nasu

a hankali ita ma Inaya ta raba jikin ta da na Nesrine ta riko hannayan ta ta na fadin " Nesi na yi kewar ki over "

wani cool murmushi ita ma Nesrine ta saki kafin ta kai hannu saman kumatun Inaya ta ce " Ni ma na yi kewar ki sosai baby na , da fatan na same ki lafiya , gaskiya yaya Zayd na kula da ke , dubi yadda ki ka yi haske , kin yi wani Fresh Masha Allah kamar na sace ki "

wani dan karamin murmushi Inaya ta yi ta na sunkuyar da kai wai ita ta ji kunya

wata yar karamar dariya RIANNA ta yi ta ce " a'a Nesi ke dai ki ka yi haske , gaskiya Diya ya iya kula da mace , ki ce mu fara tara kayan baby ? "

wata yar karamar dariya Nesrine ta yi ta na shirin Magana Tesnim ta shigo ta na kwallawa Inaya kira

" Aunty Tesnim me ya faru ? " Inaya ta fada

cike da zumudi Tesnim ta kamo hannun Inaya ta na fadin " baby mu tafi yanzu a ke shirin nada Amir yi sauri "
ta kai karshen ta na jan Inaya su ka bar wajen da gudu kamar kananan yara

da sauri ita ma RIANNA ta riko hannun Nesrine ta ce " mu tafi kar a yi ba da mu ba "
gyada mata kai Nesrine ta yi kafin su fara takawa cikin nitsuwa su ka bar part din

a tare su ka nufi hanyar babbar Fadar Malik , yau masarautar cike da mutane , duk wata masarautar da ke karkashin Mulkin Daular Saudiya sai da ku halartu a fadar , har shi kan shi Sarkin Daular Ottoman

da sallama a bakin su , su ka shigo Fadar ta kofar mata
dan Fadar an raba ta gida biyu , mata nasu wajen daban , Mazan nasu wajen daban Sai kujerar Malik ta zalar Gold an kawata ta da wasu diamond har kyali ya ke , geffen Kujerar akwai wata chair ita ma amma ba ta kai girman ta Malik ba , amma ita ma ta Gold ce har da diamond da Allamun ta MALIKAT ce

cen su ka hango Inaya zaune saman wasu lamusasun sofas ita da Tesnim
kai tsaye wajen su su ka nufa , su ka zauna , duk wani wanda ke cikin masarautar sai da halar ta , MALIKAT AL'UMU da MALIKAT INAS ne kadai ba su cikin wajen saboda Takaba da su ke yi , amma duk abun da ya ke faruwa cikin Fadar su na gani ta camera

su na a haka wasu jibga jibgan sojoji sanye da kakinsu kowane rike da manyan bindigu su ka fara shigowa Fadar da gudu su ka zagaye ko ina
da sauri Diya ya shigo cikin Fadar ya nufi bangaran Maza ya zauna saman wata sofar

ya na zama Wasu dogarai su ka fara shigowa , su ka tare hanyar wuce , su ka bude manyan rigunan su ta yadda ba ka iya ganin komai da ga zaune

su na a haka su ka fara jiyo a busa Algaita duk Fadar ta dauki sautin
daya bayan daya su ka fara mikewa su na sunkuyar da kan su
da sauri ita ma Inaya ta saka hular Alkyabar ta , ta sunkuyar da kai ta na kallon kassa ta wutsiyar ido

su na a haka su ka jiyo wani dadaden qamshi mai sanyaya zuciya ya gwauraye Fadar baki daya , duk irin qamshin da ke cikin fadar sai ya

Please Login or Register in order to submit comment