Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

" ya kai karshen ya na mikewa tsaye

sai a lokacin Aymane ya dawo cikin hayacin shi , bai ma san abun da Diya ya ce kawai shi dai ya mike tsaye , sannan ya yi wa Amir sallama
Diya kuma ya ce " Sai ka tashi ka je ka rarrashi babyn ka " ya kai karshen ya na bushewa da dariya su ka nufi Kofar lift su ka bar part din baki daya

sai da su ka fito su ka nufi part din MALIKAT INAS dan Aymane ya ga RIANNA
su na tsaka da tafiyar su Aymane ya ce " Diya wacece yarinyar nan , kuma a part din Amir ? "

yar karamar dariya Diya ya yi kafin ya ce " ka san Allah Aymane na san halin ka saboda tare mu ka girma cikin gida guda , duk ranar da Amir ya kama ka , ka na kallon yarinyar nan wlh sai ya sa an fida maka idanun nan da ba su zama waje guda "

dan karamin tsaki Aymane ya yi kafin ya ce " ni ba wannan ba , a sani na Tesnim ita kadai ce kanwar Amir , to wannan wacece da gani ba za ta wuce 15 years ba , me kuma ta ke yi a part din shi ? "

dan karamin murmushin geffen fuska Diya ya yi kafin ya ce " Aymane , Amir ne kadai zai ba ke wannan Amsar , amma zan fada maka wani abu guda , duk lokacin da ka ga yarinyar nan ka rufe idanun ka har ta wuce , dan wlh Amir zai iya kashe ko wanene saboda ita kuma a zauna lafiya "

" a kan wannan babyn , ba dai son ta ya ke ba ? "
" ka ga ba mu yi nisa da part din shi ba koma ka tambaye shi " Diya ya fada ya na kara saurin tafiyar shi ya yi gaba dan ya gaji da suruntun Aymane

ci gaba da tafiyar shi Aymane ya yi a hankali ya na sakin wani cool murmushi , gaskiya ba karamin tafiya da imanin Shi Inaya ta yi ba , shi duk duniya bai taba ganin macen da ta burge shi kamar Inaya ba dole ya samo ko wacece


▪INAYA


kai tsaye bedroom din shi ta koma da gudu ta shiga ta nufi gadon ta yi rub da ciki ta na sakin kuka

ita kan ta ba ta san lokacin da ta dauka a hakan ta na kukan ba

a hankali Amir ya turo kofar dakin ya shigo ya na sallama cen kassan makoshi
hannun rike da wani tray , shake da Fruits da wani mug na coffee
karasowa ya yi cikin dakin ya nufi Bedside drawer ya ajiye tray din sannan ya koma ya tsaya bakin gadon cikin sanyin murya ya ce " Cutie tashi na kawo miki breakfast "

Ko sannu ba ta ce mishi ba , ta ci gaba da kukan ta
a hankali ya sauke ajiyar zuciya , ya na lumshe idanun shi a hankali ya sake bude su , sannan ya zauna bakin gadon ya kai hannu saman shoulder din ta ya na fadin " Cutie "

a hankali ta janye Shoulder din ta , ta matsa kadan
janye hannun shi ya yi a hankali , sannan ya mike tsaye
a hankali ya konto saman bayan ta , ya kai dan bakin shi saitin kunnen ta , ya ce " in ba ki son wannan breakfast din , bari na baki wani "

cikin kukan nata ta ce mishi " yaya Zayd , ka kyale ni don Allah ka kyale ni "
" me kuma na yi da za ki ce na kyale ki "

" ni fa kawai na je na ce maka yunwa na ke ji , zan je wajen Aunty RIANNA mu yi breakfast tare "
" Kennan ba za ki yi breakfast tare da ni ba ? " ya fada ya na tashi da ga saman ta ya koma gefe ya zauna

a hankali ta fara rage sautin kukan ta , sannan ta juya ta na fuskantar ceiling ta kai hannu ta fara goge hawayen ta

hannu ya kai saman kumatun ta ya fara goge mata hawayen ta ya na fadin " in ki na kuka sam ba ki yin kyau "

buge hannun shi ta yi ta na kauda kai gefe ta turo dan bakin nan nata
ta na a haka kawai ta ji ya mata runfa da fafadar kirjin shi , ya na kallon face din ta ya ce " yau dai bari na cinye wannan dan bakin Tsiwaar "

a hankali ta juyo ta wurga mishi wata muguwar hararra ba tare da ta ce komai ba
daga mata gera guda ya yi ya na fadin " ya ne yan mata , na yi miki ne ? "

yar karamar dariya ta yi har sai da dimple din ta ya fito
dama abun da ya ke so kennan ya ga ta yi dariya ko zai rage radadin da ya ke ji cikin zuciyar shi

sai da ya ga ta Kamala Dariyar ta sannan sauka da ga saman ta ya koma gefe ya zauna , ya kai hannu ya dauko tray din Fruits ya ajiye saman cinyar shi ya ce " shikenan tashi ki yi breakfast "

mikewa zaune ta yi ta kali tray din sannan ta dago ta kale shi ta na turo baki ta ce " Fruits kadai ? "

" eh , ko ki na son wani abu ne " ya fada ya na dauko wani barin Apple ya kai mata a baki
girgiza mishi kai ta yi ta na bude baki ta karbi Apple din
ajiye mata tray din ya yi saman cinyar ta sannan ya mike ya na fadin " ki same ni a parlour idan kin ida " ya kai karshen ya na nufar kofar fita dakin

da kallo ta raka shi har sai da fita sannan ta ci gaba da shan fruits din ta cikin konciyar hankali


▪TESNIM


zaune ta ke cikin garden , ita da Rouksar , ta yi zugum waje guda ko kiftawa ba ta yi , ga idanun ta sun yi jazir , ta yi kukan har ta koshi
Rouksar kuwa ta na faman latsa wayar ta

Su na a haka su ka jiyo sallama
a tare duk su ka juya su ka kali Abdoul da ke tsaye gaban su , ya saki wani cool murmushi

a tare su ka amsa mishi sallamar shi sannan Rouksar ta ce " kai kuma da ga ina ? "
" I'm sorry , ina son magana da ..... " bai kai karshen maganar shi ba ya juyo ya kali Tesnim allamun da ita ya ke son magana

a hankali ta bude bakin ta , ta ce " me ya faru ? "
" nothing , ina son Magana da Amir , shi ne a ka ce min na zo wajen ki "
cikin rudu ta ce " ni kuma ? wa fada maka hakan ? "

" please ni ba wannan ba , ki kira min shi kawai , ina son magana da shi "

shiru ta yi na dan lokaci ta na kallon shi kafin ta kai ta dauki wayar ta , ta shiga contact ta fara neman number din Amir ta danna mishi kira

ko ringing biyu ba ta yi ba ya dauki kiran
dan karamin murmushi ta saki kafin ta yi mishi sallama , sannan ta ce " Akhie , akwai wanda ke son magana da kai "

cikin nitsuwa Amir ya ce mata " ina jiran ku , ke da shi " ya na gama fadar haka ya katse kiran
ta na jin ya katse kiran ta sauko wayar a hankali , sannan ta fara kokarin Tashi
ta kali Abdoul ta ce " mu je ya ce na raka ka "
da sauri Rouksar ta ce mike ta na fadin " tsaya min , mu tafi sai ku bar ni ni kadai "
gyada mata kai kawai Tesnim ta yi kafin ta fara takawa , Rouksar na geffen ta , Abdoul na biye da bayan su , su ka nufi part din Amir


▪AMIR


konce ya ke cikin parlourn shi , a kassa saman carpet , ya tada kan shi da wani pillow
Inaya na konce saman shi , ya daura hannun shi guda saman bayan shi , gudan kuma saman forehead din shi , ya na kallon ceiling , ta na rike da wayar shi , ta na game , ko da Tesnim ta kira ma ita ce ta dauki kiran , sannan ya kai hannu ya karbi wayar
ita kuma ta kontar da kan ta saman chest din shi ta lumshe idanun shi kamar mai jin barci

Amir kuwa bayan ya katse kiran ya ajiye wayar shi gefe , ya lumshe idanun shi shi ma

sun dauki wajen good five minutes a haka , kafin Amir ya jiyo Muryar Tesnim da Abdoul su na yi mishi Sallama , sai kuma wata Muryar ta uku
ya na jin su amma bai bude idanun shi ba ko sallamar su cikin zuciya ya amsa musu ita

a tare su ka karaso cikin parlourn , Abdoul na ganin Inaya konce a jikin Amir ya saki wani kyawatencen murmushi " dube su don Allah Ko kunya ba su ji " ya fada cikin zuciyar shi

Tesnim kuwa ta na ganin Inaya ta ji duk zuciyar ta ba dadi , yau ga wata konce a jikin yayan ta kuma bai ce mata komai ba , ta yi matukar kishi
Rouksar kuma kamar ta yi tsuntsuwa ta je te shako Inaya ta jefa ta , ta cikin glass din gaban su ta fada ta mutu ta huta ma

gyaran murya Abdoul ya yi mishi sannan ya ce " Zayd , sai a saki yarinyar mutane ko , ga ta Na kawo maka " ya fada da hausa

ba tare da ya bude idanun shi ba ya ce " ka daina kira na da Zayd , in ba za ka ce Amir ba ka yi shiru , sannan ni Tesnim kadai na ce ka kawo min , wacece a tare da ku "

slowly Abdoul ya juya ya kali Rouksar sannan ya juyo ya kali Amir ya ce " ni ma ban sani ba , a tare na gan su "

" shikenan sai ku koma kai da ita " Amir ya fada har yanzu dai idanun shi a lumshe

gyada kan shi kawai Abdoul ya yi kafin ya juya
har ya yi taku biyu ya tsaya cak , ya juyo ya kali Amir ya ce " Please Amir , idan Auta ta tashi ka ce mata mama na son ganin ta , tun kafin a fara Azumi rabon ta da Auta , dama² Nesrine ita ta na zuwa wajen ta "

a hankali Amir ya gyada mishi kai allamun to
dan karamin murmushi Abdoul ya yi kafin ya juya ya nufi Rouksar ya tsaya gaban ta ya ce " mu je , ya ce ya na son magana da sister din shi " ya fada da turanci

kare mishi kallo da ga sama har kassa Rouksar ta yi kafin ta ja dan siririn tsaki ta juya ta bar wajen
dan tabe baki Abdoul ya yi kafin ya juya ya kali Amir ya yi mishi sallama sannan ya juya ya bar wajen shi ma

su na barin wajen Amir ya juya da Inaya ya kontar da ita saman bayan ta , sannan ya mike zaune ya bude idanun shi ya kali Tesnim ya ce " ba za ki zauna ba kin yi tsaye saman mutane "

sunkuyar da kai ta yi ta na marairaice fuska ba tare da ta ce komai ba
" shikenan , zo zauna " ya fada ya na nuna mata geffen shi

girgiza mishi kai ta yi kamar ta yi kuka ta ce " ai ga Sister din ka nan kusan ka , ni na tsaya a nan "

slowly ya juya ya kali Inaya da ke barcin ta cikin konciyar hankali
sannan ya juyo ya kali Tesnim ya ce " kar ki bari na maimaita abun da na ce Tesnim "

a hankali ta daga kafa ta karaso geffen shi ta zauna ta na sunkuyar da kai
ta na haka kawai ta ji ya sa hannu ya rungumo ta ya na fadin " i'm sorry "

nan take kuka ya kubce mata ta kankame shi da kyau
dan bubuga bayan ta ya yi ya na fadin " shikenan ya isa haka , ki daina kukan nan mana "
cikin kukan nata ta ke fadin " Akhie , yanzu Daddy ya tafi ya bar ni "
" please ki daina kukan nan , ba ga ni ba "

a hankali ta dago da ga jikin shi ta ce " bayan ka kyale ni , tun lokacin da yarinyar nan ta shigo gidan nan ka daina kula ni , kullum ka na tare da ita ka manta da ni "

hannu ya kai ya riko kunnuwan shi ya ce " i'm sorry , ki daina kukan nan kin ji my sister "
rage sautin kukan ta ta yi ta na cewa " ni ka kyale ni "
" me ki ke so na yi , ki hakura ki daina kukan nan "

" ni ka daina kula yarinyar nan ba na son ganin ka tare da ita , na fa girme mata " ta fada cikin shagwaba

a hankali ya kai hannu ya janyo ta ya nuna mata Inaya ya ce " kin gan ta ko ? She is my wife , dan haka ba ki girme ta ba , ita ce ta girme ki tun da ta na auren Big bro din ki "

turo dan bakin ta Tesnim ta yi kafin ta ce " yanzu Akhie wannan yarinyar ita matar ka , ga Rouksar nan why ba za ka aure ta ba , sai wannan yarinyar da ko period ma na san ba ta fara ba , saboda ita ka daina kula ni , tun ranar da ka dawo masarautar nan ba ka sake nema ta ba "

hannu ya kai ya ja mata kumatu ya ce " za mu saka kafar wando guda da ke , idan ki ka ce za ki takura mata kin ji dai na fada miki "

shagwabe fuska ta yi ta na fadin " yanzu Akhie saboda wannan yarinyar za mu bata "
" ni dai ban ce za mu bata ba , amma zan so ki ba ta matsayin ta , nan gaba kadan za ta zama MALIKAT din ku , zan so a ce akwai jituwa tsakanin ku , please ki yi min wannan abun kade "

a hankali ta mike zaune ta na kallon shi ta ce " Akhie , ni gaskia ba na so , Ka fi kowa sanin ba na son raini , idan ta ce za ta raina ni wlh ba ruwa na da matar ka ce , dukan mutuwa zan yi mata "

" oh , kin iya Dukan mutuwa kenan , shikenan nan gaba kadan ke ma zan miki auren na huta "

bushewa da dariya Tesnim ta yi ta na fadin " Aure ni kuma ? Hum "
" kin zata da wassa na ke , ni fa har na samo miki miji , ki jira ki gani "
dan zaro idanu ta yi ta na shirin magana ta juyo Muryar Inaya ta na fadin " zancen me ku ke yi "

a tare Amir da Tesnim su ka juyo su ka kale ta , ta na konce idanun ta a lumshe
juyo wa Tesnim ta yi ta kali Amir ta ce " Akhie ni fa ta ban tsoro , barci ta ke fa "
dawo da kallon shi ya yi kan Tesnim ya ce " ni kai na wani lokacin tsoro ta ke ba ni "

yar karamar dariya Tesnim ta yi , ta na shirin magana kawai ta ga an tilo wani pillow ya bugi face din Amir

a razane su ka juya shi da ita su na kallon Inaya , har yanzu dai ta na konce , amma idanun ta su na bude , ta turo dan bakin nan nata

matse gera Amir ya yi ya na fadin " Ni za ki tillo ma wannan abun "
a hankali Inaya ta mike zaune ta na yi mishi hararrar wassa ta ce " ba kai ne ka ce ina ba ka tsoro ba " ta fada da hausa

dan zaro idanu ya yi ya na fadin " kin ji abun da mu ke magana a kai ? "
dan karamin murmushi ta yi ta na gyada mishi kai
" kennan ba barci ki ke ba ? "
murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta ce " ai ku ku ka tashe ni "
[26/09 à 10:33] MIMI:



❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤


(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥




💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀





👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑



【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】




Marubuciyar littafin

【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】





【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】





____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________





PAGE 17 ✍📚




bai ce mata komai ba ya mika mata hannu a kan ta zo
ba musu ta taso da sauri ta riko hannun shi ta na murmushi ta fada jikin shi ta rungume shi

rungume ta shi ma ya yi ya na cewa " ki na jin yunwa ? "
girgiza mishi kai ta yi allamun a'a
" shikenan tashi ku tafi ke da Tesnim , yau tare da ita za ki zama "

a hankali ta dago da ga jikin shi ta na kallon face din shi ta ce " wacece Tesnim ? "
juyawa ya yi ya kali Tesnim da ta tsare su da ido ta na sakin murmushi
a hankali ita ma Inaya ta juya ta kali Tesnim , sai ta sakin mata wani dan karamin murmushi ba tare da ta ce komai ba

mika ma Tesnim hannu ya yi
ba musu ta aza hannun ta saman nashi ,
a hankali ya ja hannun Inaya ya daura shi a sama , sannan ya ce ma Tesnim " na bar miki amanar ta , ki kula da ita yau "
ya na gama fadar haka ya juya ya kali Inaya ya ce " Cutie tashi ku tafi , ina da aikin yi yanzu "

a hankali ta gyada mishi kai kafin ta ce " amma za ka zo in ka ida ko ? "
a hankali shi ma ya gyada mata kai allamun eh

wani cool murmushi ta saki kafin ta mike tsaye ta na rike da hannun Tesnim ta ce " Aunty tashi mu tafi "
ba musu ita ma ta Tesnim ta mike tsaye ta na rike da hannun Inaya , ta ce wa Amir " Sai an jima "
ta kai karshen ta na juyawa ta fara takawa , Inaya na geffen ta su na rike da hannun juna kamar yaya da kanwar ta

da kallo ya raka su har sai da su ka bar wajen sannan ya tashi ya dauki wayar shi ya nufi corridor ya shiga bedroom din shi

bangaran su Inaya kuma , bayan sun baro part din Amir kai tsaye part din MALIKAT AL'UMU su ka nufa

bakin su da Sallama su ka shigo parlourn MALIKAT AL'UMU , ta na zaune ita da Rouksar babu me ce ma wani ufan

MALIKAT AL'UMU na ganin Inaya ta saki wani kyawatencen murmushi ta ce " Tesnim ina kuma ki ka gamo da ita "

dan karamin murmushi Tesnim ta yi ta na karasowa cikin parlourn ta zauna saman sofa , sannan ta janyo Inaya ta zauna geffen ta , ta ce wa MALIKAT AL'UMU " Amir ya ce na taho da ita "

mika mata hannu MALIKAT AL'UMU ta yi
ba musu ta saki hannun Tesnim ta mike ta nufi MALIKAT AL'UMU ta riko hannun ta sannan ta zauna geffen ta , ta na sakin murmushi

"Allah ya sa dai yaron nawa ba ya takura miki ? " MALIKAT AL'UMU ta fada ta na kai hannu ta shafi kan Inaya

cikin ko in kula Inaya ta ce " Ammie , wane yaron kuma ? "
yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi kafin ta sunkuyo da kai , ta kai bakin ta saitin kunnen Inaya ta yi mata rada

ni dai ban ji abun da ta rada mata ba kawai ganin na yi Inaya ta bushe da dariya
mikewa tsaye MALIKAT AL'UMU ta yi ta riko hannun Inaya ta na fadin " taso mu je "
da sauri Tesnim ta ce " momy ina kuma za ki je ? "
ba tare da Ta juyo ba ta ce " idon matambayi " ta kai karshen ta na shiga corridor

wata yar karamar dariya Tesnim ta yi kafin ta mike tsaye
da sauri Rouksar ta riko hannun ta , ta na fadin " Tes wai wacece yarinyar nan , na ga kowa sai daukar ta da sauke ta ya ke "

Tesnim na shirin magana ta jiyo Muryar MALIKAT AL'UMU ta na cewa" Tesnim ! "
kwace hannun ta , Tesnim ta yi ta nufi corridor din ta bar Rouksar nan

kai tsaye bedroom din MALIKAT AL'UMU ta nufa , bakin ta da sallama ta shigo dakin
Inaya na zaune bakin gadon MALIKAT AL'UMU

" ina momy ? " Tesnim ta tambayi Inaya
da yatsa ta nuna mata kofar Toilet ba tare da ta ce komai ba
a hankali Tesnim ta daga kafa ta nufi toilet , har ta kai bakin kofar sai ga MALIKAT AL'UMU ta fito

" yawwa Dauko min box din Turaren nan da ke dakin ki " ta kai karshen ta na rabawa ta geffen ta ta wuce ta nufi Inaya

Tesnim kuwa ta juya ta fice dakin , ta koma dakin ta
" baby taso mu tafi " MALIKAT AL'UMU ta fada , ta na mika mata hannu
ba musu ta riko hannun MALIKAT AL'UMU ta mike tsaye su ka nufi Toilet a tare
sai da su ka shiga sannan ta dauki wani towel fari ta mikawa Inaya ta ce " cire kayan ki "

ba musu Inaya ta cire rigar jikin ta , da underwear ko kunyar MALIKAT AL'UMU ba ta ji ba ta daura towel din a kirjin ta
dai'dai lokacin da Tesnim ta shigo Toilet din ta na rike da wani box navy blue mai mugun kyau , ta mikawa MALIKAT AL'UMU sannan ta juya da sauri ta fice dan lokacin sallat ya yi

bude box din nan MALIKAT AL'UMU ta yi , nan take wani dadaden kamshi ya tashi ya gwauraye duk toilet din
Ajiye box din ta yi bakin bath ta dauki wata kwalbar Fara fes ta bude ta zuba turaren a cikin ruwan bath din
sannan ta rufe , sai da ta zuba kalar turare har biyar sannan ta mike ta ce ma Inaya ta shiga cikin ruwan ta yi wanka , sannan ta yo Alwalla ta fito
da to Inaya ta amsa mata sannan ta nufi bath din , MALIKAT AL'UMU kuma ta fito toilet din

Bayan wani dan lokacin Inaya ta fito da ga cikin Toilet din , sai tashin kamshi ta ke mai dadi
ta na fitowa MALIKAT AL'UMU ta mike

Please Login or Register in order to submit comment