Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*1⃣3⃣*




*T*ana shiga d'akin tayi shirim akan gadon tamkar kayan wanki,irin su MA'U irin matan nan ne da Sam basu da fasali a tsarinsu, bayaga d'an banzan son jiki da take da shi....
Kamar wacce aka mintsina haka tayi saurin mik'ewa tsaye tana raba ido...
Wani durowa ta nufa,daga jikinsa kuma cikin wani d'an sak'o,ta mik'a hannu,poly bag en dake wajen ta janyo ta hau bud'e cikinta,tana fito da kayan dake k'unshe a ciki...
Suphagetti ne da d'an dama dan idan basu fi 10 ba to zasu iya kaiwa hakan...
K'waya d'aya ta d'auka ta nufi hanyan fita daga d'akin,a zuciyanta kuma tana sak'e²,har ta k'idasa ficewa...

*********

Tana zaune ta idar da sallah ta rasa me ke mata dad'i a duniyarta,tunaninma yau kam tama kasa yinsa,duk jinta take kamar wata daban...
Hankalinta gaba d'aya baya tare da ita a wannnan lokaci,tayi zurfi wajen tunaninta,tana son tuno wane garima dangin mahaifiyarta suke?

Shigowar MA'U d'akin shi ya sata dawowa duniyarta babu shiri,cikin wani irin kallo ta jefeta da shi tana mai mik'o mata suphagettin dake hannunta,ba ko bayani ta sa kai ta fice..
Ita kam KHUBRA da ido ta bita dan zuwa yanzun ko dai bata gama sanin halin MA'U ba duka to tabbas ta san mafi yawan kaso daga halayentan..
Cikin sanyinta ta mik'e had'e da zare hijab en dake jikinta,ta fice tana sak'a da warwara...

Har ta kammala bata sake jin ko da motsin MA'U ba,duk da hakan ba bak'on al'amari bane a gurinta,amma sai duk taji kewa na damunta,na rashin wani d'an adam...
Juyewa tayi ta d'auka ta nufi cikin d'akin nata,tana ajiyewa ta juya ta fice...

Hakimar tana kallonta amma ko sannu bare ta sa ran jin wata kalma mai dad'i,haka ta banzatar da ita,mik'ewa tayi ta janyo plask en..
Sai da ta gama k'oshi sannan ta shiga rafka mata kira...
Cikin sauri ta shigo tana sunkuyar da kanta k'asa...

Kwanon ta nuna mata,bata tsaya b'ata lokaciba ta sungumeshi tayi waje,sanin ko ta ce bata ci,kanta zata zalunta...

Sai da ta tabbatar ta tsaftace duk wani abu da tasan tayi amfani da shi kafin ta nufi d'akin shirgi da a yanzun ya zama nata...
Kwanciya tayi cike da son ganin mutumin ta na mafarki,tana wannan tunani har bata san lokacin da bacci yayi gaba da itaba...

**********

Ko da MALAM BUBA ya shiga gidan direct d'akinsa ya nufa yana shiga kamar jiya da k'yar ya iya k'arasawa zuwa shimfid'arsa wanda baima tsaya tunanin ko lafiyaba ya kifa kamar wanda aka hankad'a,take wani nannauyan bacci yayi gaba da shi...


*********

MA'U ce zaune cikin d'akinta,ta rafka tagumi,tunaninta ta yaya zata samu hanyar da kud'i zasu dinga shigo mata,dan kam wannan rayuwa lamarin yana damunta...
Banda sak'a da warwara babu abunda take,zuciyoyinta biyu kowanne tana kawo mata shawaran da a ganinsu shi ne masalaha....

Ta tabbata idan akace zata ta'allak'a ne akan d'an abunda KHUBRA zata samu to tabbas tana cikin wahala,coz ta san halin yayarta da masifar son kud'i _(kunjifa wai kura ce za tace da kare maye)..._

Kafin wani lokaci mai tsayi zuciyarta ta gama rinjayarta,kwanciya tayi tana mai farin cikin samun mafita....

*IN THE MORNING* *******

KHUBRA dake tsaka da shara,ta d'aga kai ta kalli gurin da ta jiyo motsi,tayi matuk'ar mamaki da ta ganta a lokacin da batayi tsammaniba...
''Shin dama tana iya tashi da wuri haka,amma kullum sai ibada ta wuceta?''...

Haka tayi ta tunanin abunda sam bashida wata fa'ida a gareta...
Tana nan tana tunane² har bata san lokacin da MA'U ta gama shiryawaba,sai ganinta tayi ta fito hannunta rik'e da y'ar jakarta wacce akewa lak'abi da *_(JIK'ATA GUMIN HAMMATA)_*...

Hannunta rik'e da leda ta fito tana jaan k'afarta da har yau bata samu an gyaraba...
Naira #50 ta mik'a mata ''ki siyo garin kwaki''...
Daga haka ta wuce ta fice,har tayi nisa ta dawo,KHUBRA dake sunkuye har tsoro abun ya bata dan bata ga lokacin da ta dawo ba,sai magana taji a bayanta....

_''Idan kinga ban dawo da wuri ba kina iya rufe gidan''_
Haka ta shud'a tayi gaba....

********
Ko da ya farka da safe lokacin gari har ya gama haske,rana tana shirin mamaye sararin samaniya...
Istighfari ya shiga yi,coz har aka idar da sallah bai san anayi ba,abunda a iya tsawon rayuwarsa yau ne rana ta farko da yayi rashin sallah a jam'i...
Da matuk'ar k'unar zuciya ya mik'e ya fita don d'auro alwala...

A tsakar gida ya iske LADIYO ta fito banda susar jikinta babu abunda take,kamar wadda tayi wanka da _karara..._
Ta gabanta ya zo zai wuce,cikin rud'ewa dan tasan zai mata fad'an rashin sallah a kan lokaci ne,ta hau fad'in
''MALAM barka da tashi''
Ba tare da tayi tsammanin zai amsa ba...

Yana washe baki ya juyo yana kallonta ''Arrrhhh! hajajju LADIYO an tashi lafiya?''...

Da mugun mamaki ta d'ago tana binsa da ido,sai dai tana yin wani tunani kuma ta waske tana murmushin mugunta _(hak'ansu ya cinma ruwa)_.......




_#PLEASE FAN'S KUMIN UZURI DAN ALLAH NA RASHIN POSTING,UZURI NE YA MIN YAWA,DA YASA KO ONLINE BA NAYI,YAU KUMA NASO YIN TYPING EN BUH CIWON KAI YA HANA NI,IN SHA ALLAH ZA KUJINI ZUWA GOBE,DA YARDAR ALLAH..._




*_~#TEAM KHUBRA.~_*




*_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠


*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*©®2018*
*16/ąpril,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._

*~________________________~*

*ADDU'AR TAFIYA MASALLACI.*

_ALLAHUMMAJ'AL FIY K'ALBIY NURAN,WAFIY LISANIY NURAN,WAFIY SAM'IY NURAN,WAFIY BASARIY NURAN,WAMIN FAUQIY NURAN,WAMIN TAHTIY NURAN,WA-ANYAMINIY NURAN,WA-ANSHIMALIY NURAN,WAMIN AMAMIY NURAN,WAMIN KHALFIY NURAN,WAJA'AL FIY NAFSIY NURAN,WA-A'AZIMLIY NURAN,WA-AZZIMLIY NURAN,WAJA'ALLIY NURAN,WAJA'ALNIY NURAN,ALLAHUMMA A'A'DINIY NURAN,WAJA'AL FIY ASABIY NURAN,WAFIY LAHAMIY NURAN,WAFIY DAMIY NURAN,WAFIY SHA'ARIY NURAN,WAFIY BASHARIY NURAN,ALLAHUMMAJ'ALLIY NURAN FIY K'ABARIY,WA-NURAN FIY IZAMIY,WAZIDNIY NURAN,WAZIDNIY NURAN,WAZIDNIY NURAN,WAHABLIY NURAN._

*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*

*~________________________~*

*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*

_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._

*~__________________________~*



*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*1⃣4⃣*




*B*akinta ta wage mai kama da k'ofar gari,hak'oranta kamar an shafa musu d'orawa...

''Lafiya k'alau MALAM''
Tana yi tana kwarkwasa kamar wata tsohuwar y'ar duniya...

Shi dai binta yake da kallo kamar wani wawa,haka ya sungumi buta yayi band'aki..
Ganin haka yasa itama LADIYON ta nemi guri ta k'ame kamar soja tana jiran ganin me zai kuma biyo baya...

Da mamaki take kallonsa yana alwala,mutumin da sallah bata wuce shi a jam'i amma shi ne zai yi sallah da wannan ranar...

Jikinta taja ta shiga band'aki,har lokacin bai bar gurin ba,itama tayi alwala...
Tana idarwa zata shiga d'aki taga ya biyo bayanta,da mamaki ta sake kallonsa,har ya shige d'akintan,ita kuma ta dafa masa baya...

A kan abun sallah ta tarar da shi yana washe mata baki yace

''Yi sauri kisa hijab muyi jam'i''

Ita dai ido ne nata,haka ya jasu sallan har suka idar...

After sun idar,ya shiga bata hak'urin abubuwan da yake mata,kamar wata uwarsa harda saka guiwoyinsa a k'asa....

Su LADIYO an samu abunda ake so,amma can k'asan zuciyanta tunani take akan yau shene shigowarsa ta k'arshe cikin d'akin nata,sai dai ta kasa tunawa...

Jin da tayi ana shafa jikinta,shi ya dawo da ita duniyarta..
Kallonsa tayi cikin mamakin hakan,ta kasa cewa komi...

''Haba uwar gidan MALAM BUBA kice wani abu mana kinyi shiru''
Ita dai binsa take da kallo,shi kuma sai dad'a shige mata yake...
Su LADIYO da jin haka,bata san lokacin da itama ta biyewa MALAM en suka ci gaba da shafar juna,har zuwa MALAM ya samu damar da yake nema a agurinta na cilla k'wallonsa a kwando....
Ihuuu LADIYO take tana fad'in
''Aradu MALAM kasan takan wanga harka,wayyoo dad'i,MALAM ci gaba''...

Hannu yasa ya rufe mata baki,saboda surutun nata ya soma bashi haushi..
Ita kuwa sai dad'a mak'alo shi take,kamar wata k'wad'uwa.... 😂


********

Duk wani aiki da za tayi sai da ta kammala shi sannan ta saka hijab enta..
Fitowa tayi daga gidan tana tafe cikin nutsuwa kamar yanda ta saba,haka har ta isa shagon,ta mik'a kud'in ya bata abunda zai bata,ta sake kamo hanya ta dawo...
Ko da ta dawo gidan babu ruwa sosai,hakan yasa ta fita da bocket tayi ta faman jido ruwa a mak'otansu har sai da ta cika komai dake gurin...
K'ofar gidan ta je ta kulle ta dawo,d'akin MA'U ta shiga ta kwanta a saman gadon MA'U tayi d'ai²,take kuwa baccin wahala ya d'auketa....


*********

Sai bayan komai ya lafa sannan LADIYO ta cika MALAM BUBA ta koma gefe ta kwanta...

Shi kuwa MALAM sai bayan da ya gama biyan buk'atarsa sannan ya tuna inda yake da kuma k'yamar kusantar LADIYON a yanda take,riga kad'ai ya saka ya nufi band'aki yayi wankan tsarki..
'Dakin ya sake dawowa,bai san dalilin da yasa yake jinsa wani iri ba,kamar mara lafiya...


Kud'i ya zaro ya mik'a mata kan ta samu abinda za ta dafa a gidan,karb'a tayi,shi kuma ya juya ya fice daga gidan....


********

Baccinta take ba tare da tunanin komai ba...
Tayi nisa a baccin,ta hangoshi kamar kowane lokaci cikin fararen tufafi,binsa take amma ta kasa cin masa,hakan ya sa ta durk'ushe tana kuka mai tsanani..

Kiransa take HAYATEEY,amma ko waigowa baiba bare ya kalleta....

Hakan da yayi mata shi yasa ta fasa k'ara ta zube a gurin sumammiya....


**********

Can cikin garin SUMAILA cikin wani k'auye ta sauka ta ci gaba da ratsa hanya har ta billo wani farfajiyar guri...
Gidane guda d'aya wanda ba shi da mak'ota ko k'waya...
Tunkarar gidan tayi ta shiga k'wank'wasawa ganinsa a kulle....

Bud'e mata wata y'ar yarinya tayi,tana mai bata hanya...
Murmushi tayiwa yarinyar ta bita suka shiga ciki...
A wani d'aki aka sauketa ta nemi guri ta zauna tana jiran fitowar MALAMIN...

Sai da ta shafe tsawon awanni 4 sannan mutumin ya shigo,daga shi sai dogon riga,duk ta k'udundune ga daud'a kamar ba jikin bil-adam ba...

Zama yayi yana fuskantar ta...

Ta bud'e baki za tayi magana ya d'aga mata hannu,alamar baya buk'atar tace wani abu.....

''Aikinki ba wani mai wahala bane,sai dai ta wace hanya kike so ta dinga kawo miki kud'in?''....

''Koma mene ne MALAM tayi bai dame ni ba in dai zata dinga kawomin kud'i''....

''An gama, sharad'in aikinki idan kika kuskure a cikin aikin da zan baki komai zai juya kanki''..

Tun bai k'arasaba tace
''Na amince''
Ta fad'a tana jiran ganin,me zai biyo baya...


Nan take ta ciro wasu layu da kuma k'ullin garin magani,ya mik'a mata...
''Wannan ya nuna layun,zaki binnesu a tsakiyar hanyan da jama'a suke bi...
Shi kuma wannan k'ullin ya nuna mata garin maganin,za ki barbad'a a bakin k'ofar d'akin da kija san za ta tsallaka....
Ki tabbatar ta tsallaka shi,saboda shi ne cikon aikin ki,zai sa mata farin jini wajen mutane,sai dai babu wanda zai zo da niyyar aurenta,zaki samu mahaukatan kud'ad'e ta dalilinta''......
Jin an ambaci mahaukatan kud'i ta shiga b'are baki,dan murna....

Kud'i ta fitar a jakar tata ta mik'a masa,ta masa godiya ta kama hanya,tare da alk'awarin dawowa...

********

Firgitan da tayi yasa ta farka,ga sautin k'ara da ya ratsa kunnuwanta wanda bata san daga ina yake ba,sai bayan ta farka ta fuskanci inda k'aran ya fito,ashe da tayi kenan ba iya cikin bacci kad'ai tayi ba har a zahiri tayi...

Addu'ah tayi ta mik'e tad'auro alwala,ta jima tana neman sauk'in al'amura daga ubangiji,tare da kariyarsa a gareta...
Sannan ta mik'e,ta d'auki garin kwakinta tayi waje.....

Ko rabi bata iya ciba taji ta k'oshi,hakan yasa ta maida ragowar ta b'oye.....
Tayiwa Allah godiya,ta sake kwanciya,tana tunani kan wannan rikitaccen mafarkinta.....

Da yamma tana kwance a tsakar gidan,maranta taji tana tsunkulinta kad'an² take ta gane abunda yake shirin faruwa da ita,tashi tayi ta kintsa jikinta,ta dawo ta ci gaba da sauron kukan tsuntsaye dake kan bishiyar mak'otansu,haka har akayi sallan Maghre...
Sai lokacin wani tsoro ya ziyarceta,take kuwa ta sake k'ulewa a d'akin MA'U....

**********

Cikin dare sosai ta iso,k'ofar ta shiga bugawa da iya k'arfinta...

Jin bugun yayi yawa yasa KHUBRA ta fito ta bud'e coz ta gane mai bugun,sai a lokacin ta samu nutsuwa....

Duk wani shiri na MA'U ta gama k'udurce a daren ranar zata aiwatar da komai,hakan ne ma yasa ko gidan bata nufoba sai da ta aiwatar da nufinta...

Lokacin gari ya dad'a yin shiru ta fito ta k'arasa abunda za tayi,ta koma zuciyarta wasai,sai kuma jiran ganin abunda zai biyo baya..........

#UHMMM!KU BIYONI DAN JIN YANDA ZA A K'ARKE..
LUV U.....






*_~#TEAM KHUBRA.~_*



*_REAL SMASHER._*🤞🏻😘
💠💠💠💠💠



*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*©®2018*
*21/ąpril,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._

*~________________________~*

*ADDU'AR SHIGA MASALLACI.*

_A'UZHUBILLAHIL AZIYM,WABI-WAJHIHIL KHARIM,WASUL'DANIHIL-K'ADIYM,MINASH-SHAI'DANIR RAJIYM,BISMILLAHI WASSALATU WASSALAMU ALAA RASULILLAH ALLAHUMMAFTALIY ABWABA RAHMATIK..._

*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*

*~________________________~*

*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*

_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._

*~________________________~*

_Ina mai bawa d'aukacin masoya wannan novel na *Y'AR GARUWA* hak'urin jina da kukayi shiru kwanaki da yawa,kumin afuwa na jina shiru tsawon wad'annan kwanakin,coz abubuwa sun min yawa shi yasa ban samu nayi posting ba,hope uzurina zai zama karb'ab'b'e..._

*~________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*1⃣5⃣*




*C*ikin dare ta farka,sanadin mummunan mafarkin da tayi...
Addu'ah ta jima tanayi,duk da babu halin tayi sallah,haka taita kai kukanta ga Allah akan neman sauk'i da sauyin rayuwa, wanda k'arshe sai da takai kusan asuba bata koma baccinba...
Da k'yar ta samu wani nannauyan bacci yayi gaba da ita....


*********

Da misalin k'arfe 10:15am MA'U ta fito tana ta faman murna ta san ko ba komai yanzun kam ai tayi nasara..
'Dakin da KHUBRA ke kwana ta nufa daga inda take a bak'in k'ofan ta lek'a sai dai duk iya hangenta bata gantaba,murna ta koma tana yi har da rawa na samun nasara...
Har za ta koma d'akinta ta dawo tunowa da maganar da MALAMIN ya mata,akan idan har wacce akayi dominta ta tsallaka babu komai dan ta bi ta wajen...

'Dakin ta nufa tana son tabbatarwa,ai kuwa ta kunna kai cikin d'akin,tana ta murna abunta,sai dai abunda ta gani shi ya tsorata ta ta ko zaro idanu waje,ko me ta tuna kuma ta saki ranta...
Cikin salo na bariki ta shiga tashin KHUBRA kamar da can haka take yi idan zata tashe ta....

Ko ita da kanta KHUBRAN sai da abun yaso ya bata tsoro,mamaki shimfid'e a kan fuskarta take kallon MA'U...

''Yar lele tashi maza kiyi wanka,ga abinci can na tanadar miki,maza taso kiyi wanka,zanje kasuwa zan siyo miki kaya,maza yi sauri kinji ko''

Ita maganganun MA'UN ma sun sa ta shiga wani irin shock,aiko haka taita binta da kallo kamar wata doluwa...

Janta MA'U ta shiga yi,kamar k'aramar yarinya,har bakin band'aki ta kaita,tana murmushi ta turara...

Ga KHUBRA kuwa bata gama mamakintaba sai da tasa hannu cikin ruwan wanka,nan taji shi da d'umi,wannan wane irin bak'on al'amari ne wannan kuma?
Haka taita tunane²,tayi wankan ta fito,jikinta duk yayi sanyi..
Dai² lokacin MA'U ta fito daga d'aki tana fad'in

''Kiyi maza ki shirya kinji ko,zani kasuwa na dawo,kada kiyi girkifa,idan na dawo zanyi komai kinji y'ar lele''
Fuskanta a sake take ta faman zuba kamar lalatacciyar mota,har ta fice daga gidan tana magana wanda ita kam KHUBRA batama san me take fad'aba coz tayi nisa cikin duniyar tunani....

'Dakin MA'UN ta shiga ta tarar da abinci a rufe a cikin plate da wani jug na robber mai d'an kyau...
Bata tsaya b'ata lokaciba ta d'auko ta ajiye a k'asa ta shiga bud'ewa...
K'amshi ne ya daki hancinta,tabi abun da ido,indomie ne da wainan k'wai a sama,sai turiri take,take ta shiga had'iyan miyau,haka ta bud'e jug en nan kuwa ta tarar da shi cike da tea mai kauri....
Ci tayi sai da ta tabbatar ta k'oshi tayiwa Allah godiya bisa ni'imar da yayi mata,na azurta ta da irin wannan abincin da tun da tazo garin bata tab'a cin kamarsa a dad'i ba...

Sai da ta gama d'urawa cikinta d'a'aam sannan ta soma tunanin maganar MA'U...
Tambayoyi dayawa taitayiwa kanta,sai dai babu amsa,ta barwa ranta koma mene ne ta tabbata shirin cutarta take,take kuwa ta hau kuka tana addu'ar neman tsari daga dukkan abun sharri....

Haka ta kusan wuni tana tunane²,shigowar MA'U da ta dawo daga kasuwa shi ya katse mata tunani,ta bita da kallon mamaki ganin yadda ta rik'o kaya a hannunta nik'i²....
Tashi tayi za ta karb'a ita kuwa MA'U ta hanata,haka ta k'yaleta,guri ta samu ta zauna nan ta shiga fito da kaya tana d'agawa tana nunawa KHUBRA sai zuba take...
Kayan marabarsu da babu d'aya,ita kuwa sai binsu take da ido daga KAYAN har MA'UN da ta siyo...


*********

Tunda ya fita daga gidan ko waiwayarsa baiba haka ranar yaita uzurinsa a waje...

Ita ko LADIYO tana ganin fitarsa ta zari mayafi sai gidan TABAWA nanfa suka shiga firar abunda ya faru tsakaninta da MALAM BUBA,bata b'oye mata komai ba ko da kuwa wasali haka ta sanar da ita hatta kwanciyar da sukayi sai da ta labarta mata...
_(Gareku matan aure da y'an mata masu niyyar yin aure,ba ko wane sirri ake fad'awa k'awa ba,bare kuma har ki saki baki ki fad'a mata sirrin yadda kuka kwanta ke da mijinki,ko da kuwa ciki d'aya kuka fito,ahir d'inki da fad'in wannan sirri dan gujewa fad'awa a halaka,,,,,Allah yasa mu dace)... ameen....._

Haka ta kusan wuni a gidan LADIYO kafin daga baya ta tashi ta bar gidan...
Ita kuwa TABAWA dad'i ne ya cika ta jin yadda LADIYO ta kwance mata sirrinta,tana rakata da harara tana tab'e baki,dan burinta bai wuce ganin LADIYON a k'asa ba.....

**********
Ita dai kamar mai koyan kallon wani abu,irin wad'anda akayiwa aikin idanu haka ta zama ranar,duk inda MA'U tayi idanunta na kanta kamar zasu fad'o saboda kallo....


Da yamma kuwa tun bayan sallan la'asar MA'U ta sake sa KHUBRA yin wanka,cikin kayan da ta siyo haka ta sa wani riga da siket,da wani d'an siririn gyale,duk kunya ta hana KHUBRA sakewa haka suka fita,ita dai kallon kanta take kamar wata y'ar iska...
Itama cikin shirinta suka fito,da tambaya suka nemi MALAMIN da yake gyaran targad'e...
Ai kuwa sunyi masa bayani,MALAM na kama k'afar MA'U ya soma matsawa,ta shiga kururuwa,bige² take da hannayenta da k'afa...
Amma MALAM bai saki ba,sai da yatabbatar ya gyara sannan ya saketa...

Tun da aka soma gyaran MA'U na fara ihun nan,KHUBRA take ta b'oyayyiyar dariya,har kifawa tayi saboda dariya...

Da k'yar take tafiya a da,sai gashi yanzun ta dawo normal,sai harare² da take uwa wani ya mata laifin....

Sai bayan da suka koma gida,cikin dabara MA'U take tambayan KHUBRA
''Yau kuwa kin fito daga d'aki?''

Kasa gane inda tambayan ya dosa tayi,ta tsaya tana kallonta kawai
''Baki gane ba ko?''

Kai ta d'aga tana jiran k'arin bayani

''Da safe fa nake nufi,kin fito ko kuwa sai da na shiga?''

'Dan murmushi tayi ta kad'a mata kai,kafin tace
''A'a ban tashi da wuriba ai yau,sai lokacin da kika shiga sannan na tashi''...

Ko kafin ta k'arasa MA'U ta mako mata wata uwar ashar da tasa tayi shiru tana k'ara kallonta cike da rashin yarda...

Zagi ba irin wanda MA'U bata yiba a ranar,kamar za tayi hauka haka tayi²,da taga abun bai mataba kuwa k'arshe rufe KHUBRA tayi da duka,ita kuwa tana zaune inda take ko motsi bata yiba,har tayi ta gaji,dan kanta ta rabu da ita,ta koma gefe tana huci...



Please Login or Register in order to submit comment