Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹





*©®2018*
*21/ʝųŋɛ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

_Wannan shafi tukuicine gareku masoyana kuma masoyan wannan novel nawa na *Y'AR GARUWA* a duk inda kuke a fad'in duniya ina al'fahari daku,idan babu ku tabbas babu ni ina sonku so irin wanda bazai fad'uba da baki,Allah ya barmin ku a duk inda kuke....Na gaisheku oll 👌 kuyi komai ba komai *SMASHER* taku ce..._
_Fatan munyi sallah lafiya, ubangiji ya maimaita mana..Ameen.._
*~________________________~*

_Sisinah wollah *GENTLE,SMASHER,HUBBEEY,LIPTON* tare da *AUFANA* muna matuk'ar alfahari dake wollai muna godiya da sadaukarwarki gare mu,jinjinar ban girma ga *CWEET DIDEEYLOV* Allah ya d'aukaka mana ke ki jima kiyi k'arko lokacinki ne yanzun ki ci gaba da haskawa cikin duniyar yanar gizo-gizo,muna nan biye dake duk inda kike...Godiya mai tarin yawa Allah ya k'ara miki lafiya da nisan kwana mai amfani.._

*~________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*3⃣0⃣*



*Z* ama yayi kamar wanda aka dangwarar abun da yaji daga bakin KHALEED en duk ya d'aure masa kai,kallonsa ya sake yi yana son sake tabbatarwa dan kada suzo suyi abu da ka shi yasa a wannan lokacin da ya sake kallonsa ya furta
"Da dai ka nemi guri ka zauna,dan ni har ga Allah ina buk'atar kamin k'arin bayani kada muzo muyi abunda zaisa muyi DANA SANI"

Wani banzan kallo BB ya bishi da shi had'e da sakin tsaki,ba tare da ya zauna ba kamar yadda KHALEEL en ya buk'ata ya fara magana
"Kafi kowa sanin halina kamar yadda kasan ba zan yi maka k'arya ba"

"Hakane amma kasan shi al'amari irin wannan ba a masa gaggawa,da ka dakata munyi bincike tukuna"

"Heeyy!MALAM har wani BINCIKE kake neman muyi bayan wanda nayi,ko an fad'a maka nima ina cikin mutanen da suke yanke hukunci cikin gaggawa?
Idan mafarki kake to maza ka farka dan wannan kwana² da kakemin bazai hanani abunda nayi niyyaba"...

"To Allah ya kyauta,kai matsalarka kana da shegen taurin kai,baza ka tsaya kayima mutane bayaniba sai dai ka bada magana a dunk'ule"

"Kai kuma gaka mai kullallen kai da baka iya fuskanta ko?"

"Mtssssss!Allah ya shirye ka,amma zauna muyi shawaran hanyan da ya kamata mubi kafin muje wajen D.P.O"

Jin da yayi ya ambaci D.P.O shi ya bashi damar zama
"To yanzun mene abun yi ne kam?" BB ya tambayi KHALEEL

"Ummmm!ina ganin mu bari zuwa gobe sai muje mu sanar masa duk halin da ake ciki,ina tunanin haka ya kamata muyi"

"Toh!hakanma yayi Allah ya kaimu.....Muje nama UMMI sallama zan wuce gida dare na dad'a yi"
"Ok ba matsala muje"

Mik'ewa sukayi suna masu nufan cikin gidan....
A parlor suka tarar da ita har time en tana kallo,sallama ya mata,ta bishi da fatan isa gida lafiya..
Har bakin motor KHALEEL ya rakashi sukayi sallama tare da musabiha,yayima motor en key........

《《》》

'Daya bayan d'aya take bin robber's en nata tana zuba musu ruwa yayinda cikin k'arfin hali da k'arfin zuciya take d'auka tana jerasu cikin kuran nata,haka taita fama har ta gama jerasu..
Hannu ta mik'a saman pore head enta tana goge sweat da ya tsatsafo mata,sai da ta d'an huta tukun kafin ta kama hanyan shiga cikin gari,kamar jiya haka tayi ta zagaye cikin garin,kafin wucewar awa d'aya babu komai cikin kuran nata,kasancewar garin sun d'anyi nisa da gurin da ake d'ebo ruwan,shi yasa wasu daga cikin mutanen garin basa son zuwa d'iban ruwan,yayinda wasu kuma suka fi son *"Y'AN GARUWA"* su kawo su saya....

Ta bakin kasuwa ta biyo zata koma,a dai² lokacin BABA ZUWAIRA na kan ciniki itama,ta hango KHUBRA lokacin kuma rana har ta bud'e sosai,da murmushi a fuskanta ta k'araso...

"Y'ata ta kaina da ganin wannan murmushin da kike akwai alamun nasara"
BABA ZUWAIRA ta fad'a itama tana murmushin

"Wollahi kuwa BABATA anyi nasara"

"Aaa!masha Allah,maza zo kici abinci kafin ki tafi"

"Laaa!BABA nafa ci abinci d'azu kuma ni bana jin yunwa yanzun"

"To shi kenan maza zo ki huta kafin ki tafi ko"

"A'a gara dai na koma bakin sana'a anjima sai na huta"

"To shi kenan Allah ya bada sa'a"

KHUBRA ta amsa da "ameen" sannan ta kama hanyan komawa rafi,kamar wancan lokacin haka ta kammala ta sake biyo hanyan jejin zuwa cikin gari......

《《》》

"Haba HAJIYA LAURA nafa fad'a miki yanda al'amarin nan ya kasance,wallahi yaran nan yana neman ya jagulamin lissafi,gaba d'aya ya gama sanin duk wani abu dana aikata kan wannan matsiyaciyar yarinyar...
'Dazufa da yanamin magana kamar shi ya haifeni,har da yimin wani wa'azi"

"Kai HAJIYA MURJA kina d'aukan komai da zafi,banda abunki dan yayi miki wannan maganar shi ne zai sa ki tashi hankali akan wannan maganar"

"To me kike so ayi kina ganin yadda yake maganar police kinga kuwa shirinmu yana neman rushewa"......

"Ni kam dan Allah HAJIYA MURJA ki kwantar da hankalinki,zan san yadda zanyi na ganin babu abunda ya faru"

"Uhmmm!HAJIYA LAURA kenan lallai baki san halin KHALEED ba,ko ni da nake matsayin mahaifiyarsa ina shayin shiga al'amuransa,saboda halinsa kaf irin na maifinsa ne,idan sukayi magana basa tab'a canzawa,suna da matuk'ar taurin kai,shi yasa nake jin tsoron su furta wata magana dan ina da tabbacin ba janyewa zai yiba"....

"To ai shi kenan amma dai duk yanda ake cikima zan sanar miki"

Ko sallama HAJIYA MURJA bata iya yiwa HAJIYA LAURA ba ta datse kiran,saboda hankalinta tashe yake da abunda yake shirin faruwa tsakaninta da KHALEED da yake neman tada mata K'AYAR BAYA...
Kaiwa da kawowa ta shiga yi cikin d'akin,sam ta kasa tunani hankalinta sam ya kasa kwanciya.....

《《》》

"Ke dallah kefa nake jira kin wani kwanta kamar kayan wanki,bayan kin san ke nake jira,bana son wannan rainin wayon,kawai hajiya ki tashi ina son jina a sama cikin hazo ina yawo"

Da kyar MA'U ta d'ago tana kallonsa "Haba mana kayi hak'uri zuwa anjima,ina jin bacci yanzun kome kake buk'ata idan na tashi kayi,amma yanzun ka kyaleni"

"Ke ai kinji matsalarki da an tab'aki ki ambaci gajiya ko bacci"

"To me kake so nayi maka idan ban hutaba so kake na mutu a tsaye ko da yaushe kana aiki a kaina sai kace wata engine"

"Kai baki fahimceni bane,amma ai ba haka nake nufi ba,kin gane so nake ko da one round ne na k'ara kin gane ai"
Cike da duniyanci yayi maganar yana mata winking...

"Uhmmm!baka da dama idan kaso abu kamar d'a yaso fitowa daga cikin mahaifiyarsa,idan ban amince bama bazaka barni nayi bacci cikin kwanciyar hankali ba ya zanyi da kai"

Dariya suka saka duka kafin su lula duniyar masha'a kamar yadda suka saba....

《《》》

"Yawwa y'ata ta kaina gara da kika dawo kinga yamma tayi sosai dama kuma ke nake jiran ganin dawowarki maza yanzu mu wuce gida"

"To BABA barin sa kayan a can"

"Su kuma robobin ki kaisu ina?"

"Laaaa!bari kiga yadda zanyi zasu shiga gaba d'aya"

Da saurinta ta k'arasa bakin kuran robber's en ta hau d'ora wata kan wata a kwance,sannan ta shiga d'ora coolers a gurin data samar tana gamawa suka kama hanyar komawa gida,suna tafe kowa da tunanin da yake a zuciyarsa.....

Duk inda suka gifta kaga mutane na k'usk'us akan neman sanin alak'ar dake tsakaninsu sai dai duk gulmar tasu babu wanda yasan gaskiyar al'amarin......


"Kai KHUBRA aikin nan yayi miki yawa ki bari muyi tare"

"A'a wallahi BABA ki bari zanyi,yanzu zaki ga har na gama fa"

"Kawai dai dan babu yadda zanyi shi yasa zan bar miki aikin nan,Allah yayi miki albarka"

"Ameen ya Allah....Laaa!na manta BABA ban baki cinikin da nayi d'azuba"

'Dan murmushi BABA ZUWAIRA tayi bata ce komaiba,ta zauna cikin rumfa tana gyara kayan miyan da zatayi na abincin gobe..

Har ta gama wanke cooler's en ta kawo su cikin rumfa ta kife su duk dan ruwan ya fita daga ciki..
Kud'in ta fito da ta kawo shi gaban BABA ZUWAIRA ta ajiye,a hankali BABA ta d'ebi kud'in tana lissafawa,da murmushi a fuskanta ta kalli KHUBRA
"Masha Allah,gaskiya kinyi ciniki sosai Allah ya k'ara bud'awa"
Suka amsa da ameen...

"Yawwa KHUBRA abunda nake so dake gobe idan Allah ya kaimu zan siyo miki banki na k'asa da zan na sa miki kud'in a ciki kema"

Bata iya,magana ba sai murmushi da tayi,ita kam tana son matar ganin yadda ta d'auketa kamar ita ta haifeta,tana son matar saboda bata da hayaniya kamar sauran mutane........


《《》》


Tun da sanyin safiya ya gama shirinsa cikin k'ananan kaya,fuskansa yayi wani fresh sai dai rashin fara'a kamar kowane lokaci ya fito,har ya kai bakin k'ofa akayi magana da yasa shi juyawa

"YAYANAH barka da safiya"
Fuskanta da fara'a take maganar a hankali ya d'anyi murmushi ta gefe a hankali cikin nutsuwa ya amsa mata...

"YAYANAH fita za kayi da safen nan?"
Da kai ya amsa mata yana juyawa yaci gaba da tafiya
"Ammmm!BB da ka bari kaci wani abun kafin ka fita,na kammala dama yanzun nake shirin zuwa na kiraka muyi break"

Tsayawa yayi a inda yake,kome ya tuna kuma ya dawo,d'an murmushi sukayi suka nufi dinning tare...
"Woww!delicious CWEETY yaushe kika iya girki ne kam,nasan baku iya komai ba,ko dai wani yayi ba keba?"

"Laaaa!BB Allah ni kam na iya babu wanda ya taimakamin da kaina nayi...
Tun kafin kaci har ka fara santii"

"A'a fa CWEETY ni kam babu wani santii da nake,kawai dai na fad'a ne"

"Uhmm!to ai shi kenan idan ka ci sai kunnenka ya fice kan dad'i"

"Aaaa!ai kuwa na fasa kada ina ci kunnena ya fice kiyiwa mai ni asara,maza kici abunki ke d'aya"

Dariya sosai sukayi kamar ba sune suke cikin damuwa ba,sun maida damuwansu nasu su kad'ai yayinda akan fuskokinsu babu wani abu da ya wuce annuri duk dan kada kowa ya gane halin da suke ciki...

Da kyar ta dawo dashi saboda mik'ewa yayi zai tafi,dariya suka sa dukansu,haka suke break da annashuwa..

"Amm!BB kace wani abu d'azun d'an dad'a maimaitawa naji"

Kallonta yayi yana murmushi "Me na fad'a da kika manta"

"Ba kace baza kaciba ko dan kada ko ayiwa wa asara?"

Dariya sosai yayi saboda ya tuna me take nufin ya fad'a
"Nak'i wayon na fad'a miki kiji ki dinga fad'awa saura......."

"Laaaaaa!wallahi BB a'a nawa nakema da zan fara kula samari"

"Yawwa CWEETY gara ki tsaya kiyi karatunki dama na fad'i hakane dan na tsokaneki"

"To YAYANAH d'an fad'amin kaji"
Ta marairaice fuska kamar za tayi kuka...

Mik'ewa yayi ya soma tafiya,tana kallonsa har ya kai bakin k'ofan fita daga parlor sannan ya juyo yana murmushi
"Mai ni nace"
Yana fad'a ya fice da sauri har da dariya,nan ko ZUHRA ta zauna tana ta kwasar dariya,sai da tayi iya yinta sannan ta tsaigaita
"BB nah kenan wai mai shi"

Tana ta faman dariya ta ji maganar ASHNA "Ke kuma lafiyarki kike faman dariya kamar wata tab'ab'b'iya"

"Ke dallah dakata,kuma daga yau duk ranar da kika sake cemin tab'ab'b'iya wallahi saina nuna miki tab'in hankali,banza kawai"

"Dan uwarki dawa kike?"
ASHNA ta tambaya tana nufo inda ZUHRA take

"Dake nake sai me?"

Kamata ASHNA tayi da kokawa nan ko ZUHRA ta shammaceta ta timata da k'asa ta shiga jibgarta baji bare gani,sai da taji dukan ya isheta gashi ta kasa ture ZUHRA daga kantane yasa ta fasa ihu wanda ya janyo hankalin MAMA da sauri ta fito tana fad'in
"Me ya faru ne ASHNA kike mana ihu cikin gida da wannan safiyar?".......
Maganar ce ta mak'ale ganin ZUHRA a kan ASHNA tana jibga

"Ke baki da hankali kike mata irin wannan dukan?bazaki d'aga taba sai na zo kanki?"
Har ta k'araso gurin ZUHRA bata san me take cewa ba,fizgota tayi ta kifa mata mari wanda yasata sakin k'ara wadda tafi ta ASHNA....

Cikin sauri ya fad'o parlorn kamar an harbo shi yana raba eyes,ganin ZUHRA na kuka ya nufi inda take
"Me ya sameki CWEETY?waye ya tab'aki?"

"Ba MAMA bace ta mare ni akan waccan dak'ik'iyar"
Wani mugun kallo ya jefesu da shi,kafin ya kama hannunta
"Yi shiru kinji maza je d'auko vail enki mu tafi"
Da gudunta ta bar parlorn,cikin sakanni ta dawo ya rik'e hannunta suka fice,MAMA da yar lelenta suka rakasu da harara....


A mota BB yake tambayan ZUHRA me ya had'asu da ASHNA,nan ta kwashe komai ta sanar masa dariya yayi yana fad'in
"Kinyimin dai² amma abunda ke so dake duk abunda za tayi miki ki daina biye mata kinji ko"

"To BB in sha Allah hakan bazai sake faruwaba"

"Yawwa CWEETY"

Motan shiru suka d'auki hanya.......

《《》》

"Aikin banza aikin wofi tarho d'inma tsabar tsiya irin ta y'an garin nan an rasa wanda zai taimaka ya kiramin MA'U naji halin da ake ciki..
Gashi ta barni da bashi fal kaina,gashi har yau ta gagara zuwa garin nan,kuma babu wani aike da tayimin,ba danma boka na saman dutse yana taimakona ba da yanzun mutanen dake bina bashi duk an mantar da su ba da sun zo sunmin rashin mutunci"
Ita kad'ai sai surutai take kamar wacce k'wak'walwarta ta kwance

"Amma babu komai,ai duk inda take dole wata rana zata kawo kanta zata ci gidansu a hannuna,ita da cin moriya wato ni kuma da wahala"

Sai k'wafa take saki ita kad'ai talauci duk ya isheta,MALAM en kuma da take ta faman bankawa asiri babu wata mafuta da ta samu daga gurinsa,abunda take so babu dan kuwa bai samu ba dan kuwa so take ta dinga juyashi amma yak'i juyuwa,nasara d'aya da tayi kansa an rabashi da y'arsa abar k'aunarsa,ya manta da ita wanda yanzun ko maganarta bayayi....

Wannan kenan.......

《《》》

A gidan su KHALEEL kuwa tun da KHALEED yace masa ga shinan ya fito,daga yanzun zai taho yake ta faman jiran ganin zuwansa amma shiru,hakan ne yasa shi kiran line ensa...

"MAN ina ka tsaya ne kam,kasa sai jiranka nake tun d'azun kace kana hanya fa"

"Idan ka gama min fad'an sai ka ajiye waya muna bakin gate fito mu wuce"
Daga haka ya ajiye wayan ba tare da ya kashe ba,saima hand's free da yasa ta...

"Amma kai kam koi bak'in mugu maimakon ka kashe shi ne zaka sani a hand's free?"

Dariya yayi mai sauti,KHALEEL na jin haka yayi saurin kashewa dan ya san KHALEED ba kashewa zaiba...
Yana fitowa ya tarar dasu cikin motor en...

"Aaaaaa!kace tare kuke da Momcynah"

Sukayi murmushi dukkansu kafin suka shiga gaisawa..

"Ammm!nace ba"

KHALEED ya kalleshi yayin da ita kuma ZUHRA ta sunkuyar da kanta k'asa tana murza hannunta...

"Mu shiga ku gaisa da UMMI sai mu bar ZUHRA a nan muje mu dawo"

"Noo! kada ka damu tare zamu je da ita,idan mun dawo sai mu shiga,ai ina jin nan zamu yini yau"

"Wow! kace UMMI tana da manyan bak'i"

"Ka jika da wata magana mune bak'in?"

"Noo! sub'ucewa bakina yayi ya fad'i haka" sukayi dariya gaba d'aya su uku...

Seat en baya ZUHRA ta koma daga nan motansu ta cilla kan titi sai police station..........





*_~TEAM KHUBRA.~_*




*_REAL SMASHER._*
💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹





*©®2018*
*22/ʝųŋɛ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

🍰🍩🍯
🎂🎂🎂🎂🎂
🌹🌹🌹🌹
*~HAPPY HAPPY BIRTHDAY.. ~*

_May it be the best day of your life thus far, & may your happiness grow with each passing day through the many many birthdays that surely are ahead of you._

*~HAPPY BIRTHDAY TO YOU MY SISTER'S~*
_NI'IMATULLAH M.U (AUNTY G) & RAHMATULLAH M.U (AUNTY U) wishing u many more blessing year's........Happy fruitful year's dearies._

🎂🎂🎂
🎁🎁
_Here is my gift.._ 😋📦
*~________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*3⃣1⃣*





*A* office en D.P.O aka sauke su,da yake ya d'an shiga ciki yana zagayen duba masu laifi..
Suna nan zaune kusan 30 minutes sannan ya shigo,ganinsu da yayi yasa shi sakin fuskarsa,yana mai mik'a musu hannu,sunkuyar da kawuna sukayi k'asa alaman girmamawa kafin suka bashi hannu..

Bayan sun gama gaishe² ya kallesu su duka coz bai san abunda ke tafe da suba a wannan safiyar
"Ammm!me ke tafe daku?duk da dai nasan zuwan naku ba zai wuce kan yarinyar da kuka bada report na b'atanta ba"

"Yallab'ai ba b'ata tayiba saceta akayi"
ZUHRA tayi katsalandan d'in yin magana
'Dan murmushi yayi,kafin yayi magana BB ya rigashi duk da yayi maganar ne k'asa² ta yadda ita kad'ai taji me yace
"Tambayanki akayi da zaki yi magana?"

Bata kalleshiba ta d'an sunkuyar da kanta k'asa

"Ehhh!tabbas kina da gaskiya ba b'ata tayiba saceta akayi,shin kina da masaniyar yadda al'amarin ya faru ne,kuma mene ne alak'arki da ita wacce aka sace en?"

Sai da ta kalli BB tukun,ganin ya d'aga mata kai alaman tayi magana yasa tace
"Ehh!yallab'ai tabbas ni witness ce akan wannan case en,kuma ni Y'ar uwace ga wacce aka sace ta jini"
Kaf abunda ta sani na yadda al'amarin ya faru ta sanar da shi,sai dai abunda ta rage cikin labarin bata sanar da shi mahaifiyarsu ce tasa aka aiwatar da abunba,tana gama jawabi tayi shiru ba tare da ta sake cewa komai ba..

Dogon ajiyar zuciya ya sauke kafin ya fara magana
"Shin ko akwai wani abu da zaki iya ganewa game da mutanen da suka aikata wannan d'anyen aiki? misali:kamannin wani ciki,suturan da suka sa da kuma mota ko number motan?
Shin zaki iya gane wannan ko makamancin haka?tunda kinyi bayanin kuna tare lokacin da al'amarin ya faru"

Kanta ta d'an d'age alamar tunani
Fitowarsu daga gida zuwa aiken MAMA da yadda akayi al'amarin ya faru take tunawa,da sauri kuma ta d'ago
"Yallab'ai bazan iya gane kamanninsu da number mota ba,amma motansu k'irar CRV ne bak'i sannan kuma kayan jikinsu duk bak'ak'e ne,sun rufe fuskokinsu da bak'in handkey idanunsu saye cikin black glasses,wannan shi ne kad'ai abunda zan iya tunawa game da su"...

Shiru cikin office en yayi na d'an wani lokaci,baka jin komai sai kukan AC dake aiki...

"Ammmm!gaskiya wannan case en yana da matuk'ar d'aure kai,da kamar ace mun samu photon ita yarinyar da aka sace sannan kuma an gane fuskar ko da mutum d'aya ne cikin masu laifin da sauk'i,ina tunanin aikin da sai yafi zuwa mana da sauk'i,amma duk da haka abun bai b'aciba...
Yanzun akwai wani taimako da kuke buk'ata?"
Yayi tambayar yana kallonsu duka...

A hankali KHALEED ya d'an tab'a KHALEEL
"Uhmmm!kai baza ka iya magana bane?"
KHALEEL ya tambaya yana murmushin mugunta...

Harara BB ya sakar masa sannan yayi gyaran murya,hankalin D.P.O na kansa jin yayi gyaran murya yasan akwai magana a gurinsa
"Ehhheemm!yi maganarka muna sauraronka"

"Yallab'ai dama kan maganar photo ne idan muka samo zaku iya nemota kenan?"

"In sha Allah muna fatan samota duk inda take,saboda zamu baza photonta ne cikin garin nan,idan ma bata cikin garin nan zamu bada cigiya a kafafen sadarwa da yardar Allah zamu sameta"

"To Allah ya taimaka yallab'ai,amma akwai wata alfarma da nake nema idan babu damuwa"

"Fad'i maganar da kake son yi ina saurarenka"

"Dama Yallab'ai ina son ka taimaka mana da y'an sanda da za suyi mana bincike ne su kuma lura da al'amuran wasu mutane,saboda akwai zargi akan su ina tunanin da hannunsu cikin wannan d'anyen aikin"

"To! babu damuwa in sha Allah duka ai ba zai gagara ba,za ka bada address na inda suke idan yaso komai ake ciki zasu dinga sanar da kai"

Basu suka bar police station enba sai da suka tabbatar sun samu mafita akan yadda zasu b'illowa al'amarin....
Suka yi masa sallama...
Ta hanyan kasuwa yabi dasu,da mamaki KHALEEL yake binsa da kallo,sai dai bai kai ga tambayarsa ba yaga ya fice...

Cikin kasuwan ya shiga da tambaya ya samu store en,tun da akayi maganan photo zuciyarsa ke ayyana masa abubuwa da dama,shi ya sama yanzun ba tare da yayi shawara da kowa ba ya shiga siyan kayan zane abun mamaki kamar wani Artist haka ya siya kayan,yaran store en suka bishi da kaya fal hannunsu...

Cikin ZUHRA ko KHALEEL babu wanda yasan me yake shiryawa kamar yadda babu wanda yaga kayan da ya siyo aka zuba masa su a booth...

Ya sallamesu suka kama hanyan komawa store,shi kuma ya shiga motor en yayi mata key zuwa gidan su KHALEEL...


《《》》

Tun safe kowa cikin su biyu BABA ZUWAIRA da kuma KHUBRA suka kama hanyar sana'arsu...

'Bangaren KHUBRA babu wani damuwa da yake a ranta wanda har zai dinga damunta a wannan lokaci,burinta bai wuce ganin ta kafa kanta a rayuwa ba,shi yasa ta jajirce dan ganin rayuwarta ta inganta..

Can k'asan ramin ta gangara,gurin babu mutane sosai sai y'an tsirari da suke d'iban ruwa suma,har ta gama tana shirin barin gurin wata matashiya ta matso kusa da ita fuskanrta a sake,da sallama a bakinta dai² lokacin KHUBRA tana niyyar haurawa sama
"Sannu baiwar Allah"

"Yawwa sannu"
KHUBRA tana kallonta da mamaki ganin babu wanda ta sani a garin..

"Suna na HAFSAT ina zaune cikin garin ZAKIRAI,babana shi ne SARKIN KASUWA"

"Allah sarki na gode"
KHUBRA ta fad'a tana d'an murmushi..

"Kefa baki fad'amin naki sunan ba"

"Suna na KHUBRA"

"Amma ke bak'uwa ce a garin nan ko?naga ban san fuskarki ba"

"Ehhh!haka ne,ban jima da zuwa garin nanba"

"Allah sarki na gode sosai,sai mun sake had'uwa"

Kowacce ta kama hanyanta,da yake ita KHUBRA ta riga ta gama abunda ya kawota gurin,ita kuma HAFSAT zuwanta kenan shi yasa tafiyan nasu ya bambanta......

《《》》

"Oyoyo TAKWARA yau kam ina da manyan bak'i,yaushe rabona da ganin k'afarki a gidan nan,gaishe nima da kuke zuwa kun daina yanzu, ince ko HAJIYA MURJA ta hanaku zuwa??"

"Wallahi UMMI abunda na fad'a kenan lokacin da KHALEED ya sanarmin wai nan zasu yini"

Harara BB ya sakar masa ba tare da yayi magana ba...

"Ai kuwa dai gaskiya KHALEED ya fad'a,kai dan gidanku idan kaje a matsayin wa kake zuwa??"

"Aaaaa!UMMI nifa na fishi zuwa kinga

Please Login or Register in order to submit comment