Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wakana.

Suna zaune cikin parlour a k'asa kan rug,daga ita sai singlet mai d'an fad'i na shan iska kasancewar yadda cikin ya maidata gaba d'aya ta k'ara bud'ewa,k'afafunta a mik'e duk sun kumbura sosai babu mai kallonta yace cikin watansa takwas saboda mugun girman da yayi,shi kuma MR KHALEED sai aikin matsa mata su yake,jingina bayanta tayi jikin cuistion hannunta dafe da plate na fruit da aka yanka tana ci da fork,wani ta soko jikin fork en tana dariya tayi saitin bakinsa da shi,sai data bari ya bud'e bakinsa saita janye hannunta ta nufi bakinta da abunta tana masa dariya,kai ya kad'a mata alamar zai rama yana maida face nasa alamun yayi fushi.
"Sorry JAAN....!"
Ta fad'a tana kallonsa,d'auke kansa yayi yana ci gaba da b'ata fuska,wani ta d'auko tana sake kawowa dai² bakinsa,kamar bazai bud'e ba kuma sai ya bud'e,sake janyewa tayi tana masa dariya.
"Kingafa kina d'aukan hak'k'ina JODI idan ba bani za kiyiba kibar abinki nima idan na tashi babu abunda zaisa na sammiki nawa.."

"Haba mana JAAN kasan fa ni taka ce,kuma dai nasan zaka sammin ko...?"
Tayi maganar cike da shagwab'a tana kashe masa ido d'aya
"Haba yarinya babu wani wayo da zakimin kijima na fad'a miki.."

"Haba mana...nicefa...."

Still fuskarsa tana yadda take,yana kuma ci gaba da matsa mata k'afafuntan,janye k'afar tayi ta matsa kusa dashi kallonta kawai ya tsaya yi ganin ta janye k'afan nata kuma ta matso kusa da shi,kan cinyansa ta hau tana zagaye wuyansa da hannunta d'aya,while d'ayan kuma still da fork a cikinsa,grapes ta chaka ta kaishi bakinta,sai data gama melting ensa sannan ta kalli cikin eyeballs ensa tana kuma nufan bakinsa da nata,tun kafin ta k'arasa ya fahimci nufinta,wani murmushi ya sake mata yana dad'a rik'eta sosai a jikinsa,nasa ya bud'e ita kuma ta shiga zuba masa ruwan narkakken grapes en,licking mouth nata ya shiga yi,daga haka wasa ya canja salo,nan suka lula cikin wata duniyar ta daban,sun manta da duniyar da suke da kuma duk wani abu dake zagaye da su,basa iya tuna kowa da komai sai junansu,burinsu a ko da yaushe su faranta ran junansu.
Bayan komai ya wuce sunyi wanka yana shiryata,wayansa tayi k'ara,saurin maida rigan yayi kan bed ya nufi inda phone en ke yashe,MAMA ya gani tana kiran da sauri ko ya d'auka yana karata a kunnensa cikin sallama,amsa masa tayi sannan ta furta
"SON kana jina ko.....?"

"Ehh! MAMA wani abu ya faru ne..?"

"A'a SON ina so ne dai duk abunda kake yanzun ka kawomin BABY gida akwai wani abu dake shirin faruwa..."
'Dan kallo inda take yayi yaga shi take kallo,d'an murmushi yayi mata yana ajiye wayan kan mirror,inda take ya nufa yana zuwa yad'auka rigan ya sa mata,sannan ya nufi cikin closet ya d'auko mata Arabian gown wanda yake da d'an sakewa bazai kuma takurata ba,da mamaki take kallonsa coz ta jima bata fita ba
"JAAN ina zamu kuma naga kana shirin samin kaya bayan kasan banson zafi...?"

"No JODI zamu gida ne,ban san mene yake shirin faruwa ba,MAMA tace muje yanzun.."
Kai kawai ta girgiza masa alamun ta gane,yana gama shiryata shima ya shirya,d'aukanta yayi ya nufi hanyan fita da ita,hannayenta zagaye da wuyansa har ya sanyata a mota,k'ofar ya bari a bud'e sannan ya koma ya kulle gidan,cikin lokaci k'ankani suka iso,shigowa yayi parlour yana d'auke da ita,nan suka tarar da gaba d'aya mutanen gidan a babban palour,sauketa yayi suna bin cikin parlour en da kallo ganin yadda suma ake binsu da kallo,hannunta ya rik'e suka k'arasa ciki suka zauna,sannan suka gaida iyayen nasu dake zaune,suka kuma gaisa da sauran y'an uwan nasu,suka kuma shiga sahun jiran jin me ke faruwa akayi irin wannan taron.
SADEEQ BIGGY aka sa ya bud'e taron da Addu'a sannan ABBA ya fara magana yana kallon KHUBRA dake zaune ta mik'e k'afafunta
"Al-hamdulillah da Allah ya nuna mana rana da kowannenmu yake cike da farin ciki da kwanciyar hankali,muna k'ara godiya ga Allah daya had'a kawunanmu muke zaune da junanmu lafiya ba tare da wata fitina ta b'illo mana ba,sai dai a yau ina son ku bani aron hankalinku domin a kwai wani al'amari daya ke faruwa wanda cikinku babu wanda ya sani sai mu da muke zaune lokacin da abun ya faru haka kuma kuma wasunku sun sani sai dai da jimawa,amma idan kun saurari bayanin da za ayi yanzun zaku ita tunawa...
Da farko dai ke KHUBRA shin zaki iya shaida wad'annan mutanen dake zaune gefe...?"
ABBA ta kalla da yake mata nuni da gefe da hannunsa,hannun tabi da kallo zuwa inda yake mata nuni nan ko idanunta sukayi arba da wasu yank'wanannun tsofi mata su biyu d'aya jikinta duk wasu irin k'uraje sun feso mata a jiki saboda uwar daud'a data lillub'esu,kallon rashin sani tayi musu sannan ta kalli ABBA da sauran mutanen cikin parlour'n ta ce
"A'a ABBA ban shaida suba."
Matan dake zune gefe sai kuka suke kamar wani nasu ya rasu suka kalleta suna sake b'arkewa da kuka mai cin zuciya kowa su yake kallo,da k'yar suka kalleta d'aya tana fad'in
"KHUBRA yanzun baki shaidamu ba? tabbas babu makawa mu mun san masu laifi ne a gareki kuma dama babu yadda za ayi ki shaida mu,idan har baki gafarta mana ba to tabbas baza mu tab'a gamuwa da rahama ba cikin rayuwar da zamuyi dama wadda mukayi a baya saboda munyi rayuwa ne cikin k'unci.."
K'uresu tayi da ido duk dan ta gane su,amma hakan ya gagara ta kasa bambance kamanninsu.

"Ni ce fa MA'U KHUBRA...Dana kawo ki aikatau,wanda tun bayan wanni biyar dana kawoki ban sake waiwayoki b..."
Ido KHUBRA ta zare tana kallonta da mamaki shimfid'e kan fuskarta na yadda ta kasa game kammaninta,ko tantama babu d'ayar kam LADIYO ce dan kamarsu d'aya su biyun fun can da.
Daga nan MA'U ta kwashe komai daya faru tun bayan data bar gidan,yadda tayi mata asiri kuma cikin hukuncin Allah kasancewar bata da hak'k'i Allah ya kareta,sannan ta d'ora da yadda asirin yayi tasiri akanta ita,maza suka dinga binta itama tana binsu kamar dai yadda igiyar ruwa ke kad'awa gefe zuwa gefe,kaf ta kwashe komai har ciwon da take d'auke da shi a halin yanzun,wanda tun bayyanar cutar a jikinta ta koma gidanta,kuma har lokacin bata bar halinta na biye-biyen maza ba,a haka ne wata rana suna tsaka da aikata masha'arsu a soron gidan nata kawai sai ga wata mak'ociyarsu nan ta shigo da niyyar tambayarta kasancewarta bak'uwa a unguwar,ganin da tayi musu mak'ale da juna yasa ta fasa k'ara dalili kenan daya sa mutanen unguwa taruwa kasancewar da yamma ne kuma ranar babu aiki,da yake an san ba aure gareta ba nan ko aka shiga jibgarsu babu ji bare gani ta k'arasa da fad'in
"Da kyar na samu na gudu,daga nan ban zame ko ina ba sai nayi tasha na tafi garin KASHIN DILA gurin YAYA,a lokacin dana je na sameta cikin mawuyacin hali wanda ko abincin da zata cima gagararta yake,babu gurin kwana babu suturar kirki har sai tayi bara take samun d'an abun da zata sawa cikinta,a k'ofar gida cikin rumfa na isketa gidan kuma a kulle,ko dana tambayeta sai take shaidamin cewa MALAM BUBA ya sake ta,kuma gidanma ya sallama shi ga mai gari tare da sauran kadarorin da iyayensa suka bar masa,yayi kuma sallama da mutanen garin da sunan bazai sake dawowaba.Sannan ta sanarmin da KHUBRA kin koma tare da wasu mutane da suka shaidawa MALAM BUBA a hannunsu kike kuma dai da alamun suna da alak'a tsakanin su da shi MALAM en Lamar yadda muka samu labari yanzun,to bayan nan kuma muka ci gaba da zama a garin wahalar da muke ciki tasa muka baro can muka dawo nan gidan dana zauna a nan kano,bayan mun dawo nan mun d'auki lokaci muna zuwa wannan unguwar muna neman gidan dana kawo ki aiki,sai dai Allah bai nufa zan gane gidanba sai yau da muka shigo muna neman taimakon abunda zamu ci saboda duk wata dukiya da nake da ita ta k'are yanzun,sai Allah yasa muka ga matar dana kawoki hannunta.Shi ne ta shaida mana kinyi aure tun shekaru biyu da aula wuce,min nemi son ganinki ne a gurinta shine race my jira zata kira mijinki ya kawo mata ke.
Kunji abunda ya faru tun daga rabuwarmu har kawo yanzun ...
Parlour'n kowa yayi shiru mamaki game da d'umbin al'ajabi na hali irin na wad'annan mutane da suke zaune duk ya d'aure musu kai,KHUBRA kam zuwa lokacin hawaye sun gama wanke mata fuska banda godiya ga Allah daya kareta ya kuma tsareta daga fad'awa tarko ba tare da an samu damar keta mata mutuncin taba take yi,mik'ewa BB yayi ya kamata suka bar gurin duk maganar da suke yi na ta yafe musu kan cutar da ita da suka yi,bai bari ta tsaya gurinba dan shima da kansa haushinsu yake ji,kuma yayi niyyar d'aukar mataki a kansu sai dai ya tuna wata magana da suka tab'ayi da yake ce mata sai ya d'auki mataki kansu,amsar data bashi a lokacin itace ta sake dawo masa,dalili kenan daya sashi janyeta a gurin coz yana son rarrashinta...
'Dakinsa na da ya shige da ita,d'akin ta kalla da hawaye har lokacin a cikin idonta,yana nan kamar yadda yake da,key ya murzawa k'ofan danma kada wani ya samu damar shigowa,janyota yayi ta shige cikin jikinsa,yana d'an jijjigata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take,bakin bed ya zauna ya d'orata akan cinyansa yana goge mata fuska,cikin kunnenta yake hura mata iska har sai da ta koma hayyacinta,mik'ar da ita ya sake yi tsaye tayi tunanin fita za suyi,da sauri ta rik'e shi tana sake sakin sabon kuka
"JAAN please kada ka mai dani gurinsu dan Allah baran iya zama guri d'aya da suba...kaji..?"

"Ok ok..! yi shiru babu inda zamu tunda baki so kinji ko..Zo nan na cire miki rigan kisha iska.."
Matsawa tayi jikinsa,sunkuyawa yayi a gabanta ya shiga bud'e mab'allan rigan jikinta,singlet ne a jikinta ta ciki sai nicker's,rungumeta yayi ya nufi saman bed da ita,kanta ya d'ora kan cinyansa ita kuma ta kwanta a gefenta na dama fuskarta na kallon fuskarsa,sai ajiyan zuciya take saukewa,gashinta ya shiga shafawa yana mata magan-ganu masu dad'i da kwantar da hankali,saboda kasancewarta mai d'auke da juna biyu daya tasamma tsufa ba'a son kasancewarta cikin b'acin rai,kafin wani lokaci sai gata ta ware har suna wasanni cike da nishad'i..

Can ko a parlour bayan barin su gurin MA'U da LADIYO sake b'arkewa suka yi da kuka ganin KHUBRA ta bar gurin ba tare da ta yafe musuba,kan irin cutarwar da suka mata,kuka suke suna k'arawa akan a kirata su nemi gafararta,shiru mutanen dake parlour en su kayi sai sauraren su suke sai da suka yi kukan son ransu wannan suka yi shiru, suna kuma dad's tonawa Kansu aspirin abubuwan da suka yita aikatawa Wanda aka sani dama Wanda ba a saniba,cike da tausyawa halin da suka jefa KHUBRA a ciki da mahaifiyarta data jima da rasuwa saboda girman kaidi da suka dinga shiryawa mutanen cikin parlour en ke kallonsu,da kyar UMMI ta bud'e baki tayi magana wanda yasa kowa ya maida kallonsa kanta,hatta kuwa da su masu koke-koken neman gafara,kiran KHUBRA da BB tasa ayi don kawo k'arshen komai,ko da d'an aike KHALEEL yaje ya tarar da k'ofa a kulle baiyi knocking ba ya dawo dan shima akan dole yaje saboda dai kawai bazai iya cewa UMMI a'a bane yasa yaje,sanar mata yayi da k'ofar a kulle take,sashi tayi ya koma yayi knocking ai ko kamar yadda ta umarta haka yayi,bud'ewa BB yayi sukayi ido hud'u da KHALEEL a nan ya coge ya kare k'ofar ba tare daya bawa KHALEEL damar gano cikin d'akinba ya furta
"Ya akayi ne...?"

"UMMI tana kiranku yanzun..."

Badon yaso ba ya koma ciki yana b'ata rai,shi kam babu yadda za ayima ya tasheta tana bacci,saboda haka ya fice had'e da kulle k'ofar,ganinsa shi kad'ai yasa suka kalle shi UMMI tana tambayan KHUBRA
"UMMI tayi bacci ne..."
Amsa daya bata kenan fuska a murtuke,aikuwa MA'U ta hau sheshshek'ar kuka,BB wani kallo ya jefeta dashi daya sata shiga nutsuwarta tana sunkuyar da kai k'asa,babu yadda basu yiba akan a tasota ta yafe musu,shi kuma ya kafe akan wallahi babu abunda zaisa ya tasheta,kawai suje an yafe musu saboda ubangiji yana son masu yafiya kuma itama zata yafe musu in sha Allah su tafi kawai,k'in tafiya suka yi ganin sun matsa kan sai sun nema yafiyarta su da ita kuwa yace musu idan suka takura to wallahi zai janye yafiyar da aka musu.
Babu b'ata lokaci suka fice suna kuka had'e da waiwayen gidan dan sun san shi kenan kuma suda sake ganin KHUBRA bare kuma MALAM BUBA daya koma AL-HAJI ABUBAKAR,wanda yake ji da dukiya a yanzun,ta inda cikin shekaru biyu da watanni ya bawa wasu miliyoyi baya.

*WAIWAYE....*

Tun bayan lokacin da MALAM BUBA ya kori LADIYO daga cikin gidansa,yayi sallama da mutanen garin,nan ya saida duka wata kadara daya mallaka ya tattaro kan dukiyarsa,wacce a k'arshe bayan dawowarsa ya damk'ata a hannun ALHAJI SAFWAN,inda shi kuma ya kawo shawara suka had'a kai su uku suka sake bud'e wani company da yanzun yake k'ark'ashin jagorancin KHALEED da KHALEEL.
_Wannan kenan....._

Bayan tafiyarsu aka koma maida labarin yadda al'amura suka faru a baya,kowa sai jimami yake kan yadda abubuwan suka faru.Bayan komai ya lafa su ABBA suka koma bakin aikinsu a d'ayan company ensu.
Su kuma sauran yaran aka barsu nan suna ci gaba da hiran haihuwan KHUBRA nan da wani watan suna kuma ci gaba da tsara irin shagulgulan da zasu yi idan ta haihun............

*ONE MONTH LEAP...*

KHUBRA ce kwance saman gado na majinyata masu haihuwa sai juya kai take gefe wasu nurse's na turawa daga kusa da kanta kuma BB ne yana ta faman shafa mata kai yana jera mata sannu cike da tashin hankali,har aka shiga da ita labour room en,sannan aka kulle yana waje bakin d'akin sai safa da marwa yake.
Tun yana kallon mintuna da suke shud'ewa kuma yana kallon k'ofar d'akin da aka shiga da ita,har hour guda yayi ba tare da an fito da itaba,daga hour d'aya aka tafi da rabi,sannan biyu,uku,hud'u,ganin abun bana k'are bane kuma hankalinsa na kanta gaba d'aya nutsuwa tayi masa k'aura,burinsa bai wuce sanin halin da take cikiba.
Wata nurse ce ta lek'o,jin an bud'e k'ofar yasa shi nufar gurin da sauri.
"Kaine JAAN ko waye nema ohooo...?"
Bai bata amsaba ya janyeta gefe had'e da shigewa,kallo ta bishi da shi ganin ya shige babu magana,bakin gadon ya nufa ganin cikin awanni hud'u da shigowarsu babu wani abu daya canja,duk ta gama galabaita,hannunta ya rik'o cikin nasa,idanunsa lokaci guda ganin halin da take ciki har sun gama sauyawa zuwa jaa,su kuma nurse's en sai faman damunta suke kan tayi nishi amma ina babu k'arfin yin hakan a tare da ita,gaba d'ayama sun gama bashi haushi kan tsayawa da sukayi suna b'ata lokaci tun d'azun kuma har lokacin babu sauyin da aka samu tun da suka shigo da ita,hannun long sleeve ensa ya nad'e cikin b'acin rai yace su bashi guri tunda basu san aikin suba,cikin ya shiga d'an dannawa a hankali kamar dai yadda akema masu ciki idan zasu haihu,yana kuma fad'a mata kalmomin da zasu bata k'warin guiwa,matsawa ya sake yi dai² bakinta ya sanya nashi ganin yadda take kwance tana sauke numfashi da kyar,iska ya shiga hura mata hannunsa d'aya na kan cikin yana ci gaba da daddanawa a hankali.
Cikin y'an mintuna da shigowarsa ta samu d'an k'warin jiki,nishi mai k'arfi yayi escafe a tare da ita,wanda ya bawa kan jaririnta damar fara fitowa,da sauri nurse's en suka matso,da taimakon Allah sannan da nasu taimakon suka janyo jaririn,cikin y'an mintuna ta sake sabon yunk'urin wani nak'udan take wani sabon jaririn ya sake kunno kai,a tak'aice dai sai da aka zaro jarirai uku daga jikin KHUBRA.
Ko ta kan jariran bai biba,in da matarsa take ya nufa yana jera mata sannu da Santa mata albarka,itako sai maida numfashi take da kyar Dan da ganinta ko ba a fad'a ba kasan ta sha wahala,duk jikinta yayi sweat en wahala,mouth to mouth ya shiga sake mata ko dan ta samu daidaituwar numfashi.............





*COMMENT FOR MORE PAGE'S.......* 💃💃💃💃💃




*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*






*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹



*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com

*©®2018*
*10/ɑմցմՏԵ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





6⃣4⃣



*SECOND TO THE LAST.*



*BIGGY* kuwa tun bayan daya samu aiki a revenue office,wato ofision tattara haraji,ya daina wani aiki da yake a baya,wanda ba k'aramin mamakinsa yaransa suka yiba na ganin chanji lokaci d'aya a tare da shi,da farko sun ci gaba da zama cikin gidan nasa sai dai kuma daga baya lokacin da zai yi aure kuma har lokacin akwai wasu halayya nasu da basu dainaba,dalili kenan daya sashi yanke shawaran rabuwa da su dan kada wata rana su janyo masa bala'in daya fi k'arfinsa.
Wata rana bayan ya zaunar dasu a parlour nan ya shiga yi musu nasiha yana janyo musu ayoyi da hadisai cikin abunda Allah ya sanar da shi na daga ilimi,jin ruwan ayoyin daya ke janyowa wanda suke tsoratarwa zuwa ga masu aikata halaye irin nasu dama wasunsu da kuma narkon azaba da aka tanada ga mai aikin yasa su kuka,basu tashi a gurinba sai da sukayi masa alk'awarin in sha Allah suma sun daina,yayi farin ciki sosai da hakan ya faru,nan yake shaida musu zaiyi aure nan bada jimawaba suka masa fatan sanyawar alkhairi,tun daga nan ya sallamesu da kud'ad'en da yasan idan har sun rabu cikin su babu wanda zuciyarsa zata kawo masa d'aukan abun wani ko kuma su koma irin waccan rayuwar.Tun da suka yi sallama da shi a lokacin ya musu fatan alkhairi shi kenan basu sake had'uwa ba,shima bayan sun bar gidan ya shiga parking kayansa,dillallai ya samu sukayi cinikin gidan da kayan gidan gaba d'aya,take ko ya sai da shi da komai daga shi sai kayan jikinsa ya fito daga gidan,ko bayan ya bar gidan ya d'an kwana biyu a hotel sannan daga baya ya samu wasu dillallan suka samo masa gida a wani unguwan daban,nan BIGGY ya koma da rayuwarsa,wanda kuma nan ne aka kai masa amaryarsa wato ASHNA wacce a yanzun take MAMA ga d'ansu MUHAMMAD AL'MUSTAPHA....

《《》》

*INA LABARIN BOKA...??*
BOKA kuwa tun bayan da LADIYO ta masa wannan gani a ranar da MALAM BUBA yayi musu mugun kamu bai sake dawowa gurinta ba dalilin da yasa kuwa hakan ta faru shi ne,a lokacin bayan ya bar gidan LADIYO daga nan wani gari ya wuce wanda a wannan garin akwai wani malami mahaddacin al-k'ur'ani,tun da Allah yasa wannan bawan Allah yayi aure da matarsa d'aya wacce take fitinanniya tun tana yarinya kamar su LADIYO,tun bayan aurensu data ga ba irin wanda za tayiwa duk abunda ranta ke so bane yasa ta shiga bin malamai y'an tsubbu da bokaye duk akan tana neman abunda zata malakke shi,sai daifa hak'anta yak'i cimma ruwa sakamakon shi wannan bawan Allah ako da yaushe zaka tarar da shi cikin alwala kuma yana tilawar al-k'ur'ani,a biye-biyenta ne suka had'u da BOKAN su LADIYO,wanda a ranar da MALAM BUBA ya gansu bayan ya bar nan bai zame ko ina ba sai gidan wannan malami daya fita sallar asubah kasancewarsa limamin garin nasu,kamar ko wane lokaci bayan an idar ya zauna tilawa nan a k'ofar gidan nasa yana cikin karatu,almajiransa da sauran datijjan garin masu sha'awar neman karatu suna zaune nan gaba gare shi a haka har gari yayi haske sosai..

Can ko a gidan MALAM lokacin matarsa na tsaka da bacci gari har yayi haske tana ta faman bacci bata saniba bare ta tashi ta gaida mahalicci,zuwan bokan shi ya tasheta wanda tana yin arba da shi tayi dariya kasancewar dama sun saba,haka suka shiga aikin gabansu kamar kowane lokaci.K'arfi,mu'ujiza da girman kalmomin da ake karantawa k'ofar gida suka fara tasiri cikin gidan malamin wanda suka yi sanadiyyar daya janyo jikin boka cikin lokaci k'ank'ani ya fara hayak'i,faruwar hakan ke da wuya matar malam ta daka tsalle had'e da ingije shi daga kanta ta fice a guje daga d'akin,a tsakar gida ta tsaya tana raba ido tunawa da irin hukuncin da za a mata a garin idan har aka san abun da ta aikata yasa ta fashewa da kuka dan kam muddin malam ya sani tofa lallai ne jefeta za ayi da ranta har sai ta daina motsi kuma mutane salihai ba za su mata jana'iza ba,wannan dalili yasa ta k'ara k'arfin kukan nata,babu b'ata lokaci ta jaa mayafinta ta fice da gudu a gidan saboda wani tunani da tayi na bar in garin tun kafin asirinta ya kaiga tonuwa,mutanen dake k'ofar gidan da suka ganta a haka suka bita da kallo ganin yadda take gudu iya k'arfinta,mamaki duk ya cika musu zuk'ata,tana cikin gudun ne kuma Allah ya kawo wani mai akori kura take ya banketa,dalili kenan da ko shurawa ba tayiba nan take rai yayi halinsa tace ga garinku nan sanadiyyar fashewa da kanta yayi wannan shi ya zama k'arshenta.

Shi ko boka a k'alla sai daya kwana biyu cikin d'aki ba asan ya mutu ba jikinsa har ya fara tsutsa,mugun warin da malam yaji shi yasa shi nufar d'akin sai dai warin ya wuce tunaninsa,da k'yar dai aka samu aka bud'e d'akin wanda aka fito da gawar boka dake kwance kan gadon matar malam,had'awa akayi da katifar gaba d'aya aka fito da ita,sai a lokacin mutane da dama suka fuskanci dalilin daya sa matar malam take gudu waccan ranar,tasan abunda ta aikata shi yasa ta nemi guduwa,to yanzun dai ga abunda Allah ya nufa dasu duka babu wanda yake raye...
_Wannan kenan,su boka an tafi ga kuma yanda Allah yayi k'arshensa ya kasance dama wasu daga magoya bayansa...Allah ya karemu daga mummunan k'arshe._

《《》》

*INA LABARIN TABAWA K'AWAR LADIYO...???*

Tun bayan da LADIYO tayita zuwa gidanta akan tana neman taimakonta lokacin da take son neman MA'U a waya,a wani yammaci bayan zuwanta gidan lokacin suna zaune tsakar gida sai ga mijin TABAWA nan ya shigo,kamar ko wane lokaci nan TABAWA ta bud'e ido da murya iya k'arfinta zata fara zuba masa rash in mutunci Lamar yadda ta saba,take bata ko k'arasa fad'in abunda tayi niyyaba ya d'auke mata fuska da mari ganin yadda

Please Login or Register in order to submit comment