Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Duk Wanda za ta tsayar idan taji bai mata yanda take soba sai dai yaja Babur ensa ya k'ara gaba.......
Son kud'i irin nata ya hana su tafiya.......

Sun jima tsaye ba tare da sun samu abun hawaba.....
Ita MA'U son kud'inta da ganin tsada ya hanata ta biya akaisu inda zasu.....
Haka sukaci gaba da jira,yamma na dad'a kunno kai......


'Bangaren KHUBRA kuwa wata azababbiyar yunwace tafi addabarta ga bakinta da ya bushe saboda tsabar k'ishi da ya dameta.....
Rashin sanin abunyi da kuma hali irin na MA'U yasa ta ja bakinta tayi shiru,sai raba ido da take akan hanya......


Ganin tsaiwa bazai kai musuba,da kyashin biyan kud'in motar yasa MA'U juyawa ta kalli KHUBRA,tana yatsina mummunar fuskarta......

Tunda nake a rayuwata ban ta'ba zuwa na b'ata lokaci a tsaye ba tare da samun abun hawaba sai yau da na d'auko MAI BAK'IN JINI......

Jin furucinta na k'arshe yasa jikin KHUBRA dad'a yin sanyi....
Ba tare da ta kalletaba,haka bata ce uffanba.......

''Yanda kikaimin bak'in ciki na rasa abun hawa haka wallahi saina fanshe kud'ina tare da ke MATSIYACIYA Y'AR MATSIYACI''.......
Maganan da ya fito daga bakin MA'U kenan wanda ba k'aramin sosawa KHUBRA rai yayi ba,take hawayen da bata son fitowansa ya b'alle,ita kam da ita ta zaga babu da zai sa ta damu,abunda yafi komai bak'anta mata rai zagin ABBANTA da MA'U tayi....

Ko ganin girmansa batayiba,bare d'aga masa k'afa a matsayinsa na miji ga yayarta.......
Wannan shi ne abunda ya jawo mata ZUBAR HAWAYE.....
Dad'a sunkui da kanta tayi k'asa,ta shiga goge face nata,dan ta tattabata idan MA'U ta san halin da take ciki tana mai iya jibgarta a gurin tamkar kayan wanki......


Sake tsaida wani tayi,babu ko ciniki ta afka tare da cewa ''idan kinga dama kya taho mu tafi.....

Jan k'afafunta tayi ta shiga,duk da haka bata tsiraba,k'arshema sai cikin booth d'in mashin en ta zauna,tun daga kasuwar ta y'an kaba har zuwa unguwan na rijiyar lemo......



**************


Sun is a unguwan ana sallan Maghreb,yana saukesu ta laluba cikin d'an topinta ta zaro masa kud'insa....

Kud'i sosai KHUBRA ta gani ta fito da shi,nan ta tabbatar matar tana da bak'in hali....
Tunani ta shiga yi,na irin rayuwar da zata fuskanta nan gaba,ko yaya zata kaya tsakaninta da MA'U?........








*_Ni ko nace ai KHUBRA bakiga komaiba......._*






*_~Kumin uzuri fan's in sha Allah next page zaizo ba kamar wannan ba..... ~_*






*_Masoya novel ena na RAYUWAR WANI kuyi hak'uri na jina shiru kwana biyu in sha Allah zanci gaba daga inda na tsaya,na gode sosai_*


*_~IYA WUYA MUNA TARE......~_*







*_~KEEP MOVING.....~_* 😍😍😍










*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠


*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*©®2018*

*21/mąrcɧ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_

🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._



*~__________________________~*

*ADDU'AH KAN ABOKIN GABA...*

_ALLAHUMMA ANTA ADHUDHIY,WA-ANTA NASIYRIY,BIKA AHULU,WA-BIKA ASUULU,WA-BIKA UK'ATILU......_


_ALLAHUMMA INNA NAJ'ALUKA FIY NUHURIHIM,WANA-UZHUBIKA MIN SHURIRIHEEM......_

*_~#HISNUL MUSLIM....~_*

*~__________________________~*


*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*



_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._

*~__________________________~*



*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*0⃣5⃣*




*B*inta kawai KHUBRA take a baya² har suka k'arasa k'ofar gidan.....
Mukulli ta zaro irin wanda ake kira da (KUBA) en nan ta shiga murd'awa a jikin k'ofan,da kyar ta samu ta bud'e saboda taurin da k'ofan yayi.....
Gidan bak'i k'irin da shi,ga uban daud'a da yayi,kai saika rantse bai tab'a ganin wani abu mai kama da tsintsiyaba.....
Kunna kai tayi ciki ba tare da ta damu da addu'ar shiga gida ba,duk dama dai bana tunanin ta iyata....

KHUBRA dake baya,ta tsaya k'ofar gidan kafin ta shigo....
Sai da tayi addu'ah ta sanya k'afanta cikin gidan,kasancewar mahaifinta yana koyar da ita ilimin FIQHU,AZKAR da sauran abunda ba a rasa ba na zamantakewar duniya......

Bata tarar da MA'U a tsakar gidanba,guri ta samu ta zauna gudun kada tayi laifi,coz ta san yanzun sai ta bi a hankali,tunda tasan halinsu ba k'aunarta sukeba......
Tayi nisa cikin tunani,kan mafarkinta...
Abunda take son fuskanta kan mafarkin ya gazawa tunaninta....

Tashi tayi tana k'ok'arin shiga band'aki danta samu ta rama sallolin da ke kanta,nan ta bar kayan ta shige.....
Ko uzurin da ya kaita bata k'arasaba ta tsinkayo muryan MA'U daga tsakar gida tana surfawa iyayenta zagi....
K'irjinta ta dafe had'e da zaro ido,dan ko ba a fad'a mataba tasan laifinta.....
Addu'ah ta hau yi a zuciyanta,tana me neman tsarin ubangiji tsakaninta da MA'U da kuma zaman da zasuyi nan gaba......

Fitowanta ta tarar da ita tsaye ta rik'e k'ugu kamar wata k'aramar yarinya sai girgiza take.....
Kallo d'aya ta mata ta d'auke idonta a kanta,ta sunkuya ta fara alwala......
''Don ubanki ni zaki mayar mahaukaciya ina magana ki juyamin baya,ko ubanki wannan matsiyacin bai isaba wllh''...
Maganar da ta biyo bayan hucin da take kenan kamar wata KUMURCIN MACIJI.......

K'in magana,duk da kalmomin da tayi amfani dasu sun shigeta,shiru tayi har sai da ta idar da alwalan,sannan ta juya tana bata hak'uri......

Wata uwar harara ta rakata da shi kafin ta figi kayanta tayi cikin d'aki.......

Gajiya da tayi da tsaiwa,ganin ank'i kulata bare ta samu a kirata,kan dole ta nufi hanyan d'akin bakinta na d'auke da addu'ah....
A kwance ta tarar da MA'U,nan ta tsaya tunanin koh wane hali mahaifinta yake ciki a yanzun......

Tsayawan mutum MA'U ta gani kanta cikin sauri ta bud'e idonta,tana zabga mata harara....

Kame² KHUBRA ta fara kafin da kyar ta iya furta
''Dama abun sallah nake so''...
Bata tanka mataba,haka bata tashi ba,saima dad'a rufe idonta da tayi,tana daga kwance kan gadon k'arfe irin na da ennan.....

Ganin tsaiwa bazai kai mataba,ta kabbara sallah daga inda take tsaye.....
Tana sallah tana dafe cikinta da yake ihun yunwa,a haka har ta samu ta idar ba tare da ta kai GA fad'uwaba.....

MA'U kam bacci ne ya kwasheta nan,ba tare da tunanin tashi ta gaida mahaliccinta ba.....

Har bacci ya fara d'aukanta ta tuna da k'ullin kayanta dake waje,cikin hanzari ta fita ta d'auko bata dawo d'akin ba saida ta tabbata ta kulle k'ofar gidan.....
'Dakin ta dawo ta hau bud'ewa,can k'asan kayan ta binciko wani k'ullin leda da ABBANTA ya bata tun jiya....
Bud'ewa ta hau yi,k'uli² ne mai d'an yawa irin wanda ake yinsa da sugar ennan.....
Ci ta fara,kamar wacce ta samu nama,haka ta far masa,sai da taci mai yawa,sannan ta hak'ura ta d'aure ta mayar cikin ledan......

Waje ta sake komawa cikin randa ta d'ebi ruwan da tasan zata iya shanyewa....
Godiya tayiwa Allah,sannan ta koma d'akin ta kwanta a k'asa dai² inda ta idar da sallah.....
Take kuwa bacci yayi gaba da ita......

************

Daf da kiran sallan assalatu ta farka,kasancewar ABBANTA kullum shi yake tashinta idan zashi masallaci sallah da asuba....
Fita tayi ta d'auro alwala,tsakar gidan da duhu sosai,haka ta daurewa zuciyarta tayi sauri ta dawo d'akin.......

Har ta idar da sallan MA'U ko juyin farko batayiba,haka itama KHUBRA batayi gangancin tashintaba.....
Gefe ta koma,ta had'a kai da gwiwa,tana tunanin duniya da makomar zuwanta wannan gari,tasan dai babu komai cikinsa face zallar wahala......

Ganin tunani ba kaimata zai ba,ta shiga karanta AZKAR na safiya,tana zaune har gari ya k'arasa wayewa......
Hijab dake jikinta ta cire ta fita tsakar gida......
Tsintsiya ta d'auka ta hau shara,kafin wani dogon lokaci har ta kammala,sai ga gidan yayi haske daga bak'ar daud'ar da yayi.....

Har tayi wanka MA'U bata san me yake faruwaba...
'Dakin ta dawo,da tunanin ta tasheta ko kuwa......
Tsayawa tayi tana nazarin ta inda zata fara,amma fargaba ya hanata tab'uka komai.....
Kan dole ta hak'ura,ta zubawa sarautar Allah ido......

*************

Sai misalin k'arfe 8:00am ta farka tana ta faman zabga hamma,had'e da mik'a....
Da kyar ta iya tashi tayi waje,ganin tsakar gidan a share tas,ta tab'e baki,ta rarumi buta tayi band'aki,ta jima aciki,tamkar wacce ta sami d'aki,zuwa can kuma ta fito,ta sake d'iban ruwa a bokiti ta koma....
K'arar ruwa kawai kake ji kamar wacce taje suuuu kogi,haka ta shek'ashi a jikinta ta fito,cikin abunda bai wuce minti 5 ba.......

Alwalan ma buji² akayi aka fad'a d'akin.....
Shigarta ta tarar da KHUBRA har ta gyara d'akin tsaf duk ta gyare tarkacen dake cikin d'akin.....

Babu ko sannu bare an gode,saima ladan gaben harara da yatsina da ta shiga yi......
Shiryawa tayi cikin gaggawa,tasa wata atamfa riga da zani,taja gazal a idonta......
Takalminta ta sharfad'a tayi waje ba tare da yin ko da sallan da akayi alwala domin taba......
Babu magana bare KHUBRA ta sa ran ganin abinci tayi waje,tana gaisheta ma ko ta kanta bata biba.....
Ta k'arawa k'afafuwanta mai.......


*_~ALLAH YA SHIRYA.......~_*




*_~KEEP MOVING....~_* 😍😍😍






*_REAL SMASHER🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠


*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*©®2018*

*22/mąrcɧ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_

🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._



*~__________________________~*
🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾
*APPY APPY BUFDAY*

_Hope your birthday blossoms into lots of dreams come true! May today be filled with laughter and love._

_Happy Birthday and many happy returns of the day._

🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂


*HAPPY BITHDAY 2 U!!*



H B Z
A U
Y A B
A A
T B I
R
A


*(YAYA HAYAT) ADMIN OF ADMINS.......*


_Wannan ranar taka ce,babban Admin mai kundin novels, *WRITER'S* naka *REDER'S* naka,kana k'ok'aree gurin nishad'antar da d'aukacin members enka dake cikin_
*COOL NOVELS GROUP'S 1,2,3,4 & 5, MAKEUP ND KITCHEN GROUP* _Allah ya k'ara 'daukaka,ya k'aro maka shekaru masu albarka,kana mai wadatuwa da imani,kwanciyar hankali........_

_Wannan page en naka ne kai d'aya kayi yadda kaso da shi....._ ✍🏻✍🏻


🍾🍾🎂 *HAPPY BUFDAY WULLNUP ADMIN...* 🎂🍾🍾

*~__________________________~*

*ADDU'AH YAYIN TASHI DAGA BACCI*

_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AHYANA BA'ADA MAA AMATANA WA-ILAIHIN-NUSHUUR..._


_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AFANIY FII JASADIY WARADDA ALAIYYA RUHIY WA-AZINALIY BIZIKHRIY....._


*_~#HISNUL MUSLIM...~_*


*~_________________________~*



*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*



_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._

*~__________________________~*



*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*0⃣6⃣*




*I*ta d'aya zaune tayi shiru,abun duniya duk ya taru ya mata yawa......

Tunanin gida da mahaifinta duk shi yafi damun zuciyanta,ko a wane yanayi yake? Allah shi ne masani......
Ganin babu sarki sai Allah,shi yasa ta bawa zuciyanta hak'uri......
'Daki ta sake komawa,bayan ta tura k'ofan gida,da yake ta san ita kad'ai ke gidan,gudun kuma kada wani abu ya faru......


***********

Tafiya take duk inda ta samu watsa k'afafuwanta take,tamkar wacce zata tashi sama.....
Son kud'i irin nata ya hanata neman abun hawa......

Sai da tsakiyan rana,ganin babu haza yasa ta hak'ura ta nemi keke napep,daga UNGUWAN KURNA zuwa RIJIYAR ZAKI,a ganinta nan ne unguwar masu kud'i,za tafi samun gidan aiki,idan bata samuba kuma,zuwa gobe sai ta nausa cikin gari......
Zafin rana da k'ishi su suka haddasa mata tsaiwa,ta nemi abun hawa,idan yaso sai ta k'arasa,in da ta nufa......
Ta tsayar da masu napep sama da guda goma,amma da sun tsaya suke k'arawa babur en nasu wuta suyi gaba.......
Da kyar ta samu abun hawa,kan neman ragi irin na MA'U......
Yinin ranar yawo ta dungayi gida² take bi a unguwan na rijiyar zaki,kan neman gidan da suke neman Y'AR AIKI.....

Sai da ta sha wahala,kafin ta samu gidan da suka nuna mata suna buk'ata......
Sun gama ciniki kan dubu biyar per month......

Duk iya yinta na su k'ara mata wani abu,hakan ya faskara....
Gudun kada tayi asara gashi wannan d'inma da kyar ta samu,bayan yini da tayi tana GARARIN DUNIYA yasa ta amince,akan zata kawota daga zaran sun gama shiryawa......
Abinci matar ta kawo mata da ruwa mai sanyi.......
Ta gama d'amke cikinta,sannan tayi mata sallama........
Godiya tayi ta tafi da alk'awarin nan da Sati d'aya zata dawo......


***********

Kwance take tana ta faman bacci wanda bata san lokacin da ya d'auketaba,tayi nisa cikin baccinta.......


**************

Tun daga nesa ta hango ingarman dokin wanda akewa lak'ani da KILI ( wato mai fari biyar),kansa mutum ne zaune,cikin farare tas en tufafi......
Matsowa yaci gaba da yi,wanda har sai da yazo daf da ita sannan ne ta iya gane mahayin murmushi d'auke kan fuskansa......
Sai da ya zo gabanta,sannan yaja linzamin dokin ya tsaya.....

Har lokacin tana tsaye fuskanta cike da mamakin ganinsa......
Mutumin daya ce bazai sake dawowaba yau shi ne a gabanta yau.......

Saukowa yayi cikin isa,ya tako har zuwa gabanta....
Cikin wani irin voice da bata tab'a jin irinsa ba tunda take a gaba d'aya tsawon rayuwanta,ta tsinkayo shi yana fad'in
_''Amincin Allah yaci gaba da tabbata agareki''........_

Kasa amsawa tayi saboda tsananin mamaki da yak'i barinta har yanzun......

Hannunta ya kama cikin wani irin salo,ya jata jikinsa.....
_''Haba wifey,ni en ne baki ganeba ko kuwa na zame miki wata sabuwar halitta?''......_

Kuka ne ya kufce mata,jikinta banda rawa babu abunda yake,tsabar tsoro ta kasa magana,sai hawaye dake ta ambaliya a fuskanta.....
Duk k'ok'arinsa da son ganin ta bud'e baki tayi magana abun ya gagara......
Janta yayi ya had'a jikinsu guri d'aya,ganin yanda jikinta yake ta faman b'ari......

Maimakon a samu sauk'i saima k'aruwa da aka samu.........
Kukantane ya sake tsananta,kan dole ya raba jikinta da nasa....
Fuskanta ya kama ya d'ago,tsura mata ido yayi

_''Shin bakiyi farin ciki da ganinaba ne wifey?''...._

Kai ta girgiza masa,alaman
A'a

_''Baby maganafa zakiyi,bana son wannan nodding en''......_
Cikin hanzari ta bud'e baki da niyyan magana
_''A'a,ina mamakin yanda ka dawo gareni ne,alokacin da bantab'a tsammaniba''........_

Fuskanta ya shiga goge mata,yana murmushin jin dad'i......



**********

k'afafuwanta tamkar wacce taje sharan gona,sunyi futu² kamar basu tab'a ganin mai ba.......

Sai murna take na samun gidan aikin da tayi,haka ta sauka a napep en da ya sauketa bakin titi.....
Ta sake ninkawa ta shiga cikin unguwan,a k'ofar gida taja burki,ganin k'ofan a rufe,ta shiga huci.....
Bugun k'ofa ta shiga yi,jin shiru ba a bud'eba,ta shiga dukanta da k'arfi tamkar zata karya.......


************

Cikin baccinta mai dad'i mai cike da mafarkin da a kullum shi ne birinta....
Ta tsinkayo bugun k'ofan da tamkar a tsakiyan kanta ake......
Bud'e idonta tayi,cikin sauri ta mik'e ta nufi k'ofa,har tana had'awa da d'an gudu,wanda saura kad'an ta fad'i,amma haka ta daure ta tunkari k'ofan..........





*_~Uhmmmm ko me KHUBRA zata tarar yau kam.......~_*




*_~KEEP MOVING...~_* 😍😍😍






*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠


*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*©®2018*

*23/mąrcɧ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_

🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._



*~__________________________~*


*ADDU'AR SANYA TUFAFI.*
_________________________

_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY KASANIY HAZAS-SAUBA,WARAZAK'ANIHI MIN GHAIRI HAULIN MINNIY WALA KUWATTA......._

*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*

*~__________________________~*


*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*



_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._

*~__________________________~*



*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*0⃣7⃣*




*K*okawa ta shiga yi da k'ofan,wanda da kyar ta samu ta bud'e......

K'ofan na gama bud'ewa idanuwanta sukayi arba da MA'U tsaye,idanunta sunyi jajur dasu kamar garwashi.....
Kamar ance ta kalli k'afarta,ai kuwa nan ta hangi k'afar tayi busu²,dan k'ura da daud'a......

Duk k'ok'arinta na ganin ta kaucewa yin dariya abun ya faskara....
Nan ta fara tuntsirar dariya,kamar kwancen mahaukata.......

MA'U dake tsaye tana jiran a bud'e mata k'ofa,taga ta tsaya tana mata dariya.....
Tsaiwa tayi ta dafe saman gini,tana kallonta,sai dariya take,kamar sabuwar kamu.......


Tsabar mugunta irinta KHUBRA har dafe gefen cikinta take,ita bata matsa daga kan hanya,ta bawa MA'U guri ta wuceba,ita kuma bata tsaida dariyan taba......


Kallonta MA'U taci gaba dayi,ganin abun nata ba na k'are bane,kuma ta rasa me KHUBRAN kewa wannan dariyan a tare da ita,abun ya soma bata haushi....

Ga haushin ta rufe mata k'ofa,sannan ta zo tana mata dariyar rainin wayo.......


Hankad'ata tayi cikin soron,ta shigo tare da maida k'ofa ta rufe.....
Wani gigitaccen mari MA'U ta aikawa KHUBRA da shi,wanda ta jishi,babu shiri kuwa ta had'iye dariyarta.......
Gashin kanta ta dank'a ta jata zuwa cikin gidan,sai zage² take kamar y'ar maguzawa......
Babu zato bare tsammani MA'U ta shiga jibgar KHUBRA kamar ta samu jaka ko ince kayan wanki.....

Tun tana dukanta KHUBRA na iya yin ihun neman ceto har ta koma muryanta ma bata iya fita saboda laushi da jikinta yayi.....

Sai da tayi mata dukan sa'a,sannan ta yasar da ita a gurin ta shige d'aki,ba tare da ta furta ko 'A' ba,zuciyarta kamar zata fito waje saboda haushi.....

KHUBRA dake yashe a k'asa babu,abunda ake iya ji na daga sautin muryanta,banda numfashinta dake fita da sauri²......
Ta jima kwance a gurin,wanda ta gagara koda motsin kirki......


***********

Tun tahowar MA'U da KHUBRA birni,hankalin ABBAN KHUBRA yak'i kwanciya.....
Kullum cikin tambayar LADIYO yake yaushe MA'U zata dawo da ita.....
Amsar dai guda d'aya ce kullum,dazaran lokacin da suka d'auka alk'awari yayi zata dawo da ita.....
Shi kam kullum yana jinta ne,don kuwa ya fuskanci idon MA'U bud'e yake da son nera,tsoron sa d'aya kada su cutar masa da ita.....

Abu sai dad'a gaba yake,LADIYO ta shiga tashin hankali ganin yadda malam en yake neman d'aga mata hankali,har bata so ya shigo ya tarar da ita zaune,yanzun zai dasa mata maganar y'ar tasa mai kama da aljanu.....


Yau ma zaune take cikin y'ar rumfar karan dake bakin d'akin nata,wanda daga nan kana iya hango k'ofar shigowa gidan.....

Zafi duk ya addabeta,daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta.....

Malam buba ya kawo kai zai shigo cikin gidan,da sallama a bakinsa....
Ko amsawa bata yiba ta mik'e cikin hanzari zata bar gurin.....

''Dakata LADIYO,na fuskanci kwanan nan nema kike ki mayar dani wani sha ka tafi''.....
''Ko dai yau ki fad'amin inda y'ata take ko kuma aradu ina mai kai k'ararki gurin MAI GARI''.......

Ido waje LADIYO ta juyo,nan ta shiga bashi hak'uri.....

Saboda LADIYO irin matan nan ne masu d'an karen tsoro,ammafa akwai tsokana....
Idan

Please Login or Register in order to submit comment