Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yau,bayan ta gama sawa a ranta zataje taga su MAMA...
Wani killer smile ya saki yana dad'a janta jikinsa,idanunta a rufe saboda bata son tayi kuka coz tasan halin abunta tunda yace idan tayi za a fasa tsaf zai fasa en tun ba yauba tasan halinsa a d'an zaman da tayi a gidansu.Tana jinsa yana laluben bakinta ta bud'e masa dan kam a wannan lokacin gardama ba nata bane,sannan tun farko tayiwa kanta alk'awari duk abunda zai faru bazata tab'a hana shi hak'k'in saba duk runtsi,saboda a kullum abunda take tsoro kada ta hana shi Allah yayi fushi da ita,baya ga tsinuwar mala'iku da zata yita sauka akanta.
_To k'alubalenku matan aure dama y'an mata masu niyyan yin aure,wasu suna d'aukan hakan a matsayin fansa idan miji ya musu laifi sai kuji ana cewa zamu had'u da shi a gado ne ai wallahi sai ya gane kuskurensa,shin y'ar uwa idan kika yi haka bakya tunanin faruwar wani abune kam? misali ya miki laifi yanzun shi kenan baki da wata hanya davzai gane ya miki laifi har sai kin had'a da bi ta wannan hanyar? to idan baki saniba ki bud'e kunnenki ko kad'an dan kinyi haka ba shi kika cutaba kanki kika cuta,kuma ki sani yin hakan tamkar kin d'auki wuk'ane kin dab'awa kanki,dan kuwa a lokacin da yake tsananin buk'atarki idan baki bashi kankiba to tabbas abunda ba a fata zai faru,imma dai ace daga wannan lokacin ya fara bin matan banza idan har da baya yi,imma kuma idan yana yi ya k'ara a kan na da,ya rage naki ki gyara ko karki gyara,amma kam tabbas idan kika yi haka k'arshe zaizo miki da sakamakon abunda kika jefaku ciki,sannan kuma ga tsinuwar mala'iku baya ga fushi da Allah zaiyi da ke,kafin kuma ki samu k'arin tsinuwar mutane ta soma yawo akanki,kinga saiki zab'a bashi hak'k'insa ko tsinuwar....Allah ya bamu ikon gyarawa._

Harshenta yake lalube ganin yana neman wahala ta mik'a masa nan yaci gaba da aikin dake gabansa,sai da suka gama jagwalgwala junansu sannan cike da farin ciki suka koma toilet,bayan sun gama shiryawa suka fito kai da ganinsu zaka gane wannan d'anyu ne a amarci,hannunsu sak'ale dana juna,ko a motanma yana driving hannunsa d'aya na cikin nata kamar wanda za a kwacewa ita,idan ya kalleta sai suma juna murmushi mai d'auke da sak'onni daban-daban haka har suka k'arasa mai house nasu.
Ko gama daidaita parking bai yiba ta shiga k'ok'arin fita,da sauri ya dad'a rik'o hannunta,wani kallo wa watso mata idanunsa a narke yake kallonta,kanta ta sunkuyar k'asa da sauri
"Saurin mene kike yi ne kam...Kina so mu koma ba tare da mun shigaba ko..?"

Kanta ta shiga girgizawa kamar za tayi masa kuka,dariya yayi k'asa-k'asa
"To idan kina so mu shiga ki bari mu tafi tare,bana son wannan gaggawa'n da kikeyi.."
Dakatawa tayi har ya gama abunda yakeyi sannan ya fita,shi ya bud'e mata k'ofan ta fito cikin tafiyan sa ba zai ce tayi sauriba,hannunta ya rik'e a haka suka cimma parlour'n gidan.
Sallamansu tasa MAMA da BABA ZUWAIRA fitowa daga kitchen suna fad'in
"Maraba da amarya...."
Hannunta ta fizge daga nasa tayi jikinsu da d'an gudu,rungumeta sukayi suna y'ar dariya game da tsokanarta tayi kyau kamar ba itaba.
Bayan an gama gaisawa BB,ya mik'e yana fad'in
"MAMA zanje wani guri na dawo,sai zuwa dare zamu koma in Allah ya kaimu..."
Fatan alkhairi tayi masa,k'asa-k-asa yake kallon KHUBRA data wani mak'ale jikin MAMA ita kuma sai biye mata take ita ga mai y'a,har ya kai k'ofar palour yajiyo BABA ZUWAIRA nawa KHUBRA fad'an ta tashi taje suyi sallama,fuska ta kumbura kafin ta tashi ta biyo shi,har bakin mota ta rakashi yana gaba tana binsa a baya,kamar abun arziki ya bud'e motan ya shiga,ita kuma tana tsaye dafe da k'ofar ya d'ago ya kalleta ganin fuskarta a cukune yasa ya furta
"Zo nan..."
Babu musu ta zagaya ta d'ayan side en ta zauna tana kallon waje
"Wato rakiyan ne bakya so shi ne kike wannan abun ko..?

"Nifa ba haka bane..."

"To yaya ne..?"

"Babu komaifa..."
Ta sake bashi amsa kuma har lokacin bata saki fuskar ba,juyo da ita yayi fuskarsu na kallon juna ta yanda suke iya jin numfashin junansu na sauka kan fuskokinsu
"JODI nine baza ki iya rakowa ba sai an ce ki rakani...?"
Kai ta girgiza idanunta a k'asa
"Me yasa to kika b'ata fuskanki dan ance ki rakoni...? ko dan bakya so ne shi yasa..?"
Nanma girgiza masa kai ta sakeyi
"To mene ne..?"
Shiru tayi shima shirun yayi ya jingina bayansa a jikin kujeran kallonta yaci gaba dayi,ba tare da ya mata maganaba,itama taci gaba da zama kanta a k'asa ta kasa magana.
Sun jima zaune babu wanda yayiwa wani magana,shi kuma BB zuba mata ido yayi yaga iya gudun ruwanta,gajiya yayi da shirun ya fara magana fuska babu wani wadataccen fara'a
"Wato baki san kinyi laifiba ko...?"

Idanunta ne sukayi rau-rau za tayi kuka,kansa ya d'auke daga kallon da yake mata cikin muryar kuka ta furta
"Kayi hak'uri YAYANAH dan Allah.."
Dai² lokacin hawayen suka sakko kan fuskarta,kasa jurewa yayi da sauri ya furta
"It's ok...!"
Yana janta jikinsa yana patting bayanta,ajiyan zuciya ta sauke tana dad'a kwanciya jikinsa,sai daya tabbatar ya sanyata dariya sannan ya mata sallama akan sai anjiman idan ya dawo zasu tafi,cike da farin ciki ta juya suna waving wa junansu.

Har dare tana gidan kowa sai nan-nan yake da ita musamman MAMA da FATAHIYYA,a nan su ABBA suka tarar da ita lokacin da suka dawo,sosai sunyi farin cikin ganinsu hankalinsu a kwance.
A wannan lokacin ba kowa ne zai kalli ABBA'N KHUBRA ya shaida shiba,ashe dama wahala da zaman k'auye sukasa ya fara tsofewa,cikin y'an watanni har ya soma yin shar da shi,da yake Allah yayi shi mai tsafta shi yasa cikin lokaci kad'an ya dad'a gogewa musamman kuma daya had'u dasu ABBA mutanen da suka yi gogayya da turawa,yadda suke tafiyar da harkokin kasuwancinsu yanzun idan ba wanda ya san suba ba zai tab'a tunanin ba jini d'aya bane su en,dan mutane da dama suna musu kallon y'an uwan juna.
Daf da zasu tafi KHUBRA ta matsa kusa da ABBA'NTA tana masa magana,cike da sha'awar ganin yadda y'ar tasa ta koma ya kalleta yana maida hankalinsa kanta dan ya fuskanci me zata fad'a,kamar abun arziki suka dad'a gaisawa yana tsokanarta,sai dariya take shi kuma hakan shi yasa shi yake sake jin dad'i sosai
"ABBA dama fa akwai maganar da nake ta son maka.."
Kallonta ya sake yi yana fad'in
"To y'ar albarka ina sauraronki"
Sai da tayi ajiyan zuciya sannan kuma kanta a k'asa tace
"ABBA dama ba kan komai bane sai wani al'amari da nake ganin idan hakan ya kasance kowa zaiyi farin ciki..."

Dad'a d'aure masa kai tayi saboda har lokacin bata fad'i abunda zata fad'a enba,muryarta ta katse shi daga sonyin magana
"ABBA damafa shawara ne nazo da shi,nace me zai hana ka yarda da BABA ZUWAIRA a matsayin mata,kaga itama dama bata da aure mijinta ya jima da rasuwa,kuma ABBA na baku labarin yadda ta rik'eni na tabbata bata da wata matsala...Kuma kaima yanzun ABBA baka da kowa sai ni kad'ai..."
Dakatar da ita yayi fuska a had'e yake fad'in
"Maganar dama da kika zo da ita kenan saboda futsara irintaku ta y'ay'an zamani har ni kikewa maganar nayi aure...?"
Yadda taga ya b'ata rai ya kuma zage yana ta mata fad'a yasa ta shiga bashi hak'uri,amma kam bata ji dad'iba daya k'i amincewa,haka sukayi sallama da mutanen gidan da suka rakosu har bakin mota kafin suyi musu sallama suka d'auki hanya.

Cikin motan shiru babu mai magana kanta a k'asa tana matse hawayen dake sauka kan fuskarta,maganar BB ya dakatar da kukan nata
"Me kika yiwa ABBA yayi miki fad'a....kin b'ata masa rai ko...?"

Sai da ta gama kukanta ba tare data kula shiba,shi kuma sai nasiha yake mata yana nusar sa ita hanyar da zatabi su zauna lafiya da ABBA,sai da ta bari sunje gida har sunyi wanka sun kwanta sannan ta bashi labarin abunda ya had'asu,ajiyar zuciya yayi kafin ya nuna mata illar abunda tayi,sai yanzun ta fahimci laifinta dan kam tabbas ba ita ya kamata tayi masa maganar ba.Tun daga lokacin ta k'udurce a ranta duk hanyan da zata bi sai ta bi na ganin hak'anta ya cimma ruwa kuma zata dage da addu'ah akan Allah ya tabbatar da alkhairinsa................
_Wannan kenan.._




*COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃





*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*







*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹



*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com

*©®2018*
*6/ɑմցմՏԵ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*
_cwєєt ѕíѕ *HALIMATUS-SADIYA MUHAMMAD (LEEMA)* ínα tαчαkí murnα dα fαrín cíkí nα gαmα wαnnαn nσvєl mαí cíkє dα d'umвín dαruѕѕα nα *IYA KU'DINKA* αllαh чα ѕα ѕαk'σnkí чα íѕα índα kíkє вuk'αtα αllαh чαѕα mutαnє ѕuчí αmfαní dα d'umвín вαѕírαrkí dα kíkα zuвє α cíkí dα ílímí dαkє cíkín lαвαrín..uвαngíjí чα k'αrα lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní._ *#1 ♥ cwєєt lєєmαtєєч.* 😍
*~___________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





6⃣0⃣





*K* imanin kwanaki biyu kenan da zuwansu gida,yauma yana zaune cikin parlour a lokacin KHUBRA na saman jikinsa kamar kowane lokaci da idan kaje zaka tarar dasu a hakan.Cike da so da kulawa ya kalleta yana fad'in
"JODI yanzun idan aka ce kizo a kaiki makaranta shin kina so ko kuwa...?"
Kallonsa tayi tana murmushi ba tare data ce komaiba,saima hannunta datake ci gaba da wasa da shi a jikinsa,ganin bata da niyyan magana yasa ya rik'e hannunta yana kuma kallon ta,a hankali ta d'aga kanta ta kalleshi tana murmushi
"Shi ne kina ji ina miki magana bara ki amsaba...? kin san dai bana son haka ko...?"
K'ure shi tayi da ido tana nazarin fuskarsa,ganin yanda yayi yasa ta d'an gyara kwanciyanta tana fad'in
"Ni kam YAYANAH wani karatu ne zanyi yanzun...? ina ganin bani da wannan daman dan kam lokacina ya riga da ya wuce,wanda nake da shima na addini ya isarmin,amma kam nayi girma da zuwa makaranta yanzun.."
Shiru yayi yana nazarin maganarta,lallaima yarinyar nan idan ba shirme irin nata ba,har wane girma ne za ace tayi yanzun da karatun,shi kam tabbas yana da burin ganinta tayi karatu,shirun da taji yayi babu magana yasa ta sake d'agowa tana fad'in
"YAYANAH waima me ya kawo wannan maganar ne kam yanzun...?"

Idanunsu sark'e cikin na juna yake fad'in
"Wato kefa a ganinki nan kinyi girma da zuwa makaranta ko...?"
Kai ta d'aga masa alamar eh,kuma har cikin zuciyarta take nufin hakan,d'an murmushi tayi kafin ta furta
"To waima YAYANAH kawai sai na wani tafi na zauna haka nan gemai-gemai dani nace naje koyan karatu ko me..?"
Da sauri ya katseta ta hanyar fad'in
"Haba hajiya bafa wani girman da kikayi da karatu kuma da kike wannan maganar ma SHEHU JAHA ma cewa yayi acikin labarinsa *"GEMU BAYA HANA ILIMI"* sannan kinga kuma yanzun baki san wane irin y'ay'a Allah zai azurtamu da suba,shin bakya sha'awar ace kin bada naki gudunmawar ta b'angaren ginuwar iliminsu...?"
Shiru ta sake yi tana nazarin maganarsa,ita kad'ai a zuciyarta take fad'in
"Gaskiya dai kuma da haka,ko ba komai zanyi alfahari da kasancewar hakan idan har ya faru,to amma abun tambayan shin zan iya kuwa....?"
Tambayan daya tsaya mata a rai kenan,ta kasa samun wani ya bata amsa,ganin jikinta yayi sanyi da maganar kuma da yiwuwar ya canja mata ra'ayi yasa baiyi k'asa a guiwa ba ya shiga kwad'aitar da ita amfanin karatun,wanda a k'arshe ya samu nasaran amincewarta,dan BB cewa yayi bazai mata doleba idan har ta nuna bata so zai bita a sannu har saita amince,saboda a nasa tunanin cewa yayi
_"Duk abunda wani yake so wani yayi,idan har wanda ake so yayin ba shida sha'awar hakan to tabbas baza a samu nasara ba amma idan yana so nan ne zaka ga ya dage dan ganin ya aikata wannan abun kuma burinsa zaka tarar bai wuce na ganin yayi nasara ba"_
Murmushin samun nasara yayi yana shafa lallausan gashinta dake kwance yasha gyara
"Uhmmm! JODI kenan wato kenan fa wai gani kike kin girma ko...?"

"Haba mana YAYA kaimafa kasan na girma ai yanzun ai wani abun da zanyi shi da a yanzun kam ko da kud'i banyinsa,bare kuma da hankalina ai baranma soma aikatawa ba"

"Gaskiya kam amma ni banga wani girman da kika yiba har yanzun"
Mik'ewa tayi a jikinsa ta tsaya tana juya jikinta cikin salo tace
"Haba YAYANAH kallenifa kaga yanda na koma hakama ai wani cewa zaiyi na zama uwar mata.."
Dariya kalamanta suka sashi,sai dai kawai ya gintse yana kallonta yana murmushi,janyota yayi yana maidata muhallinta data tashi
"Lallai kam babynah ta girma,amma wannan girman ai daban wanda nake nufi daban"

"To wanne kake nufi kai...? ni dai nasan na girma yanzun"

"Eh haka ne nima nasan kin k'ara girma amma ni barin fad'a miki irin wanda nake nufi.."
Kallonsa taci gaba dayi tana sauraren jin me zai ce,hannunsa tajiyo k'asan cikinta yana shafa dai² mararta yake fad'in
"Da ace kin girma ina tunanin ni ne mutum na farko da zai tabbatar da haka,kuma da nan gurin ya tabbatarmin da hakan koba haka bane..?"
Sakin bakinta tayi tana kallonsa,lallaima YAYA'N nan nata ya rainata da yawa wato nufinsa har yanzun bata girmaba kenan yake nufi? Har sai ya ganta da ciki zai yarda lallai ne kuwa ta bashi mamaki kuma tabbas ta d'auki alk'awari saita nuna masa itan ta girma.
Bata sake bi takan maganarba tayi cilli da ita gefe,idanunta ta lumshe tana jin yadda yake shafa k'asan cikinta ita kam bata san wane irine YAYA'N nata ba duk wani abu da zaiyi ya jefa zuciyar mutum cikin soyayya ya iya,gani take da ada ne aka tambayeta yaya halinsa yake zata ce babu ruwansa shi en kamili ne kuma bashi da fitina,amma kam a yanzun cikin d'an tak'aitaccen lokaci ta gama fuskantarsa a nata tunanin tsaf zata zane littafi hard cover da halayensa,katse mata tunani yayi da fad'in
"JODI ki shi shiryafa cikin satin nan zaki fara zuwa makaranta"
Daga haka bai k'ara ko wasalin 'a' ba ya d'inke bakinsa ta hanyar rufe idanunsa danma kada ta dameshi da tambayoyi,hakan data ga yayi yasa ta yin murmushi cikin sanyin murya ta furta
"Allah ya kaimu,ubangiji kuma ya bamu sa'a..."
Amsawa yayi yana yadda yake tare da sakin mata kiss a porehead enta,murmushi tayi tana sake tightening hands enta dake jikinsa,kamar masu bacci haka palour'n yayi shiru baka jin maganar kowa cikinsu amma kuma a hakan hira suke da junansu,kiran daya shigo wayan KHUBRA ne yasa ta d'ago ta kalleshi,shi enma ita yake kallo mik'ewa tayi daga jikinsa inda bayan ta d'auka kiran ta shiga gaida MAMA,tambayan da MAMA tayi mata ne yasa ta kallonsa da sauri kuma ta d'auke kanta tana ci gaba da sauraron maman dake maimaita mata tambayan
"Doughter wai kam ina son tambayanki,ranan da kuka zo gida mai ya had'aki da ABBA ne kam har kika janyo ya miki fad'a...?"
Ajiyar zuciya tayi kafin cikin sanyi ta shiga bawa MAMA labari bata b'oye mata komaiba,a b'angaren MAMA kam taji dad'i sosai da yarinyar tata tayi wannan tunanin sai dai kuma dalilin da yasa ABBA ya mata fad'a shine tayi k'aranta ta fad'a masa wannan maganar kamata yayi dama a samu mutum wanda yake babba mai cikakken hankali sai ya nusar da shi cikin hikima da siyasa,kuma tabbas al'amura zasu tafi yadda ya kamata idan haka ta faru.
Nasiha tayi mata sosai akan ta kira shi ta bashi hak'uri sannan kuma kada ta sake yin maganar da kowa,haka dai har suka gama wayan ta ajiye,suka sake ci gaba da uzurin gabansu...

Kwanaki sun ci gaba da wucewa yayin da kowace rana da zata zo ta wuce take tafe da nasarori masu d'umbin yawa.A bangaren su KHUBRA da BB ma hakan ce ta kasance inda maganar makarantar ta ya kankama,makaranta mai kyau wacce kuma zata koyi karatun babu wasa ya kaita,kuma alhamdulillah! al'amura na kyau sosai,shi da kansa yake kaita school sannan idan an tashi shi yake zuwa ya d'aukota,ko da ace yana office ranar da zaran lokacin komawanta gida yayi zai tattara abunda yake yi ya tafi,sai ya maidata gida sannan zai koma office ya k'arasa aikin ranar,wata ranar kuwa idan ya dawo tofa bai komawa sai dai gobe.
Rayuwarta a makarantar wani lokacin idan ta kalli da yawan d'aliban sai taga akwai wanda ko a shekaru ya girme mata bare kuma girman jiki da wasu tsaf sai su d'auketa suyi ta gudu da ita ba tare da nuna gajiyaba,wani lokaci idan taga haka sai take tuna BB lokacin da yake mata maganar karatun,sai dai kaga tayi murmushi ita kad'ai.
Zaune take k'ark'ashin wata bishiya tana duba littafinta da suka gama lesson,tayi nisa a dubawa taji an mata sallama,d'agowa tayi dan ita a tarihin zuwanta makarantar babu da wacce suke k'awance,wata y'ar matashiyar budurwa ta gani tsaye tana mata murmushi,kyakykyawa da ita son kowa k'in wanda ya nema bai samuba,cikin dakewa ta amsa mata suka gaisa a mutunce,kallonta waccan d'ayar tayi tana fad'in
"Idan babu damuwa kuma ban takura mikiba shin zan iya zama...?"
'Dan murmushi KHUBRA tayi ganin itama da fara'a a fuskarta tayi maganar
"Babu komai bismillah! ki zauna"

"To ai kuwa na gode sosai da amsamin da kikayi.."
Matashiyar ta fad'a kafin cikin d'an yanayi na kasancewarsu sababbi a gurin ta furta
"Ni suna na AMINA UMAR FANA,nima sabuwar d'aliba ce a nan,to kuma ban san kowa ba a nan sai yau Allah yasa na ganki nayi kuma sha'awar miki magana ban sani ba ko zamu iya zama k'awaye.."

"Allah sarki ai nima da yake sabuwar zuwa ce shi yasa kika ga na zauna nan saboda babu wanda na sani,amm! ni kuma suna na KHADIJAT ABUBAKAR SA'AD amma a gida ana kirana da KHUBRA.."
Dukansu suka yi murmushi wa junansu,a hankali suka ci gaba da hira jefi-jefi kuma mafi yawanci duk akan karatunsu na ranar da suka yi ne,sosai tarayyarsu ta basu sha'awa ganin sun taimakawa juna da abunda d'aya ya gane d'aya bai ganeba,har lokacin tashinsu yayi,dai² lokacin aka zo d'aukan AMINA inda tayi ta yima KHUBRA magiyan tazo su tafi tare,hak'uri ta bata tana kuma fad'a mata itama yanzun za a zo d'aukanta,haka ta tafi wanda suna yin gaba BB yayi parking,glass en side ensa ya sauke yana kallonta,d'an murmushi tayi kafin ya fito ya bud'e mata ta shiga,sai da suka d'auki hanya ba tare da ya kalletaba yace
"Wane mota na gani ya tsaya inda kike....?"
Shiru ta masa babu amsa,shi kuma yaci gaba da fad'in
"Kina sane da cewa ke matar aure ce ko...? to ina so ki kiyaye kule-kule babu ruwanki da kowa coz bana son fitina kinji me nace...kiyi abunda ya kawoki babu ruwanki da shiga abunda ba a sakiba kinji...?"
Kanata ta d'aga alamar taji.

Kwanaki biyu tsakani take bashi labarin AMINA da suka had'u a school irin kirkinta da kuma yadda suke zaune da juna,yaji dad'in yadda ta fad'a masa abunda ya had'asu kuma shima ya tabbatar da cewa yes matarsa kam y'ar baiwa ce,yanayin yadda yake zama suna lesson kan abunda aka musu a makaranta duk bayan sallar maghreb yasan tabbas baya asara...

Tun bayan da sukayi magana da MAMA akan dalilin daya sa ya mata fad'a a wani zuwa da sukayi a can baya,MAMA bata b'oyewa ABBA'N su BB komaiba ta sanar masa cikin hikima da siyasa shi da ABBA'N KHALEEL suka sashi gaba da maganar,sosai suka kai ruwa rana da su wanda daga k'arshe kuma yaga rashin dacewar k'in amincewar da yayi tun farko,shi da kansa ya same su da maganar daga baya,cikin lokaci k'alilan aka gama magana,da taimakon MAMA da UMMI suka sata gaba itama kuma sai Allah ya taimaka basu wani sha wahala ba ta amince,an yanke d'aurin aure kad'ai za ayi sai tariya kuma babu wani taro da zasu yi bare mutane su fahimci wani abu game da sirrinsu,cikin lokaci kad'an aka d'aura auren ALHAJI ABUBAKAR SA'AD da amaryarsa HAJIYA ZUWAIRA akan sad'aki mafi inganci,anyi taro lafiya wanda y'ay'ane kad'ai suka halarta babu wata gayyata da suka yi daga iyayen sai su.
ASHNA kam lokacin bikin tana ta fama da laulayin ciki kuma sosai take shan wahala,babban dalili kenan daya sa FATAHIYYA komawa gidanta tana taimaka mata,palour suka rashe sunata hira tsakaninsu BB,KHALEEL,SADEEQ BIGGY,KHUBRA,ZUHRA dama ASHNA dake fama da kanta amma a haka ta dage itafa saita zo dan baza ayi babu itaba,FATAHIYYA kam d'akinta na gidan ta tsere dan cewa tayi bata iya zama gaban yayyen nata da ko wanne yake manne da matarsa ita a nata ganin kam wannan fitsarar da suke gwadawa bata iyawa.
Haka aka gama taro kowa ya d'auki matarsa yayi gaba,sai fatan samun zaman lafiya da sab'awar halaye.

Lokaci baya jira sai dai a jira shi kamar yadda wannan magana take haka fa abubuwa suke,bayan kimanin watanni biyar da auren ABBA'N KHUBRA,ASHNA ta haifi zankad'ed'en saurayi Yaro yaci sunan ABBA'N BIGGY wato MUHAMMAD suna kiransa da AL-MUSTAPHA,fad'in hidimar suna da suka sha a wannan family'n b'ata baki ne,yayin da a b'angaren ZUHRA da KHUBRA kuma shiru kake ji babu wacce tayi ko da b'atan wata,sam hakan bai wani dame suba dan ganin samu da rashi duka daga Allah suke lokaci kad'an yake azurta mara shi kuma hakan ma ba abun damuwa bane tunda duka yaushe akayi auren da zasu d'aga hankalinsu,a b'angaren karatunta kuwa ta dad'a maida hankali sosai k'awancen su da AMINA kuwa sai abunda yayi gaba,mutane da dama suna mamakinsu wanda bayan tsayin watannin da suka shud'e kowacce ta san y'ar uwarta nada aure,k'awance na tsakani da Allah suke duk inda kaga d'aya cikin makaranta to zaka ga d'aya,mazajensu sun san juna yanzun baya ga ziyara da sukan kaiwa junansu,sun dad'a dagewa akan harkar karatunsu abunda ya kaisu shi suke yi babu wasa,tsakaninsu da mutane gaisuwa ce suna kuma matuk'ar girmama junansu.

Yau tunda KHUBRA ta shigo skul take baza idanu taga inda aminiyar tata zata b'illo amma shiru kake ji,zaman makarantar duk ya isheta haka dai tayi manage har aka tashi,ko data koma gida bayan ta kirata a waya a kashe aka shaida mata,yinin ranar haka ta yini wani iri da ita wanda shi kansa BB sai da ya gane haka,ko da ya tambaya bata b'oye masa komaiba ta sanar masa,addu'ah ya nusar da ita tayi

Please Login or Register in order to submit comment