Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Koda suka koma gurin KAKA sallama kad'ai yayi masa sannan ya kamo hanyan dawowa gida,tun daga lokacin ya k'udire niyyan nemo masa magani daga na asibiti har zuwa na gargajiya dan bai san da wanne za a daceba saboda masu iya magana kan ce "idan dama yak'i to sai a koma hagu"

Neman magani yayita yi bayan dawowarsa sai daya tabbatar ya samu magungunan daya aminta dasu sannan ya kama hanyan komawa garin,da taimakon Allah ko bayan gumurzu da suka sha da KAKA ya amince ya karb'i prescriptions en dan kafewa yayi akan magungunan suna kisa shi ko haka kawai bai shirya mutuwa yanzuba.....

_Kunjifa KAKUS da gigin tsufa...._


Lokaci baya jira sai dai a jira shi,haka yake inji masu iya magana kuma su kan ce "duk abunda kaga bai zoba to tabbas ba a sa masa lokaciba" k'warai kuwa dan ko idan har ansa masa lokaci sai ya zo kuma harma ya wuce.

Biki nata dad'a matsowa ko wane gefe suna shiri babu ji bare gani,zuwa wannan lokaci duk wanda yaga ASHNA da BIGGY sai ya so sake kallonsu saboda soyayya,shak'uwa gami kuma da yarda da juna dake tsakaninsu,b'angaren su KHALEEL kuwa ba a cewa komai saboda sanin su nasu tsarin ba irin na kowa bane abun dai sai wanda ya gani,biki na k'aratowa amare da angwaye hidimomi sai dad'a shan kawunansu suke haka lokacin yaci gaba da kusantowa..........






*COMMENT FOR MORE PAGE'S......*
💃💃💃




*~#TEAM KHUBRA.~*




*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹





*©®2018*
*24/ʝųlყ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





5⃣2⃣





*Y* au gaba d'aya abunda yayi saura a kwanakin da suka rage musu baifi kwanaki goma ѕhα hud'u ba,duka gidan ya dad'a hautsinewa,kowa ka gani ba shida lokacin zama aikace-aikace da hidima duk sun sasu gaba,hatta da su kansu amaren ba wani lokacin zama garesu ba,yau suna nan gobe can.

Cikin mota suke tafe sai surutu suke su uku KHUBRA,ZUHRA sai kuma ASHNA,shi kansa KHALEEL da yake driving hiran nasu har hawan masa kai yake saboda yawon da suka sha yau gashi duk ya gaji,ba shida burin daya wuce su isa gida ko Allah zaisa ya samu nutsuwa.
Daf da sallan isha suka iso gida,yana ajiyesu ko bai tsaya hiraba yayi musu sallama gami da juyawa,su kansu da yake a gajiye suke da shigansu gida,basu tsaya ko inaba sai d'aki,a kan bed ZUHRA ta zube tana fad'in
"Wash! wallahi duk joints d'ina ciwo sukemin haka wannan yawon raba I.V en yake....tabbb wallahi idan na tashi aure bazan iya wannan wahalarba,gara mutanen kada su zo."

ASHNA dake zaune kusa da ita ta kalleta tana fad'in
"Lallai yarinya ce ke,ta ina zaki wani sakowa mutane zancen aurenki bayan samarinma koransu kike,kenan wai gaki malama to waima ni da wane suna zanna kiranki ustaziya ko me....?"

"Ke kika sani kuma wannan,ni rabani da SAMARIN BANA (ASY KHALEEL) ba komai a cikinsu sai k'arya kamar ragowar yak'i....Fatan dai Allah ya zab'a mana mafi alkhairi.."

"Wollahi kin gama magana tunda kika nemi zab'in mafi alkhairi,da sannu zaki ganshi wollah...."
KHUBRA ce tayi maganar dan duk hiran da suke bata sa bakiba sai lokacin,saboda lokacin da suka shigo tana k'ok'arin cire kayanta,shirin shiga wanka ta gama nan ko tayi hanyan toilet..

Mintuna k'alilan ta fito jikinta jik'e gada ita sai towel iya cinyanta,sai k'arami data d'aure kanta ta gaba ya bada shape na harafin V.
"Ha'aaa! ya kuma naji kunyi shiru ko har kun gama hiran ne?"
Ta tambaya tana coge k'afa d'aya,ASHNA dake faman chart ta juyo tana kallonta
"Uhmm! nikam abunda nake yafi min wannan firan da kike magana"

Dariya tayi dan tasan me take nufi,batayi maganaba ta wuce tana fad'in
"To ai sai ku tashi kuyi wankan dan ni ina gama abunda nake kwanciya zanyi.....wallahi dana shiga wankan nanma kamar kada na fito saboda dad'in ruwan da naji...."

"Kina iya komawa ai in yaso sai muyi using wani toilet en.."
Hankalinta na kan waya tana chat take bada amsa,da sauri ko ASHNA ta kalleta ehfa tunda ke baza kiyi wankanba ai kya fad'i haka dubi irin gajiyar da muka kwaso amma nice haka,bari kiga ke idan kin gama chart en kyayi nan da talatainin dare"
Wayan ta ajiye tana shirin core kayanta,kafin tayi yunk'urin mik'ewa ai har ZUHRA ta dire a guje ta shige toilet en,baki ASHNA ta saki KHUBRA ko me za tayi mata ba dariyaba,tana cikin dariyan aka bud'e k'ofan hankalinsu duka ya tafi kan k'ofa suna son ganin waye haka babu knocking ya danno musu kai..
FATAHIYYA ta shigo tana fad'in
"BRIDE AUNTIES.....Ashe kun dawo amma ko ku nemeni..shi ne kuka gudo nan kuna hira babu ni..."

"Allah sarki k'anwarmu yi hak'uri kinji shigowanmu kenan muma.."

"Kai AUNTY KHUBRA shigowa'nkufa kenan kika ce bayan gashi nan har wanka kikayi kinga kenan kun jima da dawowa...Shi kenan ai tunda kuna nuna min triberlism dama ni nasan ba wani damuwa kukayi da niba....wa ya sanima ko idan kunyi aure zaku neme ni..."
Fuskanta a shagwab'e tayi maganar cike da nuna damuwa

"Yi hak'uri kinji....me zaisa mu kuwa bazamu nemeki ba,k'arewa ma ni dake tare zamu tafi kinji..."
KHUBRA tayi maganar tana rik'e hannunta..

"Su tafiya tare manya,ai ga hanya nan zaku iya abunda yafi hakama...Amma ko dai angon a ranar zai ce ku koma inda kuka fito.."
Yanayin da tayi maganar yasa su darawa dukansu,dai² lokacin kuma wayan dake saman mirror ta hau ruri,kallon gurin KHUBRA tayi had'e da tab'e baki,banza tayi suka ci gaba da hiransu har kiran ya katse,zuwa can aka sake kira nanma wayan sai ring yake
"Haba sis kina jifa ana kiranki kuma kin share kamar ba ke ake kiraba..."
ASHNA tayi magana cike da tuhuma kuma take kallon KHUBRA'N da tayi kunnen uwar shegu kamar bada ita take ba.Ganin bata da niyyan motsawa yasa ita ASHNA'R nufan gurin da wayan yake ta d'auka tana duba mai kiran,YAH KHALEEL ta gani a rubuce saman phone en sai lilo sunan yake
"Ungo ni YAH KHALEEL ke kirankima ashe kika wani share kamar bake ba,nifa wannan gulmar ne banso idan zaki amsa ki amsa,mata tana so sai wani kaucewa kike...Allah yasa ayi ai auren nan naga yadda zaki yi..Ni wallahi har so nake naga yadda zaki koma idan anyin auren..Zaki ci gaba da yi masa duhun kai ne ko kuwa ya za ayi nema ohoon muku..."

Ita dai KHUBRA shiru tayi mata bata tankaba sai wayan data karb'a ta ajiye gefenta ba tare da tayi tunanin d'aukaba,saima hira da take k'ok'arin sako musu.
FATAHIYYA ta kalleta lokacin da kira na uku ya shigo wayan nata
"AUNTY da kin d'auka kinji me zai ce miki...Kinga yanzun kada kisa shi tunanin ko wani abu ya faru..."

"Ke kyale shi ai yasan a gajiye nake ni kuma yanzun baran iya d'aukaba.....Dan yanzun yana ganin na amsa zai tsare ni da surutu ni kuma gaskiya bacci nake ji...."

"Aifa shi yasa naga kinyi baccin yanzun..kina nan kin wani yi gwaraf a gaban k'anwa zaku dasa surutu shi ne harda wani cewa bacci kike ji....Allah dai yana kallonki kuma sai dai ki tunasar da wani wulak'anci babu kyau.."

Ita dai FATAHIYYA tana kallonsu idan wannan yayi magana ta juya ta kalle shi idan wannan ya amsa sai ta sake juyawa,rashin d'aukan wayan da KHUBRA tayi yasa FATAHIYYA d'auka a hankali ta furta
"Hello! YAH KHALEEL ina wuni....?"

"A'a FATAHIYYA ya kike...? Ina AUNTY'NKI fa?"

"Lahh! YAH KHALEEL damafa gani nayi kana kira ita kuma tana shigowa tayi bacci.."

"Ok! to shi kenan na gode k'anwata,da safe mayi magana da ita dama kiranta nayi naji lafiyanta,amma tunda tayi bacci shi kenan kada ki tasheta,na gode sosai.."

Sallama sukayi ta ajiye wayan,sai lokacin hankalin KHUBRA ya kwanta saboda tunda ta d'auki wayan hankalinta bai kwantaba sai da taji sunyi sallama kuma duk abunda suka fad'a taji tunda wayan a handsfree ta sata.
Ajiyan heart tayi ASHNA kam shiru tayi musu amma lamarin na KHUBRA na bata mamaki musamman da auren ya dad'a gabatowa..
Bata kuma kulasuba har suka gama abunda za suyi k'arshe kuma kowacce ta kwanta.Ita dai tana kan waya suna chart da nata prince en kuma tana cikin garin ciki........

*ONE WEEK TO MARRIAGE....*

A gurguje ya fito daga mota ya nufi cikin gida dan dama a kwai abunda ya shigo dashi yanzun da yake ta sauri kada wani ya tsaida shi.
Karo suka yi da sauri ya d'ago dan ganin me ya faru haka,kallonta ya tsaya yi ganinta yake kamar cikin mafarkin daya saba a y'an kwanakin da auren nan ya matso,sam baya son abunda zai had'a shi da ita bare ya kawowa ransa wani tunanin ko yasa damuwanta a ranshi,sai daifa hakan da yake ba k'aramin azabtuwa yakeba,duba da yadda rashin ganin nata ya dad'a jefa shi cikin wani hali,ganin da ya mata a yanzunma duk da a rashin sani hakan ya faru,sosai ta dad'a yi masa kyau musamman da bai gantaba cikin y'an kwanakin da suka wuce,kamar an dasa su zuciyarsa sai sak'a masa abubuwa da dama take a kanta,cikin sauri ya d'auke kansa tare kuma da ci gaba da tafiya abunsa..
Kallonsa kawai tayi ta tab'e baki sannan ta juya tana tafiya abunta zuciyarta na fad'in
"Anya ko YAH ba wani abu ke damunsa ba?...Ko kuwa dai ni kad'ai nake ganin haka?....To amma idan har ba gizoba naga ya rame sosai ba kamar yanda na sanshiba...."
Da sauri kuma ta d'age kafad'a tana fad'in
"Kai to ni ina ruwana ma da damuwa'rsa....Shi ya sani ko wani abu na damunsa...Can ta matse masa ni banda damuwa...Allah yayi mutum sai d'an karen nunk'ufurci..."
Hanyan guarding ta nufa tana shiga ta nemi guri ta zauna,bata jima ba a gurin ko ZUHRA ta shigo gurin
"Ki ce nan kika yo yau kuma nan kika tuno bayan da kin daina zuwa"

"Ehh fa na gaji da zama cikin d'aki ne kawai shi yasa na yanke shawaran zuwa nan nasha iska....
"Wallahi dai kam nima haka nan nake jin zuwa nan yau shi yasa na fito ban kuma yi tunanin kina nanba..."

Suna cikin hiran motan KHALEEL ta kunno kai da sauri KHUBRA ta kwanta a k'asa saman grasses en tana rufe ido,dan ita kam bata son surutun KHALEEL a yanzun sam bata shiryawa jinsu ba,a nan ya tarar dasu shima ko ya zauna,mafi yawanci hiran tsakanin KHALEEL da ZUHRA ne dan dama ita ce abokiyar kuma y'ar rakiyar zance duk lokacin da yazo hira.Ita kam KHUBRA ko magana yayi mata amsanta tsaf sai mutum ya k'irga su saboda yadda take magana a tak'aice..

Labari suke sai dariya suke duka ta window ya hangosu su uku a cikin lambun,da yake lambun yafi kusa da window ensa shi yasa yake iya jiyo sautin dariyarsu.
Yanayinsu gwanin sha'awa haka nan yau kuma yaji yana sha'awar fita zuwa gurinsu ko ya rage damuwan dake ransa.
Suit en dake jikinsa ya zare ya sauya kayan dake jikinsa zuwa masu sauk'i sannan ya fice zuwa gurinsu dan a lokaci ji yayi ba zai iya fitanba.Tun kafin ya k'araso fuskarsa a sake ba kamar kwanakin da suka wuceba ya iskesu,ganin fuskarsa a sake wanda shi kansa KHALEEL ganin canji a tare da shi sai da yayi mamaki abu d'aya ya hana shi nuna hakan murnan da yake na ganin aminin nasa ya sakko yasashi jan bakinsa ya tsuke ko a fuska kuma bai nuna masa komaiba,hira sosai da suka jima basuyi ba suke wanda k'arshe suka gangaro kan maganar program's da za ayi a bikin,lokacin da KHALEEL yayi maganar sai da BB yaji wani iri kan maganar dinner da yayi,kawai dai ya danne ne,zuciyarsa na masa k'una,maganar KHUBRA ta katse masa tunani wanda har sai da ya d'ago ya kalleta

"Ni kam dan Allah wai dole ne sai anyi wad'annan bidi'o'in..."

Kallonta sukayi su duka suna mamaki
"To banda abunki CWEETY ai hakan shi zai nunawa duniya irin farin da muke ciki..."

Tab'e baki tayi tana fad'in
"Tabbb ni kam wallahi da da yadda zanyi da nayi dan kawai na hana wannan abun....Dan ni kam har ga Allah ba so nakeba"

"Saboda me zaki ce haka CWEETY...?

Sai data kalleta sannan tace
"Saboda bana son hayaniya ne kawai shi yasa,na tabbata lokacin zanyi ta fama da ciwon kai"

KHALEEL kam sam bai so hakan ba amma saboda jin abunda ta fad'a yasa yace
"To ai ina ganin hakan ba abun damuwa bane,abu ne da za ayi na k'aramin lokaci kuma ba dad'ewa za ayi ana yiba,so ina ganin babu wani abu da zai faru in sha Allah...."

BB kam bai ce komai ba game da muhawaran da suke saima waya daya ci gaba da dannawa kamar baya gurin,hiran ya koma tsakanin ZUHRA da KHALEEL dan ita ta maye matsayin BB na babban aboki da za ayi shawaran da shi itama amarya tana gefe tayi musu shiru kamar bata gurin......

Tun da suka shiga satin komai ya dad'a kachamewa musamman da kwanaki kad'ai ya rage musu a fara biki.
A lokacin duk wanda ya kalli KHUBRA babu lallai ya shaidata saboda kyau data k'ara akan nata,fita ko a cikin satin babu mai yinta tsakaninsu kullum suna d'aki daga su sai halinsu MAMA kad'ai ke da ikon ganinsu sai ko mai gyan jiki dake zuwa kullum tana gyaresu wanda gaba d'ayan su akewa sai dai na amaren yafi na sauran,a haka sauran kwanaki suka soma cimmusu.

Kamar yadda yake a tsare bayan kamu da walima ta mata zallah da za'a gudanar a shagulgulan bikin,sai d'aurin aure wanda daga shi sai dinner da za ayi bayan nan kuma za a wuce da amare gidajensu.

Duk wannan budirin da ake har lokacin BB baiyi kuskuren d'aukan invitation card enba bare ya gayyaci wani aboki ko wani mutum mai muhimmanci a rayuwarsa nasama da aka bashi tunda ya amsa ya bud'e closet ensa ya cillasu,tun daga ranar ko bai sake bi ta kansuba,hasalima duk lokacin da KHALEEL zai kirashi akan zaizo suje rabon card en sai dai ya bashi excuse akan aiki ya rik'e shi office,duk naci da magiya babu irin wanda KHALEEL bai masaba amma sam yak'i rakashi,kan dole ya hak'ura ba dan ya soba sai dan babu yadda zaiyi da shi.

Tun daga ranar da sukayi haka da shi ko ta k'arshe bai sake nemansa daya raka shinba sai dai duk inda zashi ya kama hanyansa shi d'aya,wasu daga cikin abokansu ko har tsiya suke masa idan sun ganshi shi kad'ai,sai dai ya fake musu da BB aiki ya tsare shi a office amma sun san babu yadda za ayi su ganshi shi kad'ai...
Haka har ranakun biki suka fara shigowa....

Kamar yadda aka shirya haka aka soma gudanar da events en ba tare da k'arya ko nuna su wasu bane,duk k'in KHUBRA na rashin son shiga taron jama'a abun ya gagara,kan dole take aiwatar da komai ba dan ranta na soba,duk inda ta juya jama'a ne daga ko wane sashi.A hankali saboda hayaniya da k'aran kayan kid'an wajen suka soma damunta nan ko ciwon kai yace bisimillah...
Duk yadda take ji ajikinta d'auriya kad'ai take amma sam tak'i nunawa mutane hakan.


*23/SEPTEMBER,2018.*

Rana bata k'arya akace sai dai uwar d'iya taji kunya,a yau ne dubban jama'a suka taru a babban masallacin na *UMAR BIN KATTAB* dake *ZARIA ROAD* dan shaida d'aurin auren,d'aurin aure mai cike da tarihi..

Shiga ta alfarma na hango manyan mutanen uku wanda duk ya gansu a wannan lokaci tabbas sai ya san sun bayyana a gurin,manyan ALHAZAWA da a wannan lokaci tarihinsu da labarinsu ya baza birni da k'auye cikin lokaci k'alilan,wanda dama dayawa daga cikin mutane sun san da su a wancan zamanin na baya sai a wannan lokaci labarinsu yafi yin shura...
Fuskokinsu kad'ai mutum zai kalla ya shaida tsantsan farin ciki dake shimfid'e samansu,jama'a sai gaisawa suke da su suna musu fata da kuma sanyawar alkhairi.

Da misalin k'arfe 10:30am KHALEEL na hango cikin shiga wacce take bayyana eh lallaifa wannan young man en akwai wani abu dake faruwa.
Kallo d'aya tak ya isa mutum ya gane hasken dake tare da shi a ranar wanda a dai² lokacin ya juya yana kallon BB daya koma kamar ba shiba,shigansu iri d'aya komai dake sanye jikin d'aya tabbas idan ka kalli d'aya zaka ganta ba aikin kowa bane sai BB dan shi yayi iya yinsa na ganin ta faru,kallon juna suka yi,sannan suka yima juna murmushi kafin suka fice a tare,BB ke driven inda ango KHALEEL ke gefensa
"Wai MAN lafiyarka k'alau kuwa...."

Kallonsa yayi ta cikin bak'in glass dake fuskarsa kafiin nan kuma ya furta
"Me ka gani kuma...?"

"Yo to kai d'in ne ai kake bani mamaki...cikin lokaci k'alilan kamar wani mai shafar jinnu..yau a ganka kana d'aci gobe kuma ka sake rikid'ewa ka koma ba kaiba"

Dariya yayi "To waya sani ne ko na koma cin wahainiya...kasan idan mutum na ci rikid'ewa yake yau ka ganshi a wannan siffar gobe kuma ya sake komawa wata"

Kallonsa kawai KHALEEL yayi ya furta
"Allah ya kyauta..."

"Ameen...!"

"To amma shi wannan glass enfa daka toshe da shi kamar wani sabon makaho,na lafiya ne kuwa?"

Banza ya masa yayi kamar bazai yi maganaba,can kuma kamar wanda aka tilasta ya furta
"Idan baka son ganinsa ba dole aka maka sai ka kalle niba ai...Duk ka wani dami mutane da surutu dama kasan daka tashi karatu ka zama *JOURNALIST* dan naga yanzun abunda kafi k'auna kenan...Mutum sai d'an karen surutu kamar ya had'iya farrot,Allah yasa kada ka koyawa k'anwata wannan zancen..."

Dariya sosai maganar da yadda BB yake da face ensa ya bashi,KHALEEL jinsa yake yafi kowa dace a wannan ranar saboda aminin nasa ya dad'a sakin jiki da shi dan yau kam gashi harda su tsokana,suna ta faman tsokanan juna suka isa masallacin inda ake jiran k'arasowarsu.....


*11:00am*
Aka fara addu'ah sannan bayan gubatar da siga da akayi a cikin massalacin wanda duk abunda ake BB na wajen masallaci yak'i shiga sai KHALEEL en kawai ya shiga,aka fara sanar da d'aurin auren inda mai sanarwar ya fara sanarwar da d'aurin auren ta cikin abun magana kamar haka...

_AN 'DAURA AUREN *IBRAHIM-KHALEEL* DA AMARYARSA *KHADIJATUL-KHUBRA* AKAN SADAKI NAIRA NA GUGAN NAIRA HAR NAIRA DUBU 'DARI BIYAR........_

Ai jin wannan sanarwa take idanun BB dake cikin glass suka soma kawo ruwa,a lokacin kam ya gama tabbatarwa da kansa ya masifar yiwa kansa,ya cuci kansa cutar da baya tsammanin akwai wata cuta da zaiwa kansa kamarta,yasan yayi k'auron baki inda yanzu gashi nan abunda ya jawowa kansa.....Ya tabbata kam yanzun hak'uri ya zame masa dole.
Gefen k'irjinsa ya dafe saboda yadda yaji yana masa zafi lokaci guda tsaiwa ta soma neman ta gagare shi,a daddafe ya nufi mota shi kad'ai yasan me yake ji a guje kuma ya fizgi motan tare da bar in gurin..............😱😱😱😱


_Wayyoooo Allah ínα masoya KHALEED (BB) ku kαwσ αgαjí kαdα wani abu ya same shi........_

_mσvє fσwαrd tσ thє nєхt pαgє..._




*COMMENT FOR MORE PAGE'S*





*~#TEAM KHUBRA-KHALEEL.~*





*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹



*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/

*©® 2018*
*25/ʝųlყ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

_rígíjí gαвjí....wαní kαчα ѕαí αmαlє...mαí kαmαr zuwα kαn αíkα....ídαn вα kαчí kα вαdα gurí dσmín вαnα ч'αr uwα kumα αвσkíчαr αíkí tα zσ dα wαní ѕαвσ mαí tαfє dα ѕαвσn ѕαlσ......_
_kαdα kují ínαtα zuвα ѕurutu gαmє dα в'αв'αtu вα kσwα nαkє nufí вα fαcє *AUNTY MAIMOUNATH O.G* dσmín kuwα вαnαmα tα dαwσ muku dα ѕαвσn nσvєl nαtα mαí cíkє dα dαrαѕí,ílímí,fαd'αkαrwα tαrє kumα dα k'αчαtαrwα ku nєmí nσvєl єntα mαí tαkєn *MEELAT TAMU*..._
_dαurє kα/kí nєmí nαkí α duníчαr ❄ domin kαdα α вαku lαвαrí........kαdαfα ku mαntα dα ѕunαn...._
*MEELAT TAMU.!*
*MEELAT TAMU.!!*
_ku nєmα ku ѕhα kαllσ tαrє dα kαrαtu,kαdα ku ѕαkє α вαku lαвαrííííí..._
*~__________________________~*
_jínjínα tαrє dα gσdíчα gαrєkí mαruвucíчαr zαmαní *HALISSA ADAMOU* ч'αr mutαn nígєr mαвucíчαr *MARAYUMA Y'AY'A NE* kí jímα kíчí k'αrkσ tαwαn αllαh чα k'αrα míkí lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní.. *SMASHER & HUBBEEY* nα gσdíчα dα kαrrαmαwαrkí gαrє ѕu.αllαh чα вαr zumuncí._
*~__________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





5⃣3⃣





*K* asa controling temper ensa yayi wanda shi ne babban dalilin da yasa shi baro gurin ko tsayawa jin sauran d'aurin auren baiba ya baro gurin,bai zarce ko inaba sai gida wanda ikon Allah kad'ai ya kai shi,gidan a cike yake da jama'a amma sam BB bai iya gane abunda ke gaban sama bare kuma magana da ake masa da bai sanma suna yiba bare ya iya basu amsa.
Bedroom ya shige nan ko ya shiga watsi da kayan jikinsa d'aya bayan d'aya har ya gama raba jikinsa da kayan ya rage daga shi

Please Login or Register in order to submit comment