Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har tsahon lokacin...

Masu iya magana kance "RANAR WANKA BA A B'OYON CIBI" k'warai kuwa haka yake wata ranar alhamis ciwo ya tasammata a cikin d'aki tun cikin dare addu'a kawai take saboda a lokacin bana gari,kuma gidan ya rage daga ita sai LADIYO wacce take nata d'akin daban itama,haka ciwon yake zuwa yana lafawa har dai Allah ya taimaka akayi asuba,a yanda take a haka ta lallab'a tayi sallar asuba,bayan nan kuma gari ya dad'a haske ciwo ya dad'a tadowa fiye da karon farko,tana wannan hali ne Allah ya kawo LADIYO shima zuwa tayi ta dubata ganin bata fitoba,samunta da tayi cikin ciwo wannan yasata hanzarin tafiya gidanmu ta kira mahaifiyata,ko kafin su k'araso gida har Allah ya sauketa lafiya,lokacin da suka shigo basuyi arba da komaiba sai da kukan jaririya nan suka k'arasa da sauri dan ganewa idanuwansu abunda suka ji gaskiyane ko kuwa,da zuwa suka tarar da ita a gefe tana maida numfashi jaririya a gefe tana tsala kuka babu b'ata lokaci iya ta gyarasu duka,tofa a lokacin ne kuma iya taimin aike kan lallai-lallai inzo gida tana son ganina a cikin kwanakin,lokacin da sak'onta ya riskeni banyi wata-wataba na shirya kayana sannan na kamo hanyar dawowa gida.
Bayan dawowata na tarar da wannan abun farin ciki daya sameni,aikuwa nayi murna sosai da ganin wannan kyauta da ubangiji yamin,bayan kwanaki 7 yarinya taci sunan mahaifiyata *KHADIJATUL KHUBRA*,tun daga ranar da FALMATA ta haihu sai LADIYO ta dad'a taso da halayenta na farko ya zamana ko d'akin FALMATA ta daina zuwa,tun kuma ranar data haihu mahaifiyata ta dawo gidan d'akin FALMATA ta tare ta shiga bata kulawa da gyara ta musamman wannan dalilin yasa LADIYO kishi mai tsanani amma sai ta dinga dannewa bata nunawa a fili,sai daifa abunda ke zuciyarta kenan a duk lokacin data bud'e ido taga FALMATA da sabuwar jaririyar ji take kamar ta cinna musu wuta su k'one gaba d'aya kowama ya huta.

Zuga kuwa da hud'uba kullum cikinsu take musamman idan ta fita tofa babu inda take zuwa sai gidan TABAWA,haka itama kullum cikin sintiri take a gidan nan,haka har suka k'ulla abunda suka k'ulla.

Wata rana da asuba lokacin bayan iya ta koma gida KHUBRA nada watanni biyu a duniya,bayan mun idar da sallah a masallaci na kamo hanyan dawowa gida,abunda ya faru a wannan ranar idan na tuno ina jin b'acin rai da nadamar abunda na aikata a wannan lokacin,a ranar ba d'akin FALMATA nakeba bayan shigowata saina tuna ai ranar ban tashetaba da zan fita kasancewar ina sauri zani masallaci,tuna hakan da nayi yasa na nufi d'akinta da sauri kasancewar gari har yayi haske sosai,da zuwana d'akin abunda ya d'agamin hankali shine na tarar da ita kwance tasa KHUBRA a gaba,daga bayanta kuma wani k'ato ne jikinsa ko riga babu ya rungumeta suna bacci a haka,ganin wannan abu ya d'agamin hankali sosai ban tsaya jiraba na shiga jibgar k'aton ihunsa shi ya farkar da ita dama jaririyarmu,dukan daya isheshi yasa shi ficewa a guje,idanuna sun rufe da tsantsan b'acin rai nan babu jira na fice daga d'akin.Faruwar hakan babu jimawa na sake dawowa a lokacin har tayi sallah jikinta duk a sanyaye,tana rungume da y'arta tana bata abincinta,na shigo babu b'ata lokaci nace ta shirya zamuje gidansu,ita dai har lokacin batayi maganaba kuma jikiinta yayi mugun sanyi fiye da farko dana tarar da ita a d'akin mayafinta kawai ta d'auka ta goya KHUBRA a baya muka kama hanya ni da ita haka har muka isa gidansu,da zuwa nace ta shiga ciki idan BABA na nan tamin sallama da shi,ta shige ta barni nan a k'ofar gida.
Bayan fitowar BABA muka gaisa a mutunce sannan na shiga koro masa bayanin abunda ya faru,shi dai yayi shiru yana saurarona har na k'are labari,sannan ya kalleni da mamaki shimfid'e a saman fuskarsa ya shiga fad'in
"Nayi mamaki daka zomin da wannan rikitaccen labarin naka mai kama da k'anzon kurege,kuma tabbas kaima ka bani mamaki da wani yazomin da wannan maganar wallahi da sai nayi k'ararsa amma da yake kaine mun barka da Allah,amma zan tambayeka wani abu game da y'ata,shin lokacin da kazo neman aurenta ka tarar da ita tana tara samari ne ko kuwa? sannan bayan ka aureta ka sameta a cikakkiyar budurwa ko a'a? tana da kamun kai ko a'a a bayan aurenku?"
Duka amsoshin d'aya ne A'a,tabbas ba haka halayenta suke ba,amma a lokacin da yake abunka sa sharrin zuciya sai nake ganin kamar fa ta aikata,nan na k'ek'asa k'asa na kuma dube shi nace
"Nifa BABA duka nasan ba haka bane amma na sani ko ta sauya hali ne bayan nan"
Sosai maganata ta b'ata masa rai amma sai ya danne ya ce
"To yanzu daka dawo da ita kuma me yake faruwa?
Nan ko na furta "Na dawo muku da ita ne,sannan kuma tunda Allah yasa haka halinta yake na saketa saki d'aya idan ta samu miji tayi aure..."
Ba sakin ne ya b'ata masa raiba illa cin mutuncin da nayi musu na saida na kawota har gida sannan kuma nace na saketa a gaban idonsa,nan ya ce
"To BUBA munji abunda ya faru mun kuma gode amma ka jirani na fito maka da y'arka,kamar yadda ka dawomin da tawa y'ar nima ina son tabbatar maka da bazan rik'e maka taka y'arba,saboda haka saika nema mata wata uwar"
Yana gama fad'in haka ya shiga gida ya fito hannunsa d'auke da jaririyar,nan ya mik'omin ita nako sa hannu na karb'a na mik'e zan tafi,maimakon na tafi sai na bud'e bakina na kuma kalli tsabar idonsa nace
"Kamar yadda ka bani y'ata in sha Allah zan rik'eta da yardar Allah kuma babu abunda zai samemu,kamar yadda zan tafi da ita yanzu to ko ku tabbatar na tafi da ita kenan bazaku sake ganintaba haka nima na tafi kenan ni da ku har abada...."
Ina gama fad'a masa ban jira ya sake maganaba nayi gaba abuna..

"Tun daga wannan rana rainonta ya dawo hannun IYA mahaifiyata saboda LADIYO ko kallo bata isheta ba,KHUBRA nada wata uku a duniya mahaifina ya rasu daga nan ne kuma IYA ta dawo gidanmu da zama a d'akin da FALMATA ta zauna,tana kuma ci gaba da kula da ita.
Kimanin watanni biyu da rasuwar mahaifina,IYA ta fara rashin lafiya a lokacin annoba ce ta shigo garin nan na amai da gudawa wanda kwanaki biyar da fara jinyar tata itama tace ga garinku nan,a wannan lokacin naji mutuwar nan da akamin a tsakanin watanni biyar na samu k'aruwa na samun y'a na kuma rasa mahaifana biyu..
Da farko na damu sosai bayan mutuwar IYA amma daga baya sai na dangana na koma ga Allah,sannan naci gaba da kula da KHUBRA duk wani abu da uwa za tayi mata ni nake mata shi dan LADIYO dai-dai da sau d'aya bata tab'a d'aukanta ba saboda tsanar da tayi mata.
Lokacin da bakinta ya fara bud'ewa na shiga koyar da ita karatun addini,a haka muka ci gaba da rayuwa duk inda zani ina tare da ita,bacci ma tare mukeyi a haka har Allah yasa ta fara wayo sosai ta fara gane wasu abubuwa.
Rana ta farko datamin wata magana na shiga damuwa amma sai dai na dake a lokacin data ke tambayeta ina UMMA'NTA? amsa d'aya na bata kamar yadda nayi alk'awarin bazan kaita gurin mahaifiyartaba shi ne nace mata ta mutu tun bayan data haifeta,ranar data ji haka yini tayi kamar mara lafiya,daga baya kuma ta ware kamar sauran lokaci.
Lokacin data k'ara girma shekarunta sun kai ta fara aikace-aikace gudun kada a zageni da kuma k'ananan maganganu dake tasowa yasa na fara barinta a gida sannan muka daina kwana tare,a lokacin ne kuma aikin gidan nan ya dawo kanta komai ita keyi tun bata iyaba har ta gama k'warewa,idan zani d'ibo ruwa ita ke karb'a ta tafi ta hanani zuwa,ina kallo tana wahala amma sam idan nayi magana sai ta nunamin babu komai..
Haka muka dunga rayuwa da dad'i babu cikin hukuncin Allah,har kuma ta zama budurwa,wanda nanma kyau irin nata data gado a wajen mahaifiyarta dan kam babu abunda ta bari na mahaifiyarta yasa hassada ta sake kunno kai ta b'angaren wannan dai shaid'aniya inda bata kyalemuba har sai da tayi nasarar rabamu..."

Nan ya kuma kwashe abunda ya faru tun daga barin KHUBRA a gidan har zuwa yau da suka zo ya sanar da su...
Al-ajabi kam sunyi shi,tasbihi kawai suke suna kuma jinjina abun,kan KHUBRA na cinyan ABBA'NTA banda kuka babu abunda take jin labarin mahaifiyarta da abunda ya faru,Allah ya isa kam LADIYO ta shata koma ince tana kan sha a gurin KHUBRA da sauran mutanen gurin musamman BB da ZUHRA da suke ganin kamar su hakan ya faru da su,kowa a zuciyarsa yake fad'in albarkacin bakinsa da kuma irin hukuncin da zai yanke mata saboda su a ganinsu hukuncin da ABBA ya yanke matama yayi kad'an...

Muryan ABBA'N KHUBRA tasa su maida hankulansu kanshi inda yaci gaba da fad'in
"Bayan faruwar wannan abun ne kuma wata rana ina zaune akayi sallama dani dana fita sai naga mutum tsaye ganin ban sanshiba na daure muka gaisa,sannan nace masa ban shaida shiba,shi ne ya kwashemin komai ya sanar dani,dama shi ne wanda na kama tare da matata,jin haka raina ya sake b'aci sosai amma sai ya shiga bani hak'uri sannan ya sanarmin shima sashi akayi kuma ba kowa ya turo shi ba sai LADIYO da taimakon k'awarta TABAWA,nan ya nemi gafarata na yafe masa sannan na sanar masa yaje ya nemi yafiyar wacce ya aikatawa laifin,na masa kwatancen gidansu saboda ni kam a lokacin bazan iya zuwa gidanba saboda a ganina da wane ido zan kalli wannan baiwar Allah ita da mahaifinta nace ina neman yafiyarsu? to kuma ana haka ne bayan wannan mutumin ya tafi,na shigo gida kwana biyu tsakani nayi MUGUN GAMO........"

Labarin mugun kamun da yayiwa LADIYO da wannan k'asurgumin tsohon banzan ya basu,nan kowa ya shiga fito da abunda ke bakinsa suna fad'in
"Sakayya ce Allah ya nuna mata,Allah ya wadaran hali irin wannan.."

LADIYO dai tana gefe babu baki sai ido tayi k'us da ita kanta a k'asa saboda kunya data lullub'eta ji take inama k'asar gurin ta bud'e ta shige,da tasan abunda zai biyo baya kenan da bata zaunaba,da tasan ta felle k'afafunta tun lokacin da MALAM BUBA'N ya saketa amma yanzun kam inaa lokaci ya k'ure mata...

*SOME MINUTE'S LEFT......*

Bayan wucewar wasu mintuna,an gama jimami da alhini,ABBA'N KHALEEL yake shaida ma ABBA'N KHUBRA cewa
"Ya kamata ka daure kaje gidansu domin neman yafiyar abunda ya wuce saboda idan babu rayuwa akwai mutuwa..."

"In sha Allah zanje na nemi gafarar BABA dama ita kanta FALMATAN..............."


😱😱😱😱😱😱😱.

*Huhhh!!! kunji fa fan's abunda ABBA'N KHUBRA yace kenan bai san MAMA'N KHUBRA ta jima da rasuwa bama ko me yake nufi???*



*~#TEAM KHUBRA.~*





*_#®EAL $MASHER._*
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹





*©®2018*
*22/ʝųlყ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





5⃣0⃣





*B* ayan k'ura ta lafa komai kuma ya dai-daita an gama jimamin abubuwa da suka gabata sannan kuma an shaidawa ABBA'N KHUBRA labarin yadda ta rayu a gurinsu a matsayin y'ar aiki da kuma matsayinta yanzun a gurinsu,daga nan kuma suka gangara kan mak'asudin zancen daya kawosu garin.
Sosai yayi farin cikin abunda suka sanar masa,daga nan ya shaida ma ABBA'N BB cewa
"Duk abunda kaga ya dace ka aikata SAFWAN ba sai ka neme niba idan ya so daga baya naji hukuncin daka yanke,saboda KHUBRA y'arka ce kuma bayan haka kuma kuna da hak'k'i akanta a matsayinku na iyayenta kuma dangin mahaifiyarta..."
Wannan karramawa da ABBA'N KHUBRA yayi masa yaji dad'inta,take kuwa shima ya yanke nasa hukuncin inda yace
"To Alhamdulillah! da Allah yasa al'amura suka kasance haka,gaskiya nafi kowa farin cikin faruwar hakan,amma magana biyu gareni zan fad'a yanzun kuma ba ga kowa ba sai kai MALAM BUBA"

Nan suka sake maida hankali gurin ABBA don jin me kuma zai fad'a
"Ina ganin a yanzu tunda abubuwa da dama sun faru zan nemi wata alfarma a gurinka..."

ABBA'N KHUBRA ya kalleshi yana murmushi yace
"Fad'i duk abunda kake so ni kuma in sha Allah idan baifi k'arfina ba zanyi maka"

Murmushin shima ABBA yayi sannan yace
"Ai nasan baifiba ma,amma dai bari mu gani.......Ba komai zan fad'a ba dama illa ina so nace maka.....tunda Allah yasa yanzun baka da kowa a garin nan mai zai hana bazaka bimu mu koma can birni tare ba,kaga kaima zakafi samun kwanciyar hankali ace kana ganin y'arka a kowane lokaci,behind ma kuma yanzun ba iyali gareka ba,sannan banajin a garin nan kana da wani d'an uwa ko kuwa me kuke gani...?"

"K'warai wannan maganar da kayi nima Allah ne yasa ban yitaba amma nima hangena kenan"
ABBA'N KHALEEL ya fad'a yana murmushi

Ga ABBA'N KHUBRA kuwa yaso musawa buk'atar tasu ganin yadda suka jajirce yasa shi amincewa..
Kowa ka kalli fuskarsa cikin mutanen gurin babu komai samanta face farin ciki da annashuwa.

Bayan wucewar wani lokaci komai ya lafa an kuma gama yanke shawara game da hukunci,shirin tafiya ya kankama in da ABBA ya kammala had'a kayansa aka sasu a mota,gaba d'aya sun mik'e da niyyar kama hanyan komawa inda suka fito..
Suna shirin fita ZUHRA ta kalli ABBA tana fad'in
"ABBA ai kunyi mantuwa..."

Duka suka juya suna kallonta da neman k'arin bayanin mantuwar da sukayi
LADIYO ta nuna musu dake cikin rumfa sai kallonsu take da fuskar munafukai musammanma KHUBRA data koma kamar baturiya dan kyau data k'ara,sai lokacin LADIYO ke nadama game da dana sanin bata aikata abunda tayiba duba da yadda KHUBRA'N ta koma,lokaci guda ta bayyanar mata a matsayin y'ar dangi mai cikakken asali,komawa tayi wata kalar tausayi ganin irin kallon da mutanen gurin ke mata.

A fusace ABBA'N KHUBRA yayo kanta yana fad'in
"Bak'ar munafuka al-gunguma kinzo kin ficemin a gida ko kuwa saina raunataki"
Wani ice ya rarumo faskare guda ya dumfarota da shi,da sauri ABBA'N BB ya rik'e shi yana murmushi had'e da girgiza masa kai
"Haba MALAM BUBA me zai kaika aikata abunda ko a baya baka aikataba,kana so ne ka k'arasa gawar da ba taka bane?...."
Da sauri kuma ya tsaya harara ya aika mata sannan ya jefeta da icen,aiko nan ta juya da niyyar guduwa d'aki icen ya sauka a tsakiyar bayanta ji kake timmm,wani ihu ta kurma su ko su ZUHRA,ASHNA,FATAHIYYA me za suyi inba dariyaba,tsabar mugunta harda rik'e ciki,BB ya kallesu yana fad'in
"Dillah ku rufawa mutane baki,ko meye abun dariya a nan kuma ohooo...."
Kyal-kyalewa KHUBRA tayi da dariya dan ita sai a lokacin da yayi magana tata dariyar tazo,nan ta shiga dariya saboda mugunta irinta KHUBRA baya ga hawaye harda durk'usawa a k'asa tasa hannu ta dafe gefen cikinta..
Kallonta yayi yana dad'a d'aure fuska,lallaima yarinyar nan ta raina shi,banda iskanci shi zai musu magana ta tsaya tana masa dariya,lallai ko zata bawa mutanen garinsu labari idan suka had'u..
Lower lip nasa ya cije yana kallonta k'asa-k'asa fuskar nan a had'e kamar bai tab'a dariyaba,ZUHRA data kalli yanayinsa da sauri ta dunguri KHUBRA tana nuna mata BB,d'an bakinta ta murgud'a k'asa-k'asa tayi magana
"Ina ruwana to da shi....."

Abunda KHUBRA bata saniba tsaf BB yaga abunda sukayi kuma yaji maganar da tayi,kwafa yayi had'e da girgiza kansa..

"Kinzo kin fice ko kuwa sai na danganaki da gaban mai gari?..."

"Wollahi MALAM ban san ina zaniba bani da kowa sai MA'U ita kuma ban san ina takeba a fad'in duniyar nan,dan Allah ka rufamin asiri dan sonka da manzon rahama kada ka koreni,idan ka koreni ina zani.....?"

"Ke dallah dakata ina ruwana da inda zaki?? ni yanzu bani da alak'a ta kusa ko ta nesa dake,tun wuri kuma ki zo ki fice kafin na fusata jikinki ya kuma gaya miki ina fatan kinji dai abunda na fad'a miki....."
Kuka wiiwii take tana bashi hak'uri amma bai biya ta kantaba,nan suka fice daga gidan,haka LADIYO ta k'ullo y'an kayanta ta fito tana kallo MALAM ya sawa gidan pad lock ya rufe gidan,sannan suka d'au hanyan komawa....

Maimakon su d'auki hanyan KANO sai gani suka yi BB dake driving ya yanke hanya,cikin garin DUTSE ya nufa,babu wanda yayi magana cikin iyayen da suke zaune,a tunaninsu a kwai abunda zaiyi a garin,basu tsinci kansu a ko inaba sai k'ofar gidan KAKA,parking yayi sannan suka fita gaba d'aya da masu son tambaya duk sun yi shiru,jikin ABBA'N BB da kuma ABBA'N KHUBRA duk yayi sanyi saboda su kam ko daga mafarki suka tashi aka kawo su nan sun gane ko ina ne,su kuma y'an matan babu wacce tayi tunanin wani abu game da gidan da suka zo.
BB da KHALEEL na gaba,basu tsaya shawara ba suka shiga gidan su KHUBRA na bayansu har cikin gidan,su ABBA na waje suna shawaran yadda zasu fuskanci KAKA dan dukansu masu laifi ne a gare shi,har basu sanma y'ay'an nasu sun shigeba.

Da sallama suka shiga kamar zuwansu na farko haka tsakar gidan yake cike da mutane sunata aikace-aikacensu game da hirarraki irin na mutanen k'auye,bayan sun gaisa da matan gidan kai tsaye suka nufi turakar KAKA dan sun san kam yana nan kamar yadda take a wancan lokacin,da shigarsu cikin turakar suka tarar da KAKA na karatun AL-QUR'AN saboda hadda gare shi,sai da ya kai aya sannan ya amsa musu sallama'n da sukayi,nan BB da tsokana yace
"Sadak'allahul-aziiym tsoho mai ran k'arfe,ashe a kwai tsohuwar hadda bata guduba..."
Dariya KAKA yayi sannan yace
"Yo an fad'a muku haddar da mukayi irin taku ce ta yanzu,mu gwagwarmayar da mukayi ai ko rabi baza kuyiba....Idan kuma ka musa to mu gwada mu gani waye zai nasara..."

Gaba d'aya suka sa dariya har y'an matan sannan suka gaisa,kallon y'an matan yayi yana murmushi kafin yayi magana su ABBA suka shigo da yake ABBA'NSU BB ne a gaba hakan yasa KAKA baiga na can bayaba,kallon ABBA yayi yana murmushi sannan ya fara magana
"Idonka kenan ko SAFWAN..."

Sunkuyar da kai ABBA yayi k'asa ba tare da yayi maganaba


"Kayi hak'uri BABA ka kuma yafemin dan Allah,komai daya faru nima ba a son raina ya faruba...."

"Ai shi kenan Allah ya yafe mana baki d'aya...."

Gaisuwa ta musamman akayi ga kaka,nan KAKA ya sake kallon BB yana fad'in
"ABOKINA wad'annan y'an matan kumafa ?"

Dariya BB yayi dan yasan da shi yake
"Baka sansuba ko...?"

"To banda abunka da na sansu zan tambaya ne.....?"

Gabatar masa da su yayi a matsayin jikokinsa da bai saniba sai yanzun....
Dariya KAKA yana kallonsu duka,ABBA ya kalleshi yaga yana kallon KHUBRA,d'an murmushi yayi yace
"BABA ka santa ne....?"

"Gidanku SAFWAN ni kuma na zama abun tsokana ne kam a gurinka?"

"A'a BABA naga kana kallonta ne kamar ka santa..."

'Dan murmushi ABBA yayi sannan ya kalli KHUBRA dake murmushi ya kuma kalli KAKA yace
"To tunda ka santa fad'i wace ce....?"


Bud'ar bakin KAKA yace
"Yo wannan kam duk wanda ya kalleta ya ganka ai yasan y'arka ce ba sai an tambayaba....kuma har mene abun wahala anan da zaku sani gaba kai da d'anka daga zuwanku,ce muku akai bazan ganeba ne...?"

Dariya suka sa mishi saboda paul daya buga gurin fad'in ko wace ce
"Haba BABA ka dai sake kallonta sosai dawa take maka kama"

Sake kallonta BABA yayi sannan ya kalli ABBA yace
"Nifa bana son shegantaka yo to dawa take kama idan ba da kaiba...."

Sai da suka gama wana shi sannan ABBA yayi gyaran murya,duka suka juya suna kallonsa
"BABA dan Allah duk abunda zaka ji a yanzu ina so ka maida shi ba komaiba,kayi hak'uri ka yafewa wad'anda suka maka laifi,nasan kasani sai dai tunatarwa dan Allah BABA..."

Murmushi KAKA yayi masa ba tare da yayi maganaba,kallon KAKA ABBA yayi sannan ya kalli KHUBRA a hankali yace
"BABA wannan da kake gani tabbas y'ata ce amma bani na haifeta ba.....jikarka ce ta wajen y'arka FALMATA....."

KAKA dake kwance idan zai tashi sai an taimaka masa jin an ambaci FALMATA bai san lokacin daya mik'e zauneba da kansa.

"Ka ce me SAFWAN...? Shin kam yaushe na fara wasa da kai kamar haka?..."

"BABA sam cikin maganar da nayi babu wasa a ciki,jikarka ce y'ar wajen FALMATA..."

Kallonta KAKA yake tabbas ga kammani nan,sai dai kuma abunda yasa yace y'ar SAFWAN ence kaf gidan kuma kaf cikin y'ay'ansa su biyu suke kama da juna,ko wasu tagwayen da ake haifarsu identical baza su nuna musu kamaba..
Hawaye KAKA ya shiga yi na tausayinta yana mik'awa KHUBRA'N hannu,da rarrafe ta isa kusa da shi sosai ya rik'eta ita ko data samu abunda take so nan ta kwantar da kanta kan laps en KAKA feeling so happier take jinta saboda kasancewarta y'ar dangi kuma gata tare da su.Kanta KAKA yake shafawa lokacin daya goge fuskarsa,nan kuma aka shiga maida zancen abunda ya faru baya,sai a lokacin KAKA ya hango ABBA'N KHUBRA dake zaune da tun shigowarsu kansa na k'asa sai yanzun daya d'ago KAKA ya kula da shi..
"Idonka kenan kaima ko ABUBAKAR?...Shi kenan kuma tun daga waccan ranar baka sake dawowaba...na sani dukanmu munyi ba dai-daiba daga mu har kai,kuma sai daga baya muka gane kuskuren da muka aikatawa yarinyar da bata jiba bata ganiba,tabbas dukanmu munyi laifi kuma sai Allah ya saka mata hak'k'inta da muka d'auka....ki gafarta mana JIKATA....."
Yanayin da KAKA yayi magana shi yasa jikin ABBA yin sanyi duka sai yaji ya muzanta a gabansa,nan ya shiga neman yafiyarsa....
Bayan nan kuma ABBA ya tambayi KAKA shin ko FALMATA tana nan ko kuwa wani auren ta sake yi..
Sai da KAKA ya matse idanunsa sannan ya shiga basu labarin tun daga ranar da ABBA ya dawo da ita gida da kuma irin yadda suka yi gwagwarmaya gurin karb'ar KHUBRA da yayi ya kaiwa mahaifinta,a lokacin da yake cikin fushi...sannan ya d'ora da fad'in
"To tun daga wannan ranar ne kuma ta shiga damuwa saboda abunda na aikata akan y'arta d'aya tal,daga lokacin ta sakama kanta damuwa sosai wacce a k'arshe duk bamu fargaba,sai da ciwo yaci k'arfinta bayan shekaru data shafe tana tare da ciwon har ciwo

Please Login or Register in order to submit comment