Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zan maka bayanin komai kaji koh''
Kai ya sake kad'awa,yana driving amma hankalinsa sam baya tare da shi,driving en kawai yake haka har suka k'arasa gida....

《《》》

Fitowarsa daga cikin gidan ransa duk a jagule,hakan yasa ya rasa ina zai nufa,rashin sanin madafa shi ya haddasa masa fasa fitan,direct ya nufi guarding duk ji yake garin ya d'aure masa wani zafi yake ji a jikinsa wanda bai san dalilinsa ba,sam ya kasa tunanin komai baya ga tuk'uk'i da yake jin zuciyarsa ke masa babu abunda yake ji,haushin kowa yake ji a yanzun......
Kasa zama yayi take ko ya kwanta saman grasses en da ke wajen,duk da rana da ta bud'e sosai a garin sai dai kuma guarding en bishiyu sun masa rumfa ta hakane kad'ai yasa babu rana cikin gurin....

Addu'ah yake kada Allah ya nuna masa irin wannan ranar mai cike da tarin k'unci,tsawon lokaci yana kwance a gurin bai sanma lokacin da su KHALEEL suka bar gidan ba,idanunsa ya kulle da suka sauya launi zuwa jaa saboda jin kansa da yayi tamkar zai tsage......


《《》》

A parlor suka yada zango,kansa a k'asa duk damuwarsa bai wuce sanin abunda UMMI ke shirin fad'a masa ba,maganarta ce ta dawo da shi cikin duniyarsa...

''SON abunda yasa nace maka ka nutsu maganace da ta fito daga bakin HAJIYA MURJA wanda bana tsammanin akwai k'arya cikinta,kuma ban son b'oye maka,nafi son kasan gaskiyar zancen''

'Dan kallonta yayi jin ta ambaci sunan HANIYAN KHALEED

''A halin da ake ciki kuma a yadda ita HAJIYAN ta sanarmin shi ne,yarinyar da kamin magana akanta ta riga ta koma garinsu,dan ta cemin iyayenta suka nemi ta koma za suyi mata aure cikin wannan satin''........

A tsorace ya kalli UMMIN nasa yana fad'in
''Wallahi UMMI k'arya ne''

Tsawa ta buga masa wadda tasa ya shiga hankalinsa ba shiri yayi shiru
''A gaban idona kake k'aryata ta,ko babu aminci tsakaninmu ya kamata ka fad'i wannan mummunar kalmar a kanta,idan na sake jin ka furta irin wannan maganar sai ranka yayi mummunan b'aci''
Cikin fusata take maganar wanda yasa shi sunkuyar da kai yana fad'in

''Ki gafarce ni UMMINA amma wallahi sam wannan maganar ba haka take ba,dan kuwa da idona na ganta yanzun,kawai dai a kwai wata manufa tata da yasa ta fad'a miki haka''....
Zuciyarsa fal b'acin rai dan shi kam wallahi shi kad'ai yasan me yake ji,taya ma za ace wani za ayi mata aure kuma cikin wannan satin amma kuma tana zaune cikin gidan bata koma nasu ba,tabbas shi kam ya san shiri ne da wata a k'asa...

Kalamai masu taushi UMMI ta shiga fad'a masa tana masa nasiha,har ya samu yaji zuciyarsa tayi masa sauk'i,kafin ya mata sallama ya fice daga gidan......


《《》》

Guri ta samu ta zauna bayan sun b'acewa ganinta,lokacin ne kuma muryan ASHNA ta dawo da ita daga kogin tunanin da ta tsunduma duk kan neman mafita ta wannan al'amarin dake shirin jagule mata.....

Tana shirin magana BB ya shigo da ganin yanayinsa ba sai ka tambaya ba za kasan yana tattare da matsananciyar damuwa....
Kallonsa MAMA tayi a tsorace take binsa da kallo danko ba k'aramin firgita tayiba da ganin yanayin nasa,kiransa tayi babu musu ya nemi guri ya zauna yana dafe kansa dake barazanar fashewa....

''SON me yake damunka,kaga kuwa yanda halittarka ta sauya lokaci k'ank'ani,maza sanarmin me yake faruwa''

''Babu komai''
Ya fata cikin cool voice nasa

''A kwai abunda kake b'oyewa SON''

''Babu fa,kawai ina jin headache ne''

''Eyyahh!Allah ya sawak'a maza ASHNA duba kawo masa magani idan ya sha sai ya kwanta ciwon zai sauka''

A zuciyarsa yake fad'in
''Tabbb!ai duk duniya yanzu kam ciwona baida maganin da ya wuce jin gaskiyar maganar da KHALEEL ya fad'amin''

''Wace magana kenan SON?''
MAMA ta tambaye shi,sai lokacin ya d'ago baki ya sake, kenan a fili yayi maganar ko me?

''Babu komaifa MAMA''

''Toh shi kenan ai kai kam dama haka kake da masifar zurfin ciki ba a tab'a gane kanku kai da ZUHRA sai kuyi tayi wata rana sai ciwo ya hallakaku''
Shi kam kallonta kawai yake ya kasa magana,harara ta cilla masa shi abun na MAMA wani lokacin har dariya yake bashi,sai dai wannan lokacin babu halin yi saboda baya cikin mood en da zai yin......

''Ko ka fad'a ko kada ka fad'a magana KHALEEL ya fad'a maka kan waccan yarinyar nasan dai bazai wuce haka ba,to wannan maganarma ba mai yiwuwa bace,dan ko na fad'a musuma aurenta za ayi a garinsu cikin satin nan''
Maganarta ta k'arshe ce ta dakatar da shi daga nutsuwar da ya fara samu,da sauri ya kalleta da jajayen idanunsa
''Dagaske MAMA?''

Yanayin da ya mata tambayar yasa ta tsaya tana wani nazari a kan fuskarsa,shi kuma ganin ta k'ureshi da ido yasa ya tashi ya bar wajen ba tare da ya sake kallon kowa cikin parlorn ba....

ASHNA ce ta kalli MAMA
''Kin gani ko MAMA dama wallahi na fad'a miki akwai abunda yake nufi da yarinyar can,tun ranar da ya dakeni akan maganar da naji ZUHRA sunayi da ita,Allah MAMA kada ki barima wannan abun kunyar ya faru.....
Numfasawa tayi tana kallon ASHNAR tana kad'a mata kai ba tare da ta furta komaiba ta bar parlorn.....

《《》》

Tun da ya fita ya barta take tunanin maganganunsa....
Wane dalili ne zai sa HAJIYA MURJA tayi mata k'arya kan wannan maganar,tunani iri daban-daban sai bijiro mata suke wanda ta rasa amsar su....

Idan ko abunda KHALEEL ya fad'a mata haka yake tabbas akwai manufar da yasa HAJIYA MURJAN tayi mata haka,sai dai koma mene ne ita ta sani,babu damuwar komai a ranta ta kauda tunanin wannan lamarin tana barin parlorn.....

《《》》

Shigowansa bed room en ya kwanta yana pacing ceiling...
Ta wani b'arin na zuciyarsa yana jin nutsuwa na saukar masa,sai dai kuma ta wani gefen yana jin tsoro wanda ya rasa dalilinsa,yana wannan tunanin bacci ya d'aukesa.....

《《》》

Can ta k'ule a bed room enta,number HAJIYA LAURA ta shiga kira,bugu biyu aka d'auka,a daddafe ta tsaya suka gaisa,aiko nan ta shiga koro mata jawabai na abunda ke shirin faruwa,yanayin da ta ga KHALEED a yanzun,da maganar da UMMIN KHALEEL ta zo mata da shi,bata rage mata komaiba ta sanar da ita......

Dogon ajiyar zuciya ta sauke,tana fad'in
''Ni kam na rasa me yaran nan suka gani jikin k'aramar yarinya da suka rud'e haka,kome take da shi ai muma y'ay'anmu nada''

''Uhmmm!HAJIYA LAURA kenan kawai dai ayi sha'ani(wai akace na birni ya zagi na k'auye),wallahi dan baki ga yarinyar bane,ni kaina yarinyar na bani tsoro duk lokacin dana kalleta,bama kamar yanzun a hakama wollahi bata fita ko ina nasan da na wajenma haka za suyita biyota mukuma namu suna jibge a gida (uwa ragunan layya)''

''Bari ke dai maganinsu za muyi cikin lokaci kad'anma kuwa,amma ki bar komai a hannuna,duk abunda ake ciki zan sanar miki zuwa dare''....

Da haka sukayi sallama,wani murmushin mugunta tayi tana bin wayan da kallo.....



Suna gama wayan ta shiga contact enta wani number tayi dialing,tana yin ring aka d'auka

''Allah ya taimaki HAJJAJU''

''Ammmm!BIGGY ba lokacin wannan wasan yanzun so nake kayi maza ka zo ina son ganinka''

''An gama ranki shi dad'e......
K'it ta datse kiran.......

In less-than fifteen minute's ya k'araso gidan cikin wani k'aton jeep black colour,baka iya hango komai na cikinta,motan na gama tsayuwa aka bud'e back seat na motan,wani zabgegen mutum ne ya fito kakkaura,da ganinshi kaga manyan basawa....

Cikin gidan ya nufa fuskarsa babu annuri a samanta,yana shiga y'ar aikinta dake parlor ya kalla yana fad'in
''HAJIYA fa''

''Tana ciki barin kirata''
Ta mik'e da sauri ta nufi hanyan d'akinta

''HAJIYA kinyi bak'o''

''Ina zuwa''
Ta fad'a ita kuma yarinyar tayi waje,bayan yarinyar ta biyo tana tafiya irinta hamshak'an mata,a tsaye ta tarar da shi ya juya baya
''Yawwa BIGGY aiki ne zan sa ka,amma nasan ba mai wahala bane a irin aikinku,a kwai yarinyar da nake son ku d'auke nisanta nake so kuyi da ita daga garin nan,koma inane ku kaita ba ruwana,wannan shi ne aikin''

Wata mahaukaciyar dariya yayi saboda raina aikin da yayi
''Yo HAJIYA wannan aiko yarana za suyi ba sai niba''

''Nasan da haka BIGGY ai shi yasa bana wasa da lamarinka,zan turo maka address na inda gidan yake''

''An gama,sai na jiki''
Da haka ya sa kai ya fice....

Yana tafiya ko ta tura masa komai,take kuma ta kira HAJIYA MURJA
''Toh na gama nawa sauran aiki yana hannunki,duk yanda za ayi anjima bayan Maghreb ki aiketa,zan miki bayani bayan kinyi hakan''

Tana gama fad'in haka ta kashe wayan,tana wani makirin murmushi........


*7:30pm*
KHUBRA ta shigo parlorn HAJIYA MURJA ita kad'ai ta tarar a parlorn,wani leder bak'i ta mik'o mata k'unshe da wani abu da ni kaina ban san mene a ciki ba,amsa tayi kafin HAJIYA ta soma magana

''Maza karb'i wannan kije waje zaki ga wani a bak'in mota ki kai masa injini''

Cike da ladabi ta amsa,har ta mik'e ZUHRA ta fito daga corridor en bed room nasu,kallon KHUBRAN tayi itama tana kallonta tana d'an murmushi kamar wanda basu saba ganin junaba suka k'urawa juna ido,fitowan BB ta waiga ta kalle shi,rana ta farko kenan da ta k'ure shi da kallo a iya zamanta a gidan,tsananin fad'uwa taji gabanta yanayi,a hankali ta waiwaya za ta fita,haka kawai taji idanunta sun kawo ruwa,da sauri ta sa hannu ta goge...

''SIS tsaya na rakaki''
Bata jira amsanta ba ta biyo bayanta,da sauri ta rik'e hannunta har suka fita daga gidan,KHUBRAN ce ta k'arasa kusa da window en motern tayi knocking,ZUHRA kuma tana jikin get,k'ofan aka zuge....

Gaisheshi tayi duk bashi da kad'ai ne a motanba,amma ita kam shi ta gani ta mik'o masa abunda ke hannunta aiko take ya mik'a hannu kamar zai amsa kawai ya fizgota cikin motan take ya datse k'ofan suka figi motan a 360...............................




*_~TEAM KHUBRA~_*



*_REAL SMASHER._*🤞🏻😘
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹





*©®2018*
*11/ʍɑվ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*

_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~________________________~*
_Ga masu buk'atar son kasancewa da group na *Y'AR GARUWA* za ku iya yin joining ta hanyar amfani da wannan link en,saboda gujewa had'uwa da maza,mata zallah dan Allah👏..._
👇
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EvdAvnFbBaX2BBMAwCCH4E
*~________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._





*2⃣6⃣*




*B*akinta da hancinta ya danne da wani handkeey take ko ta sulale uwa matacciya....
Ganin abunda ya faru yasa ZUHRA dake tsaye matsowa da gudu kuma ta hau natsowa kusa da motan...
Cikin wani razanannen murya ZUHRA ta shiga k'wala kiran sunan KHUBRA wadda tuni motarsu har ta b'ace daga line en.....

Faruwar hakan ke da wuya ta dawo da gudu ta shiga gidan babu kowa cikin parlor sai BB dake shirin barin gurin shima,a rud'e ta k'arasa kusa da shi fuskanta duk ya gama yin kacha² da hawaye,chakumoshi tayi tana kuka take fad'in
''Sun tafi da ita dan Allah YAYA karka bari su tafi da ita''

Gaba d'aya kalamanta sun gama rud'ashi,ya rasa ganema inda ta dosa,a hankali ya shiga girgizata dan kam ya gama fuskantar a kwai matsala
''Su waye ne kam,kuma waye suka tafi da ita?''

''YAYA KHUBRA sun tafi da ita,YAYA za su cutar da ita,please karka bari su gudu da ita''

Sunan KHUBRA da ta ambata shi ya masifar d'aga masa hankali,take ko ya sake ta yayi hanyan fita daga gidan,da gudu ta biyo bayanshi,sai dai ko da ya fita babu ko da k'urar motan bare yasa ran ganin ita kanta motan,tsayawa yayi ya dafe kansa baya ga *''INNALILLAHI WA-INNA ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNIY FIY MUSIBATIY WA-AKLIFNIY KHAIRAN MINHA''* babu abunda yake fitowa daga bakinsa sai wannan,wani sabon yanayi ya tsinci kansa a ciki,sam ya kasa magana fuskarsa lokaci guda har ta sauya kammani....
ZUHRA dake tsaye kusa da shi ko har yanzun banda gunjin kuka babu abunda take,kallonta kad'ai ya iya yi,kusa da ita ya matso yana son tambayanta sai dai kalmomin sun mak'ale a iya mak'oshinsa.....

Matsawa yaga ZUHRA na yi har dai² gurin da motan su BIGGY ta bari,takalman KHUBRA ta d'ebo wanda garin kokawar sata a motan suka watse a kasa,rik'esu tayi k'am ta rungume tana ta faman kuka,gwanin tausayi haka take kukan babu mai rarrashi....

Kusa da ita ya dawo hannayensa yasa akan sholders enta
''Pleasee!ya isa haka sisnah waye ya sa ku fito a daren nan?''

''MAMA ce ta aikomu''

Katseta yayi dan ko sunan kad'ai da ta ambata sai da gabansa yayi mugun fad'uwa,a zuciyarsa ya furta
''Ko me ya sameki tabbas da sa hannun MAMA a ciki,amma me yasa za ta aikata mata haka?",rashin amsa ya sashi dakatar sa tunanin,dan ko ba lokacin tunani bane,gefe suka sake komawa cikin low voice yake mata magana,ammafa hankalinsa baya tare da shi

''SIS abunda nake so dake ki dena kukan nan haka,kuma koda mun koma gida kada ki nuna damuwa kan abunda ya faru,har sai mun gano gaskiyar wanda ya aikata hakan''

''YAYA ai babu wanda ya aikata komai face MAMA''

Duk da ya sani da sauri ya dakatar da ita
''A'a SIS ba a saurin yanke hukunci,mu jira mu gama bincike tukun kin ji ko?''

Kai ta kad'a masa,hannunta ya ja suka kama hanyar komawa cikin gidan suna tafe yana bata baki kan kada ta kuskura ta nuna damuwa ko da anzo ana maganar a ganta....
A hanyan suka rabu shi ya nufi corridor da zai sada shi da bedroom ensa,suna tafe kowa zuciya babu dad'i kamar majinyata haka kowa ya shiga bed room ensa.....
Daren ranar kam a b'angaren ZUHRA da BB babu wanda ya iya cikakken bacci,gani suke kamar an had'e musu darare arba'in dan ko har fatan wayewar gari suke.....

《《》》

Tun bayan barinsu line en basu tsaya ko inaba sai k'auyen ZAKIRAI dake cikin garin kanon dabo,da yake dare ya soma yi sosai kuma suna son komawa dan ko hanya suke shirin d'auka zuwa garin kaduna,dai² kasuwarsu dake gefen hanya suka perker,sai da suka duba suka tabbatar babu kowa da yake ganinsu kafin suka kinkimota daga cikin motan,k'asan wata rumfa suka shimfid'eta tare da sanya mata ledan da ta fito da ita a tsakanin hannayenta,juyawa suka yi da mugun gudu suka bar gurin,yayinda KHUBRA ke baccinta peacefully,ko sanin inda kanta yake bata yi ba.....

Sai da gari ya gama haske mutane nata hada-hadar kasuwanci sannan ta farka,nan ta shiga k'arewa ko ina kallo,can ta kalli kanta sai a lokacin ta iya tuna abunda ya faru da ita a jiya da dare,take ko wasu zafafan hawaye masu k'una suka shiga sakko mata,ta jima tana kuka uwa baza ta dena ba,da k'yar ta mik'e ta nausa cikin kasuwar k'afarta ko takalmi babu,ita dai har yanzun tana rungume da wannan ledar.....
Yunwa ce ta fara damunta take ko ta sake sakin wani sabon kukan,tuna yadda rayuwarta ke garawa bisa doron K'ADDARA,zuciyarta fal addu'ah ta neman agaji daga mahaliccin sammai da k'assai,a hankali ta ware ledan dan duba abunda ke ciki dan kam ita tunanin yasarwa take,kud'i tayi arba da shi y'an one thousand sababbi,take ko tayiwa Allah godiya....
Guda ta zaro ta shiga bulayin neman abunda za ta karya,mai k'osai kad'ai ta samu aiko take ta tsaya sai dai gurin akwai yalwar mutane dake faman bin layi....
Kallo ne ya koma sama (wai akace shaho ya d'auko giwa) duk inda ta gifta sai dai kaga idanun mutane a kanta,bama kamar gurin mai k'osan da take tsaye uwa wacce aka dasa,har lokacin k'afafunta babu takalmi,tana nan tsaye har layi ya zo kanta mik'a kud'in tayi tana jiran a bata ba tare da ta fad'i adadin na yanda za a bata ba,kanta a k'asa ta kasa kallon kowa zuciyarta ko tarin k'unci ne a cikinta bama kamar yadda take fama da tunanin ZUHRA sahibarta,k'awarta,take ko wasu sabbin hawayen suka sake sakko mata....

Mai k'osai tana tambayarta amma sam bata sanma me take yiba,ganin haka yasa kawai ta auna mata,kafin tasa aka tab'ata,a d'an tsorace ta d'ago hannu tasa ta amsa tare da juyawa za ta bar gurin,chanjin da ta juyo da niyyar bata taga har ta yi gaba da sauri tasa wani yaro ya bi bayanta,d'an murmushi ta masa duk da tarin k'uncin dake cunkushe a zuciyarta ta amsa wash hawayen na dad'a sakko mata taci gaba da tafiya....
K'asan wata bishiya ta zauna jama'a nata kallonta amma sam hakan bai wani d'aga mata hankali ba,sai da ta tabbatar ta k'oshi kafin tunanin neman mafita ya fad'o mata....

''Ina ya kamata na dosa ni da ba ko ina na sani ba?''

Babu inda ta sani bare ta ce ga hanyar gidansu,ko da canma ba fita take ba bare daga baya da ta dawo wani gari na daban,tana zaune ta had'a kai da gwuiwa tana tunani,wani mai kuran ruwa ya d'an tsaya a kanta
''Yarinya sannu ko''

Kallonsa kad'ai ta iya ba tare da ta iya magana ba,kamar mai nazarin wani abu take kallon gurin da take zuwa wani lokaci kuma ta sake kallon mutumin ji tayi ta aminta da shi take kuwa ta bud'e baki da niyyar yin magana.......

《《》》

Haka gari ya waye musu babu wanda yayi isashshen bacci idanunsu a soye,kasa fitowa suka yi su duka biyu....

Lokacin break yayi y'ay'an HAJIYA suka fito da niyyan break,sai dai suna zuwa suka tarar da gurin wayam babu komai,kowa sai tura baki yake gaba uwa shantu,suka nufi d'akin MAMA da niyyar yi mata k'orafi....

''MAMA kinga fa ba a had'a break ba har yanzun''
Abunda ya fito daga bakin FATAHIYYA kenan da take kan gaba gurin shiga d'akin

K'wak'walwar MAMA ta tafi yajin aikin ina kuma KHUBRAN ta shiga (ni da nake gefe nace kajimin y'ar cin).........

Ta jima d'age da kai tana tunani,kafin ta soma tunanin me ya faru da ta aiketa jiya?

''Kuyi hak'uri kunji,maza kuje ku sha ko tea ne kafin na fito''
Fita suka yi suna tura mata baki,sai k'unk'uni suke,suka nufi dinning area,flask en suka kinkimo a tunaninsu a kwai wani abu cikinsa nan ko suka tarar da shi wayam shima,kuka kad'ai su HANEEF suka sa,wanda sanadin haka yasa BB fitowa fuskarsa uwa wanda bai tab'a dariya ba,wani kallo ya watso musu wanda yasa suka shiga hankalinsu ba tare da ya furta komai ba...

Cikin parlor ya kwanta idanunsa a rufe jijiyoyin kansa sun gama bayyana a fili,shi kad'ai yasan abunda yake ji a zuciyarsa,yanzun kam ko magana baya jin zai iya yi
''To amma ai bai kamata na ci gaba da zama ba yanzun,,,,,,,,me ya kamata nayi?''
Yayiwa kansa tambayar,saurin mik'ewa yayi ya koma bed room ensa,cikin abunda bai fi mintuna biyar ba ya fice daga gidan gaba d'aya.....

ZUHRA kam kasa fitowa ma tayi tana d'akinta,kuka take sosai tamkar wacce uwarta ta mutu,idanunta duk sun kumbure sun canja launi kan kukan da tayi,sai da ta ji cikinta tamkar babu komai ta fito da k'yar tana tafe tana bin bango har ta shiga kitchen...
Kallonta suka yi ganin yadda take bin bango,da ka suka tambayi juna sai dai babu amsa...

Kitchen ta shiga kallon gurin da KHUBRA ta saba tsaiwa tana aiki ta shiga yi,take wasu hawayen suka k'ara b'alle mata ganin babu KHUBRA cikin gurin da suka saba zama tare,sai da tayi kukan mai isarta da k'yar kuma ta iya dafa indomie a plate ta juye ta d'auka tayi bed room enta.....

Kallonta suka sake yi,coz tun tana cikin kitchen en suke jiyo k'amshi na tashi,gaba d'aya sun rashe suna jiran ta gama ta basu,aiko tana barin gurin suka shiga da sauri suna dubawa...
Wayam babu komai ciki haka suka janyo tsummokaran k'afafunsu suka fito,guiwoyinsu a sake....

《《》》

Fitarsu daga d'akin ta sauke wani gwauron numfashi,wayarta ta janyo ta shiga kiran HAJIYA LAURA...
Bata wani jima tana ringing ba ta d'auka cike da izza da k'asaita kamar d'iyar sarauta....

''Aiki yayi kyau mutuniyata,yanzun kam yaranmu sai yanda mukayi da su''...

''Ban fuskanci me kike nufi ba''
HAJIYA MURJA ta tambaya cike da zak'uwa da son jin labarin...

Take ko ta zayyane mata sawa tayi aka d'auke KHUBRAN daga garin,ta k'arashe zancen da fad'in
''Nasan yanzu kam tayi nisa da mu''
Wata dariya ta saki ta makiran mutane....

Sai lokacin hankalin HAJIYA MURJA ya kwanta tana fad'in
''Mun rabu da alak'ak'ai,jarababbiya aje can a k'arata''....

Tana sakin dariya itama,sun jima suna shirya makircinsu kafin suka yi sallama....




*_~TEAM KHUBRA~_*



*_REAL SMASHER._*🤞🏻😘
💠💠💠💠💠




*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*



🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*©®2018*
*14/ʍɑվ,2018*



*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹


_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*

_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~________________________~*
_Ga masu buk'atar son kasancewa da group na *Y'AR GARUWA* za ku iya yin joining ta hanyar amfani da wannan link en,saboda gujewa had'uwa da maza,mata zallah dan Allah👏..._
👇
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EvdAvnFbBaX2BBMAwCCH4E
*~________________________~*
🍟🍟🍟🍟🍟
🎂 *HAPPY BORN DAY*🎂
_OUR SURIKI *HASSAN ATK*_

🎊
🎉🎉🎉
_A birthday is just the first day of another 365-day journey around the sun. Enjoy the trip. *HAPPY BIRTHDAY*_



Please Login or Register in order to submit comment