Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

haɗa ido, tana shirin magana ya sa ɗan yatsansa akan bakinta yace, "Shiiii bari na duba na gani." Yana gama faɗa be jira cewarta ba ya ɗauki fitilar ƙwansu da ta kasance sabuwa dal da ita ya fita waje yana haske-haske.


🙄🙄🙄🙄🙄 Uban iya a dawo lafiya garin leƙe-leƙen idan ka kai kanka cen kai ka sani, ka fita ka bar Amarya Allah sa kar a gwada muku ɗiban albarka ba😂

Barkanmu da Juma'a🥰

_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._

[18/12/2021, 19:47] Ameera Adam🌚: 51...

Takawa yake a hankali yana haskawa musamman wuraren da ya fi jin tashin sautin muryar me kukan, sashen hanyar banɗaki ya nufa daga cen bayan bishiyar Tsamiya yake jin tashin kukan mace, kukan ba ƙaramin taɓa zuciyarsa ya yi ba dukda be san wacce take kukan ba amma ya tabbata kukan na fitowa daga ƙaraƙashin zuciyarta ne. Abu da tun bayan fitowarsa ta fara jin tsoro na neman mamaye zuciyarta. Fitowar ta ya yi daidai ta hango shi da ta yi ya lula cen, da sauri ta ƙwala masa kira amma be waiwayota ba har sai da ya zagaya wurin bishiyar. Zuwansa ke da wuya ya ji ɗiff kamar an yi ruwa an ɗauke ya nemi kukan da yake ji ya rasa, sai ma kukan tsuntsaye da ƙananan ƙwari da ke tashi a wurin, juyowa ya yi yana daɗa haskawa daga cen jikin bango ya hango kamar inuwar mace a zaune ta cusa kanta cikin ƙafafuwanta. Yana ƙarasawa ya nemi inuwar ya rasa. Ganin haka ya sa Abu ta ƙara ƙwala masa kira a karo na biyi don haka ya juya da sauri ya nufi wurinta. Yana zuwa ta ja hannunsa cikin ɗaki a ɗan tsorace take kallonsa ta ce, "Ya Saif yanzu fa dare ne wallahi tsoro nake ji, a daren nan za ka je wurin bishiyar tsamiya ana zaune ƙalau." Jinjina kai ya yi yace, "Na leƙa in gani ko yara masu ganin ɗaki ne aka bar wata daga ciki." Abu ta kwaɓe fuska ta ce, "Gaskiya ni tsoro nake ji wallahi." Aljihunsa ya shiga lalube zuwa cen ya zaro wani ƙullin magani yace, "Bari na aika a kawo mana garwashi dama Ammi ce ta bani garin maganin nan na turare ne." Yana juyawa zai fita zaraf Abu ta bishi saboda ta gama razana da kukan da suka ji da farko. Babu yadda ya iya haka ya wuce yana gaba tana biye da shi, wani Dogari ya kira ɗaya daga cikin Dogarawan ƙofa ya aika aka ɗebo masa wuta suna zuwa ɗaki ya turara musu sannan ya ɗauko kazar da ya kawo musu ta amarci, a hankali ya fara bawa Abu amma saboda kunya ta kasa karɓa ta ci. Sai da ƙyar ta iya gutsira ta ci gutsire biyu daga haka ta ce ta ƙoshi. Saif ɓata fuska ya yi sai da ta ga ransa ya ɓaci sannan ta saki jiki ta suka ci gaba da ci. Bayan gama ciye-ciyensu suka gabatar da sallar nafila tare da addu'o'i sannan suka wuce kan gado suka ya da zanzo. Saboda gajiya Abu tana kwanciya bacci ya yi gaba da ita, Saif kwanciya ya yi a gefenta ya fara ƴan juye-juye. Abu cikin bacci ta fara jin baƙon lamari daga wurin Saif, da farko yi ta yi kamar ba ta ji shi ba amma daga baya da ta ji lamarin na neman gagar kundila ta shiga neman alfarmar ya ɗaga mata ƙafa. Gabaɗaya Saif birkice mata ya yi tun tana magiya har bakin ta ya yi laƙwas.

(Bari mu wuce wurin kar na je na aiwatar da ɗiban albarka😂🤣)

Washegari Salman tun farar safiya ya miƙe ya faɗa banɗaki ya tsarkake jikinsa, be bi ta kan Safiyya ba dukda yadda ta galabaita ko motsin kirki bata yi saboda ko kaɗan Salman be bi da ita ta lallami ba. Kai tsaye cikin gidansu ya nufa yana zuwa aka fara jansa da tsokanar ango-ango. Fulani Maryama na ɗakinta ta jiyo su ba ta kai ga miƙewa ba ta ji Salman ya shi ga wurinta, da mamaki ta kalleshi don gari ma be gama wayewa ba ta ce, "Salman lafiya da farar safiya haka? Ko Jakadiya sammako ta yi muku?" Yana daga tsaye yace, "Zuwa na yi na gaya muku a tura a gyara waccen yarinyar, gaskiya fa yarinya ta yi ƙoƙari don lokacin da nake tuki sai da na so wuce ƙofar mazugal..." A hassale ta katse cikin ɓacin rai ta ce, "Kai baka da hankali ne Salman ni Mahaifiyarka kake gayawa haka? Saboda rashin mutumci."

Saif tun asuba ya taimakawa Abu ta gyara jikinta, ba ƙaramin tausaya mata ya yi ba, guntun tsaki ya ja ganin yadda zanin gadon ya yi da ya tuna dole sai ya ciro shi an shiga da shi cikin gida domin a tabbatar da amarya ta kai ƙimarta ko bata kai ba. Janye zanin gadon ya yi ya shimfiɗa wani sannan Abu ta hau ta kwanta ta koma bacci jikinta da ɗan ɗumi alamun zazzaɓi.


SHAFIN DAI NA SAN BA ZAI MUKU DAƊI BA😢😢😢 AMMA KUYI HAƘURI HAKA YANAYIN LABARI YAKE GABA ZA KU FAHIMCI DALILIN HAKA, KAR KU MANTA A DUNIYA BA KOMAI MUTUM YAKE NEMA KUMA YA SAMU BA.😢

_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._
[19/12/2021, 12:46] Ameera Adam🌚: 52


Jakadiya da zumuɗi ta nufi gidan Amaren don tabbatarwa idonta tsegumin abin da aka umarce ta, da sallama ta samu shiga ɗakin Safiyya. Da fululluka ta fara cin karo da alkyabbar Safiyya, da ƙafa ta shure su ta fara kyaɓe baki ta ce, "Ƴar nan sannu kin ji. Girman kenan muma duk da haka muka zo nan. Yoo Allah na tuba ku ai da girmanku tun da ga alama daga ke har Abu kun kai sha biyar-biyar. Mu kuwa fa mu da sha bibbiyu aka haɗa mu da ƙaratan mazaje ai ba muyi ma langwaɓewarku ba. Tashi mu gani." Safiyya miƙewa ta yi a hankali da sauri Jakadiya ta ja gefe tana dafe ƙirji, Safiyya sai rangwaɗar da kai gefe take saboda azaba. Jakadiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce, "A'a lallai Salman gara da Takawa ya hanzarta aka yi auren nan. Allah na tuba da an ƙara wani lokaci wataƙila muma ya fara kawo mana farmaki, dubi yadda ya yi wa yar mutane tambaɗar rashin imani. Kai Amma dai Maryama ta haifi Jarababbe, ko dan ai be yar a ƙasa ba saboda lokacin Maryama da Takawa har guduwa yake tana nemansa saboda Jaraba." Safiyya ta gaji da surutan Jakadiya a ɗan fusace ta ce, "Kin zo taimaka mini ne ko surutu kika zo yi mini, ko kuma in sa a kira wacce za ta taimaka mini." Jadiya ta harareta a fakaice ta ce, "A'a wa kuma za ki kira a wannan yanayin da kike ciki wacce ta wuce ni." Jakadiya na surutu tana gyara gadon, sannan ta taimakawa Safiyya ta gyara jikinta. Tana gama gyarawa ta shimfiɗa wani zanin gadon, jikinta zafi zau da zazzaɓi ta koma kan gadon ta kwanta saboda ba ƙaramin jin jiki take ba.

Jakadiya na gamawa ta wuce wurinsu Saif tana shiga ta tsaya a bakin ƙofa tana rangaɗa sallama, kasancewar ta ga takalmansa a bakin ƙofar. Saif ne ya fito yana ɗan murza idanu don shima baccin ya koma. Washe baki Jakadiya ta yi ta ce, "Allah ya taimaki Yarima, dama na zo ne domin na taimakawa Abu ta gyara jikinta sai kuma zanin gado da zan ɗauka, ka ga na matar Salman kai amma dai Salman an yi jarumin namiji, dubi yadda zanin gadonsu ya yi kaca-kaca da..." Cikin ɗaure fuska Saif ya ɗaga mata hannu yana faɗin, "Ban tambaye ki ba." Juyawa ya yi ya ɗauko mata zanin gadonsu ya miƙa mata yana jan guntun tsaki, yana shirin komawa ta ce, "Ai zan gyara Abu." Be juyo ya kalle ta yace, "Na gyara matata." Jakadiya ba haka ta so ba don ta so ta ga yadda Abu ta yi don ta ji daɗin isar da labari. Don haka ta ɗan tsuke fuska ta ce, "Amma ai ka san a ƙa'ida ni nake gyara duk wata sabuwar amarya." Saif ya kuma tamke fuska yace, "Ni na ɓata abata kuma na gyara ta." Yana gama faɗa ya shige ɗaki. Jakadiya haushi ya kuma turniƙeta ta juya ta mita da ƙunƙuni. "Eh ai ya nuna mini idonsa ya buɗe wai shi ya yi sabon aure, ai wallahi kamar kumbo kamar kayanta yaron nan babu abin da ya bari na Zaliha. Duk mugun halinta ya kwashe tsaf.


Me babban ɗaki gabaɗaya ta shiga damuwa sakamakon ciwon Maryo da ta tashi da shi, wannan karanma ranga-ranga aka ɗauke ta zuwa asibiti. Sai da ƙyar Allah ya bada iko aka samu damar shawo kam ciwon nata. Ba ƙaramin faɗa likitan ya yi musu ba saboda yace tana cikin matsananciyar damuwa shi ya sa ciwon nata yake yawan ta shi akai-akai. Babu yadda suka iya a wannan karanma amsawa Likitan suka yi sannan suka ci gaba da bata kulawar da ta kamata. Ko kaɗan Sarki Abdallah be sanarwa da Fulani Fahima halin da Maryo take ciki ba, don ya san za ta shiga cikin matsananciyar damuwa.

Lokacin da aka kai zannuwan gadon su Abu Inna Habi ba ƙaramin farinciki ta yi ba don ko ba komai, Abu ta kankaro mata daraja da ƙima a idon mutane. Sai dai tun daren ranar idanunta ya gagara bacci saboda miyagun mafarkan da ta dinga yi Maryo, wanda abun ba ƙaramin tsoro ya bata ba. Haka kawai zuciyarta take raya mata akwai damuwa saboda wannan mafarkan da take yi har sun fi na kwanakin baya muni. A daddafe take cinye kwanakin don ganin ƴan biki da sauran ƴan uwa da suka halarci bikin sun watse domin ta je ta tunkari Sarki Aminullah da maganar bakinta ayi wacce za a yi a ƙare, don ta ga ji da dakon zunubin da take yi ba dare babu rana.


Bayan sati biyu da biki amare da angwaye ba ƙaramin murzar amarci suke yi ba cikin so da ƙauna. Safiyya babu yadda ta iya har ta fara sabawa da halin Salman saboda tuni zuciyarta ta afkawa soyayyarsa. A ɓangarensa shima ya ɗan rage wasu abubuwan yana ɗan lallaɓata wurin mu'amala ba kamar baya ba da yake yi mata ta ƙarfi da yaji. Sai dai babu wata hira me daɗi da take shiga tsakaninsu. Tsayawa gayawa me karatun soyayyar da ake ɓarza a gidan su Saif ɓata lokaci ne, amma a wannan lokacin ne Abu ta tabbatarwa zuciyarta babu wata ƴa mace da za ta iya samun gurbi a zuciyar Saif. Wani abun idan ya yi mata ita take jin kunya ba shi ba, saboda Saif gawurtaccen namiji ne a fagen iya soyayya, har mamaki take idan ya yi wani abun domin a baya ta ɗauka yadda yake shiru-shiru ta za ci babu wata duniyar gajimare da ya sani.

(Maryo fans 😂 na san ji kuke kamar ku ɗebe mini albarka😂)

Sarki Aminullah ba ƙaramin ɓacin rai ya shiga ba lokacin da ya gama jin zantukan da Inna Habi take gaya masa, kallonta ya yi ya ga yadda take zubda hawaye sai kuma ya ji ta bashi tausayi musamman da ya tuna yadda Maleek ya kafe kai da fata akan Maryo matarsa ce. Wayar salularsa ya sa wani Dogari ya ɗauko masa nan take aka danna lambar Sarki Abdallah, yana ɗagawa murya babu walwala Sarki Aminullah yace, "Sirikina ina buƙatar ganin yarinyar nan Maryo wacce Maleek yace matarsa ce, ina buƙatar ganinta cikin gaggawa daga yai zuwa gobe." Yana gama faɗar haka ya datse kiran.



_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._
[20/12/2021, 13:01] Ameera Adam🌚: 53...



*Amun afuwa pls saboda na ɗan yi kuskure wurin rubuta Sarki Aminullah ya ɗaga waya ya kira Sarki Abdallah, sai daga baya na farga wallahi idan kun duba yanayin shekarun labarin a lokacin babu wayar sadarwa. Yanzu mu barshi akan Sarki Aminullahi ya aikawa da Sarki Abdallah da takarda akan yana buƙatar ganin Maryo ciki gaggawa. Amun afuwa da wannan kuskuren*🌚

Sarki Abdallah jikinsa ne ya yi sanyi lokacin da ya gama karanta wasiƙar da aka aiko masa daga masarautar Kano, Fulani Fahima a lokacin tana zaune a gefensa ta ce, "Allah ya taimake ka wata muhimmiyar magana aka faɗa?" Kallonta ya yi yana nannaɗe wasiƙar hannunsa yace, "Sirikina ya buƙaci a mayar da Yarinyar cen cikin gaggawa saboda muhimmiyar magana. Hasalima ya tabbatar mini da cewar ba matar Maleek bace. Ba mayar da ne damuwa ta ba, babbar matsalar ta yadda za mu fuskance su da yanayin da yarinyar nan take ciki, kuma shin wani abu ya taɓa shiga tsakanin Maleek da ita? Kuma wanne jawabi za mu yi wa Me babban ɗaki wanda za ta gamsu?" Fulani Fahima ba ƙaramin daɗi ta ji domin dama ta jima da son haka, saboda ta san ko ba daɗe ko ba jima dole sai kowa ya san halin da Maryo take ciki don haka take ganin babu fa'idar ɓoyewa. Gyara zama ta yi ta ce, "Allah ya taimake ka ina ganin wannan ba abin damuwa bane. Mu fito mu gaya musu gaskiyar yadda ciwon ya same ta, ita kuma Me babban ɗaki sai mu nuna mata rubutacciyar samfefar da aka aiko. Wata ƙila ma damuwar da yarinyar nan take ciki zai yi mata sauƙi idan ta koma hannun mariƙiyyarta. Amma ina fargabar Allah ya sa babu wata mu'amala da ta shiga tsakaninsu." Jinjija kai yake cikin gansuwa da jawabanta shi ya sa yake ƙara ƙaunarta saboda duk wani abu da yake neman ɗaure masa kai ita take warware masa. Ba'a ɗauki lokaci ba ya sanarwa da Me babban ɗaki halin da ake ciki, da farko fitittike musu ta yi sai daga baya da ya lallameta sannan ta amince. Amma tun a lokacin da fara hawaye na rabuwa da Maryo saboda ba ƙaramin sabo suka yi ba, gabaɗaya kayan Maryo ta shiga haɗa mata tana haɗawa tana share hawaye gwanin ban tausayi. Ita kuma Maryo da take kwance akan ƙaramin gadon ƙarfe bata san abin da yake faruwa ba.

Ɗan aiken Sarki Aminullah yana zaune yana jiran amsar da zai koma ya isarwa da shugabansa saƙon da aka ba shi, Sarki Abdallah ne ya umarci Dogari Lurwanu da ya rubuta amsar wasiƙar kamar haka.

_Assalamu alaikum Sirikina fatan alheri a gare ka da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya. Na riski saƙonka daga hannun Dogarinka Umaru, na yi matuƙar mamakin jin yadda wannan al'amari ya kasance, amma ina me baka haƙuri babu a dadi bisa ga wata larura da ta faɗawa wannan yarinya da ka aiko da takadda akan ta. Kasan duk abin da ya samu bawa rubutacce ne daga Ubangiji, kuma ba mu ɓoye maka saboda wata manufa ba sai don muna son nema mata magani na ɗan wani lokaci. In sha Allah za mu dawo da ita hannu da hannu da yardar Allah idan Allah ya kaimu rana ita yau me zuwa._

_SAƘO DAGA MASARAUTAR ADAMAWA_

Tambarin Masarautar Adamawa aka buga a jiki tare da naɗe farar takardar samfefar wacce aka yi rubutun ajami, aka bawa Dogarin da ya kawo takardar tare da guzurin da zai yi a hanya. Maleek tun da ya ji labarin tafiyar Maryo hankalinsa ba ƙaramin ta shi ya yi ba, dukda ya san ba matarsa bace amma idan ya kalle ta tana rage masa kewar Shukransa. Yana zaune a ɗakin Me babban ɗaki ita kuma tana lallaɓewa Maryo kanta, ya zuba mata ido yana tuna irin rayuwar da suka yi da ita da abubuwan al'ajabin da ta dinga yi kafin faruwar lalurarta, murmushin yaƙe ne ya suɓuce masa yana jin kewarta a zuciyarsa. Kallon ɗan bakinta da take cunowa gaba ya yi wanda da alama zafin kitson ne ya sa take ɗan tura baki don dai babu bakin magana ne, ta shi ya yi tsam ya ƙarasa wurin Me babban ɗaki yace, "Tsohuwa wannan kitson fa takura mata yake dubi yadda goshinta duk ya fito a bari sai an jima a ci gaba." Ya faɗa yana ƙoƙarin janye Maryo. Duka ta kai masa a baya ta ce, "Matsa mini daga gabana sakarkaru idan na biye ta yarinyar nan kanta a haka zai lalace dubi don Allah yadda fuskarta ta yi kyau amma da ta bar kai kamar na maza. Dududu kitson ƙwaya nawa ne ƙwaya takwas ne fa, na ƙi na sake ta ba zan saki kannan ba sai na gama." Maleek ficewa ya yi daga ɗakin yana mita don ya ga gaban goshin ta ya yi jawur.

Lokacin da Saƙon Masarautar Adamawa ya samu Sarki Aminullah duk sai ya ji babu daɗi, dukda ya san komai muƙaddari ne amma yana jin kunyar a dawo da ita ga mariƙiyarta domin ta sha yi masa zarya amma ya ƙi bata dama. Lokaci ɗaya ya ji be kyauta ba a gefe ɗaya kuma yana fargabar irin larurar da za su yi tozali da ita wacce aka ce Maryo na ɗauke da ita.

Kwanci tashi babu wuya a wurin Allah, kwanakin da Sarki Abdallah ya ɗiba sun cika. Sun shirya tsaf daga Me babban ɗaki, Maleek, Fulani Fahima, Maryo da Sarki Abdallah su kaɗai suka shirya tafiya don Fulani Fahima cewa ta yi ba za ta tafi da autarta ba ta zauna a wurin su Fulani. Duk budurin da ake Maryo bata sani ba sai dai jikinta yana bata akwai wani wuri da suke haramar tafiya. Maleek ne ya taimaka mata ta shi ga rumfar keken dokinsu wanda aka tanadarwa Me babban ɗaki amma ta ce fur ita da Maryo za su shiga, ganin haka ya sa Maleek shima ya shiga keken dokin na su Maryo. Fulani Fahima da Sarki Abdallah a wani keken dokin daban. Keken dokin Dogarai ne a gaba da suke ɗauke ba bindigogin farauta na sassaƙen itace, saboda koda za a samu farmakin wata dabbar, sai na su Me babban ɗaki yake bin su sannan na Sarki Abdallah yake biye da na su Maryo sai kuma keken dawakai biyu a baya da suke gadin su Fulani Fahima. Tafiya suka yi me nisan gaske sai da suka shafe wuni guda da rabin rana sannan suka ƙarasa Masarautar Kano me ɗumbin albarka. Maryo tun da ta ji tafiyar ta ƙi ƙarewa jikinta ya bata wataƙila Masarautar Kano suka nufa idan kuma ba cen bane to wani wurin ne me nisan gaske.

Lokacin da suka sauka a ɓangaren Fulani Maryma suka sauka saboda duk abun Fulani Maryama tana matuƙar karrama duk wanda aka ce mata ya fito daga ɓangaren Sarki Aminullah ne, a wani ɓangaren kuma saboda ace ta fi sauran matan Sarki haba-haba da mutane ya sa take washe baki kamar wacce aka yi wa kyautar kujerar hajji. Me babban ɗaki tana riƙe da hannun Maryo har suka shiga ɗakin Fulani Maryama, shigarta ɗakin ke da wuya ta ji kanta ya yi wani irin sarawa, har sai da ta hannu ta ɗan dafe gefen kanta. Alamun zirarowar jini ta ji a hancinta, da sauri ta ɗauko ƙyallen wurin Saif ta fara gogewa. Fulani Maryama sai umarni take bayarwa ana jido kayan ciye-ciye da shaye-shaye ana direwa a gabansu. Tun da ta ƙyalla ido ta ga Maryo haka kawai ta ji gabanta na dukan uku-uku, suna haɗa ido da Maryo ta ji cikinta ya hautsine ita kuwa Maryo bata san ma me take yi ba. Ga wanda ya ga Maryo ba zai taɓa tsammanin tana da matsalar ido ba, saboda idanunta a buɗe suke tar za ta yi ta ɗan waige-waigenta kamar tana ganin abin da yake faruwa. Fulani Maryama bayan sun gaisa da su Me babban ɗaki tana son ta yi maganar Maryo tana jin tsoro ga shi ta ga sai kallonta take suna haɗa ido. Wani tsoron Maryo ne ya ɗarsu a zuciyarta haka dai ta ja bakinta ta tsuke. Inna Habi tun da ta ji shigowarsu Fulani Fahima ta kasa zaune ta kasa tsaye, daga cikin labulenta ta hango wucewar Maryo. Ta ga ta daɗa haske sosai sai dai ta ɗan rame hakan ne ya sa tsayinta ya ƙara fitowa sosai. Dabara ce ta faɗo mata don tana san ta shiga wurin Maryo ta san da zamanta a gidan tun da lokacin da Maryo ta tafi ba su koma sashen matan Sarki ba. Nakiyar da ta yi wa Fulani Maryama ta ɗauka ta nufi ɗakin bakinta ɗauke da sallama ta shiga, sai da ta ajiye musu a gabansu ta koma gefe ta fara gaishe da Me babban ɗaki. Tana shirin gaishe da Fulani Fahima suka ji an aiko da kiransu daga Fadar Sarki Aminullah. Inna Habi kallon Maryo take da mamaki duk sai ta ji ta muzanta don sun haɗa ido da Maryo ya fi a irga amma ba ta ga alamun za ta yi mata magana ba bare ta nuna ta santa. Jiki a sanyaye ta miƙe za ta fita Baiwar da ta isar da saƙon kiran ta tabbatar da ana nemansu har Inna Habi. Amsa mata suka yi sannan suka ta fice domin sanarwa da Dogarin da Sarki Aminullah ya aiko. Fulani Maryama ba ta so yadda aka ware ta ba amma ta tabbata koma meye akwai wani muhimmin abin da ya kawo su. Saboda da gama bikinsu Salman ko wata guda ba a yi ba kuma daga Fulani Fahima har Sarki Abdallah sun halarci bikin.


Gabaɗaya suka hallara a cikin fadar Sarki Aminullah, Sarki Aminullah tare da Sarki Abdallah suna kan mazauni ɗaya. Cikin fadar iya waɗannan mutanen ne kawai sai Dogarawan da suke tsaron bakin ƙofar. Sarki Aminullah ne ya buɗe zaman nasu da Addu'a sannan ya gaishe da Me babban ɗakin cikin girmamawa. Kallon Inna Habi ya yi ya kalli jama'ar wurin ɗaya bayan ɗaya yace, "Maƙasudun wannan taron kusan za mu iya cewa ke ce kika jagorance shi, shin za ki iya sanar da mu gabaɗaya domin jin ta bakinki don sauran su tabbatar daga gare ki maganarnan ta fito." Inna Habi ta share ƙwallar idonta ta ƙara sanar musu da cewar Maryo dai ba matar Maleek bace hasalima budurwa ce ko auren fari bata taɓa yi mata ba. Jinjina kai gabaɗaya suka yi saboda labarin ba sabo bane a wurinsu tun da tuni an sanar da su a baya. Sarki Abdallah ya numfasa ya kalli Inna Habi yace, "Baiwar Allah amma kin san da haka me ya sa kika bari har muka tafi da ita, yanzu da wani abu ya shiga tsakaninta da yaron nan ya kike gani lamarin zai kasance, tun da mu gabaɓaya mun san matarsa Shukra kuma duk wanda ya san Shukra idan ya ga Maryo ba zai ce ba ita bace." Inna Habi jiki a sanyaye ta gaya musu dalilinta a lokacin iƙirarin cikin jikinta da Maryo take yi na Saif da kuma yadda ta ga Maleek ya dage akan Matarsa ce, ita a ganinta idan Maleek ya tafi da Maryo ba za a fahimci cikin jikinta ba shege bane. Gabaɗaya jikinsu sanyi ya yi musamman Sarki Aminullah, Sarki Abdallah ya kuma kallonta yace, "Ma sha Allah da kika fahimci kuskurenki kuma ba ki ji tsoron komai ba kika faɗi gaskiya, don kuskure kam an yi shi amma hamdalar da za mu yi da babu wani abu da ya haɗa Maleek da Maryo tun da na tuntuɓe shi tun a gida. Amma a yanzu muna so ki sanar da mu tsakaninki da

Please Login or Register in order to submit comment