Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Fulani Maryama take yi wa Sarki Aminullah. Shi kansa Salman sai ya ji ba daɗi dukda matsanancin haushinta yake ji kasancewar ta yi masa iyaka da hayewa karagar mulki, amma ko sama da ƙasa za ta haɗe baya jin zai iya barwa Saif kujerar Masarautar Kano.

Sarki Aminullah ya kalli Fulani Maryama yace, "Za mu yi miki alfarmar ci gaba da zama a cikin ɗakinki amma muddin muka lura da hatsaniya ko tashin hankali tabbas za mu ɗauki mataki a kai. Abin da kika aikata kin cancanci zuwa gidan horo amma darajar 'ya'yan dake tsakaninmu ba za mu iya aika ki ba domin idan mun yi haka kamar mun tozarta kanmu ne." Sarki Aminullah na gama faɗar haka ya kawo ƙarshen zaman taron tare ta yin nasiha mai ratsa jiki da jan kunne akan kiyaye dokokin Ubangiji. Kafin wani lokaci tuni fadar ta yi tsit kowa ya watsa cikin gida aka samu zancen tattaunawa. Masu kwashewa Fulani Maryama na yi masu yi mata addu'a suma suna yi. Kafin tashin taron sai da Sarki Aminullah ya ƙara jaddada cewar Salman na nan a matsayin Ɗansa kuma ko da wasa ya ji wani zance na ɓilla zau ɗauki mummunan mataki a kansu.

_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI_
[30/01, 10:57] Ameera Adam🌚: 71...


Masarauatar Kano.

Abin duniya goma da ashirin ne ya haɗewa Sarki Aminullah domin idan yace ba ya son Maryama ya yi ƙarya, ita ce matarsa ta fari uwar 'ya'yansa ya bata dukkan yarda amma ta rasa da me za ta saka masa sai wannan miyagun ayyukan, tabbas lamarin akwai cin zuciya, juwa ce ta fara ɗaukansa don haka ya nemi wuri ya zauna. A yanayin da yake yana buƙatar mai tausarsa ta bashi baki amma wa zai kira? Gani yake duk wacce ya kira za ta ga ya yi kiranta ne saboda abin da ya faru. Yana nan zaune Fulani Zaliha da sauran matansa suka shiga kamar sun san abin da yake ransa. Fulani Bilkisu ce ta fara magana kasancewar ita ce matarsa ta biyu ita ce babba tun da babu Fulani Maryama.

Ruwa mai sanyi ta ɗebo masa na cikin randa ta miƙa masa, bai musa mata ba ya karɓa yasha sannan ta fara da cewa,"Allah ya taimake ka ya baka yawan rai Sarki mai adalci Sarkin talakawa Sarki mai karamci da mutumci." Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya gyaɗa mata kai ta ci gaba da magana, "Allah ya taimake ka a madadina da na iyalanka baki ɗaya muna ƙara jajanta maka da baka haƙuri bisa abin da ya faru." Kamar jira yake murya a shaƙe yace, "Me na yi wa Maryama da za ta saka mini da haka?" Fulani Zaliha ta karɓe zance da cewar, "Baka yi mata komai ba! Haka zalika karka ɗora damuwa da tashin hankali a zuciyarka. Ina me bawa Sarki haƙuri domin wannan yana daga cikin shafin jarrabawarka. Allah ya gwada kai ne domin ya jarabci imaninka." Sarki Aminullah ya miƙe tsaye sai da ya yi taku biyu yace, "Tabbas haka ne kuma muna godiya ga Allah (S.W.T) akan abin da ya jarabce mu da shi." Nan suka ci gaba da bashi baki sai da suka ga ya huce sosai sannan suka yi masa sallama suka fice kowacce ta wuce sashenta.

Kwana biyu a tsakani sai ga saƙo daga Masarautar Zazzau lamarin ba ƙaramin girgiza shi ya yi ba domin banza bata kai zoma kasuwa. Bayan da Sanƙira ya gama karantawa Sarki Aminulla numfasawa ya yi ya kalli Ɗan aiken yace, "Ku bashi kyakkyawan Masauki zuwa wayewar gari." Ɗan aiken ya ɗago ya russhnar da kai ƙasa yace, "Allah ya taimake ka umarnine daga ubangidana cewar kar na kai wayewar a gari a Masarautar nan." Ƙura masa ido Sarki Aminullah ya yi yana son gano wani abu daga Bafaden amma ya gaza ganowa, Sarki Amullah ya ya kalli Sanƙira yace, "A rubutu martanin amincewa zuwansa sannan a bawa Bafaden guzuri kafin tafiyarsa." Gabaɗaya fadawa suka ruɗe da cewar, "Godiya yake Sarkin Musulunci, godiya yake Ɗantoron giwa, sikari ba ka yi farin banza ba, Sanƙira ya amsa shi ma ya yi godiya."


"Ka kwantar da hankalinka Ranka shi daɗe in sha Allahu babu abin da zai faru sai alheri, wataƙila akwai muhimmin abin da zai kawo shi amma na tabbata ba tashin hankali bane, da tashin hankali ba zai aiko da ɗan aike ba." Sarki Aminulla ya jinjina kai domin yana jin daɗin yanda kodayaushe Fulani Zaliha take ƙarfafa masa gwiwa akan abubuwa da dama, kallonta ya yi ya ji kunyar ta duk ta kamashi. Dafa kafaɗarta ya yi da hannu biyu yace, "Zaliha!" Yanda ya kira ta shi zai tabbatar maka da muhimmancin maganar da zai furta mata.

"Don Allah ki yafe mini ke da Saif domin na cutar da ku na zalince ku. Har yanzu zargin kaina nake kamar ban cancanci zama shugaban Al'umma ba tun da a tsakanin iyalina ma ban kwatanta adal..." Hannu ta sa ta rufe masa baki sai kuma ya sakar masa murmushi da cewar.

"Hakan bai kyautu daga gare ka ba domin da a ce magauta za su ji wannan kalaman naka da abin da suke buƙata ne ya samu, wani ya yi rawa ballantana Ɗan makaɗi." Waro ido waje ya yi yace, "Waye haka?"

"Wacce ta yi mini iyaka da farincikina ma yafe mata ballanta kai? Dama tun can bamu riƙe ka ba. Ɗan'adam ajizi ne ko kana nufin Allah ba zai jarrabce ka ba?" Matse mata baki ya yi yace, "Ni dai ban ce ba kar haɗani da Ubangiji." Gabaɗaya suka saka dariya Fulani Zaliha ta ce, "Ka san mene ne babban abin da ya fi faranta mini?" Sarki Aminullah ya girgiza mata kai ta ci gaba da cewa, "Da Allah ya bayyana gaskiya ina da ƙarashen numfashi, na ji daɗi da Maryama ta wanke mu dangane da kisan da ake zargin na tura Maryo ta yi maka. Tabbas wannan babban farinciki ne mun godewa Allah." Rungumota ya yi yana cewa, "Mu ajiye wannan maganar saboda kunyarta nake ji."

"Mun barta, amma fa dole a nemi maganin lalurarka domin ko ba a faɗa ba Maryama ta yi mana jirwaye mai kamar wanka, don haka tun da lalurar ta cuta bace ba za mu ci gaba da zura maka ido ba." Haɓarta ya tallaɓo da hannu biyu yace, " Fillo wai yaushe kika fitsare idonki? Mamaki nake wai yaushe Zalihata ta zama haka." Fulani Zaliha ta yi dariya ta ce, "Tun ranar da ka fitsarar da ni." Yana shirin magana Fulani Zaliha ta ci gaba da yi masa magana.

"Allah da gaske na ke a da mun ɗauka lalaurar daga Allah ce tun da har magunguna an nema ba a dace ba amma yanzu tun da mun fahimci sihiri ne mai zai hana a nemi magani tun da ai mun yi haƙuri shekara nawa muna tare a haka tun ba ma ni ba da aka cuceni, tun da ƙuruciyata ina jin na haifi Saif ko shekara uku bai yi ba ka haɗu da matsalar. Ni an ya ma ban fasa yafiyar da na yi wa Maryama ba." Ta faɗa cikin zolawa ai kuwa Sarki Aminullah mai zai yi ba dariya ba. Idan ka ga yanda yake yi wa iyalaninsa sai ka rantse ba wani mai sarauta bane. Ya dube ta yana riƙe kunnuwa sa biyu yace, "Kaina bisa wuya zan sa a nemar mini magani ko dan na wuce gori, ita kuma Maryama ba zan ce komai ba sai yanda kika ce."

Fulani Zaliha ta ce, "To a hanzarta gaskiya tun kafin na yi maka bore! Yauwa Ranka shi daɗe na ke ganin mai zai hana yaron nan akai masa matarsa ina ganin take-takensa sai hanya-hanya yake yi mini da alama wallahi matarsa yake son akai masa kawai don bai fito ya faɗa bane." Sarki Aminullah gabaɗaya ya shafa'a da zancen Saif saboda ruguntsimin da aka yi, jinjina kai ya yi yace, "Haka ne tun da yau talata mu bari ranar Juma'a ranar albarka a kai masa matarsa ina ga haka ya fi." Fulani Zalina ta amsa masa sannan ta sauya murya zuwa damuwa idonta na cikowa da hawaye ta ce, "Allah Sarki Abu ko suna wacce duniyar oho? Allah ya tsare su a duk inda suke." Gabaɗaya suka amsa da Amin, shi kansa Sarki Aminulla duk sai ya ji babu daɗi.

Fulani Zaliha da kanta ta rinƙa gyaran amarya, Maryo ba ƙaramin kunya take ji ba domin ba wani sabo ta yi da ita ba. Ba kamar Abu da take 'yar ɗakinta ba, ita kuwa Fulani Zaliha nunawa ta yi kamar ba ta lura da abin da Maryo take yi ba, Inna Habi ba ƙaramin daɗi take ji ba domin duk wanda ya ƙaunaci na ka kaima abin ka ƙaunace shi ne tana jin daɗi yanda Fulani Zaliha take ƙaunar 'yanmatan nata biyu.

Saif tun da ya ga Maryo a sashen Mahaifiyar yaje zarya shine shiga ɗauko wannan mayar da wannan, yanzu ma Fulani Zaliha na zaune tana shafawa Maryo lalle a jiki ya shiga, lallan ba ƙaramin kyau ya yi mata a jiki ba abinka da farar fata jikinta sai sheƙi yake, daga ita sai ɗaurin ƙirji saboda gyaran da take yi mata kar ya ɓata kayan jikinta. Duk zaryar da Saif yake a tsakanin sauran ɗakunan yake yi wannan karon ne ya yi shahadar kutsa kai cikin ɗakin ya wayance da ɗaukan abu. Saif yana shiga har tuntuɓe yake yi yana waigen Maryo. Gabaɗaya kunya ce ta kamata ta sunkuyar da kai ƙasa, yana shiga ɗakin ya maƙale a bango yana leƙensu jin shirun ya yi yawa ya sa Fulani Zaliha ta ce, "Idan ka ga leƙen ka zo ka wuce tun ranka bai ɓaci ba." Kamar sabon munafuki haka Saif ya wuce sumi-sumi yana sunne kai ƙasa. Yana fita Fulani Zaliha ta saki murmushi tana mamakin wai yau Saifullahinta ne zai yi mata dabara.

RANAR JUMA'A

Duk abin da ya kamata a yi na gyaran ɗaki da duk wanda ake yi wa amarya an riga da an yi wa Maryo dare kawai ake jira ya yi akai amayar ɗakin mijinta.

Tarba mai kyau Sarki Aminullah ya sa aka shiryawa baƙinsa matafiya daga ƙasar Zazzau, abinciccika aka yi kala-kala tare da tanadar kayan ciye-ciye da shaye-shaye. Sarki Muhammad Safyan shi da Yarima suka taho da ɗan wurin Fulani Zannira mai suna Umar, sai fadawansa da masu tsaronsa da masu yi masa hidima.

A fadar Sarki Aminullah aka yi musu masauki sai da suka ci suka sha kamar wani abu bai taɓa shiga tsakanin Sarakunan biyu ba, sannan Sarki Muhammad Safyan ya bada umarnin a fito da Abu da take cen cikin keken doki hannunta ɗauke da Naufal, tun da ta ji sun sauka a Masarautar Kano take jin kamar ta yi tsuntsuwa amma ina babu wannan halin saboda yanda masu tsaronta suka kafa suka tsare.

Saif yana zaune a a gefe bayan sun gaisa da su Yarima yana shirin tashi ya ga an shigo da Abu cikin wulaƙantacciyar shigar kayan Bayi. Wata irin saranda ya yi bakinsa na rawa yace, "Abu ke ce." Abu na jin haka ta fashe da wani irin kuka ta miƙa masa Naufa tana cewa, "Don Allah ka yafe mini Saif wallahi ban tabbatar da na aikata kuskure ba sai na masifu suka fara afka mini." Jikinsa na rawa ya sa hannu ya karɓi Naufal yana kallon yanda yaron ya yi wayo sosai kammaninsa dana Mahaifinsa sun ƙara fitowa.

Sarki Muhammad Safyan ne ya katse musu magana sannan suka nemi wuri suka zauna, Sarki Muhamma d Safyan ya kalli Sarki Aminullah cikin wata irin murya yace, "Aminullah ta fe na ke da muhimmiyar magana ba da wasa na zo, a baya ka san irin abin da yake tsakaninmu amma ba wannan ne a gabana ba ina san ina. Ina tafe da tuhuma a gare ka kuma ina fatan zaka bani haɗin kai domin na fi som yanda muka lafiya a rabu lafiya."

Fatan alheri 🥰

_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._
[31/01, 21:41] Ameera Adam🌚: 72...


Sarki Aminullah tattara hankalinsa ya yi wurin Sarki Muhammad Safyan sannan yace, "Wannan wace maganace ina fatan ba za ta ƙetare iyaka ba." Ya yi maganar cike isa irin ta goggun Sarakunan da sarauta ta zame musu jinin jikinsu. Sarki Muhammad Safyan ya saki murmushin taici yana ƙoƙarin danne ɓacin ran da yake taso masa, mayar da kallonsa ya yi wurin Abu dake gefe sannan ya zaro sarƙar hannunsa wacce Yarima ya karɓa yace, "Wannan Sarƙar kince baki ita aka yi, yarinyar da take cikin Masarautar nan ce ta baki, Ina 'yar uwar Sarƙar da mai sarƙar suke? Me ya sa ka killace mini 'ya'ya tsawon shekaru? Me ya sa za ka ɗau fansa ta wannan sigar. Tabbas wannan Sarƙar ta Hasana ce ina ta Usaina da Usainar suke?" Sarki Aminullah ya dube shi cikin rashin Fahimta yace,

"Ya kamata ka fito a mutum ka yi mini bayanin da zan gane abin kake nufi."

Sarki Muhammad Safyan ya tamke fuska kamar ta fusataccen bijimin Sa yace, "An sace mini 'Ya'ya shekara goma sha Takwas baya! Wannan sarƙar da kake gani ba guda ɗaya bace guda uku rak aka sassaƙar mini su masu ɗauke da tambarin Masarautar Zazzau." Sarki Aminullah ya yi murmushin yaƙe yace, "Ta wannan sigar ka ɓullo? Muhammad Safyan!" Sarki Aminullah ya kirashi da wata irin kausasshiyar murya wacce take nuna tabbas maganarsa babu alamun wasa a ciki. Ya ci gaba da cewa, "A yanzu shekaru sun ƙaru girma ya ƙara kama mu bana tunanin abin da ya faru a baya zamu ƙara maimaita shi domin jiya ba yau bane. Wacce riba zan samu idan na rabaka da 'ya'yanka bayan nima na haifa, don Allah idan akwai abin da ya kawo ka ya kamata mu tattauna ba wannan ba." Sarki Muhammad Safyan ya harzuƙa cikin ɓacin rai yace, "Aminullah wannan karon a Uba na zo gare ka ba Sarkin Zazzau ba! Ina tsaye a matsayin Uban da zai tsaya kai da fata domin ƙwato haƙƙin ƴaƴansa. Ka gaya mini ina ka kai mini ƴaƴana?" Sarki Muhammad Safyan ya yi maganar a tsawace har sai da Abu ta tsora.

Sarki Aminullah Ya jinjina kai yace, "Lallai da alama tura za ta fara kai bango amma da alama wankin hula zai iya kaika dare..." Da sauri Sarki Safyan ya katse Sarki Aminullah. Ganin lamarin na nema yamutsa hazo ya sa Saif ya tausasa harshe cikin kwantar da murya yace, "Allah ya taimake ka har yanzu bamu fahimci maganar da kake yi ba, mai zai hana ka yi wa Mai martaba..."

Sarki Muhammad Safyan ya bugawa Saif tsawa yana cewa, "Dakata yaro! Wannan ba maganarka bace karka sake ka ƙara saka mana baki." Saif babu yanda ya iya haka ya ja bakinsa ya tsuke saboda da alama iyayen nasu biyu sun ɗauki zafi.

Ganin an kara samun saɓanin rashin fahimta ya sa Sarki Muhammad Safyan ya kalli Abu ya buga mata tsawa yana faɗin, "Ke wa kika ce ya baki sarƙar nan?" A firgice Abu ta ce, "Wallahi Maryo ce kuma da kanta ta bani ana gobe zan tafi." Ƙirjin Saif ne ya buga da wani irin bugu mai tsanani. Sarki Aminullah ya kalleta cikin damuwa a zuciyarsa yana ayyanawa wannan wacce yarinyar ce da tun zuwanta gidansa ake ta samun matsaloli.

Sarki Aminullah kallon Saif ya yi yace,"Maza ka je ka kira mini Matarka da Mahaifiyarta."

Kamar jira Saif yake da sauri ya fita ya nufi sashen Fulani Maryama hannunsa ɗauke da Naufal, yana shiga wani irin wari ya fara dukan hancinsa da sauri ya tsartar da yawu yana rufe hanci. A gaggauce ya isarwa da Inna Habi saƙon Maimartaba ya fita yana waigen ɗakin fulani Maryama da tsirarun ƙuɗaje suka fara yanyame ɗakin.

Inna Habi tun da suka samu saƙon kiran Sarki Aminullah suka yi hamdala domin warin da suka wayi gari da samunsa ba ƙaramin cika musu ciki ya yi ba. Ba su kawo komai ba amma kuma jin kiran ya basu mamaki domin a iya saninsu Sarki idan ya yi baƙi baya kiran wasu daga cikin gida zuwa Fada. Suna shiga tun daga nesa Maryo ta hango Abu a zaune sai dai duk ta yi baƙi ta rame. Kuka ta fashe da shi ta ƙarasa ta rungume Abu tana ci gaba da rusa kuka. Za ta fara magana Sarki Aminullah ya katse ta cewar,

"Ya isa haka domin akwai muhimmiyar maganar da ke tafe da mu." Fadar ce ta tsit Maryo ta hau wara ido domin ba ƙaramin tsorata ta yi ba tana tsoron kada a ce mata Abu bata dawo da Naufal ba.

Sarki Muhammad Safyan ƙurawa Maryo ido ya yi gabansa na faɗuwa, ita kanta Abu sai yanzu ta lura da wani abu. Tun ranar da ta fara tozali da Yarima ta rasa a inda ta san mai yanayin kamarsa, tsoro da fargabarsa ya hanata zama ta ƙare masa kallo.

Sarki Aminullah ya miƙawa Maryo sarƙar da ya karɓa ya gani daga hannun Sarkin Zazzau. Da sauri ta karɓa tana murmushi ta ce, "Abu yanzu sai da kika cire sarƙar nan da kin ɓatar min fa kinsan ko Inna ba ta san na baki ba." Sarki Muhammad Safyan ya zuba mata ido yana ganin yanda take magana, amma gudin kar ya yi hanzari ya yi shiru. Sarki Aminullah ya katse Maryo da cewar, "Bama son sakarci a wurin nan." Shiru Maryo ta yi Sarki Aminullah ya ci gaba da cewa, "A ina kika samo sarƙar nan." Maryo ta yi shiru ta kalli Inna Habi domin ita kanta ba za ta ce ga inda ta samo ta ba abu ɗaya ta sani Inna na bawa wannan sarƙar muhimminci. Maryo ta sunkuyar da kai ta ce, "Allah ya taimake ka Inna ce ta siya mini tun ina yarinya."

Kallon da Sarki Aminullah ya yi wa Inna Habi shi ya tabbatar mata da yana buƙatar ƙarin bayani daga gare ta don haka ta russunar da kai ƙasa ta ce, "Allah ya taimake ka kamar yanda na gaya maka a baya na tsinci yarinyar nan, a ranar da na tsince ta tare da wannan sarƙar na tsince ta sai wani murjani." Sarki Muhammad Safyan ya yi karaf yace, "Kika tsinceta ita kaɗai ko kika tsince su."

Inna Habi ta ce, "Allah ya taimake ka Ita kaɗai na tsinta tana jaririya." Sarki Muhammad Safyan ya yi kabbara yana cewa, "Tabbas Allah shi ne abin godiya amma ya tabbata wannan yarinyar jinina ce, zo mu ga idonki matuƙar kina da tawadar Allah a idonki tabbas kece Hasana." Maryo da kanta ya gama ɗaurewa da waɗannan mutane masu dajara sai wurga idanu take tana neman da wacce yake magana.

Sarki Muhammad Safyan da kansa ya tako wurin Maryo ya ɗago da kanta yana kallon ƙwayar idonta, Maryo sai gani ta yi ya rungumeta yana furta, "Alhamdullah Allah na gode maka da ka bayyana mini ɗaya daga cikin ƴaƴana da na rasa." Sai kuma ya raunana murya yace, "Ko a ina zan samu Usaina? Ina ma Allah zai bayyana mini ita kamar yanda nake ganinki a gabana." Daga bayansa ya ji ance.

"Ita ma ka same ta domin ita ma tana nan da ranta." Sarki Aminullah ya faɗa murya ɗauke da ƙwarin gwiwa. Da sauri Sarki Muhamma Safyan ya miƙe ya ƙarasa wurin Sarki Aminullah yace, "Don Allah tana ina a wane wurin take." Sarki Aminullah yace, "Idan har wannna Hasana ce to babu ko tantama Matar Maleek ita ce Usaina."

"Waye Maleek don Allah gaya mini shi, tabbas wannan Hasana ce wallahi Usaina tana da cindo a ƙafarta." Sarkin Zazzau ya yi maganar cikin ɗoki. Sarki Aminullah ya yi murmushi yace, "Ɗan ƙanwata ne yake aurenta." Sarkin Zazzau cikin farinciki yace, "Masha Allah yanzu yau ni nake jin daddaɗan labari akan tagwayena, Allah me iko yanzu Usaina har ta yi aure?" Sarki Aminullah ya yi dariya mai sauti yace, "Kana mamaki ne? Ita ma ta gabanka ga mijinta nan." Kunya ce ta kama Maryo da sauri ta sunne kai ƙasa tana murnushi. Haka kawai ta fara jin wani irin farinciki na ziyartarta ganin abin take kamar a mafarki wai yau ita ce take gaban Mahaifinta. Sarki Muhammad Safyan yace, "Ikon Allah ka ce da na yi abin kunya a gaban Siriki." Cikin zolaya Sarki Aminullah yace, "Idan baka yi a gaban wannan sirikin ba ka yi ai a gabana." Kallon rashin fahimta Sarkin Zazzau ya yi masa, Sarki Aminullah da ya fahimci haka sai yace, "Ina nufin ka yi abin kunya a gabana tun da ni sirikinka ne Ɗan wurina ne yake aurenta."

Sarkin Zazzau ya saki baki da mamaki yace, "An ya Aminullah babu lauje cikin naɗi kuwa?" Sarki Aminullah sai yanzu maganarsa ta tsawon shekaru ta faɗo masa da ya taɓa gayawa Sarkin Zazzau lokacin da suka rabu baram-baram dutse a hannun riga. Murmushi ya yi ya kallin Sarkin Zazzau yace, "Dama na gaya maka cikin ikon Allah auratayya sai ta haɗa zuri'armu ta yanda duk wani rashin jituwa ya kau daga gare mu. Allah ne ya yi wannan haɗin kuma shi ya barwa kansa sanin alherin da ke tattare da haka."

Abu da ke gefe wani irin daɗi ta ji domin ta san ko babu komai ta goge tabon ɓacin ran da ta dasawa Maryo a zuciyarta. Ko ba komai tafiyarta ta kawo abubuwan alheri da dama, silar tafiyarta ya sa Saif ya auri Maryo. Uwa Uba kuma ta sanadinta Maryo ta sadu da iyayenta.

Har lokacin Sarkin Zazzau bai gama amincewa da a rashin sani aka yi auren Maryo da Saif ba, gani yake kamar yana da sa hannu wurin sace masa ƴaƴansa. Sai da aka bashi labarin Maryo tun daga ranar da Inna Habi ta tsinceta har zuwanta Masarautar Adamawa da abubuwan da ya faru. Ya matuƙar jinjinawa Inna Habi akan namijin ƙoƙarin da ta yi wurin rainon Maryo da yanda ta bata kulawar da ta dace. Nan take hira ta ɓarke aka ci gaba da ciye-ciye da shaye-shaye. Maryo na hannun Mahaifinta kamar wani zai ƙwace masa ita. Anan ya fahimci irin tsantsar shaƙuwar da ke tsakani Abu da Maryo abin ba ƙaramin birgeshi ya yi ba.

Maryo tana son ta karɓi Naufal amma ta rasa ya zata yi saboda wata irin kunyar Saif da take ji, shi kuwa da sun haɗa ido zai kashe mata ido ya sakar mata murmushi. A wannan zaman ma sai da Abu ta jaddada maganarta na saki a wurin Saif don har ga Allah ta cirewa zuciyarta son ci gaba da zama da shi. Shiru Saif ya yi yana nazari ya riski muryar Sarki Aminullah yana cewa,

"Saif ina gani ka sauwaƙewa yarinyar nan zai fi domin kana gani ta sanadin rashin sakin da baka yi mata bane har ta guje mana ta yi tafiya mai nisa, shi zaman aure na mutum biyu ne idan ɗaya ya nuna ba ya yi shi kenan." Saif ya gyaɗa kai sannan yace, "A yi mini afuwa ranka shi daɗe zan aiwatar da abin da take buƙata amma ba zan iya aiwatarwa yanzu ba." Hakan ba ƙaramin daɗi ya yi wa Sarakunan biyu ba, Sarkin Zazzau har a zuciyarsa ya ji ya aminta da

Please Login or Register in order to submit comment