Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tafka babban kuskure da ka tsaya, a tunaninka za ka iya tarar aradu da ka ne? Karka manta tasirinta ya rinjaye naka da ninki biyu. Ba ƙarfinku ɗaya ba domin da ka tsaya ja da bayinta na tabbata sai ta ƙone ka da ƙarfinta domin ta fusata fushi mai tsanani. Na aiko Gurubu ya ɗauke ka domin niyyarta ta hallaka ka gabaɗaya, saboda ka taɓa mata 'yar uwa da Ɗan da take jinsa tamkar nata." Tsohon ya faɗa ransa a ɓace. Salman ban da haki babu abin da yake yi don haka ya ɗago da rinannun idanunsa yace, "Wallahi sai na koya mata hankali saboda waccen abar za ta azabtar da ni haka?"

"Bari ba shegiya bace da Ubanta. Amma idan ka shegantata akwai lokacin da za ka nemo mata uba ka saƙala mata. Yaƙi dan zamba ne domin ba a shigarsa sai da shiri don haka ina baka shawara da karka tunkareta gaba da gaba saboda za ka tunatar da ita babban ɓacin ran da idan ta ganka a gabanta sai ta cinyeka ɗanye." Salman ya dube shi yace, "Yanzu haka zan zura mata ido kenan ta ci bulus?"

"Bata ci bulus ba sai dai bana san ka da yawan gaggawa domin wata ra zai kai ga danasani. Yanzu ka zauna a nan ka ƙarasa jinyar idan kuwa ka koma na tabbata sai ta illata ka. Haka zalika ka yi sake ɗan zaki ya girma domin tuni ta jima da kwaye maka baya, domin ta fahimci shirinmu tun da ɗauke maka matarka a yau ɗin nan. Maganar da nake yo maka a yanzu cikin da ke jikin matarka tuni babu shi saboda tsananin firgitar da ta yi. Sai dai mu bi ta wata hanyar ba wannan ba, domin wannan tuni da babu ita."

Kamar wacce a tsikara haka ta mike ta nufi sashen Fulani Zaliha, bata kula kowa ba ciki har da Fulani Zaliha, tana shiga ta samu Abu a kwance cikin wani yanayi. Jaririnta yana gefe idanunsa a kakkafe suna kallon sama. Gabaɗaya ido suka zuba mata suna kallo abin da za ta yi. Kan Abu ta fara zuwa ta sa hannuwanta biyu ta dafe kanta da ƙarfi sai ta saka bakinta a saitin kunnenta ta hura mata wata irin iska, firgigit ta miƙe tana kalle-kalle kamar me matasalar ƙwaƙwalarwa. Sai kuma ta wata uwar ƙara ta ƙara zubewa a wurin. Hannuwa biyu Maryo ta ɗaga tana godewa Allah domin bata taɓa tsammanin haka ba. Ɗaukan jaririn ta yi ta ɗora shi a ƙafarta ta fara matsa masa ciki take wani farin ruwa ya fara fita daga bakinsa, zuwan can ya tsanyare da kuka sai da kyar Maryo ta lallashe shi bayan ya yi shiru ta miƙe za ta fita har ta je bakin ƙofa ta waigo ta ce, "Kar wanda ya taɓa ta zata warware ta farka da kanta, amma yaron za ku iya ba shi kulawa. Tana gama maganar ta furzo wasu duwatsu guda biyu daga bakinta ta murmushe su a wurin sannan ta fice.

Tana fita ta ci karo da Saif kamar ita yake nema suna haɗuwa ya wurgo mata tambaya. "Me ya sa kika musu haka?"

"Ta yaya zan barsu bayan kowannensu yana buƙatar jin ɗumin ɗan uwansu, idan ka yi haka kamar ka tsorata da lamarinsa ne. Kowacce Uwa ya fi kyautuwa gare ta da ta bawa Ɗanta kulawa." Ta karkaɗe hannuwanta sannan ta bi ta gefe ta wuce.

Bayan wani lokaci Abu garau ta miƙe kamar ba ita, haka ta rungumi Ɗanta tana mamakin kwanciyarta a wurin sai dai babu wanda ya sanar da ita komai. Salman na wurin Dattijo yana ci gana da samun sauƙi, sai dai fir tsohon ya hana shi tafiya a cewarsa sai ya ƙara samun lafiya ya kintsa shi. Sarki Aminullah haka ya rinƙa kiran masu magana ana bawa Maryo don ganin ta warke ta samu lafiya garau. Marasa lafiyar da suka jikkata sakamakon ƙudan zuma suna samun sauƙi waɗanda suka mutu haka Sarki Aminullah ya aika aka yi musu sutura aka binne su tare da bawa iyalansu tallafin kuɗi da kayan abinci.

Kwanci ta shi babu wuya an yi suna Yaro ya ci sunan Sarki Aminullah suna kiranshi da Naufal, ranar suna an sha shagali 'yan uwa da abokan arziƙi daga sassan garuruwa haka suka zo bikin taya murna. Fulani Zaliha farinciki a wurinta baya musaltuwa haka daga wurin 'yan uwanta na nesa da suka zo. Fulani Maryama saboda baƙin ciki ɗaki ta shige ta fashe da kuka Jakadiya na lallashinta tana bata baki, domin wannan shine ga ƙoshi ga kwanan yunwa saboda gabaɗaya ta rasa ta yanda za ta yi ta cutar da yaron. Kamar wanɗanda aka shafewa tunani da tunanin Salman haka kowa ya manta ta shafinsa, kuma tun daga wannan lokacin babu abin da ya sake faruwa akan Abu da Jaririnta ba. Lokacin da Maleek ya zo bayan suna duk wasu abubuwa na shirin biki da ya tambayi Maryo ce masa kawai ta yi ya yi duk abin da ya dace, saboda wani abin na shi ba ƙaramin kunya yake bata ba. Don yanda yake zumuɗin bikin yanda ka san bai taɓa aure ba.

Sannu-sannu bata hana zuwa...

Ranar wata juma'a bayan gudanar da sallar Juma'a aka gabatar da ɗaurin auren Maryo da Maleek a babban masallacin juma'a na gidan Sarkin Kano da ke cikin ƙwaryar garin Kano. Dubbannin mutane ne suka halarci ɗaurin auren wanda ya tara manyan mutane, attajira, 'yan siyasa da dai sauransu. Kafin ranar an gabatar da bukukuwa na al'ada kamar yanda yake wanda ya haɗar da kamu saka lalle da du abin da ya danganci shagalin bikin aure.

Murna wurin Maleek abin baya musaltuwa, haka daga wurin Maryo dukda ta san ba wata zazzafar soyayyar take mata ba amma sai ta tsinci kanta cikin farinciki da annushuwa. Saɓanin Abu da take taya mijinta kishi, don Abu fushi take da Maryo sosai ko magana ta yi mata sama-sama take amsawa. Saif duk wanda ya kalle shi ya san yana cikin matsananciyar damuwa saboda yanda ya rame ya ƙanjame ya lalace. Da Fulani Zaliha ta takura da abin da yake damunsa ƙin gaya mata ya yi. Sai Abu ce ta sanar da ita abin da yake faruwa tun daga farko har ƙarshe, tausayin Ɗanta ne ya kama ta domin ta san idan ta ce za ta yi magana ita kanta ta san bata yi wa kanta adalci ba, kuma Fulani Fahima da wane ido za ta kalle ta? Wannan dalili ya sa ta kira Saif ta rinƙa tausarsa tana ba shi baki.

Ranar ɗaurin aure da yamma Maleek ya aika kiran Maryo, da farko ƙin zuwa ta yi amma Inna Habi ta matsa mata. Tana zuwa ta same shi a babban zaure, mutane sai kallonta suke saboda yanda ta yi shar da ita sai zuba ƙamshi take. A kunyace ta ce, "Barka da yamma!" Shauƙin ƙaunarta yake ji har a zuvciyarsa, ya riƙo hannunta yace, "Da baza ki zo bane?" Ɗagowa ta yi tana shirin ƙwace hannunta ta ce, "Mutane suna kallonmu" Kashe mata ido ɗaya ya yi yace, "Sai me?" Shagwaɓe fuska ta yi ta ce, "Amma ai..." Wata murya ce ta katse ta sakamakon jin yanda ta ratsa gaɓɓan jikinsu gabaɗaya sautin muryar na faɗin, "Don Allah ku taimaka mini azzalumai ne wallahi cutar mu suke son yi." Saif da tsaye a bakin ƙofar ya kalle su yana sakin wani shu'umin murmushi. Jiki na rawa Maryo ta fisgota da ƙarfin tsiya ta maƙureta a bango tana cewa, "Wace ce ke?"

🌚Na baku gari kowa wace oho


_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._
[19/01, 19:22] Ameera Adam🌚: 65...



Da sauri Maleek ya ƙarasa yana ƙoƙarin cire Maryo da sauri ta waigo gare shi tana cewa, "Don Allah karka dakatar da ni bansani ba ko an turota ta illata ni, wataƙila kaidin Salman ne." Maleek ne ya sauke idanunsa a kan Matar kusan numfashinsa ne ya ƙafe ya shiga nuna ta da hannu bakinsa na rawa. Daga can ɓangaren matar ta zuba masa ido jikinta na rawa numfashinta na niyyar ɗaukewa ta ce, "Kai... Kai ne?" Tana faɗin haka ta zube a wurin. Da sauri Maleek ya ƙarasa ya tarota ta faɗa jikinsa yana jijjiga ta. Maryo ta kalli Saif da yake kokarin barin wurin tana son ta tambaye shi game da wannan macen da ta gani mai siffarta sai kuma ta haƙura. Kallon Maleek ta yi tana shirin tambayarsa ta ga ya saɓi matar ya ɗauke ta kamar jaririya ya wuce cikin gida. Can sashen Fulani Maryama ya wuce ta ita haka ya tafi ya bar Maryo a soro cikin tunane-tunane iri-iri, saboda gabaɗaya kanta ya gama kullewa. Kafin wani lokaci tuni gidan ya karaɗe da zancen Maleek ya ɗauko Amarya babu lafiya. Babban abin da ya ɗaure wa mutanen gidan kai bayan sun ga ankwantar da Maryo sai ga wata ta shigo. Sai da Maryo ta shigo suka tabbatar da ba ta farkon bace domin waccen sanye take da yagaggun kaya kuma Maryo ta fi ta haske da gogewar fata.Wannan maganganun da ake yi ne suka ƙarasa kunnen Inna Habi tana zuwa jikinta ya yi wani irin sanyi domin tun da take bata taɓa ganin matsananciyar kama irin wannan ba. Ita kanta Maryo abin ya matuƙar bata mamaki, sai dai tana tsaye ta kasa koda motsa ɗan yatsanta ne. Inna Habi ce ta sauke ajiyar zuciya ta ɗebo ruwa ta yayyafa mata domin ji take tamkar Maryonta ce kwance a wurin. Tana tashi ta fara bin mutanen wurin da kallo a hankali ta furta, "A ina nake nan." Tana tuno wanda ta gani ta zabura zata fice daga gidan da sauri Maleek ya kama ta ya riƙe ta gam, ido ta zuba masa ta hau kiciniyar kwacewa tana cewa, "Ina fatan wannan mafarkin kar ya zame mini gaskiya, Ya Allah ka farkar da ni." Maleek ya hura mata iska a fuska lokaci ɗaya ta sauke ajiyar zuciya ta ci gaba da kallonsa kamar ta samu sabuwar hallita.

"A ina kika ɓoye mini tsahon shekaru kin barni ina bulayi?"

"Waye kai?" Ta faɗa tana ƙoƙarin ƙwacewa.

"Na san an cutar da ke amma don Allah ki karki watsawa soyayya ƙasa a ido, ki taimaka ki yi mata hallaci domin ta wahalar da ni fiye da tunaninki." Maleek ya faɗa mata a shagwaɓe kamar zai yi kuka. Idanun mutane yana kallonsu kowa na kashe ƙwarƙwatar idonsa. Maryo da ke gefe ta tsuke fuska ta ce, "Wace ce ita." Don ita gabaɗaya ta manta da cewar ya taɓa iƙirarin ita matarsa ce. Sai a lokacin ta juya ta kalli Maryo, zaro idanunta waje ta yi a tsorace domin ko a mafarki bata taɓa yin tozali da hallita mai matsananciyar kama da ita ba sai yau.

"Shukra ce! Ita ce wacce soyayyarta ta haukata ni har ta makanta mini ido na ce ke ce matata." Inna Habi da ke gefe ta ce, "Wannan ba maganar tsaiwa bace ya kamata mu nemi wuri a yi zancen a zaune." Maleek ƙin sakin Shukra ya yi domin gani yake kamar za ta kwace ta gudu ya sake rasa ta, hannu ya ɗora a kan fuskarta yace, "Inna 'yan biyu suke?" Sunkuyar da kai ƙasa ta yi ta ce, "Suna can wurin Iyatu a bakin kasuwa."

"Wace ce ita?" Maleek ya tambaya a ruɗe.

"Wata tsohuwa ce da nake bar mata yara na tafi aikatau idan na dawo sai na karɓe su." Shukra ta faɗa tana ƙoƙarin kwacewa ta ce, "Lokacin tashinta ya kusa bari na je na karɓo su don idan banje ba sai na ƙara mata kuɗi."

"Aikatau Shukra? Kece kike aikatau? Me ya sa haka me ya sa za ki yi aikatau alhalin kuna da gata?" Maleek ya yi maganar hankali a tashe. Shukra ta saki murmushin takaici ta ce, "Zamana a wurin nan ya fiye mini kwanciyar hankali Maleek, domin rayuwa nake yi mai cike da 'yanci saɓanin rayuwar da na yi a ba..." Tun bata rufe baki ba ya saka hannu ya rufe mata yana girgiza mata kai. Inna Habi ce ta riƙe hannunta suka wuce ciki Maleek ya rufa musu baya. Kamar wacce ƙwai ya fashewa a ciki haka Maryo ta bi su zuwa cikin ɗakin.

Kafin wani lokaci tuni maganar Shukra ta ƙarasa har kunnen Sarki Aminullah, Sarki Abdallah da sauran waliyan Maleek waɗanda ba su tafi ba. Maleek ba ƙaramin tausawa Shukra ya yi ba dangane da tarihin rayuwar da suka fuskanta ita da tagwayenta. Inna Habi ta goge hawayen fuskarta tana kallon Maryo da Shukra, Maryo ta share hawayenta ta ce, "Amma da kin yi haƙuri kin zauna da mijinki ya fiye miki wannan wahalar da kika sha, sai dai duk abin da ya samu bawa daga Ubangiji mai kyau ne."

"Duk abin da ya koro ɓera daga rami ya faɗa wuta to ya fi wutar zafi. Na so jure wa haka amma na ga ba zan iya ba domin neman rayuwata ake da abin da na haifa. A ranar da zan baro Masarautar Adamawa muna kwance cikin dare ni da 'yan biyu na ji katangar ɗakinmu ana rusa ta, ban yi aune ba na ji muryar da ko a mafarki ba zan manta da ita ba ƙasa-ƙasa tana cewa. Maza ku ƙone ta tana ciki da yaranta gabaɗaya. Inna jin haka da sauri na goya Hassan shi kuma Usaini na rungume shi na saka hijabi na fice da gudu a lokacin wutar har ta fara ci a ɗakinmu. A cikin daren nan haka na rinƙa gudu ko waiwaye bana yi har Allah ya sa na fice daga gidan. Na samu nasarar ficewa ne lokacin da aka tattara a bakin sahshenmu kowa na ta'ajibi. Ina ganin Sarkin ƙofa ya wuce na fice da sauri hannuna ɗaya rungume da Usaini ɗayan na toshe masa baki don lokacin wuya ta sa ya fara tsala kuka. Ina fitowa na haɗu da wasu fatake na nemi taimakonsu suna wuce da ni zuwa garin da za su yada zango. Haka na ci gaba da gwagwarmaya har Allah ya kawo ni garin Kano na rinƙa faɗi tashi har na samu gidan da zan riƙa yi musu aiki suna bani abinci muna ci nida yarana. A taƙaice kenan dalilin fitowa ta amma idan kece za ki iya ci gaba da zama kuwa." Maryo ta girgiza.

Babu jimawa Sarki Aminullah ya sa aka kai Shukra Fada, bayan an karɓo 'Yan biyunta daga wurin Iyatu. Abu tsayawa ta yi tana kallonsu lokacin da ta ƙarasa ganin abin da ake ta jita-jita a kam maganar Maryo ta rikiɗa zuwa mutum biyu.

Sarki Aminullah ido ya zuba musu yana kallo ya ɗauki lokaci mai tsayi sannan ya numfasa ya fara magana, "Dukkan yabo godiya sun tabbata ga Allah subhanahuwata'ala, wannan al'amarin ya faru ne cikin ikon Allah. Maleek ba za mu bar maka su gabaɗaya a matsayin matakan ba domin da alama akwai alaƙa mai ƙarfi a tsakanin Shukra da Maryo don haka sai dai ka zaɓi ɗaya." Takawa na gama magana Maryo ta gyara zama ta ce, "Allah ya taimake ka na haƙura na bar mata shi saboda dama rashinta ne ya sa alaƙarmu ta yi ƙarfi har da ta kai ga batun aure." Maleek da Inna Habi ba ƙaramin tausayin Maryo suka ji ba. Sarki Aminullah ya san za a yi haka domin idan bai manta ba rashinta ne ya sa aka bashi Maryo a matsayin Shukra. Wannan dalilin ya sa ya yanke wata shawara da cewar, "Bisa ga la'akari da abubuwan da ya faru idan aka warware aurenta da Maleek zan ɗaura mata aure da babban Ɗana kuma magajin wannan masarauta." Daga Maryo har Inna Habi a firgice suka kalle shi jikin Maryo har rawa yake tana tsaka da tunani ta ji Sarki Aminullah ya sallame su.

Duk inda nutsuwa take ta yi gabas Maryo ta yi yamma domin tun da Sarki Aminullah ya furta haka shi kenan ta rasa nutsuwarta. A ranar labarin duk abin da ya faru ya karaɗe cikin masarautar. A ranar ne Saif ya kwanta rashin lafiya banda amai babu abin da yake yi yana ambatar sunan Maryo. Tun suna ɗaukan lamarin da wasa har abin ya fara gagarar Kundila. Kwanan su Maleek guda suka tattara zuwa garin Adamawa.

A wannan karon SarkinAminullah ba ƙaramin damuwa ya yi dangane da ciwon Saif ba, da kansa ya aika aka kira masa Fulani Zaliha ya tambayeta abin da yake damunsa. Da farko ta yi niyyar ɓoye masa ganin ɓoyewar bashi da amfani ya sa ta sanar da abin da yake damunsa.

Kwana biyu da yin maganar Sarki Aminullah ya sa aka kira masa Inna Habi, Maryo, Abu, Saif da sauran matansa gabaɗaya. Bayan ya gabatar da maƙasudin zaman na su ya kalli Maryo zai yi magana Abu ta yi karaf ta ce, "Allah ya taimakeka don Allah ka yi mini wannan alfarmar domin kai kaɗai ne za ka iya tabbatar da ita." Maryo ta dubi Abu ta ce, "Karma ki wahalar da bakinki domin hakan ba zai taɓa yuwuwa ba."


_LITTAFIN NAN NA KUƊI NE DA NAIRA 200 ZAKI KARANTA SHI CIKIN KWANCIYAR HANKALI, ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN, FIRST BANK 3090957579 AISHA ADAM, ZA'A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR,0706 206 2624, DAN GIRMAN ALLAH IDAN KINSAN ZAKI FITARMUN DA LITTAFI NA YAFE CINIKINKI._
[22/01, 16:55] Ameera Adam🌚: 66....


Waiwaye...

Kafin wani lokaci tuni ɓatan Rayzuta da Farratu ya karaɗe ciki da wajen masarautar Daulatul Jinnul Sahara, hankalin Sarki Kisumu ba ƙaramin tashi ya yi ba. Nan take ya baza masu tsaron cikin Masarautar aka shiga bincike a tunaninsa bincike suke yi a baɗini kuma ninke shi suke yi domin kusan kaso casa'in da tara sun san yanda aka yi Rayzuta ta ɓace. Yana nan zaune Labari ya ishe masa a sirrance na tafiyar da aka yi da Rayzuta da mai ɗakinsa, wannan labarin ya same shi daga bakin Mahaifin Furzaan sakamakon wani amintaccen dogari da ya sanar masa. Lokacin da Furzaan ya ji labarin ji ya yi kamar ya yi hauka, nan take Sarki Kisumu ya bada umarnin zama na gaggawa a cikin fada. Ransa ba ƙaramin ɓaci ya yi ba ganin yawan Dogarawa masu tsaron Masarautar ace wai har a ta fi da matarsa da 'yarsa ba tare da sun yi ƙoƙarin dakatarwa ba. Suna nan zaune yana tsaka da jawabi Furzaan ya miƙe jikinsa har rawa yake yace, "Ranka ya daɗe a yi mini izini na tafi Masarautar Sarki Buzaag na sare kanshi dana Bulbuta da ɗansa Zulik domin sun munafinci Masarautar nan dole ne a yi musu hukunci mai tsanani. Ka bani dama na je na taho da Rayzuta da Mahaifiyarta domin na yi rantsuwa sai sun girbi abin da suka shuka da hannunsu." Sarki Kisumu ba ƙaramin daɗi ya ji ba domin ya tabbata bai zaɓawa 'yarsa zaɓon tumun dare ba. Cikin ƙarfafa masa gwiwa yace, "Tabbas kai Ɗan halak ne kuma na ƙara tabbatarwa daga tsatson jinin Aminina ka fito. Amma ka sani kai kaɗai ba za ka iya karawa da su ba domin na san wane ne Sarki Buzaag ba tun yanzu ba. Ba za mu farmake su yaƙi ba matuƙar ba su suka fara kawo mana hari ba, don haka zamu zuba musu ido don ganin abin da suke da niyyar yi. Amma matuƙar suka cutar mini da iyali sai na yi mummunan ɓata musu..." Bai rufe baki ba wani Bawansa ya faɗo fadar jina-jina yana haki yana nuna ƙofa yana cewa, "Ranka ya daɗe ga Bulbutu can da rundunar Sarki Buzaag sun kawo mana hari sun kashe dubbannan mutane nima da ƙyar na..." Harbin kibiyar da aka sakar masa a baya ne ya katse maganar da yake yi nan take ya faɗi ya mutu. Hankalin Sarki Kisumu ya kai matuƙar ƙolokuwar tashi da sauri ya mike yana ɗaukan kayan yakinsa. Haka suma sauran mazauna wurin kowa ya fice a guje yana neman kayan yaƙinsa. Sanƙira tuni ya yi shelar ɗaura ɗamarar yin yaƙi saboda kowa ya kasance cikin shiri.

Furzaan kamar jira yake tuni ta ɗauki kayan yaƙinsa ya fita ya fara ragargazar maza yana kai su ƙasa. Kafin
wani lokaci tuni wuri ya hautasine da ƙura ban da ƙarar ƙasusuwan jikinsu da manyan miyagun ƙarafuna babu abin da yake tashi a wurin. Sai dai sarkin yawa ya fi Sarkin ƙarfi, munafukan Masarautar Sarki Kisumu tuni suka rikiɗa zuwa kaiwa tsagin Sarki Kisumi farmaki. Lokacin da Mahaifin Furzaan, Furzaan da Sarki Kisumu suka lura da haka sai yaƙin ya fara sauya salo. Ganin ana neman kai tawagar Sarki Buzaag ƙasa ya fusata su suka fara buɗe musu wuta wani Barde ne ya kawowa Sarki Kisumu suka Mahaifin Furzaan na ganin haka ya tare sukar ta huda cikinsa har zuwa bayansa. Nan take jini ya yi tsartuwa idanunsa suka fara kafewa, Sarki Kisumu ya wurgar da takobinsa ya ƙwalla ƙara ya rungumo abokinsa yana ci gaba da kuka kamar ƙaramin yaro yana cewa, "Me ya sa za ki mini haka? me ya sa ba za ka bari mu tafi tare ba." Wannan kukan da Sarki yake yi ne ya ja hankalin Furzaan ganin Mahaifinsa a ƙasa cikin jini ba ƙaramin ɗaga masa hankali ya yi ba. Da sauri ya ƙarasa ya rungume shi yana kiran sunansa. Daga cen gefe a fusace Babban Barden ya ɗauke Barden da ya kai wa Sarki suka mari yana cewa, "Baka da hankali ne ba ka ji sharaɗin da Mai gida ya kafa mana ba yace duk rintse kada mu kashe mutanen da ya lissafa mana yanzu da shi ka samu da ya kenan?" Furzaan na jin haka ya miƙe a fusace ya ɗau takobinsa ya fille kan Barden da ya kashe mahaifinsa nan fa faɗa ya ƙara ɗaukan zafi, Mahaifinsa yana gabda mutuwa ya kalli Sarki murya a shaƙr yace, "Kabar faɗin haka domin ba komai bane don Amini ya sadaukar da ransa ga amininsa. Na ji daɗi ƙwarai da ni zan fara tafiya na barka, amma ina me jadadda maka ko bayan raina ban yarje Furzaan ya auri wata ba bayan Rayzuta kuma ko zai mutu na fi son ya mutu a tafarkin jarumta ba jarumin da aka ci shi da yaƙi ba." Ya saki murmushin ƙarfin hali ya ci gaba da cewa, "Dama na gaya maka na girmeka tsaurin ido ne ya sa kake abota da ni amma na girmeka na riga ka aure, na riga ka haihuwa kuma yanzu ma sai na riga ka mutuwa. Yaro matsa gefe me gidanka na magana." Waɗannan kalaman tun suna yara ƙanana Mahaifin Furzaan yake gayawa Sarki Kisumu, tun ba su yi hankali ba har suka fara zama samari. Wani lokacin idan suna tsokamar junansu Mahaifin Furzaan na faɗin haka yake kashe bakin Sarki Kisumu. Don haka a wannan lokacin da mutuwarsa ta zo ya ƙara jajjada masa. Sarki Kisumu na jin ƙarashen zancensa ya rungume shi ya fashe da wani irin matsanancin kuka, duk wanda yake wurin idan ya ga irin gursheƙen kukan da yake yi sai ya tausaya masa. Tuno rayuwarsu ta yarinta ya rinƙayi da barkwancin Amininsa tare da sauƙin kai irin nasa. Kasa taɓuka komai ya yi ya rungume gawar Amininsa yana ci gaba da kuka.

Ko a girgiza kurna ta fi magarya domin duk lokacin da ka daidai Giwa da ɗantsako banbancin a bayyane yake, Sarkin yawa ko cikin maye yake ya fi Sarkin Ƙarfi. Duk yanda Furzaan ya kai ga ƙoƙarin kashe Dakarun Sarki Buzaag sai da suka yi masa ƙawanya sannan suka ɗaure shi da wata murtukekiyar igiya. Kan Sarki Kisumu suka koma shima da ƙyar suka yakice shi daga jikin gawar Amininsa suka ɗaure shi, sanann suka yi ƙoƙarin tafiya da shi. Furzaan na gaba Sarki Kisumu na biye da shi, Masarautar ta yi tsit sai gawarwakin mutane da kukan mata da ƙananan

Please Login or Register in order to submit comment