Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

up sannan nayiwa Ayanah tasha kyau har tagaji kamar aljana saboda tsabar kyau wow masha Allah Allah yayi halinta gurina n dariya mukayi sosai sannan nasaka atamfa pink da gyale da takalmi da jaka dukk sai yan kunne da sarƙa.


A gurin Auren ɗaure kuwa mutane ƴan ƙasashen waje da na Nigeria da abokin Aryan na gurin ball da sauran su mutane sun cika gurin sosai ga Manyan malamai kusan shida Aryan ne sanye yake da shada ruwan golden sunyi an ko da Fauzal gaskiya ba ƙaramin kyauwa suka yi ba su Daddy da Uncle da Alhaji Zayyanu mai motocin da Malam liman da Abba dai dai ƙarfe 12:00 pm aka fara sanarwa ɗauren Auren su.


*AN ƊAURA AUREN ARYAN DA AMARYAR SA AYANAH AKAN SADAKI MILIYAN HUƊU ALLAH YA BASU ZAMAN LAFIYA DA ZURI'A TAGARI*..........


*Hassy Soja*

07063617906



⚡ *ARYAN&AYANAH*⚡



_Love and romantic story_


_*HASSY SOJA*_🌹✍🏻:

*T SOJA* 😉



🌹 *ELEGANT ONLINE* 🌹







_Bismillah Rahamani Rahim_


*Page __________57&58__________*

*AN ƊAURA AUREN ARYAN DA AMARYAR SA AYANAH AKAN SADAKI MILIYAN HUƊU ALLAH YA BASU ZAMAN LAFIYA DA ZURI'A TAGARI AN ƊAURA AUREN AFFAN DA AMARYAR SA AMRHA AKAN SADAKI MILIYAN BIYU ALLAH YA BASU ZAMAN LFY*



Addu'oi akayi agurin sannan malamai su tafi gida su Daddy da Abba da Malam liman Uncle da Alhaji Zayyanu mai motocin sai murna akeyi kamar me ango Aryan kuwa an sha kyau sosai fuskar sa kamar wanda ace masa Ummi ta mutu jiyake kamar ya haɗiye zuciyar sa fauzali ne ya kalle sa yace "dan Allah kayi murmushi kada agane kana cikin wani hali pls " murmusawa yayi sannan yace "muje gida dan Allah "da mamaki yake kallon sa yace "kamar ya muje gida"!? Affan ne ya karaso gurin yana murmushi muryar sa sukaji yace "Aslm Alkm yan uwana" Amin wslm ango kasha kamshi" dariya sukeyi sannan yace " Allah ya bada zaman lfy dan Allah ka riƙe mani kanwata please" Murmushi Aryan yayi yace "insha Allah kuma nagode sosai .



A cikin gida kuwa guɗa kawai ke tashi su Maa da Mommy sai washe baki ake Ummy kam ba'a magana saboda yau tana cikin farin ciki sosai ya bayyana a fuskar ta zazzaune muke a cikin ɗakin da sallama Mommy tashigo cikin ɗakin kallona tayi tace"My angel to an ɗaura Aure shike nan kin zama matar Aryan, wani irin faɗuwar gaba naji sai da hantar cikina ta kaɗa nace" An ɗaura kuma"!? Eh menene na tambaya kuma"!? Amrha da Aina'u suna zaune guɗa Aina'u tayi tace "Masha Allah gaskiya babu abun da zamuce sai dai Allah ya bada zaman lafiya wow, juyawa Mommy tayi har zata fita sai ta jiyo tana kallon mu tace"ku gyara zuwa anjima za'ayi walima insha Allah misalin ƙarfe 7:00 pm " to Mommy Allah ya kaimu"Amin fice wa tayi daga cikin dakin da gudu na tashi na shige toilet na rufe ƙofar da key wani irin kuka ne ya suɓuce mani kamar raina zai fita jikina har rawa yakeyi nace"shike nan Aryan ka cuce ni wayyo Allah na innalillah wa inna ilaihir raji un burin ka ya cika wayyo ni Ayanah, da sauri su Aina'u da Amrha suka taso suka zo dai dai kofar toilet din suka tsaya yana ƙwala mata kira amman ina sauti kukanta kawai sukeji.


Sai kusan awa ɗaya na fito daga cikin toilet din fuska na ya kumbure saboda tsabar kukan da nayi kaina har ciwo takeyi kamar zai raɓe gida biyu dafe goshi na nayi taso sukayi suka zo inda nake cikin tausayawa Aina'u tace "dan Allah my ƙawata kinyi hakuri please kin san dukk abun da ya faru kaddara ce sai ki rungume ta hannun biyu kin ga yanzun har kin sa ciwon kai ya kamaki.



Amrha tace "wannan gaskiya ne ki masu biyaya wallahi wata rana zakiyi farin ciki mai daurewa" ahankali na zauna saman bed ina ajiyar Zuciya ina sauraron su wani sabon kuka ne ya suɓuce mani ba shirya ba haka suka cigaba da lallashin na har na saka sannan Maa tashigo cikin ɗakin da sallama tace" tashi kije kiyi wanka, jikina babu kwari haka natashi na shige cikin toilet ɗin.


Bayan nayi sabon wanka wata mai make up tashigo tayi mani tunda ta fara mutane da ke shigowa cikin ɗakin suna kallona baki kowa ya saki tana gama make up din wani irin kyau sosai kamar wata aljana saboda kyauwan da nayi sai cewar ake wow Allah yayi halita gurin nan ni dai ban ce komai ba orange ɗin Atamfa mai ratsin baƙi na saka sannan su Mommy suka shigo karasowa gurina tayi tace "Masha Allah gaskiya ƴarinyata an sha kyau sosai murmushi dai nayi gyale orange ta yafa mani sannan ta riƙo hannuna muka fito daga cikin ɗakin harabar gidan muka fito mutane ne zazzaune saman kujeru, kusa da wata kujera aka zaunar da ni Malama Zuwairiya ce ta hau saman munbari sannan ta fara wa'azi mai shiga cikin jikin mutane ai kuwa ban san sanda kuka ya suɓuce mani ba muryar sa nayi yace "Amarya kukan amarci ake tun kafin aje gidan nawa"!? Ɗago jajayen idanuwana nayi mukayi ido huɗu da shi da sauri na ma ƴarda idanuwana ƙasa bayan ta gama wa'azin ne sannan tayi Addu'oi zaman lfy sai ta sauka ƙasa Aina'u ce ta fara raba kayan biki har da cincin da rubobi sannan mukadawo cikin falon gaba ɗaya muna zauna ƙasa.



Aryan kuwa tunda aka gama walima ya wuce gidan sa wanda ya gina saboda yana cikin damuwa kallon sa fauzali yayi yace "uhmm Ango kasha kamshi ko da yake ai ba'a kai Amaryar ba bale hhhh" wani mugun kallon ya bishi da shi saboda takaici ko magana ya kasayi ruwa ya watsa sannan ya fito ɗaure da towel yayi kwan ciyar sa saman bed ya dafe goshin sa...




Daddy ne yashigo tare da su Uncle da Alhaji bature da Malam liman gaba ɗaya kowa yana cikin falon gyara murya Daddy yayi yace "to Alhamdulillah lallai Allah yayi gaskiya da yace Aure ma rahama ne a mutane yau Allah ya bamu ikon Aurar da ƴaƴa guda ukku kuma Alhamdulillah Allah ya baku zaman lfy mai ɗaure wa, Ayanah! Ayanah!! Gabana yace rasss rasss rasss murya na na rawa nace"Naam Daddy " ajiyar Zuciya yayi yace "Allah yayi maki Albarka kamar ƴarda kikayi muna biyaya kema Allah ya saki farin ciki mai ɗaurewa Allah ya baku zaman lfy da haƙuri sannan kada kiyi wasa da sallah ki riƙe ibadar ki hannu biyu kinaji ko"!? Cikin kuka nace "eh insha Allah Daddy, yauwa Allah ya maku Albarka sannan amshi wannan key ɗin Mommy ta amsa tace "mota Daddyn yara kai masha Allah jama'a ku sanya mata Albarka kowa sai da saka Albarka sannan yayi addu'a sosai Mommy itama ta ɗauka tayi mani faɗa sosai itama Maa tayi nasiha mai ratsa Zuciya sannan tayi Addu'oi zaman lfy Ummy kuwa tace"ni kam dukk abun da zan ce kun riga kun ce sai dai abun da zan ce uwar mijinki ki ɗauketa amatsayin mu kamar ni kada ki bari awulaƙanta ta kinji ko Ubangiji Allah ya baku zaman lfy mai ɗaure wa, kuka nake sosai kamar raina zai fita Wasu ƴan gayu ne suka shigo bayan sun gama gaisawa sannan kuce mune mukazo ɗaukar Amarya Mommy tace "Masha Allah gata nan kuje Maa tace " ni ce uwar ta tare da ni za'aje riƙo hannuna tayi muka fito haka inaji ina gani aka raba ni da su Ummy motocin guda 30 suka zo ɗaukar mu shiga cikin motar akayi Uncle ne yazo buɗe ƙofar ya riƙa hannuna yace "riƙa wannan shine gatan kowa Allah ya bada zaman lfy" rufe kofar motar yayi ni kam babu abun da nakeyi inba kuka ba har driver yaja motar ya fita daga cikin gidan gudu ake shararawa wata haɗaɗar Unguwa ce mai shegen kyau ciki aka shiga sosai sannan aka iso gidan horn yayi da sauri mai gadi yazo ya buɗe masu get ɗin suka shigo cikin gidan gulove masu kyau kamar na,zinari saboda haɗuwar su kala kala suke irin red , blue, green, yollow , black , aka fara cewar wow kowa sai cewar yake wayyo Allah gaskiya Ayanah kin da ce da gida saura ƴan baya dai dai part ɗin Ummi akayi parking .


Maa ce ta riƙo hannuna muka fito daga cikin motar gaba ɗaya mutane nan suna bayan mu cikin gidan muka shiga zamu shiga cikin falon Maa tace "ƙafar dama zaki saka ahankali na saka kafata ta dama da sallama muka shigo cikin falon Hajiya kakus ce zaune sai su Momyn Hisham da Aunty Amarya da Mom sai Ummi dake gefen Hajiya kakus sai su Alhaji Zayyanu da Alhaji Ahmad da Uncle musa amsa muna sallama sukayi miƙewa tsaye Hajiya kakus tayi cikin farin ciki tace "barka da zuwa sabon gida kuma sabuwar Rayuwa " matsowa tayi tajawo hannuna muka ƙaraso Maa kam wani irin farin ciki ne ya mamaye mata Zuciya kusa ita ta zaunar da ni tace"masha Allah Amarya ƴar lalle, sai yanzun hankalinta ya sauka ga su Maa murmushi tayi tace "sannun ku da zuwa kun sha hanya, Dariya Maa tayi tace "wallahi kuwa to Hajiya ga Amanar ƴa na kawo maku dan Allah ku riƙa muna ita amana, jin jina masu kai tayi tace "insha Allah tazo gida kenan ai mu babu da wata matsala sai dai Allah ya bada zaman lfy "Amin tashi muje na kai ku part dinta tashi mukayi Hajiya kakus ta riƙe mani hannu har muka fita daga cikin falon tafiya muke sosai sannan muka iso wani irin haɗaɗin gida ne mai shegen kyau key tasaka ta buɗe ƙofar turawa tayi wani irin shegen kamshi ne mai dadi yafe dukan hancin mu saboda dadin sa har ƙara lumshe ido nake.


Muna shigowa cikin haɗaɗin falon purple da pink ne pentin ɗakin wasu shegun kujeru ne waɗan da suka amsa sunan kujera ga pilesma tv ƙatuwa kamar cikin gida saboda haɗuwar su tafiya muke har up muka hawa ɗakin biyu ne agurin amman akwai ɗan ƙaramin nisa tsakin ɗaya da na biyun buɗe na biyu Hajiya kakus tayi tace "Bismillah " rutse idanuwana nayi addu'ar nema tsari nayi sannan na aka shiga cikin ɗaki wani shegen zanin bed ne pink mai ratsin purple da black ahankali aka karaso da ni zaunar da ni Hajiya kakus tayi tace........


*Dan Allah kuyi hakuri yau kam mu haɗu page na gaba*

*Hassy Soja*

07063617906

⚡ *ARYAN&AYANAH*⚡


_Love and romantic story_




_*HASSY SOJA*_🌹✍🏻:

*T SOJA* 😉



🌹 *ELEGANT ONLINE* 🌹


*Dan Allah kuyi mani afuwa bani da lfy ne kwana biyu shiyasa kukaji ni shiru kwana biyu Amman yanzun Alhamdulillah*💃💃💃💃




*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I'm
selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Call me or Whatsapp me 08066268951
Or 09022823910






_Bismillah Rahamani Rahim_


*Page __________59&60__________*

Hajiya kakus tace "sannu ƴan nan bar na haɗo maki ruwa sai ki watsa nasan kin gaji sosai, ni dai fuskar na lulluɓe take da gyale orange sakina tayi sannan tajiya sai da ta matsa sosai sannan ta buɗe wata ƙofar shiga cikin toilet din tayi kusan minti biyar sai gata ta fito daga cikin toilet din tace "taso ki watsa ruwa sannan sai kiyi sallah " jikina rawa yakeyi sosai Maa ce ta riƙo hannuna muje har cikin toilet din gefen madubi na ciro towel ɗan ƙarami sannan tace "amshi wannan idan kika gama wanka sai ki ɗaure wannan" Amsa nayi nace "Uhmm Uhmm Uhmm dan Allah ki tsaya nayi sauri " riƙe haɓa tayi sai dai tayi murmushi tace "ok ina jinki" da sauri na ƙarasa gurin buɗe kofar glass ɗin nayi na cire kayan jikana nayi daga sai pant sai bres cire su nayi saman ɗan wani ƙarfe na ajiye su shaya na kunna ruwan dumi ne suka zubo mani cikin kuka ne ya su ɓuce mani har shasheƙar kuka nake sannan na haɗe kukan bayan na gama wankan fuska na na wanke sannan na ɗaura towel ɗin nayi alwala fito nayi daga cikin gurin kallona tayi tace "kukan dai kike har yanzun ko"!? Kina son na tafiya ta ne"!? Girgiza mata kai nayi sai ajiyar Zuciya da nakiyi.


Wata irin shegiyar rigar bacci ce haɗaɗa shara shara komai na jikin ka an gani idan kasaka ta miƙa mani tayi tace "saka wannan rigar" kallon rigar nayi sosai murya na na rawa nace "Maa wannan rigar fa ana ganin komai na jikina fa"!? Eh zaki fi jin saukin yin bacci shima mijinki sai zai sauki gurin kwanciya da ke" turo baki nayi cikin shagwaɓa Kwalla ne suka zubo mani cikin shasheƙar kuka nace "ni Allah wannan abu tayi ƙarama sosai ko fa cinyoyina ba kai ba" dariya maganar ta bata ɗaure fuska tayi tace "amshi ki saka ban son shimen banza da yofe" jikina babu kwari haka na saka rigar kamar ga jikina akayota kallon jikina nake ina turo baki hijabi mai hannu ta miƙa mani amsa nayi na saka har ƙasa sannan muka fito daga cikin toilet din su Hajiya kakus anan zaune saman kujera ƴar karama miƙewa tsaye Hajiya kakus tayi tace "Masha Allah yanzun zakiji sauƙin yin bacci" darduma ta shimfiɗa mani ƙaraso gurin nayi na hau saman sallayar sallah magriba nayi bayan na sallame miƙewa tsaye nayi natada sallah Isha'i bayan nagama sallah ne Hajiya Kakus tace "bari nazo" fita tayi daga cikin ɗakin bayan ta fita Maa ta kalle ni tace"my angel dan Allah kiyi masu biyaya kinga Matar nan har rawar jiki takeyi akanki kinji ko"!? Ɗaga mata kai nayi ina ajiyar Zuciya, magana tayiwa Aina'u tana ɗaga mata kai kallon mutane tayi tace "Amman kuje waje motocin yanzun ana jiran ku "haka suka fita daga cikin dakin bayan tafiyar su ne Maa tace "bari na amso abu waje nadawo da sauri ta fita daga cikin ɗakin sai da tayi minti biyar sannan Aina'u tace "my ƙawata ga jakarki da asuba idan kikayi wanka sai ki saka "ajiye mani Saman kujera amman dai an nan zaki kwana ku"!? Murmushi tayi tace "sosai ma kuwa tashi zaune nayi na hawa bed ina ajiyar zuciya ajiye jakar tayi sannan tayi tsaye tana kallona lumshe idanuwana nayi wayar ta ce ta fara ringigin ɗin wayar ta taji dauka tayi .


Tace "bari na amsa waya sannan" da kallo na bita da shi har ta fita zaune nake har na fara jin bacci zan kwanta ne naji ana Knocking ɗin kofar ɗakin Hajiya kakus ce tashigo cikin ɗakin hannunta ɗauke da kulolin abinci tace, tashi ki ci abinci sannan ki kwanta, tashi zaune nayi nace "Uhmm Uhmm na koshi sai dai ko Aina'u idan tashigo cikin ɗakin "Hajiya kakus tace "ayyah ai har sun wuce gida ki dai ci abinci sannan tajuya har zata fita Tace "Amma kina da alwala ko"!? Cikin jin kunya nace" eh Hajiya "to Alhamdulillah Allah ya bamu Alkhairi ficewa tayi daga cikin dakin sai yanzun nakejin yunwa rabuna da abinci tun ranar da akayi mani lalle saukawa nayi ƙasa na buɗe kulolin abinci farfesu naman kaji ne ɗaya kular da na buɗe shinkafar kaza ce sai kwai da wainar kwai cokali biyu nayi sannan natashi naje na kwanta bacci yayi awan gaba da ni.....


Aryan ne tare da fauzali cikin motar fuskar sa kamar wanda ace masa Ummi ta mutu haɗa rai yayi dariya fauzali yake har suka shigo cikin gidan part ɗin Ummi suka wuce koda suka shiga cikin falon Hajiya kakus ce zaune tana jiran sa bakin su ɗauke da sallama, kallon su tayi tace, haba mai gida yanzun dan Allah kun kyauta kenan ace an kawo ƴar mutane agidan nan Amman sai yanzun fa ƙarfe sha biyu tashi ka wuce gurin ta cikin jin haushi ya suke miƙe suka fita daga cikin falon part ɗin sa suka wuce har zai wuce, sai fauzali yace "to ni Ango ga kazar Amarya nan sai dai munzo cin abinci miƙa masa ledar mai zane yayi kallon sa yake da mamaki yace "wato har da kaza ma ka siyo "!? Murmushi yayi yace ""Eh mana dai ahankali kada aji ma ƴar mutane wlh" mtsss amsa yayi cikin jin haushi ya wuce cikin falon fauzali ya juya ya fita daga cikin falon.


Matatala ya hawa har zai shiga ɗakin sa sai ya kalle hannun sa yaja dogon tsaki sannan yajiya ya wuce ɗakin ta Knocking ɗin kofar ɗakin yayi ahankali ya turo kofar wani dadin kamshi ne ya dake hancin sa lumshe ido yayi kun torchlight yayi haske ne ya mamaye ɗakin hangota yayi kwance saman bed cikin tsawa yace "keeee! Keeee!! Wata irin zubur tayi jikinta har rawa yake saboda tsabar tsoro ɗaure fuska yayi yace "wato ke har damar bacci ta baki"!? Kallon sa take cikin jin haushi cikin ranta "to me zanyi masa"!? Afili kuma taɓe baki tayi tace "kamar ya " himmm! Jefe da ledar kazar yayi yace "to gashi nan tunda dama ku ƴan kauye babu abun da suke so kamar su ci sai kazae Amarya " wani irin takaici ne ya mamaye mata zuciya bata san sanda kuka ya suɓuce mata ba tace "wallahi ni nafi ƙarfin da azaka ce mani mayya kasan wace ce ni AYANAH!!! Oh! Dai wannan kuma matsalar ki ce batawa ba malam, ficewa yayi daga cikin ɗakin bin sa tayi da harara gyara kwan ciya ta nayi ko kallon ledar kazar banyi ba har bacci ya ɗaukeni.


_Asuba tagari_


Washe gari da safe wata irin mahaukaciyar yunwa ce ta taso mani jikina har rawa yake saboda tsabar jin yunwa tashi nayi jikina har rawa nashiga toilet na kurkure baki nayi sannan na fito kallon ɗakin nake ahankali na zauna najiyo abinci da Hajiya kakus ta kawo mani ko da na buɗe har yayi sanyi ɗauko kulolin abinci nayi na saka hijabina, fitowa nayi ina kallon tsarin gidan saukowa nayi daga saman bene kallon parlour nake sosai zan cinye sa saboda tsabar kyaun sa gefen na kalla an rubuta *KITCHEN* da manya harufa ajiyar Zuciya nayi cikin jin dadin na wuce cikin kitchen wow gaskiya kitchen ɗin ba ƙarya ya haɗu sosai haka nagama kallon kitchen sannan na ɗaura girkin shinkafar kaza minti biyu tukunyar tayi zafi sosai kashe gas ɗin nayi sannan na fito waje tafiya nake har zan hau saman bene najiyo muryar sa yace "idan kin gama shirmen naki sai kizo parlour inda magana da ke " ban san yana nan zaune parlour ba har sai da zan wuce naji muryar sa taɓe baki nayi na wuce ɗakina shi kuma Aryan tunda sanda ta shigo parlour yake kallon ta da gefen idon sa taɓe baki yayi ya cigaba da abun da yake, Ayanah kuwa tunda ta shige ɗaki ta zauna tana cin abinci bayan ta gama ne ta miƙe ta wuce cikin toilet ta watsa ruwa fito tayi da ɗaure da towel tana duba kayan da zata saka abun da ya bata mamaki shine kala biyu na ƙwari sauran kam dukk ƙannen kayan ne haushi cika ta ciro yellown abaya tayi tace "haba dai har naji dadin ganin wannan rigar sakawa tayi sannan ta zauna kusan minti sha biyar sai ta tuno da Aryan yana parlour......



Yana jirana dogon tsaki naja mtsss sannan na miƙe tsaye na ɗauke hijabi nasaka fitowa nayi ina kallon sa na ɗauke kaina, saukowa nayi daga saman bene kallon parlour kamshin da yaji ne yasan ita ce zagayowa nayi kujera dake kallon bene ita ce na zauna ina kallon gefena kallo ɗaya yayi mani sai yasaki wani munafukin murmushi sannan ya ɗaure fuska yace "Keeee!! Kina jina dai ko" ko kallon inda yake banyi ba, jin jina kai yayi yace "himm! Magana ta farko ita ce ni ke Auren ki ba ke ka Aure na ba dole ki kiyaye Umarni na bana son shishigi bana son rashin kunya doka ta farko ita ce Mopping da wanken toilet da girki kuma kullum ko kuma babu ruwan ki da shiga harka ta sannan ina ja maki kunne bana son ƙawayen banza da gyaran gida yazama dole gyaran daƙina yau doka zata fara kuma wlh ko da wasa kikayi masu da ni himm! Zaro ido nayi ina kallon sa nace"lallai kam tunda ga baiwar ka kenan ko"!? Ɗaure fuska yayi yace "wato Keeee!! Dai kunnen kashe gareki kenan"!? Sai dai na ruba kuma bazanyi wannan aiiiii wani irin kyakkyawan mari ne ya watsa mani wanda sai da nasaki wata irin ƙara cikin nuna isa da izza yace "wlh daga yau sai yau dukk ranar da kika ƙara mani wannan rashin kunya himm wlh zakiji babu sauƙi agurina mtsss yaja dogon tsaki sannan ya miƙe tsaye ya wuce har zai wuce, sai kuma yajiyo yace "ki tashi ki fara gyara mani part ɗina sannan kuma dukk wanda yazo gurin ki ki tabbas kin saka hijabi saboda babu muharmanki acikin su juyawa yayi yafice daga cikin falon.....


Kuka ne ya suɓuce mani ba shirya ba nace"ke nan haka zamu zauna kullum yana wulaƙantani wayyo ni Ayanah na shiga ukku na haka na cigaba da kukana babu wanda yake lallashina haka Natashi Ɗakin sa nashiga da sallama wani irin haɗaɗin ɗaki wow iya haɗuwa ya haɗu toilet na shiga na gyara sa sosai sannan na fito na gyara masa bed din sa na saka turaren ɗaki mai kamshi sannan na fito falo goge goge nayi ko ina jikina dukk yayi ciwo haka na haura sama na shige ɗakina ruwa na watsa sannan na fito cire kayan jikana nayi daga ni sa bres da pant riga da siket na saka na feshe jikina da turaruƙa masu shegen kamshi kwan ciya nayi saman gado bacci ya ɗauke ban shirya ba ban tashi ba sai ƙarfi 11:30am tashi nayi na fito falo Knocking ɗin parlour naji anyi saukowa nayi daga saman bene ƙarasowa nayi na buɗe ƙofar Hajiya kakus ce nagani tsaye bakin ƙofar murmushi ta sakar mani tace "ƴar nan " cikin jin kunya nace"Barka da safiya Hajiya" shigowa cikin parlour tayi zaunawa saman kujera tayi tace "Masha Allah ina mijina"!? Kamshin turaren sa ne ya game falon jiyowa nayi mukayi ido huɗu da shi da sauri na ɗauke kanta, da sallama ya shigo cikin falon ƙarasowa yayi yace "Uwar gida da ke babu wata " dariya tayi tace "rufa mani Asiri ni gadai uwar gida nan" zaunawa saman kujera yayi yace "an tashi lfy ya gajiyar biki"!? Ai gajiyar biki Alhamdulillah yauwa Aryan ga Amanar ka nan an baka dan girman Allah ka riƙe muna ita amana kaga yanzun kai ne uwar da ubanta kaine komai nata Allah ya baku zaman lfy ke ma dan Allah kiyi masa biyaya kinji ko"!? Cikin sanyin murya nace "insha Allah Hajiya komai wahalar sa zanyi tunda Aljannahata nake nema.


Masha Allah haka dai ta cigaba da muna nasiha sannan ta miƙe ta fice daga cikin falon shima Aryan miƙewa yayi ya wuce part dinsa da kallo na bisa taɓe baki nayi na cigaba da kallon waya na....



*A BANGAREN SU UMMY KUWA*


Ummy ce zaune cikin ɗakin su Amrha kayan Ayanah ne take haɗa guri ɗaya Mommy ce ta shigo da sallama juyowa tayi tana kallon ta Murmushi tayi tace "Aa Mommyn yara ke ce yanzun"!? Dariya tayi tace "wlh kuwa dama zuwa anyi na faɗa maki Daddyn su yana kiran ki" ajiye jakar tayi sannan tace "to muje dama kayan Ayanah ne nake gyarawa waɗan da za'a kaima ne" Allah sarki wlh nima inason zuwa gurin my angel cewar Mommy miƙewa Ummy tayi suka fito daga cikin ɗakin karasowa cikin falon

Please Login or Register in order to submit comment