Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɓata mishi.
sanin irin zazzafar soyayyar da Saifuddeen ɗin keyiwa Zaleeha yasa Ummi sanin cewa bazai taɓa iyayin haƙiƙanin barranta da ita ba.
Itakuwa Zaleeha asanyaye ta miƙe, cikin sanyin da ayanzu ya zama tamkar ɗabi'arta tace.
"Ummi ina Raleeya, da Hayatuddeen."
ɗan murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Raleeya na kitchine, Hayatuddeen kuma kinsan yau weekend yanacan yana baccin nasa da baya gajiya dashi."
Kanta taɗan jinjina, sannan tace.
"To bari inje kitchin ɗin in taya Raliya aikin".
Da sauri Ummi tace.
"A a jeki kwanta". Zata kuma yin mgna Ummi tace.
"Nace kije ki konta ki huta".
ganin yadda Ummi tayi mgnar cikin bada umarnine yasata cewa.
"To Ummi bari naje na ɗan kwanta."
Kai Ummi ta jinjina mata, saboda duk wani koke koken da tayi adaren jiya, Ummin najinta, hakanne ma yasa tasan cewa Zaleehan bata wani samu ishashshen bacci ba. Tana fitowa daga ɗakin Ummin kuwa, sukai karo da Hayatuddeen wanda da dukkan alama yanzu tashinsa, dan sai hamma yake ta zubawa tare da miƙa.
Ganin Zaleehan yasashi sakin murmushi, ƙarasowa yayi tare da kamo hannunta, cikin kulawa yace.
"Good morning my beautyful Aunty, ya jikin naki?"
Kanta taɗan jinjina masa alaman da sauƙi, idanunta ne suka sauƙa akan Saifuddeen wanda ke zaune akan kekensa ya basu baya, yana ta faman aikin danna wayarsa, saurin ɗauke idanunta daga kansa tayi, tare dayin ƙasa da kanta.
Dai-dai lokacin Raleeya ta fito daga cikin kitchine, gaisawa sukayi cikin kulawa kuwa Raleeya ke tambayarta jikinta, nan tace mata da sauƙi. Hayatuddeen ne ya kamo hannun Zaleehan, tare da zaunar da ita akan ɗaya daga cikin kujerun falon, cikin kulawa yace.
"Adda Zaleeha dan Allah minti biyu, ki jirani anan ina zuwa."
kai ta jinjina masa tare da sadda idanunta ƙasa tana wasa da ƴan yatsun hannunta.
Ameena ce ta buɗe ƙofar falon ta shigo bakinta ɗauke da sallama, shirye take tsab acikin kayan aikinta, ga kuma kekyawan ɗanta Adeel da ke riƙe ahanunta, shigowarta falon kuwa yayi dai-dai da fitowan Ummi daga ɗaki.
Jin ƙamshin turaren Ameenan ne ya sashi ɗago kansa ya kalleta.
ƙarasowa cikin falon tayi, da ganin Zaleeha kuwa sai taji gaba ɗaya ranta yayi ƙunci, ɗan durƙusawa tayi, aladabce ta gaishe da Ummi', fuska ɗauke da fara'a da kulawa Ummi ta amsa tare da miƙa hannu ta karɓi Adeel dake ta yi mata dariya irin tasu ta yara.
Ɗago kai Zaleeha tayi, karab kuwa suka haɗa idanu da Ameena'n, kasancewar dama idanun Ameena'n akanta suke, ta tsareta da idanu kamar ta samu tv. Cikin sanyi Zaleehan ta janye idanunta, tare da cewa Ameena'n'.
"Ina kwana." zazzaƙan muryar Zaleehan da Ameena taji shiya sanya bugun zuciyarta tsananta, wanda har yasa ta kusa daburcewa, cikin in ina ta amsa da "La fi..ya." dan zata iya rantsewa cewa bata taɓa jin murya me daɗin a zahiri irin ta Zaleehan ba.
Kallon Adeel dake hannun Ummi Zaleeha tayi, cikin sa'a kuwa yaron shima kallonta yake, murmushi tayi masa sai kawai ya buɗe baki yana mata dariya, wani irin kyau yaron yayi mata, musamman ma yanda dimples ɗinsa suka lotsa da yana dariyan, lokaci guda taji ya shiga ranta, hakan yasa ta miƙa hannu dan ta ɗaukeshi, babu ƙiwa kuwa yazo wajenta, karɓansa tayi tana sakin sassanyan murmushi. Ummi ne itama tayi murmushi cikin kulawa tace.
"Lallai Adeel yaga ɗiyarsa, tunda dai baiyi mata ƙiwa ba." Kallonta Zaleehan tayi da ɗan mamaki, kai Ummi ta jinjina tare da cewa.
"Ai me sunan Baba Malam ne."
Wani irin farinciki ne ya cika zuciyar Zaleehan, sai kawai ta rungume yaron ajikinta tanajin sonsa sosai aranta haka nan sai takeji kamar itace ta haifeshi in ba gizo idonta ke mata sai takega kamar yaron yana kama da ita, musamman dimples ɗinsa irin nata ne sak.
Dai-dai nan Hayatuddeen ya fito daga kitchine hannunsa ɗauke da cup, wanda aka zuba yoghurt acikinsa, akusa da Zaleehan ya zauna tare da miƙa mata yoghurt ɗin, cikin kulawa yace.
"Adda Zaleeha amsa kisha, al'ƙawari nayiwa Zakariyya cewar yau sai nasa kinci abinci, saboda haka dan Allah kisha kafun agama break fast." ɗan marairaice fuska tayi, sai dai kuma ita kanta tasan cewa tana matsanancin jin yunwa, hakanne ma yasa ta amsa, tare da ɗan sha kaɗan, kan Adeel da har yanzu ke kan cinyarta take shafawa, sosai yaron ya shiga ranta tana jin sonshi da ƙaunarshi har cikin ranta.
Duk wannan wainar da ake toyawa Ameena idanu kawai ta zuba musu, itakam Allah yasani bata gajiya da kallon Zaleeha, to itama da take mace, bata gajiya da kallonta, inaga kuma Namiji haka yasa kishinta kuma ninkuwa a ranta.
Hayatuddeen ne ya ɗago kansa ya dubi Ameena'n, murmushi yaɗan saki cikin kulawa da girmamawa ya fuskanceta tare da cewa. "Aunty Ameena ina kwana."
itama murmushi'n ta mayar masa tare da cewa.
"Lafiya Auntan Ummi, ya rigima." murmushi kawai yayi, batare da yace mata komai ba, ya maida hankalinsa wajen Zaleeha tare da kissing goshin Adeel dake kan cinyar Zaleeha, wanda da dane kuma ta tabbatar tsayawa zaiyi yayita mata rigima, amma yanzu gaba ɗaya hankalinsa naga Zaleeha.
Hakanne yasa asanyaye ta juyar da kanta ɓangaren Saifuddeen, ai kuwa idanunsu ne ya haɗe, dan dama kallonta ya keyi, murmushi ta sakar masa, domin tuni haushin nasa da takeji ya gushe, ayanda take matsanancin sonsa batajin zata iya dogon fushi dashi bare ta ɓata rawanta da tsalle, shiɗin ma murmushi yayi mata tare da miƙa mata hannunsa, ganin Idanun su Ummi baya kansu yasa ta kama hannun nasa, gamamakinta sai gani tayi yajawota dab dashi, har jikinsu na gogan na juna, kasancewar jiyan ba'a ɗaki ɗaya suka kwana ba, hakan yasa bata gaishesa ba sai yanzun, ahankali tace.
"Ina kwana." Kansa ya jinjina mata alaman lafiya, sannan ya tallafo haɓarta, kiss ya ɗaura mata akan kumatunta da kuma bakinta, baruwansa da wani jin kunya wai dan su Ummi na falon bare yasan idon Ummi baya kansu.
Gaba ɗayansu sunga abun da Saifuddeen din yayiwa Ameena hakan ne yasa suka janye idanunsu gefe, Zaleeha ma da tsautsayi yasa ta ɗago, idanunta sun gane mata abun da ya faru, kawar da kanta gefe tayi, tare da ƙara manne Adeel ajikinta, ko ajikinta itakam, bata ma ji wani abu adangane dasu ba, saidai zuciyarta ta tsegunta mata cewa. "Halan Ameenan matarsa ce kenan." Ummi kuwa, tashi tayi gaba ɗaya ma tabar falon, dan ta gano cewa wannan sabuwar kulawan da Saifuddeen ɗin ya fara bawa Ameena agabansu wani salone, kawai yayi ne saboda wata manufarsa ta daban. Ameena kuwa da gangan ta kamo lips ɗinsa itama ta tsotsa, cikin sanyin murya tace. " I will miss you dear" sake manna masa wani kiss ɗin tayi, sannan ta ɗan janye daga jikinsa, Hayatuddeen kuwa baki ya sake yana kallon ikon Allah,
Zaleeha kuwa sam bata ƙara ɗago kanta bama sai wasa takeyiwa Adeel wanda da ka gani kasan tana jin son yaron har cikin ranta.
Ƙarasowa inda suke Ameenan tayi, tare da sanya hannu ta ɗauki Adeel, tana sakin murmushi me ɗauke da ma'anoni kala kala, haka ta saɓa Adeel akafaɗanta ta fice daga cikin falon, wani irin farinciki takeji acikin ranta, wannan kiss ɗin da Saifuddeen yayi mata agaban Zaleeha ji take kaman kyautar zuciyarsa ya bata a gaban Zaleeha ji takeyi ya gama mata komai dan ko ba komai ya nunawa Zaleeha itama matarsa ce kuma yana sonta murmushi kawai take tayi.

Tashi Zaleeha tayi ta wuce ɗakinta, kusan rabin cup tasha yoghurt ɗin sannan ta kwanta. Acan falo kuwa Raleeya ce ta gama shirya musu abinci akan dinning area, Ummi ne tace da Hayatuddeen yaje ya ƙira Zaleeha tazo suyi beak, koda yaje ɗakin nan ya isketa tana bacci. Dawowa yayi ya faɗawa Ummi'n, hakan yasa Ummi tasa Raleeya ta ɗeba mata nata break fast ɗin daban.

Saida suka kusa kammala break fast ɗin, Ummi ta ɗago kanta ta dubi Saifuddeen wanda yake tsakalan chips yana kaiwa bakinsa, ahankali yake tauna abincin, yanayin komai nasa cikin nutsuwa.
Gyara zama Ummi tayi tare da ɗan muskutawa ta kamo hannunsa, ɗago kansa yayi, tare da sakarwa Ummin nasa murmushi.
Itama Ummin murmushi tayi masa, cikin kulawa tace.
"Ka bani key ɗin side ɗin Zaleeha,"
Fuska ya ɗan kwaɓe tare da mata alamu.
Shiga baisan inda key ɗin yakeba".
Kwaffa tayi tare da cewa.
"Uhumm yayi kyau." Fuska ya ɗan kele,
tsareshi da ido Ummin tayi tana mai nazartanshi kana tace.
"To Inaso kashirya anjima ka raka Zaleeha ta bawa Baba Malam haƙuri, ko kuma shima car keys ɗin naka duk baka san inda sukeba."
take yanayin fuskarsa ya sanja, kansa ya girgiza, tare da aje spoon ɗin hannunsa. Idanu Ummi ta zuba masa ganin ya mata alamun dan Allah tayi haƙuri, sai kuma yaja wheelchair ɗinsa yayi baya, tare da juyawa yabar wajen baki ɗaya,
da idanu Ummi ta bisa har ya fice daga cikin falon.



Wasa farin girki sannu sannu dai bata hana zuwa sai dai a dadde ba'a jeba



Littafina na kuɗine. in kina buƙata ga number 09097853276 katin mtn zaki turo na ɗari 300 ko kimin transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.




By
*GARKUWAR FULANI*
[17/09, 7:29 pm] +234 803 620 1562: Ngs,ego Jin baƙon ƙamshi ajikinsa ne yasa ta rumtse idanunta kana ta tashi zaune tana jifansa da wani irin kallo me ɗauke da ma'anoni da yawa.
Jitayi ranta ya ƙara matuƙar ɓaci, kirjinta kuwa har ƙuna yake mata, saboda tsabar kishinsa da take, menene ma'anar wannan ƙamshin da yake? wato hakan na nuni da cewa yazo ne ya nuna mata alaman da zata gane cewa ya je ɗakin Zaleeha.
Wani irin haushinsa ne taji ya kamata, take taji ranta ya cigaba da tafasa, ɗan ƙanƙance idanunta tayi tana binsa da wani irin kallo mai cike da so da gaurayen kishi, wanda har hakan yasa yanayin zafin kishinta, ya kasa ɓuya akan fuskarta.
Ganin irin kallon da takeyi masa ne, ya sashi ƙura mata ido cike da ɗan mamaki, dan zallan ɓacin rai da kuma kishi yake gani acikin ƙwayan idanunta.
Ahankali yaɗan turo wheelchair ɗinsa kusa da ita, tare da ɗan kai hannunsa zai taɓa ta, afusace ta ɗaga masa hannu, cikin wutar kishin dake cinta tace.
"Da Allah Karka taɓa ni banaso, kaje kawai, ka koma can inda ka fito, kaje can ka taɓa ta, tunda dama haka kakeso kuma ka zaɓa."
taƙare maganar tana ne sake ƙara sautin kukanta, wanda yake ɗauke da tsananin takaici da kuma azababben kishi. Shiru yayi cike da mamaki ya zuba mata kyawawan idanunsa, sosai yake nazartar ta, wuta-wuta haka yake ganin kishi acikin ƙwayan idanunta, ɓoyayyan ajiyar zuciya ya sauƙe, batare da tunanin komai ba, ya sake ɗan tura wheelchair ɗinta ya nufo gareta, asonsa shine ya ɗan kwantar mata da hankali sannan ya kuma rarrasheta.
Ganin haka yasa cikin matsanancin kishi tace. "Nace maka kada ka taɓani,sannan kuma kada ka matso kusa dani, kafita min aɗakina kawai, dama yarona ne ka kawomin saboda haka, kafitamin daga ɗaki, kaje can inda idan ka shiga kake jimawa, ka koma ka cigaba da jimawan ka!" Tafaɗi haka cikin kishin da ya rufe mata ido, har acikin ranta ƙuna takeji, kishin Saifuddeen din da kuma haushin Zaleeha da takeji suna neman tarwatsa mata zuciya ta mancema yau ranar Zaleeha ne sai takeji kamar girkinta ya kaimata abin kuwa baya rasa nasaba ne da saba ita kaɗai gareshi duk da tasan yanada wata matar amman yanzu sai takega kamar ita yayiwa kishiya.
Ganin yanda gaba ɗaya idanunta suka rufe yasa shi girgiza kansa, tabbas yasan ayanzu idanunta sun rufe, bazata taɓa fahimtar komai ba, juyawa yayi cikin nutsuwa ya fice daga cikin ɗakin, ko waiwayenta baisake yi ba.
Ganin ya fitane yasa ta fashewa da sabon kuka, tare da faɗawa saman gadon, hakanan takejin kaman tayi ta kurma ihu ko zataji sauƙin abun dake zuciyarta, ya zatayi da kishin Saifuddeen dake damunta? ina zata kai baƙincikin abun da takeji, akullum akuma koda yaushe, akullum zata ga Zaleeha saita ji duk ta raina kanta.
Saifuddeen kuwa kaitsaye ɗakinsa ya wuce.
Yana shiga ɗaga kai yayi ya kalli agogo, ganin ƙarfe 12:10 am na dare ne, ya sashi ɗan zaro idanunsa, dan ya shiga ɗakin Zaleehan ne tun 11, amma sai 12 yake fitowa kwata kwata baisan ya ɗauki lokaci acikin ɗakin har haka ba. Ahankali ya ƙarasa tare da rage hasken wutan ɗakin, kan haɗaɗɗen makeken gadonsa ya kwanta, kana ya jawo blanket ya rufa ajikinsa, wata irin sassanyar ajiyar zuciya ya sauƙe, tare da ɗan lumshe idanunsa, sosai yake mamakin mood ɗin da yaga Ameena aciki, sam bai taɓa ɗaukan cewa zafin kishinta har yakai haka ba, har yanzu yana mamaki, dan kwata kwata baiga dalilin da zaisa ta ɗau zafin kishi ta sanya aranta ba, aganinsa bai kamata ma tayi kishi da Zaleeha ba, dan idan da zata lura, Zaleehan ba wani damuwa tayi dashi ba, ko bayan haka ma bata nuna kishi akansa, amma ya lura gaba ɗaya tunda Zaleeha ta dawo gidan Ameena ta tashi hankalinta, Allah ma ya san zuciyarsa, shi adalci kawai yake son ya kamanta atsakaninsu bashi da niyar tauye haƙƙin kowa a cikinsu, domin ko wacce da matsayin ta a ranshi da zuciyarshi da rayuwarshi. Ɗan sake lumshe idanunsa yayi ahankali moment ɗinsu da Zaleehan ya dawo masa, lokaci guda yaji wani irin kasala ya saukar masa, take yaji tsikar jikinsa na zubawa, ga kuma wani irin fitinannen feeling dake neman hautsuna mai tunani, tunowa da taushin breast ɗinta dayaji a tafin hannunsa shi yasa yaji gaba ɗaya jijiyoyin jikinsa na miƙewa, harshensa yasa ya ɗan lashi kyawawan laɓɓansa, acikin ransa yace.
"Uhumm komai nata me kyau ne, yanayinta, fushinta, kukanta, tsoronta, dama duk wani yanayin da take ciki kyau yake mata."
tunowa da irin yanda take ta ƙif ƙifta idanu, yasa shi sakin wani killer smile, cikin zuciyarsa yace.
"baki kam akwaishi cakwai-cakwai amma sai shegen tsoro, kamar farar ƙura."
sake gyara kwanciyarsa yayi, tare da kai hannu ya ɗan dafe saman mararsa, da kuma manhood ɗinsa dake ta faman harbawa, tunanin Zaleeha kaɗai ya birkita masa lissafi, gefe guda kuwa ga kyawawan saman breast ɗinta, dake ta faman yi masa gizo acikin idanunsa, wanda yasa yaji yayi weak.

Ɓangaren Zaleeha kuwa Saifuddeen ɗin na fita, ta sake hayewa can saman gado ta takure, tare da matse jikinta waje ɗaya, sosai wani irin tsoro ya shigeta, musamman ma akan abunda yayi mata yanzun, tuna abunne yasa taji gaba ɗaya tsikar jikinta na tashi, tana jin wani iri ajikinta, blanket ta ja ta rufe jikinta, tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, cikin sakalci haɗi da zallan shagwaɓa, kaman yana gabanta tace. "Allah saiya sakamin, wai har zai gyaramin wuyan rigana, saikace shiya sakamin rigar ko ance masa ni ƴarin yace da sai an gyara min rigata". Tafaɗi maganar tana me sake naɗewa acikin bargon nata, zuciyarta cike take da fargaban kada ya kuma dawowa, gashi bata da key ɗin ɗakin balle ta rufe, ahaka dai atakure bacci me nauyi ya ɗauketa. Ɓangaren Ameena kuwa kuka tayi sosai, duk kuwa yanda taso bacci ya ɗauketa abun yaci tura, dan zuciyarta tafasa take, baƙin ciki da kishi sun hanata sakat, ga kuma wani sabon ƙuncin rai da tasamu kanta aciki, musamman ma da ta tuna da irin jimawar da Saifuddeen ɗin yayi anan ɗakin Zaleehan, tasan cewa yana ɗakin Zaleehan ne, saboda taƙira Hayatuddeen ne kan cewar ya kawo mata Adeel, sai yake shaida mata cewa Adeel ɗin na wajen Zaleeha, kuma Saifuddeen ya tafi zai ɗaukoshi, wannan abun shiya sanya taji ta tsani komai, take wani irin zargi ya ɗarsu acikin ranta, zuciyarta ce keta raya mata abubuwa, musamman akan jimawan da Saifuddeen ɗin yayi aɗakin Zaleeha, gashi wani ƙarin haushin, shine kwaso ƙamshin jikin Zaleehan da yayi ya kawo mata ɗakinta. Haka ta dinga juyi tana ta sambatun baƙin ciki da kishi duk akan Zaleeha, da ga ƙarshe ma ganin bacci bazai ɗauketa ba, saboda fitinannen kishin dake damunta yasa ta tashi ta zauna, sake saka sabon kuka tayi, saikace kamun aljanu can kuma ta miƙe taje tayi al'wala tazo taita nafilfili tana addu'o'in Allah ya sassauta mata zafin kishinta kuma Alhamdulillah ta ɗanji sanyi.

Washegari.

Ƙiran sallan asuban farko ne ya sauƙa acikin kunnuwanta, azabure ta ɗan farka, tana me kakkame jikinta, dan dama baccin nata atsorace tayi shi, ahankali ta zuro da kyawawan ƙafafunta ƙasa, bayan tayi addu'an tashi daga bacci, kaitsaye toilet ta wuce, ruwan zafi ta haɗa tayi wanka, tare da ɗauro alwala, koda ta fito wani jan jallabiya mai kyau na mata ta sanya ajikinta, sosai tigan tayi mata kyau dan tana ɗaya daga cikin na aurenta, kasancewar rigar ƙiran tukish ne yasa aka ƙawata jikinta da wani irin haɗaɗɗen ado, harma da hula akayi mata, duk da cewar rigar bata bayyana shape ɗin jikinta ba, amma ta yi mata kyau sosai, hijab ta sanya sannan ta tada sallah, saida tayi raka'atanul fajir, sannan tayi sallan asuban, koda ta idar Azkar tayi sannan taɗan taɓa karatun Alƙur'ani.
Tana kai karshe kuwa miƙewa tayi, wani ɗan ƙaramin vail ta yane kanta dashi, sannan ta fesa turarenta me dadin ƙamshi, wayarta ta ɗauka, sannan ta nufi hanyar fita daga ɗakin, cikin nutsuwa ta murɗa handle ɗin ƙofar ta fice. Kanta tsaye sashin Ummi ta nufa, bakowa afalon, hakan yasa ta nufi ɗakin Ummi kaitsaye, tana knocking kuwa aka bata izinin shigowa, murɗa handle ɗin ƙofar tayi ta shiga, anan kan sallaya ta samu Ummi najan carbi, durƙusawa tayi ta gaisheta cikin girmamawa, fuska asake Ummi ta amsa, mata. Bata wani jima aɗakin Ummin ba, ta miƙe tsaye, kaitsaye ɗakin Goggo Dada ta shiga, nan ta iske goggo dadan itama najan carbi, cikin girmamawa ta gaishe da goggo dada'n, haka goggo Dada ta amsa mata cikin kulawa da sakin fuska.
Koda ta fito daga ɗakin goggo dadan, anan falo suka haɗu da Raleeya, bayan sun gaisane, suka nufi kitchine saboda ɗaura breakfast, Raleeya ne me fere dankali, ita kuwa Zaleeha ferfesu take haɗawa, sai kuma sandwich, aikin suke cikin nutsuwa suna ɗan taɓa hiransu. Koda Ummi ta fito falo, ganinsu a kitchine suna aiki,yasa tayi murmushi, nan kan kujera ta zauna, tare da maida hankalinta ga TV inda take kallon Sunnah tv. Saifuddeen kuwa tunda ya tashi da asuba ya wuce masallaci bai dawo ba sai yanzu, tafe suke Hayatuddeen na riƙe masa saman kekensa, sai zuba yake yana basa labarai kala-kala, ahaka suka ƙaraso falon Ummin.
Ummi naganinsu haka ta saki murmushi, har acikin ranta tana godewa Allah daya haɗa mata kan ƴaƴanta, kana yasanya musu soyayyar juna azuƙatansu, wannan haɗin kan nasu shine matakin nasaran rayuwarta.
Ƙarasowa gabanta Saifuddeen yayi, cikin body language ɗinsa ya gaisheta, amsa masa tayi tana murmushi. Hayatuddeen ne yazo ya zauna akusa da ita, cikin kulawa ya kamo hannunta yace.
"Ummi kinsan me?" dubansa Ummi tayi da kyau, dan duk atunaninta serious magana ce, cikin nutsuwa tace.
"A'a saika faɗa." pink ɗin laɓɓansa wanda suke shige dana Hammansa ya lashe, tare da cewa.
"Wallahi Ummi ƙamshin girki nakeji tun fa kam mushigo cikin falon nan, tun da ga gate, to ni narasa a ina ƙamshin yake fitowa."
ya kare maganar yana ɗan kallon ƙofar kitchine. Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Ehem aikin kenan, to su Raliya ne suke dafa break fast."
Murmushi yayi tare da suɗe bakinsa, dan dama yunwa yakeji.
Dai-dai lokacin kuwa Zaleeha ta fito daga kitchine din hannunta ɗauke da food flask, lumshe kyawawan idanunsa da suka sauƙa akanta yayi, sosai tayi masa kyau cikin jan rigar saikace wata sarauniya, Raleeya ne ta fito da sauran kayan abincin da suka girka, nan suka shiga jerawa akan dinning table. Ameena ce ta shigo cikin falon, Adeel rungume akan kafaɗanta. Sanye take da uniform ɗinta na aiki tayi kyau sosai cikin shigar nasu.
Ƙarasowa cikin falon tayi, tare da durƙusawa ta gaida Ummi.
Cikin kulawa Ummi ta amsa, tare da tsare Ameenan da ido, cikin kulawa hankalinta a tashe, tace.

Please Login or Register in order to submit comment