Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kowa yaji saiya girgiza, saboda Maryam macece abun soyuwa ga kowa, bata banbance kowa natane.

Nan take labarin rasuwar ya kewaya gaba ɗaya cikin danginsu yan uwa da maƙoto, lokaci ɗaya kuwa iyalan familyn suka ruɗe da koke koke.
Saida Ya Habu yagama sanarwa kowa, kafun yake dannawa number'n Mama ƙira, wayar bata wani jima tana ringing ba Mama ta ɗaga, Kukan da taji Habun nayi ne yasa hankalin ta matuƙar tashi, cikin ruɗewa tace.
"Tun safe nakejin gabana na faɗuwa, Habu faɗamin wani abune ya samu Zaleeha ko?".
Jin abun da ta faɗa yasa Ya Habu sake fashewa da kuka, cikin matsanancin kuka yace. "Mama Maryam ne, Maryam tatafi ta barmu, Maryam tayi nesa damu ta yanda har abada bazamu sake ganinta ba, Mama Allah ya karɓi rayuwar Maryam ɗazun nan, shikenan Mama Maryam tatafi inda bazamu sake ganinta ba...."
Tunda Mama taji yace Maryam ta rasu, shikenan ta daina fahimtan sauran maganganun da yake faɗi, har wayar hannunta ta faɗi kasa batare da ta sani ba, akiɗime ta shiga jujjuya kanta, maganan rasuwan ƴarta ta Maryam ne ke yawo acikin kunnuwanta, ƙafafunta ne sukai mata nauyi, hannu ta ɗaura aka ta saki wani irin fitinannen kuka, wanda yasa Zahira fitowa daga cikin ɗaki da sauri, ganin Maman zaune daɓas aƙasa tana kuka, yasa Zahiran ƙarasowa cikin tashin hankali tace.
"Mama meya faru?." Cikin kuka Mama tace.
"Tarasu Zahira, Maryam ta rasu, tabar mana duniyar."
Wani irin ƙara Zahira tayi take kuma ta faɗi awajen tana kuka.

Can cikin asibiti kuwa Dr. Adnan ne ya nemo ambulance inda aka sanya gawar Maryam aciki.
Da ƙyar Baba Malam ya iya rarrashin Ya Ameenu, sai-dai kuma har yanzu bai-daina kuka ba,
Cikin minti kaɗan saiga Malam Adam yazo, zuwan Malam Adam ɗin shiya taimaka wajen rarrashin Baba Malam da kuma su Ya Habu da Mamy, suka bar kuka, amma Ya Ameenu kam hawaye sun kasa daina zuba, daga cikin idanunsa.
Malam Adam ne yayi duk wani abun da ya dace, shine ma yasanya Ya Ameenu amota, sannan dukansu suka nufo gida.

Nan gidan nasu kuwa tunkan isowan su tuni ya cika da ƴan uwansu na kusa, nan fa kuka ya dawo sabo, kaitsaye falon Baba Malam aka wuce da gawan, nan kan tiles ɗin falon aka kwantar da ita kudu da arewa tana fuskantar gabas Ya Ameenu ne ya zauna inda yasa gawan agaba ya fashe da wani irin kuka, wanda saida yasa kowa kuka awajen, ganin kukan yayi yawane yasa, Malam Adam ya tara gaba ɗaya jama'an gidan, nan ya bawa kowa alƙur'ani, yace sufara karatu, sannan ayanzu Maryam addu'a take buƙata, bawai kuka ba, nan aka fara karanta mata al'ƙur'ani, Baba Malam ne yasa gawan agaba, yana mata karatun al'ƙur'ani hawaye na tsiyaya daga idanunsa, Ya Ameenu kuwa muryarsa kwata kwata ta daina fita saboda tsabar kuka.

Ɓangaren Ameena kuwa, koda taga tafiyan su Baba Malam gida tare da gawan Adda Maryam ɗin, excuse ta ɗauka, dan batajin zata iya zama, mutuwar Adda Maryam ɗin yasa gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, koda ta fito daga asibitin, adai-dai-ta sahu ta hau, dan bawani iya mota tayi ba, shiyasa bata fitowa da motar da Saifuddeen ɗin ya saya mata wajen aiki, sannan kuma tasani sarai, duk wani abu na ƙarfe ba karɓanta yake yi ba, da ta fara amfani dashi zai lalace, shiyasa ma kawai ta ajiye motar, gudun kada Motar ta mutu da wuri.

Zaune suke dukansu afalon Ummi suna hira, lokacin dawowar su Saifuddeen da Ahmad kenan daga sallan magriba.
Bakinta ɗauke da sallama ta shigo ɗakin, jikinta amatuƙar sanyaye.
Da mamaki Ummi ke kallonta, dan kuwa tasan bayanzu ne lokacin dawowanta ba, kasancewar duty'n dare takeyi sai nanda kwana uku zata koma na rana, cikin kulawa Ummi tace. "Ameena lafiya kuwa naganki haka asanyaye."
Hawaye ne suka zubo daga cikin idanunta, hakanne yasa hankalin su Ummi tashi, hannu Raliya tasa ta amshi Adeel dake riƙe ahannunta, cikin sanyin murya tace.
"Ummi ɗazu fi ta na aiki nasamu ankai Adda Maryam ɗin su Zakariyya haihuwa, kuma bazata iya haihuwa da kanta ba, sabida yaron ya rasu a cikinta sai anyi mata theater, kuma anyi mata theater'n, an ciro ɗan ba rai, bayan anfito da ita daga ɗakin theater'n ne kuma Allah yayi mata rasuwa, Ummi Adda Maryam ɗin su Zakariyya ta rasu."
Ta ƙare maganan tana kuka, don dama ita akwaita da tsoron mutuwa, kona wanda bata sani ba ma kuwa. Salati su Ummi suka sa, cikin matsanancin tashin hankali Ummi tace.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Maryam ta rasu? Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!." taƙare maganar hawaye nabin kan fuskarta, Raliya ma salatin tayi take kuma sai idanunta suka kawo ƙwalla, Kuka Ummi ta fashe dashi, tare da sanya hannu ta rufe fuskarta, haka nan rasuwar maryam ya daki zuciyarta, yatuno mata rasuwar Abbansu Saifuddeen da Ya Nuruddeen ɗinsu sosai kuka yaci ƙarfinta.
Saifuddeen kuwa hankalinsa ne ya tashi matuƙa, sakamakon jin rasuwar Adda Maryam ɗin, Ahmad ma dake gefe shi da kansa saida yaji ƙwalla a idanunsa, saboda alokacin bikin Zaleeha da Saifuddeen sosai suka ɗan saba da Adda Maryam ɗin, kasancewar itace ta tsaya akan duk wani abu da ya shafi bikin, macece me sauƙin kai, da sakin fuska.

Hayatuddeen ne ya shigo falon afujajan fuskarsa gaba ɗaya tayi caɓa caɓa da hawaye, dan yanzun Zakariyya ke sanar dashi, rasuwar Adda Maryam ɗin, yazo faɗawa su Ummi kenan ya iske su ahaka, faɗawa jikin Ummi yayi tare da sakin kuka, cikin kukan yace.
"Ummi dagaske Adda Maryam ta rasu, yanzu Zakariyya ke faɗamin, Ummi Zakariyya kuka yake sosai har kaman zai shiɗe."
ɗan shafa bayansa tayi, tare da ciresa ajikinta, dan kukan nasa, ƙara mata nata kukan zaiyi.
Duban Saifuddeen wanda yayi ƙasa da kansa tayi, kana ta kai duban ta ga Ahmad, cikin sanyin murya tace. "Ahmad kuje can gidan Baba Malam ɗin da Saifuddeen"
Jin jina kai Ahmad yayi, nan ya miƙe tsaye, zunbur Hayatuddeen yayi tare da cewa zai bisu, basu hanashi ba, haka suka shiga mota, kai tsaye suka nufi gidan Baba Malam, zuciyoyinsu cike da alhinin abun da ya faru.

Ummi kuwa miƙewa tayi ta shige ɗaki, dan taji mutuwar Maryam din sosai, tabbas Maryam yarinyace me hankali, da kuma daɗin zama, uwa uba mutunta na gaba da ita, Ameena ma asanyaye ta koma ɓangarenta, Raliya kuwa bayan Ummi ta bi, ɗauke da Adeel akan kafaɗanta.

Koda su Saifuddeen suka isa gidan, Ya Habu wanda idanunsa suka kumbura shi yayi musu jagora zuwa falon Baba Malam, domin anan gaba ɗaya mazan familyn suke tare, sun saka gawan agaba suna tayi mata karatun alƙur'ani, bayan sunyiwa Baba Malam ɗin ta'aziyya da kuma Ya Ameenu wanda har yanzu idanunsa ke tsiyayar da hawaye, nan dai sukayiwa sauran jama'an dake cikin falon gaisuwa, alƙur'anin suma suka ɗauka suka soma karantawa, muryan kowa na tashi amma banda na Saifuddeen, danshi koda yaushe saidai yayi karatunsa azuciyarsa.

Can Abuja kuwa, Ya Ahmad hankalinsa amatuƙar tashe yake, yayi kuka harsaida yaji numfashinsa na ƙoƙarin ƙwacewa, haka Aunty Lubna ma tsakaninsu babu me rarrashin wani, sam baiduba cewa dare yayi ba, haka ya haɗa kayansa, inda yasa Aunty lubna ma tahaɗo nata kayan dana yaransu, duk da ƙaramin yaronsu data ƙara haihuwa, nan suka zuba yaransu amota suma suka shiga, kaitsaye suka kama hanyar Gombe, dan bayajin zai iya bari har gobe kafun ya taho, gaba ɗaya ma ya manta da wani batun hawa jirgi, ya ƙudurta aransa cewa bazai taɓa tsayawa ba harsai ya gansa acikin garin Gombe, haka yake tuƙin mota yana hawaye, tsananin tausayin mahaifinsu yakeji, dan yasan Baba Malam ɗin saiya fisu jin mutuwan Maryam ɗin, saboda kowa yasan Baba Malam, to yasan akwai ƙauna me zafi tsakanin sa da Maryam, daga gefe guda kuwa idan ya tuna da ɗan uwansa Ameenu, sai yaji kukan nasa ya tsananta, saboda yasan mutuwar Maryam ɗin zata wujijjiga Ameenu, domin kuwa yasan Ya Ameenu'n nayiwa Maryam wani irin ninkekken so.

Zakariyya kuwa wanda yasha kuka har dana fitar hayyaci ne, ya jawo wayarsa, number'n Zaleeha ya nema tare da danna mata ƙira.
Dai-dai lokacin kuwa Zaleeha na kwance akan ƴar katifarta, gaba ɗaya yau ɗin tun safe tarasa mekeyi mata daɗi, hakanan take yawanjin faɗuwar gaba, da kuma tsinkewar zuciya, wanda bata san dalili ba, saidai addu'a kawai take ta yi abakinta, kasancewar kwana biyun Balkeesu na yawan matsa mata da ƙira, hakan yasa, yau ta sanya wayarta a silent, dan kwata-kwata bata son damuwa, wannan dalilin yasa, sam bataga ƙiran da Zakariyyan keyi mata ba.
Zakariyya kuwa saida yayi mata 10 missed calls, ganin bata ɗaga ba yasashi fashewa da wani sabon kuka, da ƙyar Hayatuddeen ke iya tausansa.

Su Saifuddeen basu bar gidan Baba Malam ba, sai wajen ƙarfe shaɗayan dare.
Dan bayau ne za a kai Maryam din makwancinta ba, dole sai tayi kwanan keso, gobe kuwa da ƙarfe goma insha Allah za ayi sallan jana'izar ta, koda suka koma gida direct ɗakinsa ya wuce, inda ya murzawa ƙofarsa key, sam yau baison Ameena ta dameshi, dan ƙwarai rasuwar Adda Maryam ta daki jiki da zuciyarshi.

Ɓangaren Mama kuwa taso tahowa yau ɗin, amma babu abun hawan da zata hau tazo, haka taci kuka har idanunta suka kumbura, Zahira ma kukan take sosai, bata iya rarrashin Mama, haka Maman ma bata iya rarrashinta Maman Mama da Babantama sosai mutuwar Maryam ta shigesu.

Agidan Baba Malam kuwa kwana akayi anawa gawan Maryam karatun alƙur'ani, yanda suka ga safiya haka suka ga dare, kab gidan babu wanda ya iya runtsawa, Mamy tayi kuka harta godewa Allah, idanunta sunyi luhu luhu dasu, sam bata banbance su Maryam da ɗanta na cikinta, har gaban abada kallonsu take mazaunin ƴaƴanta na cikinta, haka suma sun ɗauketa uwace, basa taɓa banbantata da mahaifiyarsu, wannan dalilin yasa shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakaninsu, sau da yawa Maryam saitayi shawara da Mamy, batayi da Mama mahaifiyarta ba, haka ma Zakariyya duk wata damuwarsa koda ta kuɗi ce, Mamyn yake faɗawa, dan gaba ɗaya uwa suka ɗauketa.

Washegari ana idar da sallan asuba kuwa Ya Ahmad wanda suka kwana ahanya suka samu isowa gidan, nanne fa wani sabon kuka ya tashi, dan ganin gawan Maryam da kuma yanda ƴan uwansa ke kuka yasa gaba ɗaya hankalinsa yayi masifar tashi, haka yazauna yana kuka kaman ƙaramin yaro.


Zakariyya kuwa koda ya sallame sallan asuba, wayarsa ya ɗauka still ƙiran Zaleeha yayi amma no answer, nan ya shiga rubuta mata saƙo kamar haka.
_"Adda Zaleeha Ina ta ƙiranki bakya ɗagawa ko, kowa yaƙira wayanki bazaki ɗaga bako?, saboda kinsawa kanki zuciyar kafurci aranki, kin bijirewa Baba Malam, kin bijirewa kowa, kin gujewa gaba ɗaya danginki, kinƙi bin umarnin mahaifin mu, kin tafi can wata uwa duniya cikin kafurai kinje kin zauna, wataƙila ke kam bazaki dawo ba harsai gaba ɗayanmu mun ƙare, har sai kin rasa kowa naki na a faɗin duniya sannan zaki dawo, shikenan kici gaba da zama Adda Zaleeha, Adda Maryam kam tatafi ta barmu, tabar mana duniya'n, tayi nesa damu inda bazamu ƙara ji da ganinta ba yadda kika gujewa dangi duk suma sun guje miki gashi babu wanda ya tunaki,sannan nidana tunakin na kiraki baki amsaba."_
Yana rubuta saƙon yana kuka sosai, yana gamawa kuwa ya tura mata, inda ya kifa kansa ya cigaba da kuka."

Da duru-durun Asuba Mama da Zahira da wasu ƴan uwanta suka samu isowa gidan, ganin gidan nasu acike shiya ƙara ɗaga musu hankali, Nan Mama ta buɗe ɓangarenta ta shiga, anan falonta ta zauna tana wani irin kuka me cike da ban tausayi da tsantsar nadama.

Zaleeha kuwa yau makara tasoyi, tana tashi tayi alwala tayi salla, tana nan zaune akan sallaya tajiyo sallaman Aisha, cike da ɗan mamaki ta amsa mata tare da bata izinin shigowa.
Aishan ne ta shigo ta zauna hannunta ɗauke daɗan kula, agaban Zaleehan ta aje kulan tare da cewa.
"Kinganni da sassafe ko, wallahi kinsan yau ƙarfe 6 dai-dai muke da lecture shiyasa da zan fito nace Inna tabani abun karin kumallonki na kawo miki."
Murmushi Zaleehan tayi, tana ƙoƙarin cewa wani abune taga screen ɗin wayarta ya kawo haske, hakanan taji ƙirjinta ya buga, zuciyarta ta tsinke, jawo wayartata tayi tare da dubawa, text message ta gani da sunan Zakariyya, nan ta cire wayan a key, tare da shiga cikin message ɗin.
Hannunta na ɓari jikinta na rawa, haka tashiga karanta message ɗin, maganansa na kusa da na ƙarshe shine abun dayasa taji gaba ɗaya duniyar ta tsaya mata kanta yayi wani irin mugun sarawa duhu ya wulgawa ganinta, azabure ta miƙe tsaye, cikin wani irin gigita haɗi da kiɗima da tsananin tashin hankali ta dannawa numbern Zakariyyan ƙira, bugu biyu kuwa ya ɗauka, yana kara wayar akan kunnensa ya saki kuka, abun dayasa hankalin Zaleeha tashi kenan, lokaci guda bakinta ya soma ɓari, murya asarƙafe tace. "Zak....kar iya, ina Adda Maryam, meya sameta, mekakeson faɗamin Zakariyya?"
Cikin matsanancin kuka Zakariyya, yace.
"Adda Maryam tarasu Zaleeha, Adda Maryam ta rasu tun daren jiya, tatafi inda bazata ƙara dawowa ba, tayi nisa nisa irin na har abada....."
Kuka ne ya ci ƙarfinsa hakan yasa ya kasa ƙarasa maganan.

Tun afaɗan maganganunsa na farko, ta dainajin komai, duk wani abu najikinta tsayawa yayi, wayar hannunta ne ta sulale inda ta faɗi ƙasa, wani irin ƙara ta saki take kuma ta faɗi awajen sumammiya, cikin matsanancin tashin hankali, Aisha tayi kanta tana jijjigata, haɗi da ƙiran sunanta, ihunta da su Elizabet sukaji ne yasasu shigowa aguje, ganin Zaleehan asume yasa Elizabet dafe ƙirji cikin ɗaga murya tace.
"Innalillahi, a madadin tace Oh jesus meya ke faruwa?" Uncle solomon ne ya fita da gudu, bajimawa ya shigo hannunsa riƙe da kofin ruwa, ƙarasowa yayi inda ya ɗan yayyafawa Zaleehan ruwa afuskarta.

Azabure tatashi, cikin wani irin tashin hankali, damƙo Aisha tayi tana me jujjuya kanta, take kuma sai ta fashe da wani irin kuka mai matuƙar tada hankali, cikin kukan take ja da baya, tana me sake girgiza kanta, hankalinta amatuƙar tashe tace.
"Aisha Adda Maryam, Adda Maryam ɗina ta rasu, Adda Maryam tabar duniya batare da na sake sanyata a idanuna ba, wayyo Allah na wayyo ni, kaicon rayuwata, kaicona !!!" Wani irin azababben kuka ta saka kukane mai cushe zuciya da numfashi, lokaci ɗaya ta miƙe tsaye wayarta kawai ta ɗauka tare da buɗe jakanta, kuɗi ta ɗauko wanda batamasan ko nawa bane, takalmi ta zura aƙafafunta, ƙoƙarin fita daga cikin ɗakin take Elizabet ta riƙota cikin kulawa tace.
"Zaleeha ina zakije, dan Allah kitsaya ki nutsu tukun"

Faɗawa jikin Aishan tayi tana wani irin kuka, kanta ta girgiza cikin kuka tace.
"Adda Maryam ɗina Uncle Solomo Addana, Adda Maryam ɗina ta rasu"
Hawayen tausayin Zaleehan ne suka kwaranyo daga cikin idanun baki ɗayansu cikin sanyin murya Aisha tace.
"Muje to na rakaki ki hau mota, amma kafun nan ki kimtsa tukunna."
Kai Zaleeha ta girgiza cikin matsanancin kukan dake neman shiɗar da ita ya tafi da rants.
Hannunta Aisha ta kama suka nufi ƙofar fita daga gidan Solo da martasa na biye dasu a baya.
Gaba ɗaya Zaleeha bata cikin hayyacinta, hakanne yasa Aisha mannata da jikinta, domin kukan da Zaleehan keyi yasa bata ko iya ganin gabanta.
Suna kawo bakin titi kuwa sukai sa'a nan suka samu wata mota, wanda kaitsaye Gombe zata taho, da kwai ma mutane cike acikinta, Aisha ce tayi mata komai, tasata acikin motar, hannun Zaleehan dake kuka ta kamo, nan ta ɗan ɗaga mata hannu, itama hawayene ke zuba akan fuskarta, murya asanyaye tace.
"Allah yajiƙanta yasa al'janna tazamo makoma agareta, kiyi haƙuri kinji Zaleeha, dukkan me rai dama mamaci ne, kowa lokacinsa yake jira, dayazo kuma babu jinkiri."
Kai Zaleeha ta jinjina, tare da sakin sabon kuka, nandai Me motar yaja suka tafi, kowa dake cikin motar kallon yanda Zaleeha ke kuka suke, wasu kukan nata ya damesu, wasu kuwa matsanancin tausayinta ne ya kamasu, domin kukan da take irin kukan nanne me karƴar da zuciya, kukan da take, kukane me fitar da irin tsananin tashin hankalin da take ciki, kukane da duk me imani dole zaiji tausayinta.



Sbpejg Acan gidan Baba Malam kuwa, kamar yadda Maryam ta buƙata kafun rasuwarta, Ya Ameenu da kuma Baba Malam ne sukayi mata wanka, wanda da ƙƴar suka iya daure zuciyarsu, nan ma Ya Ameenu saida ya durƙushe awajen yayi kuka sosai, har saida yaji numfashinsa na ƙoƙarin cushewa a ƙirjinsa, Baba Malam ma hawaye ne keta tsiyaya daga cikin idanunsa, haka dai suka kammala yi mata wanka, Ya Ameenu ne ya zura mata likkafani, sannan yayi mata duk wani abun daya dace, sosai jikinsa yake rawa, sakamakon kukan da yakeyi, ga wani irin jiri dake neman kadashi.
Bayan sun kimtsa ta ne suka koma gefe suka zauna, dan kuwa da sauran lokaci, ƙarfe goma ne za a sallaceta, yanzu kuwa ƙarfe 9 ne dai-dai.

Can ɓangaren Zaleeha kuwa, tunda ta shiga cikin motar, ta tura kanta tsakankanun cinyoyinta har zuwa yanzu bata ɗago ba, kuka take sosai harsaida numfashinta ya soma ƙoƙarin ɗaukewa, sosai motar tasu ke tsula gudu akan titi, hakanne yasa cikin abun dabai wuce awa uku ba suka iso cikin garin Gombe, nan cikin tashan gombe line aka sauƙe su, zuwa lokacin idanunta sun kunbura sunyi luhu-luhu dasu,
kaitsaye bakin titi ta nufa, wani mai adai-dai ta sahu wato keke napep ne, ya tsaya agabanta tare da ɗan leƙo kansa, cikin kulawa yace. "Ranki ya daɗe tafiya ne?".
Bata iya cewa dashi komai ba, kawai faɗawa cikin keke napep ɗin tayi, nan ta jingina kanta da jikin keken, kana ta rumtse idanunta, wasu hawaye masu ɗumi ne suka silalo daga cikin idanunta, dubanta me adai-dai-ta sahun yayi, cikin yanayi naɗan mamakin ganin hawaye akan fuskarta, yace.
"Hajiya ina zamu ne?".
Kasa amsa masa tayi domi , bakinta yayi mata nauyi sosai, batajin bayan kuka zata iya motsa laɓɓanta dan tace wani abu, wayarta dake hannunta ta kunna, cikin text message ta shiga, ataƙaice ta rubuta masa.
"New G.R.A, da kuma layin da zai sauƙe ta."
miƙa masa wayar tayi, amsa yayi ya karanta, yana gama karantawa ya miƙa mata wayar, cikin ransa yace.
"Masha Allah wannan gata kyakkyawa amma kuma da dukkan alama kurmace bata magana, amma dai Allah yayi baiwar kyau anan, ko me yasata kuka kuma oho?" Ganin zancen zucin bazai kaisa ko ina ba, ya sashi tuƙa keken nasa yaja sukai gaba.
Kamar yanda ta rubuta masa arubuce kai tsaye cikin G.R.A ɗin ya nufa da ita, har kuwa cikin layin da tayi masa kwatancen ya kawo ta, gaba ɗaya bata cikin hayyacinta saboda haka batasan da cewa sun iso ba, dawani idanu zata kalli ƴan gidansu? da wani bakin zata basu haƙuri? mezata ce dasu? da wani idanun zata kalli gawan Adda Maryam ɗinta? Da wanne ƙafar zata shiga gidansu da wanne ido zata kalli Baba malam me zata ce mishi?.
waƴannan tambayoyin sune abun da suka cika zuciyarta, juyowa me adai-dai-ta sahun yayi, cikin kulawa yace.
"Ranki ya daɗe mun iso fa."
Sai alokacin ta buɗe idanunta da suke alumshe, gaba ɗaya kuɗin dake hannunta ta damƙa masa, wanda ita kanta bata masan ko dubu nawa bane, idanunsa ya waro waje, cike da mamaki, dai-dai lokacin ita kuma tafice daga cikin napep ɗin, ƙofar gidan nasu cike yake da jama'a wanda suka fara taruwa danyin sallan jana'iza, tsaye tayi tana kallon tankamemen gidan nasu, lokaci guda kuma wasu hawaye masu tsananin zafi suka fito daga cikin idanunta, da ƙyar take iya jan ƙafanta haka ta nufi cikin gidan, bataji bakuma ta ganin kowa agabanta, hakan yasa tafiya kawai take, sai faman cin tuntuɓe take tayi, amma bata ko kulawa, da wani dutse ta buge har saida babban ƴar yatsar ƙafarta ta fashe, amma koda kaɗanne bata ji zafi ajikinta ba, domin kuwa zafin dake cikin zuciyarta, ya zarce na wannan ciwon, wannanne yasa wasu daga cikin mutanen da suka zo jana'izan suka tsura mata idanu, saboda yanayinta ya gama nuna cewa bata cikin hayyacinta.
Tana jefa ƙafanta acikin gidan taji wani irin abu ya daki zuciyarta, kaitsaye sashin Baba Malam ta nufa, sai faman gauraya hanya take, tana zuwa dai-dai bakin ƙofar shiga falon Zakariyya yazo zai fito sukayi karo da juna, amatuƙar mamakance Zakariyya yasoma ja da baya yana komawa cikin falon, dai-dai lokacin kuwa nan cikin falon Baba Malam ne zaune yana kuka mai tsananin taɓa zuciya, kuka yake sosai wanda hakan yasa gaba ɗaya mutanen falon suma suka fara zubda ƙwalla, cikin kuka murya na rawa Baba Malam ke cewa.
"Ya Allah ka jiƙan Maryam kayi mata rahama,ya Allah ka ƙara mana haƙurin rashinta.
Tabbas mutuwa ta yanke mana ƙauna, mutuwa ta nesantani da ƴata me tsananin biyayya agareni."
Sai ya kuma saki shessheƙan kuka mai cike da ciwo a zuciya murya a disashe yace.
"Inama ina ma da ace mutuwa tana bada zaɓi.
To wallahi dana bata zaɓi ta ɗauki min Zaleeha a doron duniya tabarmin Maryam, dana bata zaɓi ta nesantamin Zaleeha daga wannan duniyar ta barmin Maryam! Da ta ɗauke Zaleeha dana huta da baƙin cikin da take ƙunsamin."
Ya ƙare maganar yana kuka sosai.
Waɗannan maganganun sune suka dira acikin kunnuwan Zaleeha, Zakariyya kuwa bakinsa na rawa, cikin ɗan ɗaga murya yace.
"Adda Zaleeha!." Ƙiran sunan Zaleehan da yayi, shiya sanya gaba ɗaya mutanen falon suka kai dubansu ga ƙofan shigowa, ae kuwa tabbas suka ga Zaleehan ce tsaye, hawaye na shatata akan fuskarta kaman an buɗe famfo, dai-dai lokacin kuwa aka fito da gawar Adda Maryam daga ɗakin Baba Malam, angama kimtsata tsaf saura ai mata sallah kawai akaita makwancinta na gaskiya.
Cikin wani irin gigita Zaleeha ta ɗaga ƙafanta da niyar ƙarasowa cikin falon, Baba Malam ne ya ɗaga mata hannu, alaman dakatarwa, kanta ta shiga jujjuyawa tana kallon gawar Adda Maryam ɗin, take ta saki wani irin firgitaccen kuka mai tsananin ƙarfi, tare da sulalewa anan jikin ƙofan falon, tana wani irin kuka mai tada hankali.

Daga Ya Ahmad zuwa kan sauran ƴan uwanta kuwa babu wanda ya dubeta, dai-dai za afita da gawan Adda Maryam ɗinne, Ya Ameenu yasake sakin wani irin kuka mai tsuma zuciya, take kuma sai wani irin jiri ya ɗebesa haka yatafi luuu, ya faɗi ƙasa sumamme, abun daya ƙara ɗaga hankalin su Baba Malam kenan, Cikin kuka Baba Malam yace amiƙo masa ruwa, Zakariyya wanda ke kuka sosai ne ya miƙowa Baba Malam ɗin ruwa, nan Baba Malam ya ɗan yayyafa ruwan akan fuskar Ya
Ameenu'n, saida ya ɗauki kusan mintuna 7 bai farfaɗo ba koda ya farfaɗo kuwa da wani irin kuka mai tsanani ya tashi, kuka yake sosai tare da rirriƙe Baba Malam yana nuna masa gawar Adda Maryam, Wannan abun shiya ƙara sanya gaba ɗaya mutanen falon kuka, cikin kuka Baba Malam yasanya hannu ya dafa kafaɗan Ya Ameenu'n, cikin matsanancin

Please Login or Register in order to submit comment