Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a iyaka waya ya tsaya kamar yanda ka faɗa da farko, amma taɓa jikin wata mace, wanda ba muharamma ta ba gaskiya bazan iya ba."     
Hararansa Khamis yayi tare da cewa. 
"Shiyasa nace bazaka taɓa wayewa ba, yanzu mene amfanin kallon BF matuƙar bazakanemi inda zaka gusar da sha'awan ka ba? hmmm nidai wallahi shanawa ma yanzu na fara ehe."     
Murmushi kawai Hayatuddeen yayi tare da playing vedio'n sa ya cigaba da kallo, yana mejin wani irin abu acikin jikinsa, sau dayawa yakanji kamar ya daina kallo, amma kuma zama da Khamis yasa kallon BF ya zame masa tamkar wani kallon film, yayi sabo da ganin BF sosai, saboda haka koda yace zai daina sai yaji ya kasa, duk da cewa yasan kallon BF din ba kyau, amma sosai idan yana kallo yakejin kansa cikin wani irin shauƙi, saboda  yanajin cewa shima yanzu yazama saurayi shekara 20 da yake dasu, sunsa yanajin kansa kaman ɗan 30 years.
Shida kansa yasan da taraiyar sa da su Imran tafi mishi daɗi da al'khairi to abin ta kaicin Imran F.C.E yake Sulaiman kuma da Isma'il Kashere University suke. Zakariyya kuma da yake nan cikin G.S.U ɗin sai kuma ya kasance Department ɗinsu ba ɗayaba, tofa wannan dalilin ne ya rabashi da tsoffin abokansa a makaranta ya haɗashi da wannan ɗan banzan khamis ɗin mai ƙafafu kamar faskaren wawa.

Wannan yana ɗaya daga cikin illar abokai, dole iyaye mu lura da abokan yaranmu muddin sun fara tasawa.
Zakiyi shekara 14 kina bawa ɗanki/ƴarki tarbiya mai inƙanci to. Tofa daga shekara 15 zuwa 18 akai ashirin zaki fara yaƙi da gasa da abokanshi da zasu fara bashi tasu tarbiyar da in kinyi sakaci da addu'a dasa ido cikin awa ɗaya zasu kore taki tarbiyar nan su ɗaura tasu, shike nan sunyi nasara a kanki sun cuci rayuwar yaronki damake kanki, hattara garemu iyaye mu kula...!

Tashi tsaye Khamis yayi tare da cewa. 
  "Saika tayi ae, kazauna nan a haka kada ka nemi ƙarin wayewa akan wanda kake dashi, ni kaga ma tafiyata, saboda yau ƙarfe 7 dai-dai muna da wani show me zafi a night club, nasan ma idan nace kazo ba zuwa zakayi ba."                  
Kai Hayatuddeen ya jinjina tare da cewa.       
"Saimun haɗe gobe, danni ma nasan driver ya kusa zuwa ɗauka na,  aje night club lafiya amman banda ni kam, bazanci amanar hamma da Ummynmu ba."       
Dukan wasa Khamis ya kai masa, sannan ya juya ya fice daga cikin class ɗin.                 
Bawani jimawa shima Hayatuddeen ɗin, sule driver yazo ya ɗaukeshi.                           

Ƙarfe takwas na dare dai-dai  yadawo daga masallaci, kaitsaye part ɗinsa ya wuce, kasancewar akwai wani aikin sirri wanda zai gabatar, domin ansashi binciken wani riƙaƙƙen ɗan fashi, wanda ya addabi mutane, sannan kuma har zuwa yau ankasa gano inda yake, saboda hakane ma aka danƙawa Saifuddeen ɗin ragamar case ɗin ahanunnsa, kasancewar sun san ya ƙware wajen iya computer, da computer kaɗai zai iya gano musu inda mutumin yake.          
Yana  shiga ɗaki kayan jikinsa ya soma ragewa, inda ya zauna daga shi sai 3 guater da kuma farar singlet, laptop ɗinsa ya jawo tare da sanyata  gaba, nan ya maida gaba ɗaya hankalinsa ga aikin da yakeyi.             

Da misalin ƙarfe 9 kuwa Ameena tashigo cikin ɗakin.    ganin cewa yana gudanar da aiki me mahimmanci,  yasa batayi ƙoƙarin damunsa ba, kan gado kawai ta ɗale tare da kwanciya, sama-sama taɗan latsa wayarta daga haka bacci ya ɗauketa, ko data'n ta dake akunne bata kashe ba.    
Shikuwa Saifuddeen har wajen 12 na dare yakai yana aikin bincike, cikin sa'a kuwa yagama haɗa duk wani information da yake so, dan kuwa ya gano inda mutumin yake, saida ya turawa ogansu komai kafun yake rufe laptop  ɗinsa, nan ya ɗauro alwala sannan yazo ya kwanta, ganinta haka bata rufe jikinta ba, yasashi rufa mata blanket, tare da gyara mata konciyarta, cikin mintuna kaɗan bacci ya ɗauke sa.      

Washegari kuwa ya tashi da ayyuka masu yawa akansa,  hakan yasa tunda ya fita daga gidan bai dawo ba sai wajajen 3pm,  nan ma dai part ɗin Ummi ya zauna.   Koda dare yayi ya tafi zuwa ɓangaren su, nan yasamu Ameena har tayi bacci, yaji daɗin hakan kuwa, don dama baiso ya isketa idanunta biyu, gudun kada ta ce zata ƙara neman wani abu daga garesa.              
Aikinsa ya ɗan taɓa kafun bacci ya ɗaukesa.       

Yauɗin ma dai baitashi da niyan zaman gidan ba, dan yanzu aikin nasa yaɗau zafi wani abun dole sai ya fita da kansa yaje ofishin sirri na DSS.  
Cikin nutsuwa yagama kimtsa wa, cikin wani lallausan yadi me kyau da tsada, yayi kyau matuƙa, Ameena dake tsaye tana kallonsa ne tasaki murmushi, tare da ƙarasowa kusa dashi,ido ya ɗan zuba mata ganin ta sunkuyo kanshi a hankali ta dai-daita fuskarsa da nata, batare da yayi  aune ba sai kawai jin bakinta yayi, acikin nasa tanayi masa tsosan sweet,  sam bai hanata ba saboda haƙƙin tane, saidai kuma baiwani biye mata ba, cikin mayen soyayyarsa ta ɗago idanunta ta kallesa, kallo ɗaya yayi mata yaɗan ɗauke kansa, murmushin yasakar mata tare da shafa gefen fuskarta, cikin body language ɗinsa yayi mata alama kan cewa.
"Saiya dawo."
Fatan al'khairi tayi masa, yana fita tafaɗa kan gado, tare da sakin ajiyar zuciya.       
Shikuwa  Saifuddeen saida ya biya ta wajen Umminsa kafun ya fito, inda sule driver yayi driving ɗinsa suka fice daga cikin gidan.

Ameena kuwa yau a ɓangaren Ummi ta wuni, ba ita ta koma sashinsu ba sai da magrib ta gabato.      
Tanayin sallah kuwa ta ɗauki tsumin ta ta sha, tare da turara jikinta da turaren ƙamshi.
Nan dai ta kimtsa kanta tsab, dan tana matuƙar begen mijinta, kwana uku kacal amma tayi mugun missing lallausan jikinsa.     
Duk da cewa ya jima da dawowa amma bai shigo gidan ba saida  yayi sallan Isha, ɓangaren Ummi yaje suka ɗan taɓa hira, kafun ya komawa part ɗin nasu.        
Yana shiga ɗakinsa ya iske Ameena zaune akan gado, tasha ado cikin sleeping dress masu kalar pink.                 Yau ita da kanta ta haɗa masa ruwan wanka. 
Koda ya fito daga wankan, amsan towel ɗin hannunsa tayi, nan tashiga goge masa ɗan danshin ruwan dake jikinsa, haka dai yaɗan kimtsa inda ya hau kan gado ya kwanta. Itama Ameenan kwanciya tayi akan gadon, tare da  zagayowa ya zama suna fuskantar juna,     ɗan ranƙwafowa tayi tare da kamo hannunsa ta ɗaura akan waist ɗinta,   bakinta ta ɗaura akan nasa,  inda ta kamo laɓɓansa tana sucking,  lumshe idanunsa yayi cikin ransa yace.  
"Oh ni Saifuddeen naga takaina, nadawo kaman wani alawa, ko yaushe tana cikin tsostsotseni ita ko gajiya ma batayi ne."     
Ameena kuwa gaba ɗaya ta fara manta inda take, sosai take romancing ɗinsa,  gane abun da take nufi yasashi, kasa hanata abun da takeso, saboda haƙƙinta ne, idan ya hanata sai Allah ya tambayesa.                     Kamar dai wancan daren haka awannan daren ma Ameena ta more Saifuddeen,
Ido ya lumshe dai-dai lokacin data zauna kan cinyoyinshi suna fuskantar juna,
Zaleeha yake jida gani a cikin jikinshi da zuciyarshi, shiyasa a take lafiyarshi ta harba ya miƙe ƙam yana ta harbawa da cika,
Ajiyan zuciya ya sauƙe da ƙarfi jin ta haɗe kanta dashi, yana mai mmkin duk abinda fa  Ameena zata mishi baya tashi har sai dai in ya tuno Zaleeha ya kawota cikin ransa,
Haka nan yake jin tausayin Zaleeha dan wallahi Allah yasan karonta dashi bazai mata ta daɗiba, ya guturta kashe bakin tsiwar nan a dare ɗaya,
yanaji a jikinsa tabbas Zaleeha matarsace zata dawo da ƙafafunta zai kuma yi maganinta yana dai-dai ƙugunta, a haka dai yana cikin tunanin Ameena tayi ta bidirinta a jikinshi, ido ya ɗan lumshe sai da aka ɗan zo bakin boda ne, sai ya jawota jikinshi ya ruggumeta da ƙarfi tare da sauƙe tagwayen numfarfashi.

Dan gane da gajiyar jiki kuwa, sai ma abun daya ƙaru, don kusan yau zaice yamafi ranan jin gajiya, sam bayason wahala, bazaice Ameena bata gamsar dashi ba, sannan bazaice bayajin daɗin kasancewa da ita ba, saidai ajikinsa yanajin tabbas akwai wani  babban gurbi wanda bata iya cikewa, hakanan yakeji kamar akwai wani abun da ta rasa baijin irin gamsuwar da yake buƙata ba, hakan kuma baya rasa nasaba da bata iya jure tsawon lokacin da yake buƙata, yana buƙatar gamsuwa ta sosai da sosai ita kuwa Amina macece dole tanada rauni.         
Wanka yayi sannan ya dawo ya kwanta, ajiyar zuciya yaketa sauƙewa dan yagaji sosai, itama Ameenan kwanciya tayi bayan tayi wanka, haka takejin ranta ƙal, bata da wani sauran damuwa.
Hannunshi ya ɗan sa a hankali ya s....!






sbpeny. Shafa gefen fuskarta, yayi har zuwa wuyanta,
ido ta zubawa jajayen laɓɓansa da bata gajiya da tsotsansu. Shi kuwa janye hannunshi yayi a hankali kana gyara kwanciyarsa.


Washegari kuwa gidan nasu ya karɓi baƙoncin Adda Maryam da kuma Ya Ameenu, dan dama Ya Ameenun turawa Saifuddeen ɗin saƙo dakansa yasanar masa da zuwansu.
Aɓangaren Ummi Maryam ɗin ta sauƙa, cikin girmamawa kuwa suka gaisa da Ummi, nan taƙara basu haƙuri akan abun daya faru, tare da yi wa Ummin murnar ƙarin auren Saifuddeen.
Hayatuddeen dakansa ya je ɓangaren Ameena inda yace tazo su gaisa da Adda'n Zaleeha, wato Adda Maryam ɗin, jin haka yasa Ameena tasanya hija binta, nan ta nufo ɓangaren Ummi'n.
Cikin girmamawa suka gaisa da Ameena', sosai Adda Maryam tasaki jikinta suka sha hira da Ameena'n, hakan kuwa yasa Ameena taji daɗi sosai, take taji ƙaunar Adda Maryam ɗin ya cika zuciyarta.
Hira sosai suka sha, sai wajajen Sallan la'asar Ya Ameenu yazo ya ɗauki Adda Maryam ɗin suka koma gida, turarukan wuta masu ƙamshi Ummi ta haɗawa Adda Maryam ɗin, nan tayi ta mata godiya, saboda Maryam macece da bata rena kyauta, komin ƙanƙantan abu idan kabata zata nuna maka farin ciki kana kuma zatayi maka godiya sosai.
Bayan zuwan Adda Maryam da kwana huɗu ne.
Saifuddeen ya turawa Ameena saƙo kan cewar tashirya yanaso zasu fita.
Koda Ameena taga text message ɗin sosai zuciyarta yayi fari, wani irin daɗi taji, karon farko kenan da zata fita tare dashi.
Wanka tayi inda ta kimtsa kanta cikin wani haɗaɗɗen lace mai laushi, babu laifi kuma tayi kyau.
Koda zasu fita saida tabiya ɓangaren Ummi tayi mata sallama.
Nan ta fito dan Saifuddeen ɗin yace tasameshi amota, tana ƙarasawa jikin motar tasa ta buɗe, nan tashiga ta zauna agidan baya, inda shima anan yake zaune, sosai yayi kyau cikin shigar shadda dake jikinsa, inda ya kafa hula mai kalan coffee akansa.
Yayi kyau ƙwarai, hakanne yasa ta kasa ɗauke idanunta akansa, shikuwa kallo ɗaya ya mata tare da ɗan gutun murmushi kana ya kauda kanshi dan ya lura in yabar lips ɗinshi kusa da ita zata cafesu yanzu tayi sabon nata.
Sule driver ne ke driving ɗin motar.
Kaitsaye G.R.A gidan Baba Malam suka nufa.


Agaban tanfatsetsen gate ɗin gidan sule driver ya tsaya tare da danna horn, cikin mintuna kaɗan aka wangale masa gate ɗin ya tura hancin motar ciki.
Yana gama dai-dai-ta parking ɗin motar kuwa ya buɗe motar ya fito, zagayowa yayi inda ya buɗewa Saifuddeen ɗin murfin motar, tare da fito masa da kekensa.
Cikin nutsuwa Saifuddeen ɗin ya hau kan keken, Ameena kuwa da kanta ta buɗe murfin motar ta fito, sosai tashiga ƙarewa yanayin gidan kallo, tabbas gidan yayi kyau, cikin ranta tace.
"Zanso ganin wannan Zaleeha, idanuna sun zaƙu dason ganinta sosai, inason ganinta sosai a zahiri ido da ido kodan naga me take dashi wanda ya ɗauke hankalin Saifuddeen da dangishi ji wai an kwasota tazo ta gaida iyayen kishiyarta, wannan abu yayi masifar ci mata rai badan ma Ummy ta gaya mata gidansu Zaleeha zasuje ba ai ita a zatonda ko ɗan wani garding zasu je to koma meye haɗina da gidan".
sosai tsarin gidan ya tabbatar mata da nagarta da darajar masu gidan.

Zakariyya wanda ya fito daga ɓangaren Mamy ne ya hangosu, cikin sauri ya ƙaraso garesu, fuska ɗauke da tsananin farin ciki yace.
"Oyoyo Hamma Saifuddeen, yau kaine agidan namu."
murmushi Saifuddeen yayi tare da miƙawa Zakariyyan hannu, suka yi musabaha, cikin girmamawa Zakariyya ya dubi Ameena, fuska ɗauke da murmushi yace.
"Sannu da zuwa Aunty Ameena."
Murmushi Ameena tayi tare da cewa.
"Yauwa Zakariyya ya makaranta?".
tasan sunan Zakariyyan ne saboda, yawanci tana ganinsa wajen Hayatuddeen.
Zakariyyan ne yayi musu jagora zuwa sashin Baba Malam,
Suna tafene tana mai maganar zuciya.
"Uhum kalli ƙaninta shi da yake na mijima yanada kyau irin kyan da ba'a gajiya da kallon fuskarsa inaga ita mace." sosai taji kishin Zaleeha ya daki ranta tana masifar son Saifuddeen shiyasa kuma take masifar kishinsa, ya zatayi da ranta randa zataga Saifuddeen yashiga ɗaki ɗaya da wata mace sun rufe ƙofa ina zata sa ranta?."
A haka tana zancen zuci suka isa cikin gidan
kasancewar Mamyn ma bata sashinta tana nan wajen Baba Malam ɗin.
Koda suka shiga da matuƙar farin ciki Baba Malam ya tarbesu, cikin girmamawa haɗi da mutuntawa suka gaisa, yaji daɗin ganinsu ƙwarai, nan Mamy ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye, itama taji daɗin ganinsu hakanan, saidai kuma ganinsu haka yasa taji sha'awan inama ace da Zaleeha ce, tabbas tasan da zuciyar Baba Malam sai yafi haka sanyi.
Cikin body language Saifuddeen suka sha hira shida Baba Malam, sosai Baba Malam yayi musu nasiha mai shiga jiki, Mamy kuwa kayayyakin humra ta haɗawa Ameenan ta bata, sosai kuwa Ameenta taji daɗi, tabbas taga kirkin mutanen hakan nema yasa ta ɗanji zafin kishinta ya ɗan ragu akan ƴarsu dan ita a zatonta Mamy ce maman Zaleeha.
Nan dai sukayi musu sallama, inda har bakin motarsu Mamy da Baba Malam ɗin suka rakasu. Kaitsaye gida suka dawo, inda Saifuddeen yayi masauƙi a falon Ummi.

Washegari yau ya kamana monday sannan kuma yaune Ameena zata fara zuwa aiki nan Federal Medical Center wato (F.M.C) Dan angama yi mata komai, inda kuwa suka amsheta batare da wani matsala ba, saboda takardunta masu kyaune.

Kamar kullum yau ma saida taje ta gaishe da Ummi, kasancewar babu wadataccen time yasa sama-sama taɗan taya Raliya aiki, dan kuwa ƙarfe 7:30 ne dai-dai lokacin zuwa wajen aikin nata, suna kammalawa ta koma ɗakinta, nan ta kimtsa kanta cikin kayansu na nurse, wato riga da wando farare da kuma ɗan madaidaicin hijab, kayan suna mata kyau ba laifi, sannan kuma basa fidda tsiraicin ta, don basu kama jikinta ba ko kaɗan.
Tana gama kammala shirin nata, taɗauki ƴar handbag ɗinta, kai tsaye ɗakin Saifuddeen ta nufa, nan ta iskesa yana aiki ya saka laptop ɗinsa gaba, zama tayi anan kusa dashi, ɗago kansa yayi ya kalleta, murmushi ta sakarmasa, kana ta miƙe, ƙarasowa gabansa tayi, ɗan ranƙwafowa tayi tare da manna masa kiss akan laɓɓansa, cikin soyayya tace.
"Kakulamin da kanka saina dawo."
tana faɗin haka ta juya tana me ɗaga masa hannu, murmushi yasakar mata tare da ɗaga mata hannu, tana ficewa kuwa ya sauƙe ajiyar zuciya, cikin ransa yace.
"Alhamdulillah, aini naji daɗin fara zuwa aikin naki ma, nasan ko bakomai zakina dawowa agajiye, daganan kuma zan huta da jarabanki, da kuma wannan tsotse tsotsen naki Allah kiyaye hanya hajia rabo tawo."
Murmushi yayi tuno wasu abubuwan da Ameena ke mishi shida kanshi yasan Ameena ta sonshi irin zazzafan so ɗin nan shiyasa yake ƙoƙarin ganin ta samu nitsuwa dashi.
Kansa ya maida ga laptop ɗinsa inda yaci gaba da aikinsa cikin kwanciyar hankali.
Sai dai can cikin ransa yana jin ɓaƙin cikin duk fa abin take mishi ta taɓa yiwa wani ƙaton,
A saman lips ɗinsa yace.
"Waya sanima iya sau dubu nawa ya kusanceta wata ƙil shinema ya maida jarabebbiya yana ɗaya daga abinda yake sashi kasa sakin jiki da ita.

Ameena kuwa Sule driver ne yakaita wajen aikin nasu, cikin ɗaya daga cikin motar Saifuddeen wanda baiwani cika hawanta sosai ba.

*** ***

Alhamduillahi akwana atashi asaran me rai, rayuwa tana ta tafiya kwanaki sun shuɗe i zuwa makonni makkonni su juya i zuwa watanni.

Yau Ameena da Saifuddeen suke cika wata biyu da sati biyu cif-cif da aure, harzuwa yau kuwa Saifuddeen bai taɓa jin son Ameena acikin zuciyarsa ba, sai-dai kuma yana iyaka ƙoƙarinsa wajen ganin ya sauƙe haƙƙinta dake kansa, sannan kuma yanajin daɗin aikin da yakeyi, ga kasuwancinsa na tafiya. ɓangaren Ameena kuwa sosai rayuwa ta miƙa mata, domin Saifuddeen bai rageta da komaiba duk abinda takeso zai mata in ta buƙaci nitsuwa dashi kuwa yana iya ƙoƙarin shi, kana tana zuwa aikinta cikin kwanciyar hankali, idan ta dawo daga wajen aiki kuwa haka Ummi takesa Hayatuddeen yakawo mata abinci har sashinta, sosai takejin daɗin zama da Ummi da kuma su Raliya, wanda ayanzu takejin cewa sun zame mata ƴan uwa, haka kuma aduk lokacin da take da buƙatar Saifuddeen baya hanata sannan kuma aduk ƙarshen sati yakan tambayanta ko tana da wani buƙata na kuɗi? koda tace batada shi kuwa, yakan bata wasu kuɗi yace ta riƙe watarana ko zatayi amfani dashi.

Sai dai a cikin ƴan kwanakin da suka wuce gaba ɗaya takan kasa ganewa kanta, hakanan take fama da matsanancin ciwon kai, sannan kuma bata wani jin daɗi, sai-dai kuma abun baishiga jikinta ba, dan tanayin komanta batare da gajiyawa ba.
Yaudai tunda ta fito wajen aiki takejin yanayin jiri naɗan ɗibanta, haka dai ta share, har zuwa kusan la'asar, jin abun na tsanantawa ne yasa tayi tunanin cewa kodai yunwa ne takeji, hakan yasa, batare da lokacin tashinsu yayi ba, ta ɗauki excuse, kaitsaye Napep ta tara ta nufo gida.
Koda tashigo cikin gidan ɓangaren Ummi ta nufa, dan har wani ji take cikinta na murɗawa, hakan yasa ta al'laƙanta abun da cewa, yunwa ne kawai keson takurata. Afalo ta iske Ummi da Hayatuddeen wanda dawowansa daga makaranta kenan, jakarta ta ajiye, zama tayi akan sofa tare daɗan ƙaƙalo murmushi, cikin son daurewa yanayin da takejin kanta aciki tace. "Ummi sannu da gida."
Cikin kulawa Ummi tace. "Yauwa Ameena har kuntaso daga wajen aikin?."
Girgiza kai tayi tare da cewa.
"A'a wallahi, kawai dai naɗanji yunwa na damuna ne shine nace bari na gudo gida."
Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.
"Ayya sannu to, Raliya na kitchine bara nace ta zubo miki abinci kici ko". Ummi taƙare maganar cikin kulawa.

Akunyace Ameenan ta miƙe tare da cewa.
"Bari naje na zubo da kaina kawai Ummi kada asata wahala."
Nan tamiƙe ta wuce kitchine ɗin.
Ummy kuwa cewa tayi.
"To inaga fa gwara Sule ya rinƙa kai miki abinci bana son wuni da yunwa da kikeyin nan."
Tana ƙoƙarin shiga kitchin ɗinne tace.
"Ba komai fa Ummy in naji yunwa ina sayan abu inci kinga wani Lokacin kuma inama tafiya da abinda zan ci."
Kai kawai Ummy ta jinjina, ita kuwa Ameena.
Raliya ta iske tsaye tana ta ƙoƙarin haɗawa Saifuddeen pepper chicken soup.
Cikin kulawa Ameena tace.
"Sannu agogo sarkin aiki."
Murmushi Raliya tayi tare da faɗin.
"Ke kuma likita bokan turai ba."
Dariya sukayi su dukansu, nan Ameena ta buɗe food flask ɗin da aka zuba haɗaɗɗiyar fried rice aciki, plate ta ɗauka inda ta ɗebi kaɗan, coslow ta zuba asaman shinkafan sannan ta buɗe wata ƴar kula wanda ke ɗauke da liver sauce, kaɗan ta zuba akan abincin, sannan ta sanya spoon tundaga cikin kitchine ɗin tasoma ci. Dubanta Raliya tayi tare da sakin murmushi, har acikin ranta tana ƙaunar Ameenan badan komai ba kuwa saidan ƙaunar Saifuddeen da Ameenan keyi.

Saifuddeen kuwa shigowarsa cikin falon kenan, yana riƙe da kwalin holandia milk inda yake sipping da kaɗan kaɗan.
Dai-dai lokacin Ameena ta fito daga cikin kitchine ɗin, hannunta riƙe da plate ɗin abinci.

Ɗan jim tayi tare da lumshe idanunta, lokaci guda taga wani duhu naneman mamaye ganinta, taku ɗaya zuwa biyu tayi, taji gaba ɗaya jikinta ya saki wani irin jiri mai ƙarfi ya kwasheta, nan tatafi luuuuu tafaɗa kan kujera, take kuwa plate ɗin hannunta ya faɗi, abincin ya tarwatse acikin falon.
Arazane su Ummi da Hayatuddeen sukayo kanta, cikin tsananin damuwa Ummi tace.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Ameena! Ameena lafiya kuwa?." aruɗe Ummi tayi maganan tana me jijjiga Ameena'n, Saifuddeen ne ya tuƙa wheelchair ɗinsa inda ya ƙaraso cikin sauri, hannunsa yakai yaɗan taɓa fuskar Ameena'n, tare da ɗan bubbuga kumatunta.

Ahankali taɗan buɗe idanunta wanda sukayi luhu-luhu dasu, dishi-dishi haka take ganinsu.
Hannunta ya kamo ya riƙe acikin nasa, cikin kulawa ya ɗaura hannunsa akan goshinta, jin zafi ajikinta yasa shi ɗago kansa ya kalli Ummi.
Jin jina kai Ummi tayi tare da cewa.
"Hayatuddeen miƙomin wayata naƙira Dr Adnan."
Cikin sauri kuwa Hayaruddeen yamiƙo mata wayan nata.
Dialing numbern Dr Adnan ɗin Ummi tayi, bugu biyu ya ɗauka, nan ta shaida masa abun dake faruwa, cikin sauri kuwa yace.
"To Ummy ganinan zuwa."

Anutse Saifuddeen ya gyarawa Ameenan kwanciyarta akan kujera, inda har yanzu yana riƙe da hannunta acikin nasa. Hakanne yasa Ummi taji wani irin sanyi acikin ranta, saboda dama burinta ne taga Saifuddeen ɗin na kulawa da Ameena.
Cikin mintuna ƙalilan Dr Adnan da ya iso, har zuwa lokacin kuwa Ameena dishi-dishin take gani a idanunta.

Jininta Dr Adnan ya ɗiba, sannan yace zaije yayi checking ɗin jinin nata, yana dawowa, amma kafunnan asama mata wani abu taci.

Ummi da kanta tahaɗawa Ameenan maltina da madara, nan ta ɗan ɗagota cikin kulawa ta bata tasha, tana gama sha kuwa ta koma ta kwanta, gefenta Saifuddeen ya koma, nan dai sukayi jigum suna jiran dawowan Dr Adnan.
Inda duk bayan minti ɗaya sai Ummi tayiwa Ameenan sannu.

Turo ƙofar falon Dr Adnan yayi ya shigo, fuskarsa ƙunshe take da zallan farinciki marar misaltuwa.
Zama yayi akan kujera tare da duban Ummi, murmushi yayi inda ya kuma duban Saifuddeen, cikin farin ciki ya tashi ya rungume Saifuddeen ɗin, abun daya basu mamaki kenan.
Ɗan janye jikinsa yayi tare da kamo hannun Saifuddeen ɗin ya riƙe, cikin yanayin farin ciki yace.
"Congratulation My brother, tabbas ƙarfin ikon Allah ya wuce misali Alhamdulillah yau dai ɗaya daga cikin tabbacin da Dr Acash ya bamu ya tabbata saura na biyu, domin da yardan Allah ka kusa zama Baba, dan kuwa Ameena na ɗauke da ciki har na tsawon wata biyu!!"

Cikin tsananin mamaki Saifuddeen dasu Ummi ke kallon Dr Adnan.
Kai ya gyaɗawa Ummy tare da ce mata,
"Eh Ummy matar Saifuddeen nada shigar ciki har na tsawon

Please Login or Register in order to submit comment