Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Baba Malam cikin son kontarda hankalin Saifuddeen yace.
"Ka nemo matar da take sonka,
Ni zanyi maka komai na auren ko sisinka bana buƙata."
Shifa yanzu ganinsu yake kamar al'mara,
su kuwa nan suka gama tattauna komai.

Ganin azahar tayine yasa suka yi addu'a suka tashi a taron kana suka sallami Ummi suka fita baki ɗayansu su.
Anan matsallacin jikin gidan nasu sukayi salla kana su Baba Malam da Dirankadi da Malam Adam suka tafi.

Su bappa Ali kuwa suka dawo cikin gida sukaci abinci sannan suka ƙara jaddawa Saifuddeen batun auren sannan suka tafi.

Su Babba Ali na fita Ahmad ya kwashe da dariya harda dukan cinya cikin jin daɗi ya kalli Saifuddeen daya haɗe fuska girarshi ɗaya ya ɗaga mishi tare da cewa.
"Ya akayi ne angon mata biyu a wata ɗaya, kai Alhamdulillah lallai wannan dattijon ya cika adali mutun, kaga nanda mako biyu kana tare da sabuwar amaryarka dal a leda."
Wani irin bugu ya ya kaiwa Ahmad,
da sauri ya kauce tare da cewa.
"Sai fa an maka auren na."
Dariya Ummi tayi ganin yadda Saifuddeen ɗin ya haɗe fuska cikin dariyar tace.
"To wai duk wannan haɗ...!



Littafina na kuɗine turo katin mtn na 300 ta wannan numbers 09097853276 ko ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.


Masu iya magana dai sunce kyauta da kayan wani mugunta dan haka masu fitarmin da littafi ku bari,



By
*GARKUWAR FULANI*
[06/09, 3:30 pm] اسماء بشير:     
                       


"Wai Duk wannan haɗe fuskan na memene wai? dan ance za'a ƙara maka aure?." kanshi ya sunkuyar ba tare da yace komaiba.
Ahmad ne ya gyara zama tare da duban Saifuddeen ɗin, cikin zolaya yace.
"Manya kenan angon mata biyu, gaskiya bakowani namiji bane zai taki sa'a irin wanda ka taka, auren mata biyu awata ɗaya kacal, lallai Saifuddeen kai ɗan gata ne."
Harara Saifuddeen ya watsa Ahmad ɗin tare da haɗe fusks, wani irin abu yakeji a maƙoshinsa, sam shi atsarinsa babu auren mace wanda ta wuce sama da ɗaya a rayuwarsa.
Ummi ne ta ɗan saki murmushi tare da duban Ahmad, cikin kulawa tace.
"Ni kaina naji na gamsu da batun ƙarin auren Saifuddeen, amma kuma sai-dai bansan wace kalar matar kuma zai ƙara samowa ba, musamman ma yanzu da yace babu wata wacce ya keso."
Murmushi Ahmad yayi cikin nutsuwa yace.
"Saifuddeen ai mai farin jini ne, muna nan zaune zamuga wata santaleliyar budurwa ta bayyana, don neman aurensa! In wata ta gudu wata zata zo. Ita kuwa ɗiyar taki Zaleeha in taga dama tafi ruwa gudu."
ya ƙare maganar yana  gimtse dariyarsa, don sosai yakejin wani irin farin ciki yau ɗin, don yasan ta hanyar ƙarin auren Saifuddeen ɗinne kaɗai Zaleeha zata shiga cikin sense ɗinta kuma tanannne Saifuddeen zai samu nitsuwa.
Cin ƙufula Saifuddeen ya ɗauki ɗaya daga cikin pillow kujerun falon, nan ya wurgawa Ahmad ɗin, da sauri Ahmad ya kauce yana dariya,   duban Raliya dake zaune Ahmad yayi, cikin son ƙara tsokar Saifuddeen ɗin yace.
"Nikam zan fita, idan na fita kuwa sai inda mai na ya ƙare, saboda zan zaga gari, ko Allah ma zai sa na samawa ɗan bazawarin abokina mata ta biyu!."
Yanzun kam harta Ummi saida tayi dariya, shikuwa Saifuddeen sake kwaɓe fuska yayi nan yasake wurgawa Ahmad ɗin pillow, da sauri Ahmad ya kauce kana ya fice daga cikin falon yana murmushi.
Ahankali ya danna madannin wheelchair ɗinsa, inda ya ƙaraso har gaban Ummi dake zaune,  Raliya kuwa miƙewa tayi inda tabi bayan mijinta.
Hannun Ummin Saifuddeen ya kamo, karyar da wuyansa yayi, tare da shagwaɓe fuska, narai-narai yayi da idanunsa, tare da ɗan yaɓe lips ɗinsa, hakan yasa yanayinsa ya koma kamar na ƙaramin yaro,  ganin yanda yayi da fuskar ne yasa Ummi fuskantar me yake nufi, cikin yanayin lallashi ta kama hannunsa, tausasa murya tayi tare da cewa.
"Nasan bakaso amma haƙuri zakayi ka ƙara auren nan Saifuddeen, tun da dai kaga shi baban Zaleehan da kansa ya faɗa, kuma ai dai nasan kafahimci me yace, tun da dai yace akan maganar ƙarin auren,  ba shawara yake ba ka ba, umarni ne."
Kai Saifuddeen ya ɗan girgiza, tare da ɗan lumshe idanunsa, kana ya buɗe su alokaci guda, duban Ummin nasa yayi, cikin body language ɗinsa yake yi mata alaman cewa.
"Bashi da ra'ayin ƙarin aure, sam babu auren mata biyu atsarinsa, idan ma ya ƙara auren ya zaiyi da matar?."
Kanshi ta shafa cikin bashi ƙarfin guiwa tace.
"Je kasha maganinka, daga gobe zamuyi mgnar, kana Kayita Addu'ar Allah ya tabbatar maka da al'khairi a cikin lamarin."
Kanshi ya gyaɗa mata cikin bin umarninta ya juya ya nufi side ɗinshi.
Ita kuwa ta koma cikin ɗakinta zuciyarta fal farin ciki,
Adda Rahama ta kira ta sanarwa abinda ke faruwa, abinda yayi matuƙar faran ta mata rai, nan tace.
"In sha Allah zanzo in ya Adnan ya barni."
"Allah ya kaimu." cewar Amin Amin ta amsa kana sukayi sallama.

Washe gari da yamma, Saifuddeen na zaune gaban Umminshi cikin nitsuwa yake mata tambayar meyasa zata bari aƙara mishi aure bayan tasan shi mai raunine.
Wani irin yalwataccen murmushi Ummin tayi tare kamo hannunshi, bata kai ga basa amsa ba.
Adda Rahama wanda tun ɗazun ta shiga kitchine haɗo wa kanta abun da zata ci, ta dawo cikin falon, zama tayi tare da duban su Ummi'n.
Nan Ummi ta sauƙe ajiyar zuciya tare da duban Adda Rahama'n, cikin kulawa tace.
"Kinjisa wai shi bayason wani ƙarin aure, waishi mai raunine."
Dubansa Adda Rahama tayi cikin kula tare da ɗan nutsuwa, cikin son fahimtar dashi tace.
"Akan maganar ƙarin auren nan, ba wai zaɓinka aka nema bafa, zaɓin da aka baka dai kawai shine ka fito da wata, wanda kake ganin ta kwanta maka arai, amma ƙarin aure kasa aranka cewa in sha Allah babu fashi, ita wanda kake mutuwar so ɗin ba guduwa tayi daga gareka ba, saboda haka nidai ina goyon bayan da kasakeyin wani auren, don gaskiya bazamu barka kaci gaba da zama ahaka ba."
Fuskarsa ya haɗe tare da dubansu su duka biyun, cikin body language ɗinsa, yayi musu alaman cewa.
"Ahakanne zai ƙara aure bayan ko yaushe bisa keke yake, kodai sun manta cewa shi ba cikakken lafiyayye bane, ko kuwa sun manta da cewar shiɗin mai rauni ne, ayanda yake ma gaskiya baijin zai iya zama da mata biyu."

Murmushi Adda Rahama tayi tare da tasowa, ta ƙaraso inda yake, hannunta ta sanya inda ta dafa kafaɗunsa, cikin ƙauna haɗi da tausayinsa tace.
"Ni na tabbatar kai ba rago bane, nasan zaka iya rayuwa da mata huɗu ma ba biyu ba,  kai jajirtaccen Namiji ne Saifuddeen, saboda haka kada kabari rauni ya ziyarci tunanin ka, tun ada kai jarumi ne, haka ayanzu ma kai ɗin, you are the super hero, sannan kafi kowa sanin nakasa bata taɓa zama kasawa, sai-dai ga wanda ya bari zuciya da kuma tunaninsa suka mace, saboda haka ako yaushe kasa azuciyarka cewa, kai ɗin jarumi ne!! Sai dai kuma in salon tirjiyarka ce hakan".
Taƙare maganar tana me ɗan bubbuga kafaɗunsa tana murmshin zanca wai shi mai raunine kaji yaro da wayo wato ace bazai iya jure mu'amala da mata biyu ba.
Shiru yayi tare da lumshe idanunsa,  hakan na nufin cewa kenan bashida wani zaɓi? ko kuwa dai ƙaddaransa ne take ƙoƙarin canzawa?
Ganin yayi shiru ne yasa Adda Rahama komawa kan kujera ta zauna, nan ta shiga cin abincinta hankali kwance.

Da sallama Hayatuddeen ya shigo cikin falon Ummi, ganin su azaune ga kuma Hammansa daya haɗe fuska, yasan yashi ƙarasowa cikin falon, jakar makaranta da kuma littatafan dake hannunsa ya watsa akan kujera, zama yayi daɓas akan sofa, tare da miƙe ƙafafunsa, cikin shagwaɓa haɗi da kasala ya ɗago indo ya dubi Ummi, asangarce yace.
"Ummi am so tired, ƙafana bayana kaina idona kunennena ɗuwawuna kai ko'ina ɗina ma ciwo suke min!."
Murmushi Ummi tayi, tare da cewa.
"To sannu auta na, ae dai ku kam gaba ɗayan ku haka kuke, abu kaɗan ke gajiyar daku, sai kace ba gwaraza ba."
Sake shagwaɓe fuska yayi, cikin salon sakalci yace.
"Wallahi Ummi makaranta ba daɗi, duk acika ku da lectures, yau fa ko ɗan hutu bamu samu ba."
Ƙare maganar yayi yana me ɗago kansa, inda ya kalli Saifuddeen, wanda ya haɗe fuska, inda ya kawar da kansa gefe, da'alamu cewa ba ya cikin yanayi me daɗi, cikin kulawa haɗi da faɗuwar gaba, asanyaye Hayatuddeen ɗin yace.
"Hamma!."
Kasancewar Saifuddeen ɗin ya juyar da fuskarsa, zuwa wani ɓangare na daban hakan yasa baiji ƙiran da Hayatuddeen ɗin yayi masa ba, don dama sai yana kallon ka ne, sannan yake karantar abun da kake faɗa, ta hanyar kallon yanayin motsin bakinka shiyasa yake da yawan kallon ammanfa ga wanda yake son ya gane abinda zai faɗa.
Ganin Hamman nasa baisan da cewa yanayi ba, hakan yasa ya taso da sauri ya, ƙarasowa gaban Hamman shi hannunshi ya ɗaura a akan kafaɗan Hamman nasa, ahankali Saifuddeen ya ɗago da kansa, duban Hayatuddeen ɗin yayi, sai kuma ya kau da kansa gefe.
Hakanne yasa jikin Hayatuddeen yayi sanyi sosai.
A take kuma yaji gabansa ya faɗi, ƙirjinsa ne ya shiga duka, cikin zuciyarsa yace.
"Nashiga uku badai Hamma na yasamu labarin cewa, yau na fita amakaranta, na bi Khamis muntafi yawo ba?."
Cikin ɗari-ɗari da fargaba ya kalli Ummi, wanda ke ƙoƙarin tashi, don komawa ɗaki, da sauri ya rufa mata baya, jin mutum abayanta yasata juyowa, kafe Hayatuddeen ɗin tayi da ido, tare da cewa.
"Lafiyanka ƙalau kuwa kake biye dani, sai kace wani ƙaramin jariri, kodai ka aikata wani rashin gaskiya ne?."
Ummi tafaɗa tana me ƙare masa kallo, don tsab tasan yaranta, da zaran sunyi wani abun da ba dai-dai ba, takan saurin ganewa, ko daga halin rashin nutsuwa da zata gansu aciki, kamar dai yadda ta fara zargin yanayin canji nitsuwar Hayatuddeen.
Ƙifi-ƙifi Hayatuddeen ɗin yayi da idanunshi tare da cewa.
"A'a babu abun danayi, kawai dai naga ran Hamma Saifuddeen ne kamar aɓace yake."
Ajiyar zuciya Ummi tayi tare da cewa.
"Hmm rabu da Hammanku, gata ake son a mishi shi kuma wai baya so."
Da sauri yace.
"Ummi wanne irin gatane?."
murmushi tayi tare da cewa.
"Wai fushi yake don ance masa ya ƙara aure, shine yake ta faman haɗa rai sai kace wanda akace yayi wani abun, wanda ba dai-dai ba."
Cikin zaro ido Hayatuddeen yace.
"Haaah Ummi to kuce ni inyi auren mana, tunda shi baya son gatan ni kuyi mini."
Cikin mamaki da al'ajabi da zazzaro ido Ummi tayi kana tayi kasake tana kallonshi da nazartanshi.
Shi kuwa da sauri ya dawo nitsuwarsa gudun karta ramfoshi.
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Hayatuddeen ya sauƙe, ya godewa Allah da yasa, ba asirinsa bane ya tonu, domin yasan tabbas idan Hamman nasa, ya gane irin abubuwan da yake yi, to fa kashinsa ya bushe, yasan sai anrabasa da duk wani abu nasa najin daɗi.
Gyara tsayuwarsa yayi tare da cewa.
"To Ummi me yasa zai ƙara aure, yaushe ma yayi auren?."
Harara Ummi ta watsa masa, tare da cewa.
"To kai mekasani acikin aure da kake tsoma baki cikin abun  da babu ruwanka?."
Kanshi ya jujjuya tare da cewa.
"Wallahi ba abinda na sani, kawai a auro mishi mai sonshi tunda hegiyar nan taƙi zama."
haɗe fuska Ummi tayi tare da cewa.
"Hayatu baka da kunya fa ba yayarka bace kake ce mata hegiya, to a kul wlh kada in sake jin ka zagarmin ƴata dan mu dai Zaleeha bata ƙi muba bata mana wani laifiba ita dai auren ne da bata so."
Murmushi yayi tare da ɗan shafa kansa yace.
"Afwan ya Ummi bazan sakeba, nima nasan Zaleeha na sonmu amman dai ina jin haushinta in na tuno wai bata son Hamma nane yasa ta gudu."
ya ƙarishe mgnar tare da, juyawa ya inda ya fice daga cikin ɗaki, a falo ya samu Adda Rahama, har yanzun Saifuddeen na zaune afalon,   komawa kan sofa yayi ya zauna, inda ya matso kusa da Adda Rahama wanda kecin abinci,  dubansa Adda Rahama tayi tare da cewa.
"Bafa zanci dakai ahaka ba, jeka wanko hannunka."
Ɗan shagwaɓe fuska yayi tare da cewa.
"Dan Allah Adda Rahama, muyi karɓe-karɓe, don nagaji, dama kafun na zauna ne kikace na wanko hannun nawa."
Kai Adda Rahama ta girgiza tare da cewa.
"Allah ya shiryeka, sarkin lalaci kawai, da ace kai mace ne, tabbas da anyi uwar son jiki."
Murmushi kawai yayi tare da amsan spoon ɗin dake hannunta, haka suka shigayin karɓe-karɓe, idan tayi loma guda, ta bashi spoon ɗin shima yayi, duk wai saboda tsananin ganda, ɗauko spoon kaɗai ya gagaresa.
Ummi ce tafito ɗaga cikin ɗaki, hannunta ɗauke da wayarta, duban Saifuddeen tayi tare da cewa.
"Bappa Ali ne ya ƙira."
Ɗago kai Adda Rahama tayi tare da cewa.
"Akan maganan auren ne ko?."
Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.
"Ƙwarai kuwa, koda na faɗa masa cewa, babu wacce ayanzu Saifuddeen ɗin keso, cewa yayi wannan ba uzuri bane, za'a ne mamasa ko acikin dangi."
Idanu Saifuddeen yaɗan zaro waje, kasancewar yana kallon Ummin nasa, hakanne yasa ya fahimci me take faɗa.
Murmushi Adda Rahama tayi, ɗan satan kallon Saifuddeen ɗin tayi, cikin kulawa tace.
"Hakan ma yayi, tun da dai shi yace bashida zaɓi."
Hayatuddeen ne ya ɗago kai tare da duban Ummi, cikin nutsuwa yace.
"Acikin dangi kuma tab, nikam dai banso Hamma ya yi auren dangi, to idan ma hakane ae ga nan Amina da Asma'u, duk suna sonshi, musamman  ma Ameena, dake bala'in sonsa ae sai ya zaɓi ɗaya acikin su ko?."
Ɗan jim Ummi tayi, nan kuma tasaki murmushi, cikin gamsuwa da kalaman Hayatuddeen tace.
"Tabbas, ka ga kuwa ni na manta ma da batun Ameena, gaskiya yarinyar akwai hankali, sannan kuma tana da kirki sosai, don ko lokacin da yake jinya a Hospiatal ɗin Abuja, ta kula dashi sosai, gaskiya na yaba da hankalinta sosai tana son Babana."
Duban Ummi Adda Rahama tayi tare da cewa.
"Okay wannan nurse ɗin ba, gaskiya nima yarinyar ta kwanta min arai, sai-dai kuma wacece Asma'u, don ban shaida ta ba."

Carab Hayatuddeen yayi inda yace.
"Wata jarumar film ne, kinma santa ae, wannan Asma'u Ahmad Matawalle wanda take rawa da waƙa, tauraronta yana haskawa sosai."
Idanu Adda Rahama ta ɗan zaro tare da cewa.
"Mai rawa da waƙa kuma? chab awani gidan? gaskiya a'a, Ameenan dai tayi, don ƴar gidan mutumci ce da dukkan alama, kuma Saifuddeen da yawan kishi ai bazai iya aurenta ba."
Cikin gamsuwa Ummi tace.
"Tabbas nima Ameenan tafi kwanciya min arai, don dai ita Asma'un kam sam batayi ba, don idan ma muka zaɓeta bamusan da wanne ita kuma zata zo ba, duba da irin lalurar da yake fama da ita ma, sam baidace ya auri wata ƴar nanaye ba, wanda suka saba cuɗanya da maza, ko yaushe suna cakuɗe da maza awaje guda ga Saifudden da ɗan karen kishi, balallai ma yasamu ingantacciyar kulawa daga gareta ba, Ameena ɗin dai ita muka zaɓa."
Nan Adda Rahama ta jinjina kai cikin gamsuwa.
Shikuwa Saifuddeen daya duƙar da kanshi kasa, sai alokacin ya ɗago, kasancewar bai kallesu ba, hakan yasa baiji mai suka tattauna ba.
Madanannin wheellchair ɗinsa ya danna, kai tsaye yanufi hanyar barin falon, don yagaji so yake yaɗan je ya kwanta ya huta.

Yana fita Ummi ta dubi Hayatuddeen wanda keta aikin zubawa cikinsa abinci, cikin kulawa Ummi tace.
"Hayatuddeen bani wayarka."
Adaburce ya ɗago kansa, kasancewar yakai loman abinci bakinsa, hakanne ya sakashi ƙwarewa, take tari ya sarƙesa, da mamaki Ummi ke kallonsa, yayinda Adda Rahama kuma keyi masa sannu, botle water ta miƙo masa, nan ya amsa haɗe da kafa bakin goran abakinsa, saida yasha sosai kafun yaji ya samu relief,   cikin kulawa Ummi tace.
"Sannu, haba kaima sai cikawa cikin ka abinci kake babu ko tsayawa, tayaya bazaka ƙware ba, bacin abincin ba guduwa zaiyi ba, kana abu kamar mara gsky."
Shiru yayi tare da ƙoƙarin neman hanyar barin falon.
Dubansa Ummi tayi tare da cewa.
"Ina kuma zakaje? bacewa nayi kabani wayarka na ɗau number'n Ameena ba."
Jin haka yasashi sauƙe gagarumar ajiyar zuciya,  zaro wayar daga cikin al'jihun wandonsa yayi, nan yashiga contact ɗinsa, inda ya laluɓo number'n Ameena'n, nan ya miƙawa Ummin nasa.
Tsab Ummi ta kwafe number'n Ameena'n, inda ta sanya awayanta, kana ta miƙa masa wayarsa, haka ya wuce sama sumu-sumu, daganinsa kasan bashida wadataccen gaskiya.

Nan Adda Rahama da Ummi suka ci gaba da tattaunawa akan sabon auren da za'a ƙarawa Saifuddeen ɗin, sai ayanzu ne suma suke ganin cancantar yin hakan, saboda Zaleeha ta gujesa, tana ganin cewar shi nakasashshe ne, yayinda su gani sukeyi dan shi nakasasshene yasa ta gujeshi sannan babu wata mace wanda zata iya zama dashi, hakan yasa dole ne ma su Aura masa Ameena, tun da dai ita tana son shi, sun tabbatar da cewa kuma zata kula dashi. Sun ɗan taɓa hira kafun Adda Rahama ta tafi, Ummi kuma ta nufi ɗaki ta kwanta, bayan taƙira Bappa Ali ta sanar masa zaɓin da tayiwa Saifuddeen ɗin, sosai shima Baffa Ali'n yayi na'am da batun, nan take yaƙirayi Baba Malam ya sanar masa, da batun,  sosai Baba Malam yaji daɗi, don kuwa ko ba komai hakan da sukayi sun karramasa.

Saifuddeen kuwa yana shiga ɗakinsa, ya soma rage kayan jikinsa,  ƙarasawa gaban tankamemen bed ɗinsa yayi, nan ya sauƙa akan wheellchair ɗinsa, inda ya hau gadon.
Lumshe idanunsa yayi tare da jawo blanket ya rufe jikinsa,   maganar ƙarin auren nasa daya dawo cikin kunnensa ne, ya sashi jin wani ɗaci a maƙoshinsa, sam shi baima ɗauki abun agaske ba, yasan suna faɗa ne kawai, amma shi ina yaga ta wani ƙara aure, shiru zaiyi ya ƙyalesu, yasan nan da kwana biyu suma zasu daina batun.

Yana nan kwance, yaji vibration na wayarsa, don dama akusa dashi take.
Kasancewarsa wanda bayajin magana, ko kuma wani sauti, hakan yasa koda yaushe wayarsa a vibrate take,  domin ta hakanne kaɗai zai gane cewar an turo masa saƙo, domin idan kunnensa baya ji, to ai jikinsa naji, don aduk sanda wayan ke kusa dashi, ko kuma take jikinsa, to zai jita tana rawa, hakan kuwa alamane na cewar an turo masa saƙo, ɗaukan wayar yayi tare da dubawa, ganin  saƙon na Ummin sane ya sashi buɗewa.
Number'n wayane arubuce da kuma rubutu aƙasan sa kamar haka.
"Wannan number'n itace number'n matar da na zaɓa maka amatsayin wacce zaka aura, saboda haka kayi saving ɗinta."
Yana gama karanta saƙon ya tashi zaune cikin hanzari, jiyayi gabansa ya faɗi, cikin sauri ya jawo rigarsa wanda ya cire, nan ya sanya tare da hawa kan wheellchair ɗinsa, ahanzarce ya nufi part ɗin Ummi'n dan yafa lura su da gask suke nufin ƙara mishi auren.

Koda yaƙarasa falon ta bai ganta ba, kai tsaye yanufi bedroom ɗinta.
Tsayawa ajikin ƙofar yayi, tare dayi mata knocking,  Ummi dake kwance jin ana knocking yasa ta tashi ta zauna, murmushi tayi don tasan cikin biyu za'ai ɗaya, ko Saifuddeen ko kuwa Raleeya.
"Shigo." Ta faɗa ataƙaice.
Da sauri ya tura ƙofar ya shiga, Ummi na ganinsa taɗan tsume, tare da dubansa.
Ƙarasowa yayi har gabanta, inda ya kamo duka hannayenta, kansa ya shiga girgiza mata, alaman "a'a."
murmushi tayi tare da cewa.
"A 'a me? bazakayi auren ba ko kuwa me? ko bakason zaɓin danayi maka, ba kuma zaka iya karɓanta matsayin zaɓina ba?."
Shiru yayi tare da ɗan lumshe idanunsa, kansa ne ke sarawa, cikin body language ɗinsa, yace.
"Bawai zaɓinki bane banaso Ummi, ni auren ne banaso, ki dubeni ki gani fa, tayaya zan iya rayuwa da mata biyu, ko kun manta abun da Dr. ya faɗa ne, ina ɗauke da nakasa banjin cewa, zan iya bawa mata biyu kulawan daya dace dasu ba."
Dariya Ummi tasanya, tare da dubansa, saida tayi dariya sosai sannan taɗan soma tsagaitawa, shikuwa Saifuddeen kafeta yayi da idanunsa, tare da sanya mata fuskan tausayi.
Ɗan tsagaitawa da dariyan Ummi tayi tare da cewa.
"Ikon Allah, Yau kuma Saifuddeen kaida kanka kake ƙiran kanka da Nakasashshe? duk saboda ance ka ƙara aure shine har ka aminta cewar kai nakasashshe ne, har kuma ma kake ƙiran kanka da hakan, tsawon lokaci ban taɓa ji kaƙira kanka da wannan sunan ba, amma yau sai gashi da bakinka ka faɗa, ka kuma nanata.  hmmm lallai ma kuwa to wallahi in sha Allah auren nan babu fashi, sai anyi shi, na kuma gama yi maka zaɓi, umarni ne idan kuma kace a'a, shikenan saika ƙira surukin naka wanda ya yanke hukuncin, kace masa kai bazaka bi umarninsa ba."

Idanunsa ya lumshe, jin zuciyarsa yake tayi masa nauyi, a kasalance, cikin yanayi marar daɗi yace da Ummi, ta sanar dashi, "Wacece zaɓin nata?."
Nan Ummi tace.
"Idan yana buƙatar sani, zai iya zuwa ya tambayi Adda Rahama, zata sanar dashi koma wacece."
Jin haka yajuya yafita jiki a mace, yana mai saƙawa ransa to wacece ina take ina suka samota da zasu liƙa mishi ita, tuno babu in da zai samu amsoshin duk waɗanan-nan tambayoyin sai wurin Adda Rahma.
Ae kuwa kaman jira yake cikin sauri ya juya ya fice daga cikin ɗakin.
Kai tsaye ɓangarensa ya nufa, inda ya kimtsa kansa,  koda ya fito text message ya turawa Ahmad kan cewar yana son ganinsa.
Kasancewar Ahmad ɗin na cikin gida, hakan yasa mintuna kaɗan sai gashi ya fito.
Cikin body language Saifuddeen ɗin yace da Ahmad.
"Ya kaishi gidan Adda Rahama."
Sanin kwanan zancen yasa babu musu, Ahmad ya ɗauko musu mota, nan suka shiga, inda ya jasu zuwa gidan Adda Rahaman bayan sun biya jonapwd sun ɗauƙi ishaq wanda a zaton Saifuddeen ishaq zaibi bayanshi.

Koda Adda Rahama ta gansu batayi mamaki ba, don tun kafun zuwansu Ummi ta ƙirata ta yi mata bayanin komai.
Tray ɗin drinks masu sanyi ta dire agabansu, Ahmad ne ya ɗauki kwalin exotic ya miƙawa ishaq kana shima ya ɗauka inda yasoma kwankwaɗa, don shi fes yakejin ransa bashi da wata damuwa.
Hakama ishaq da shi yafi kowa jin haushin Zaleeha, kuma Babanshi ya mishi bayanin son ƙarawa Saifuddeen aure da Baban Zaleeya ya shiryawa.

Saifuddeen kuwa fuska ya marairaice, duban Adda Rahama yayi, tare da ɗaukan wayansa, cikin message ɗin Ummi ya shiga, nan ya nuna mata fuskar wayar, tare da yi mata alaman tambaya, kan cewa.
"Wacece? Ina take?".
Murmushi Adda Rahama tayi masa tare da cewa.
"Miye abun tada hankalinka haka ne Saifuddeen? da ka nutsu ma don amaryar taka ba ɓoyayya bace awajenka kasanta."
Cikin son ƙarin bayani ya zubawa Adda Rahama'n fararen idanunsa.
Duban tsab Adda Rahama tayi masa, kana cikin nutsuwa tace.
"Nasan kasan Ameena ae, wannan nurse ɗin da ta baka kulawa, lokacin da kake jinya a Abuja, kafun ku wuce India, to ita ce dai Ummi ta zaɓa maka, nima kuma nayi na'am don yarinyar akwai hankali, Masha Allah.
Ka tuna har gida tazo itada Mamanta suka dubaka da jiki."

Idanunsa ya zazzaro waje tare da jujjuya kai da ƙarfi sosai yashiga mamaki, lokaci ɗaya yaji kaman an watsa masa ruwan zafi, amamakance ya ɗan ƙanƙance idanunsa, cikin yanayin maganarsa wanda ya saba, wato body language yace.
"Allah ya sauwaƙe ni dai na auri wannan Ameenan, mezanyi da ita bazawara ce fa!."
Cikin tsananin mamaki Adda Rahama ta dubeshi,  kallonsa tayi da kyau tare da faɗin.
"Kai Saifuddeen banda sharri bazawara kuma? wa ya faɗa maka cewar bazawara ce?".
Murmushin gefen baki yayi, tare da jijjiga kansa, in a body language ɗinsa yace.
"Impossible!, nine zan auri bazawara? chab hmmm Allah ma ya sauwaƙe, sam banason sauran wani wlh Allah ya kiyasheni suɗe ƙashin da wani ya rigani tsotsa."
Baki Adda Rahama ta buɗe fuska cike da tarin mamaki sauƙe a jiyan zuciya tayi tare da cewa.
"Wai nikam wayace dakai itaɗin bazawara ce?."
A shagwaɓe ya rubutawa Addan nasa.
"Ae basai an faɗa min ba, duk ckekken Namiji in dai ya nitsu idan mace bazawara ce zai gane ta ido, kuma nayi imani cewa Ameena bazawara ce, saboda haka ni dai bana sonta wlh bazan iyaba, ba kuma zan aure ta ba."
Ahmad da Ishaq kam dariya sukeyi sosai fahimtar abinda yake faɗin.
Baki Adda Rahama ta taɓe, inda ta gyara zamanta, dubansa tayi da kyau,ido cikin ido tace.
"Naji koma dai bazawara ce, ita Ummi ta zaɓa maka a matsayin mata, sannan da kake ta maganar cewa, ita bazawara ce, kai ɗin dakake magana saurayi ne kai? inace kaima bazawarinne tunda dai kayi aure."
Bakinsa ya turo gaba, a shagwaɓe ya narke fuska, cikin body language yace.
"Wallahi ni banason Ameena, yarinyar da idanunta abuɗe suke, ta fa riga da tasan Namiji, sannan kuma har yanzu ni matashin saurayi ne, tayaya ma zan yarda na auri Ameena."
Duban Adda Rahaman yayi tare da kamo hannunta, cikin yanayin daya saba musu alaman magana

Please Login or Register in order to submit comment